TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI PAGE 74

 7⃣4⃣






*ban manta daku ba,kuna raina,lady ,maman zainab, Aisha habib, Firdausi,sede kundena comments why?*😒


*soupnas* comment dinki nasani farin ciki keda *maman nour* comments dinku yana kayatarwa kucigaba da gashi 💃🏼, *maman nour* wai ina kawalliyarki *earmeenatuwa*🤣






Aisha tace "bangane ba yaya? "


Yana cigaba da kuka yace "iyayen faseelat Sun daukemun ita sun tafi daita"


Aisha farin ciki ya mamaye zuciyarta batasan lokacin da tasaki murmushi ba tace "Allah yasa daga can ai can"


Jin abinda tace Fahad ya tashi zaune yana mata kallon mamaki yace "me kk cewa ne Aisha? kina farin ciki da abinda yafaru ko? "


Aisha ta zumburo baki tace "to da so kake nace Allah yasa su medo maka ita? Saboda ita kamanta duk wata soyayyata idonka ya rufe akanta se kuma nakijin dadin tafiyarta, wlh naji dadi Allah yasa susa dole ka saketa ,hakanan batasan ya zaman mu yake ba tayi duk yadda tayi taja hankalinka har ka aurota ni ba abinda zance sede nace Allah yaraka taki gona "


Ranshi ya baci sosai da dane da seya mazge bakin amma ya dau alwashin barin dukan matanshi ya ciza lips yace "toko Allah baze amshi adduar ki ba saboda bame kyau bace, faseelat tananan dawowa gareni nida ita mutu karaba, don we love each other insha Allah we will die together"


Aisha dake jin haushin maganar shi kamar me ta turo baki gaba ,


Yaja tsoki yace "stupid bansan time din da zaki dena kishin hauka akan faseelat ba, ita kullum tana girmamaki tana sonki ke kuma ba wacce kika tsana kamarta"


ya tashi tsaye ze fita Aisha tace "bazaka jira ni mutafi tare ba? "


Beko waigo ba yace "batare mukazo ba kinsan hanyar gidan inkinso zuwa "

Yajuya ya bar gidan, 


Aisha taja tsoki tace "so yake nayi addua sumedota kome?wlh yaya ya raina ni da yawa wai yagama cemin yanason ta har kuma yayi tunanin zanyi wata kyakkyawar addua can"


Mommy da tundazu tana kan dining tana jinsu tafito da cup ahannu tana kyalkyata dariya, 


Tace "ke kuma dan ubanki waya ce kice mishi haka keda yazo ki rarrasheshi "


Aisha tace "mommy ba abin dariya bane wannan yazaai yazo yana fadamin wai he love her inba raini ba"


Mommy tace "to seme dan yace yanason ta tuntuni ina fadamiki kidena fiddo  mai kiyyyar ta a fili kirika nuna kinasonta"


Aisha ta mike kafarta akan kujera tace"bazan iyaba niba wacce natsana kamarta Allah nagani da nasota kafin nagane hainta ta take ita ,ni wlh har mamakin zuciya ta nayi duk yadda natsaneta ranar da ya nakada mata duka seda naji tausayinta "


Mommy ta zauna ta kurbi tea tana murmushi tace "kin shirya zaman gida ko? Tunda kinsan ba zuwa zeyi daukar ki ba "


Aisha tace "hmm zezo ai Wadda ake makalewar batanan kinanan zaki ganshi "


mommy tai dariyar manya tace "amma kinyi kuskure karki kara irin wannan "


Aisha tace "to"


Fahad gida yakoma yayi kwance zuciyar shi na kuna yarasa ina zesa kanshi ba arziki da yunwa ta cishi ya tashi ya hada tea yasha,



akai akai yakan leka unguwarsu faseelat amma gida kulle, har dare yagaji yakoma gida, 


Aisha taci wanka tana jiran yazo daukarta har 9:30 shiru bezo ba ta tashi ta dauko gyale mommy ta kalleta tace "ina zaki? Bakince ze dawo ba kijira shi "


Aisha ta yafa gyale akafada tace "mommy baze zo ba tunda har aka kai wannan time din bezo ba tafiya zanyi maybe yanacan ko abinci beci ba "


mommy tace "aiko baki isa ba ki samu wuri ki zauna, har se randa yaga dama yazo da kanshi daukarki "


Aisha ta turo baki gaba tace "Dan Allah mommy kibarni in tafi wlh hankalina duk baa kwance yake ba, yaya yana bukata ta yanzu "


mommy tace "yanzu kikasan haka ai, kicire gyalen nan "


Aisha ta turo baki ta tafita daga dakin mommy nata kiranta taki amsawa, daga karshe mommy tace "zakizo kisameni ne "



Aisha ta fita tasamu napep ta haye yakaita bakin gidansu, ta kwanwasa baba tsoho ya bude ta shiga ciki, 


Ta kitchen tabiyo ta shigo gidan, fahad na kwance akan gadon faseelat rungume da kayanta ta shigo dakin, 


Dukda yaji kamshinta amma be nuna ba, tana sanye da riga da wando na Sari ta haye gadon idanunshi a lumshe ta riko hannunshi tana cewa "yaya kaci abinci kau? "


yayi banza ya kyaleta tace "yaya kayi hakuri da abunda yafaru plsss katashi kaci abinci kar ciwo yakama munkai"


Fahad ya bude ido yana kallonta ,ta langabe kai tace "plsss katashi kaci abinci? "


ya yamutsa fuska yace "Aisha plss leave me alone ba ruwanki da naci abinci ko banci ba just go to ur room "


kamar zatai kuka tace "yaya da ruwana mana yanzu in wani abu yasameka fa?bansan ganinka cikin wannan halin na damuwa kayi hakuri katashi kaci wani abu "


Yace "bazan ci ba ko dole ne, kitashi kibani wuri, damuwa kuma zan cigaba da zama acikinta har lokacin da farin cikin rayuwata zata dawo gareni "


Aisha ta tashi tafita daga dakin tana kuka, fahad yaja tsoki yace "u don't love me da kina sona da kinso faseelat"


Aisha tafada kan bed ta cigaba da rusar kuka, ita ba maganganun nashi ba suka fi kona mata rai aa yadda yabi ya rude harda sukin cin abinci saboda mace, ta sha kuka har tagaji, har 2 takasa yin bacci shima ba baccin yake ba idonshi biyu, 


Kanta na ciwo Ta tashi ta shiga kitchen ta hado mishi tea me kauri ta dawo dakinshi, yana kwance yanata kallon silin tazo ta zauna akan gadon murya dishe tace "Dan Allah yaya katashi kasha ko da tea ne ba don ni ba "


yayi mata banza tai ta magiya hardasu kuka sannan ya tashi zaune ko kallon fuskarta be ba ya mika hannu ze amshi cup din, taki bashi ta kai cup din bakinshi seda yashanye shi tasss sanan ta dauke cup din, 


Tai murmushi ta share hawayenta tace "nagode da ka daure kasha "ta ajiye cup din a bedside table ta tashi zata bar dakin ya riko hannunta yace "anan zamu kwana"


Ta dawo ta kwanta gefenshi ta rungumeshi ba dadewa bacci ya dauketa,shiko yakasa koda rumtsawa sema kukan faseelat da yayita masa yawo akunne kamar lokacin yake dukanta duk da AC dake dakin yayita zufa, 



Da safe,


tun 7 ya isa kofar gidansu faseelat lokacin har abba yafita yana tsaye bakin kofa omer yafito cikin shirin shi ze tafi school, fahad ya mika mai hannu ya mishi sallama fuska murtuke omer ya mika mai hannu ya amsa gaisuwar, ya zare hannunshi tun kafin fahad yace komi omer yawuce ya shiga mota yayi tafiyarshi, 


fahad yayi tsaye zuciyarshi na kara zafi,can sega abul yafito shima ze tafi school ko kallon fahad beba yawuce warshi, sega su ishak da Mubarak sunfito suma zasu tafi school kasancewar yau Monday abun yabashi mamaki suma basuko kalleshiba ishak ya garkame gida suka juya suka tafi abun su, 


dana sani yakara cika zuciyar fahad yara kananu ma Sun dena ganin girmanshi ,ya dade tsaye sannan ya shiga mota ya nufi gida time to time seya share hawaye bakin ciki da suke fitowa ta gefen idonshi, 


Ya koma gida yayi kwance, Aisha tayi rarrashin  yakasa koda shan ruwa ne har tagaji se yanzu takara gane faseelat ta mata nisa azuciyar fahad gatade zaune dashi amma zuciyarshi tana wurin faseelat seta karajin tsanar ta aranta ,damuwar shi yasa itama tashiga damuwa, yakasa komi se aikin tunani, itama faseelat na can tana fama da ciwo da damuwa amira ma nacan tana kukan anty, fahad akewa punishment amma su duka suke azabtuwa, har Aisha taji gwara faseelat din ta dawo kota samu fahad dinta yasamu natsuwa, 



Wansafe tunda asuba fahad yafita da mota a masallacin unguwarsu faseelat yayi salla ana sallamewa yafito yakoma bakin kofar gidansu ya tsaya yasan de dole abba yafita sallar asuba, yana nan tsaye yara yaran sukai tawuceshi suna shiga gida, can zuwa sega yaya omer yana zuwa ya daga mishi hannu yace "assalamu alaikum" yawuce abunshi,  fahad bewani damu sosai ba shide burinshi yaga abba, yana tsaye sega abba yazo ze wuce yashiga gida, yayi sauri ya duka yafara gaishe shi memakon ya amsa seya mika masa hannu suka gaisa fahad na zukunne be tashi ba,cikin ladabi yace "abba Dan Allah ina neman yafiyarku kuyi hakuri akan abinda na aikata, nasan ban kyauta ba kuma nayi nadama Dan Allah kuyi hakuri "


abba yace "banji dadi ba yadda ka wulakanta min diya raina ya baci amma ni na yafe maka sede ina bukatar ka rubuta mata takardarta saboda zamanku atare akwai cutarwa "


Fahad da kanshi ke Duke ya dago arazane besan lokacin da ya mike tsaye ba, sannan yakoma kasan yana magiya "Dan Allah abba kuyi hakuri inason ta sosai bazan iya rayuwa batare daita ba, wlh nayi alkawari bazan kara dukanta ba Dan Allah kuyi hakuri wlh itace rayuwa ta zan kiyaye duk wani abunda ze bata mata rai koya taba lpyarta"


Jin abinda yake cewa cikin ran abba yace "nan wurin ba lpy "🤣


Yace "nide nafada maka Dan Allah kakawomin takardanta in kuma bahaka ba zamu shiga kotu "yana gama fadar haka ya shige gida, 


fahad yaida yin zaman dirshan awurin yana hawaye da kukan zuci seda gari yayi fayau sanann yatashi ya nufi gidan umma, 


umma ko kullum setaje asibity suna zaune a dining sun hallara don yin breakfast yashigo gidan duk sukabishi da kallo umma ko kallonshi batai ba bare ma yabata tausayi, 


yazo yaja kujera ta kusa da daddy ya zauna murya na rawa yabawa daddy labarin abinda abban faseelat yace, 


yace "Dan Allah daddy kaje kabashi hakuri wlh nayi nadamar dukanta tun daga lokacin da abun yafaru "


umma tai karaf tace "alhaji dan Allah ka kyaleshi karka shiga wannan maganar kaje kaji kunya kaima kasan sunada gaskiya gwara ya saketan yafi tunda beda hali "


Fahad idonshi cike da hawaye yake kallonta, 

daddy yace "a, a bahaka yakamata ba, zanje nasamu abban nasu in roki yafiyarsu, ka kwantar da hankalinka kaji "


fahad de bece komi ba ya tashi yafita tun kafin yakai gida zazzabi ya rufeshi yana zuwa ya shiga wurin Aisha ya kwanta ya kudundune jikinshi na mazari, Aisha ta rude tai ta kuka ta kira doctor ba dadewa okaton yazo ya dubashi jinin shi yahau yabashi drugs da shawarwari ya fita, dakyar Aisha tasamu yasha maganin da aka rubuta mishi badadewa bacci ya dauke shi dan cikin magungunan akwai na bacci acikinsu kwananshi ukku ba bacci saboda rashin faseelat, Aisha na zaune gefenshi tai tagumi tana kallon fuskarshi duk yabi ya rame har baki ma yayi ba wata kwanciyar hankali duk harijan cin nan ya tafi 🤣yau kwana ukku ba tabi 😅,


awurin aikinshi anyi neman wayoyinshi amma switch off ba karamar asara suke yiba mutane  sunyi zarya gidanshi sede baba tsoho yace bayanan, don fahad yabashi umarnin fadin hakan, 



Yau akayi sadakar ukkun khalil su hjya suna cikin tashin hankali har yau, jamila duk tabi ta zube ta rame duk kibarnan ta tafi hartafi lokacin da take budurwa rama, hjy ma ta kanjame don bata bacci rashin ganin gawar nema yakara tada mata hankali, zakuyi mamaki innacemaku hjy ce kebawa jamila abinci abaki don mugun tausayinta takeji tana ganin kamar itace takashe mata miji, kullum lil khalil yana hannunta ,


bayan yan gaisuwa Sun wuce da marece sosai mamar jamila sun hadu falon hjy tafadawa hjy yau zasu koma gida kuma tareda jamila zasu tafi, 


Hjya tafashe da kuka tace"dan Allah zulai kubarmin yarinyar nan awurina wlh yanzu ba abunda nake kallo naji dadi se ita da danta, ina rokon kubarmin ita tazauna anan nawani lokaci ,zuwa lokacin da zansamu natsuwa nida kaina zan medo muku ita na rokeku "


Maman jamila tace "hjy zamu tafi daita ne don amata wanka, kuma anan zata karamiki damuwa tunda har yanzu taki dena kuka ga danta dabata damu dashiba,dawainiya zata miki yawa ki kula daita ki kula da danta, gwara mutafi daita can "


hjy tace "wlh bata karamun damuwa, wanka kuma zansamu unguwar zoman da zata mata wanka, kula daita da danta bawani abu bane wurina, nide ina rokonku wannan alfarmar"


dakin yayi shiru na wani lokaci jamila na kuryan hjy kan dadduma tanajin komai hawaye suka kara zubomata wai hjy ce kuka tana rokon abar mata ita inama ace lokacin da khalil yana raye ta nuna mata wannan soyayyar ba yanzu ba, 


Baban jamila yace "toshikenan hjy ga jamila nan zata cigaba da zama anan kamar yadda kika bukata, Allah yakara mamu hakurin rashin khalil "


Maman jamila tai shiru dan taso tatafi da yarta takula daita sosai , 


hjy tafara godiya "nagode sosai Allah yabar zumunci"


sukace "amin "


Maman jamila ta tashi tashiga ciki tasamu jamila dake zaune ta zauna tace "jamila zaki zauna nan din? "


jamila ta daga kai tana matse baki,itakanta jamilar tausayin hjy takeji saboda Halinda tashiga, lalle mutuwa waazi ce gasu ba sulhu sun dedeta,


maman jamila tace "to amma ki kula da kanki sosai don dinkin jikinki ya warke kuma ki daure kiyi hakuri jamila khalil de yatafi baze dawo ba addua kawai zaki rika masa "


jamila tace "to mama"


maman jamila ta tashi tafita hjya nata godiya suka tafi garinsu, 



Unguwar zomar dake dora musu ruwa itace ta cigaba da yiwa jamila wanka kuma tana bakin kokarinta, 


Khalil ko yanacan yana daukar darasi musa ya girme shi dan yayi 45 amma yanayin yadda yake tafiyar da rayuwa ya burge khalil, yana aiki ne a babbar ruga shima likitan fata ne, bayada wani hali sosai amma kullum dasafe se anfita da Kula da bokitai na kunu wanda ake kaiwa asibity ana rabawa patients marassashi, da yadawo daga asibity yake sauya kaya bayasa kananan kaya, kuma kayansa duk ba tazarce suna da dan shape Iya gwiwa yaiya dressing sosai anan khalil yakara daukar cause din saka hula ashe ba bakin ido ake kaita ba 😬tsakiyar goshi ake dedeta ta, 


Shima musa ya karu da khalil dan yalura khalil kosu na magana yana dannar counter dinshi in suka tsagaita wani lokaci yana ganin bakinshi na motsi ,shima yanzu ya dage rikon counter yana tasbihi kuma yakara kula da mahifiyarshi akan baya don yayi mamakin dukda khalil bejin dadin mahaifiyarsa amma burinshi ya rayu dan ya kara kyautata mata bare shi tashi da yakejin dadinta , 



da drugs suka saki fahad ya farka tsakar dare dakyar Aisha tasamu yasha tea tayi iyayinta yakara shan magani yaki wai beso yayi bacci ,idanshi biyu har asuba yakara komawa gun abba, 


abba beji wani tausayin shi ba yakara memeta mishi abinda yafada jiya don umarnin alhaji babba ne kuma shi bemasan su ummi sunyi wata magana da mahaifiyar fahad ba yade san tana zuwa amma besan komi daganan ba, 


fahad ya koma gida ya dukunkune dan zazzabin da yakara rufeshi fiyeda jiya, 


sabeer ya kira wayar fahad many times besameshi ba, tun karfe 7 yayi parking kofar gidanshi yafara knocking gate, baba tsoho ya bude mishi yaganshi tsaye baba tsoho da yasaba ganin shi yana faraa yace "barka da zuwa alhaji "


Sabeer yace "ina kwana baba, mutumen yana ciki kau? "


baba tsoho yace "eh yana ciki sede yace duk wanda yazo ace bayanan"


Sabeer ya girgiza kai yace "OK Allah yasa lpy nizanshiga naganshi"


baba tsoho yace "afito lpy "


sabeer yawuce ciki yatsaya bakin kofa ya danna door bell shiru yadade tsaye yanata dannawa sannan Aisha taji tazo tabude mishi, 


idanunta jawur dan tana shan kuka akai akai ta yadda fahad be damu daita ba, ga kuma damuwa da halin da yake ciki "tana ganin sabeer taji dadi ,


sabeer ya kalleta tayi wani kala abun tausayi yace "Aisha lpy kuke "?


Aisha tace "sabeer yaya yadena kula dani baya bacci baya cin abinci baya zuwa aiki baya komi se tunanin faseelat, tun jiya baya lpy har yau nayi iya kokarina yaki shan magani doctor ma yace jinin shi ya hau sosai, yarage damuwa amma yaki,dan Allah kaje kamishi magana koyaji ya rage yiwa kanshi wannan horon"


ta matukar bashi tausayi yace "kiyi hakuri insha Allah ze dawo dede muje naganshi "


Aisha tawuce tahaye step sabeer na bayanta har cikin dakin faseelat da fahad ke kwance cikin duvet, 


Aisha na tsaye sabeer yaje ya zauna kan bedside ya dan yaye duvet zuwa kan fuskar fahad yaganshi duk yayi wani wuriwuri dashi, 


be wani mamaki ba don yasan yana matukar son faseelat ,sede yaji haushi yadda ita Aisha ke azabtuwa saboda da damuwarshi 


Fahad ya bude ido ya kalli sabeer, sabeer yace"yanzu fahad dan an dauke faseelat shikenan Kagama rayuwa, kazauna kana wahalar da kanka da matarka, ka ki yin aiki kaki zuwa office kasan asarar da akeyi kuwa kuma kasan kamfani baze dauki asara ba "?


Fahad da muryarshi ta Marassa lpy yace "I know and I don't care ,idan har basu barmin faseelat ba mutuwa zanyi she's my life bazan iya dena tunaninta ba kona second "


sabeer yadan saci kallon Aisha don shi kanshi yaji haushin maganar yaga tana ta kallon fahad tana hawaye, 


Yace ma fahad "to cewa sukai bazasu baka itaba kome? "


fahad yace "naje 2times  wurin mahaifinta he's asking for her divorce later nabashi hakuri amma beyiba "


Sabeer yace "Dan Allah friend karika hakuri da yadda rayuwa tazo maka, yanzu kaga Aisha daita dakai bazaa gane marar lpyar ba, ka daure karika shan magani ko kasamu lpy "



"yanzu ka kwantar da hankalinka kabani address na gidansu zanje nasamu mahaifinta nakara bashi hakuri zan kuma nemi alfarmar yafadamin asibitin da suka kaita, kaje kadubota koka dawo dede "


fahad yafada mishi adress din ,


sabeer yace "zanje nasameshi insha Allah zanyi bakin kokarina wurin shawo kanshi amma katashi kasha magani"


fahad yace "magani baze yimin wani amfani ba faseelat itace maganin rashin lpy ta "


Sabeer ya tabe baki yace "Allah yasawwake to, bari natafi gidan nasu "ya mike tsaye, 


fahad ya meda kanshi cikin duvet, da hannu sabeer yayiwa Aisha dake tsaye tana hadiyar zuciya magana akan ta biyoshi, ta bishi suna fita kofar dakin, sabeer ya juyo yace "kiyi hakuri Aisha da yanayin shi, karki bari suratan shi su dameki naga kamar baya cikin hayyacin shi, kiyi hakuri ki sa masa ido "


Aisha tai murmushin da yafi kuka ciwo aranta tace aiba yanxu nafara jin irin wadannan daga bakinshi ba, afili tace "Tom nagode Dan Allah kayi bakin kokarinka wurin samo mishi address na gidan nima zanso yaganta koya dan samu sauki "


sabeer ya lumshe ido ya bude yanajin matsanancin tausayinta yace "I will do my best "


ya juya yatafi ita kuma takoma dakin ta kwanta gefen fahad don hakanan take kokari amma zuciyarta matsanancin ciwo take, 


sabeer na cikin mota yana tuki hannunshi daya akan bakinshi yana tunanin maganganun fahad,yace"kammmm amma wlh Aisha na hakuri, wannan irin so haka to ko ya zaman nasu yake? nide insha Allah bazan bari matana sugane wacce nafiso ba,"


har yaisa unguwarsu faseelat gidannasu a kulle dayake komi acikin natsuwa yafi hankali seya nufi wasu samari dake zaune can gaba da gidan bayan ya musu sallama yatambaye su kosun san inda zesa mu alhaji maaruf,suka fada mishi ai shagon shi nanan kofar keke, ya musu godiya ya kama hanyar kofar keke don ganawa da abba,















gaskiya duk group din da baa comments zandena turawa aciki kunsamu awani wuri, yan groups dina kuma zanfara removing marassa magana wasu ma tunda suka shigo basuyi magana ba kar in cire mutum yaji badadi shiyasa nafada kurika comments please, 


shalele novels group 

Shalele value group 

shalele boost group 

raggon miji fans 123


duk wace batason ganinta awaje tarika comment.




Post a Comment

0 Comments