TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI PAGE 85

 8⃣5⃣






*Godiya da ban girma ga anty ta anty hanne ado writer of fini a uba nafiki a miji,wacece uwa,and now iyayen ko mazan, ina rokon Allah yakara miki budi yakara miki lpy ya shiryamiki zuriar ki, ya kara miki basira da daukaka yasa kigama da duniya lpy a karshe ya tsunduma ki aljanna, ke masoyiyace nagode da soyayya Allah yabar kauna*



*readers🗣kunemi novels na anty hanne akwai darussa da dama,zakuji dadinsu*



*ni shalele wlh inajin dadi na 😂💃🏼sede naji bugul alert ya shigo daga masoya, kamar kunsan ba abinda yafimun dadi kamar naji alert😂 kai ina godiya Allah yabiyaku yakara maku budi kuyita cikani da alheri nagode😘😘😘😘*






Tana zuwa tai parking ta shiga sedata tattaro duk sauran kuzarinta da faraa sannan tai sallama ummi tafito tana amsa sallamar, tai tsaye baki hangame tana kallon muguwar ramar da tayi, faseelat nata murmushi taje ta rungumeta ,tana cewa "I miss you so much ummi "


Ummi ta cirota daga jikinta tace "faseelat duk laulayin cikin ne haka? kinbi kin kanjame kin fada dubi skin dinki yadda duk ta yamutse kode baki lpy ne? "


faseelat tai murmushi tace "ummi se ahankali wlh banijin dadi sosai laulayi nake ba kadan ba ina wahala sosai bana bacci sosai bana iya cin abinci sosai sometimes ma tea kadai nakesha ga amai, kimin addua ummi Allah yaragemin wahalar nan "


ummi tace "amin to amma kin canza kinga idanunki kuwa? "


faseelat ta shafo su tace"me sukayi ummi? "domin ko madubi bata cika dubawa ba, 


Ummi tace "sun karayin luhu luhu fuskarki kuma tai firit "


faseelat tai yake tace "ummi lubiya  nakeso kimin yau inanan har dare yanzu kimin lubiya da dare kimin tuwon dawa miyar kuka plsss "


Ummi tace "seme kuma Kikeso? kinsan ke shalele ce komi kikeso zakisamu "



faseelat tace "su kenan ni ai banso kina wahala"



ummi tai murmushi tace"kishiga ki kwanta ki huta yanzu zan shiga namiki "


faseelat tace"nagode ummi "


ta nufi daki ummi tabi bayanta da kallo duk yan kugun sun zube tace "to Allah ya kawo sauki"ta shiga kitchen ,


faseelat nashiga dakin tai kwance akan 3seater sede ba bacci ne idonta ba, ta kulle idonta gammm tana tunanin different moments da takeganin fahad yana wa Aisha abubuwa romantically, tunaninta yatsaya akan tafiyar su, yanzu Hero zeyi tafiya baze fadamata ba? saboda dan karamin laifi yanata gana mata azaba dama duk kalaman da yake fadamata karyane kenan, da yanzu ze tafi yabarta cikin ciwo da damuwa shiko ko ajikinshi, wai ko hero naso yagama da duniya lpy? Idan na mutu fa Kafin su dawo?baze yiwuba nasan dole ze sauko hero bazeiya wata ukku yana fushi dani ba "

Tanata tunani abinka dame ciki se bacci, 


seda ummi tagama tazo ta tadata taje tayo brush tazo cin lubiyar, sede me? takasa cin ta kirki tanajin dadinta amma damuwa bata barinta cin abinci ta dauka tameda kitchen, tadawo


ummi tace "tunda bakiiya ci me zaki ci? "


tace "bakomi nakoshi dayake bama wani cin kirki nake yanzu ba "



ummi tace "Allah yaraba lpy, ai inajin yanzu yakai 2month nanda 2month zaki ragejin laulayin daya fara girma "


faseelat tai murmushi tace "ummi gidan yaya zanje nagano anty fadila "


Ummi tace "keda baki lpy? kibari harki samu sauki mana shi haryanzu be barinta fita daganan se gidan alhaji babba yace setayi 3month wai, "


Faseelat tace "ummi gwara naje tun biki fa bari natashi na shirya"



ummi tace "tow kibi sannu Allah ya kiyaye"



Tace "amin"tatashi ta wanke jikinta tasa hijab tafita, ummi tai shiru tana ta nazari gaskiya tana wahala mutum yayi fesss ga kasusuwa, 


Faseelat tashiga mota ta tafi gidan ya omer, 


Tana shiga gidan tafara knocking a bakin kofa, omer yazo ya bude, 


Waze gani his sister acikin mummunan yanayi, gabanshi nafaduwa yace "sister meke damunki amma baki lpy ko? "


faseelat tai murmushi tace "yaya ciwo ne kawai mushiga daga ciki "


yabata hanya tawuce ciki yabi bayanta da kallo,dama laulayi haka yake ma wasu? 


faseelat tashiga ciki tai zaune kan kujera tana meda numfashi take kiran" anty !anty!! Fito fito yau manyan baki gareku agidan"itako fadeela tana toilet wanka 


jikin omer mace yazo ya zauna kujerar dake facing tata,yana kallonta yace "sister kode akwai abinda ke damunki ne? bayan laulayi "


faseelat tasaki murmushi tace "Dan Allah yaya karka damu kanka wlh ba abunda ke damuna, cikin ne kawai kuma lokaci ne nanda wasu watanni kome zezama labari "


yayi shiru yanata kallonta but he smell something fishy,


Fadeela tafito tanata faraa tace"sannu da zuwa anty maraba "


faseelat tabita da kallo har ta zauna tayi fesss Abunta tayi mulmul cikin kankanin lokaci, 


Faseelat tace "yawwa anty, ya gida ya kuke? "


fadeela tace "lpy lau ya jiki jiki? Allah yaraba lpy"


faseelat tace "amin" tana harararta tace"anty kema fa akwai Alamar tambaya kode yaya yagama cika aiki? "


fadeela ta dukar da fuska tana dariya, 


faseelat tajuya wurin omer taga yanata murmushi yana wa fadeela kallon kasa kasa, tai murmushi tace "hakane ko yaya? Munkusa samun baby"


yace "ihhm amma not very soon"


faseelat tace "I'm happy sis akula da mu sosai"


Fadeela ta bugar da maganar ta hanyar cewa "me zaa kawomiki akwai white vegetable rice da stew akwai sakwara, sobo zakisha ko kunun aya ko mango juice? "


faseelat ta zaro ido tace "anty kuna shagali walla wannan jerin abincin fa shiyasa duk kukayi kiba"


omer da fadeela sukai dariya ta cigaba da cewa "toshi ke tayaki ko? "


fadeela tace "anty duk shi ya girka tayashi kawai nake baya bari na yin kome "


faseelat tai murmushi tace "yar gata, to yanzu ni a koshe nake sede duk inda naga kunun aya bana bari akawomun nasha nasa albarka"


fadeela tai dariya ta Tashi, 


Faseelat tai shiru se tunanin soyayyarsu da fahad ya fadomata yadda yake tayata abubuwa kullum yana fadin banso kina wahala,


Omer yaga ta tafi tunani yace "hmmm I knew it theres something behind it"acikin ranshi, 


ya tashi ya haye sama yanajin haushi yasanta komun nacinshi bazata fada ba tunda tasan baya yin mijinta, tunda Allah yadora mata wahala base tai tayi ba, 


Fadeela ta dawo ta ajiye plate da cups asama da robunan Faro biyu cikeda kunun ayar, itako tanata tunani, 


ta koma ta zauna tace "anty ga yanan "


faseelat tai sauri ta dawo tace "OK nagode" ta dauka ta shanye roba daya, tanata santi, 


Sunanan ta daga kai ta kalli agogo 3:30 tasan yanzu Sun daga, 


se karfe 5 tafito ta tafi gidan baba babba sannan tadawo gida seda akai ishai takoma gidanta, 


gidan tsit se tsoro ma yakamata katon gida ita kadai aciki ,ta tsaya tunani gidansu de ba yarinya gashi ma bataso asan bakowa gidan seita don duk Wanda zeji yasan baa kyauta ba tunda bata lpy, 



Hakanan ta daure ta haye sama tayo wanka tai shafai wuturi sannan ta dauko kurani tafara karatu daga bakara da niyyar tanason ta sauke tunda yanzu tanada lokaci available, 


Tanata karatu har 11 sannan tayo alwala ta kwanta bacci kuwa ya dauketa, 


suko su fahad tuni suka isa Sudan jikin abba de gashinan sede ace dasauki, umma koda taganshi da Aisha tayi tunanin don faseelat bata lpy ne bazata iya tafiya ba, 


Data tambayeshi ita seyace tana gidansu wannan ya kwantar mata da hankali,


ranar sunyi saa khadija da lady da safiyya sunzo sunanan, 


dasafe suka wuce Malaysia, 


Tunda faseelat ta tashi tai salla tai karatu ta gyara gidan ta dan kwanta bacci tana tashi batajin yunwa tai wanka ta kunna data se kuma ta sauka tafita garden shan iska, 


gidan jinshi take badadi samm ashe har gwara tana ganin shi yana wulakanta tan da rashin ganinshi  gabadaya, kewar shi data addabi zuciyarta ne yasa kullum tana like da waya tana kallon pic nasu da nashi shikadai dana marigayiya amira, 


ita kadai take rayuwa kuyum kamar mayya, wani lokaci su Mubarak sukan leko ta, 


Itake fita tasiyo abunda take bukata 5million de itace taketa amfani daita, Kafff maganinta sun kare taje tasiye  wasu da abubuwan da takeso, 


cikin sati biyu takeyin saukar kurani bayaga nafilfili datakeyi duk dare, 



Bayan wata daya, 




Lokacin kuma cikinta yana wata ukku cifff sosai yake motsi damuwar da take ciki bata hanata kula da kanta ba hakan yasa tatafi asibity donyin antenatal bayan da aka duba cikin akai mata blood test da alluran da akeyi se akamata scanning tana kwance tana kallon abinda ke wakana acikin TV din, 


Itakam ta gansu rututu abun yadan bata tsoro har takasa kilga yawan abinda take gani, bayan angama ta tashi akabata results nata, they're 4 in number dadi yagama kasheta taita ma likita godiya kamar shi yabata baby's din sannan takoma gida, 



Kullum jira take taga fahad ya kira amma shiru wata daya da sati biyu bawasa bane, yanzu takan samu sauki kafin ciwon ya motsa mata hakan yasa takanji bukatar mijinta akusa daita, kuma ba yadda taiya sede ta hakura


Zaune take a garden tai zaman dirshan kafafunta mike tana ta kallon pic na Hero awayarta, tana ta hawaye yadena sonta yanzu bayayin ta idan bahaka ba bayadda zaai yakai haka beko ji muryarta ba, 


Tana kallon pic din take rera wakar novel din raggon miji wadda shalele ta raira wadda taiwa suna da *(kewa)* wakace me ban tausayi da karya zuciya tana wakar tana hawaye, ga kadan daga cikin baitocin wakar"duniya babu tabbaci, rayuwa seda hakurii,ni faseelat ya zanyi ne da raina, don fahad yadena so aguna"

*(fans shalele naji daku dan jindadinku na rera muku waka zan turomuku ita bayan kunsha karatu kuji ta zakuji ta very sweet muryar cakwai😂se abi ahankali banda group na maza don kar asamu matsala🤣seriously waka donku fans💃🏼*


abun gwanin ban tausayi, 


tadade nan sannan ta tashi takoma bedroom ta kunna sunna TV tana kallo, idan tana kallonta takanji saukin abinda ke damunta saboda malamai dake waazuzzuka da dama, 


Tana cikin kallo ne wani malami(sheik gombe) yana waazin mata, akan bin bokaye Wanda ya gabatar a sokoto abun yadaga mata hankali,


 yace" se kina zaune da miji lafiya lokaci daya kiga ya sauya ya tsaneki anjuya mai kwakwalwa anjuya mai tunani bakomai bane ankaishi wurin boka ne kowani ka surgumin dan tsubbu yahadashi da bakaken aljanu sunata watangariri da rayuwar shi, mata sekun dage da addua dake da yaranki gabadaya dan wasu cikin ku shedanu ne basuda  imani ko kadan, zasuiya yin komi dansu samu biyan bukatarsu"


Waazin yake ita kuma tana tunani da zuciyarta take shawara"akwai fa alamar tambaya akan al'amarin fahad daga samun yar matsala se sumar dani se tsana haka kawai? to idan asirinne wazai mashi asiri? duk nan kusa ?"


Tace "to nasan abinda zanyi nasan komin laifin da nai masa bazaace ya kwashi 2month baya ganina ba kuma ya dawo da fushi dani ,Nide nasan mijina na sona bazemin irin wannan kiyayyar ba kuma baze iya 2month bama batare dani ba ,zanjira lokacin dawowarsu I wish ba asirin bane ,"


Shiru tanata kewar  mijinta har ,2weeks sukayi kuma basu dawo ba hakan na nufin 3month zasuyi yanzu kam abun yamata yawa kukan ma ta dena ,


Takoma awo cikin is  4months amma yayi girman ban mamaki  ga yawan motsi, fatar cikin tabude tayi wasu line kugunta yakara girma ,she complain about the movement doctor yafada mata lpy lau cikinta yake sede tarage damuwa don bp dinta yahau sosai ,


Bayan 1 month takoma awo su fahad jirginsu yasauka Nigeria batanan lokacin kusan karfe 11 na safe ita kuma tun 9 tabar gidan ,sunyo kibarsu hankalinsu kwance,


Koda suka shigo gidan kwasss dashi ,hannuwansu cikin na juna suka shiga dakin fahad wanka kawai sukayi suka kwanta da niyyar yin bacci fahad beiya baccin ba seda yadan huta da aisha,


Karfe 12 faseelat tabaro wurin doctor tadawo gida ganin sabuwar mota fa ke yasa tagane sun dawo  farin ciki yarufeta don ganinshi kawai takeso tayi kotaji dede aranta,


Dasauri ta shiga ciki bakowa falon ta wuce daki ta fesa wanka ta saka doguwar riga black color ta fesa turare  sannan tafito ,tasan karfe 1:30 dole yafito zuwa masallaci ,tashiga kitchen ta dafa kuskus fari already tanada stew takwashe ta kai dining sannan ta zuba tafara ci domin yunwa takeji don yanzu bata iya 30 mnt bataci wani abu ba ,


Tanaci tana duba wall clock dake jikin dining ,


Bayan ta gama takoma falo ta zauna ,


1:35, segashi yafito ta naganin yafito tamike tsaye ko kallonta beba zewuce tace "sannu da zuwa"


Yaja dogon tsoki yafita,hawaye suka gangaro mata yanzu kenan asirin aka mishi takoma ta zauna tafashe da kuka mecin rai ,tana kuka take cewa"waye yamin haka ?saboda me ? Ya cutar dani ya cutar da hero dina Allah yaisa bamu yafeba"

Seda tasha kukanta sannnan ta tashi ta haye sama dasauri dukda hawan step namata wahala segashi tafito da hijab jikinta da key na motor a hannu tazo bude kofa yabude yashigo beko kalli inda take ba yawuce tabi bayanshi da kallo zuciyarta na zafi,hawaye suka zubo mata ta sharesu da hannu ta fita ,


Tashiga mota tafita ba inda ta tsaya se arriyad islamic center ,ta shiga tayi saa tasamu malan yahya tamishi bayani yace"asiri ne akamishi amma insha Allah zamu temaka ze samu lpy" 


Yabata magunguna masu hadi na sha,na turare, dana shafawa,ta amsa tai godiya akai list kudin maganin nera 15k kamar anbata kyauta taita godiya tafita, tana ta Sauri ta koma gida ,


Da shigarta tasamu aisha zaune a main falo aisha tajuyo tana kallon cikinta da yayi kato kamar me cikin yan biyu wata tara ,ta dauke kai zuciyarta na zafi ,


Faseelat ta shigo ciki da ledarta rike ahannu ta matsa wurin aisha tace"anty kundawo lpy ?"


Aisha tace "lpy lau"inshort 


Faseelat tajuya ta haye sama ,don ta dena mamakin Aisha tunda tana gani kome ke faruwa,


Hijab kadai ta cire ta fidda sauran maganin a ledar tabar nashan tafita kitchen ta wuce direct ba drinks daze rufa asirin magungunan inba zobo ba ta hada zobo tajuye magungunan ciki ,tahada shi sosai yaji kayan kamshi takai fridge,


Akan dining kulas kadai tagani sun cinye abincin ta dauka ta meda kitchen,tawuce daki tai laasar tana fitowa taga aisha da keys zata fita ranta yayi dadi,


ta shiga kitchen ta  dauko jug takoma daki tanada ganyen magarya tasan amfaninshi bayan sit birth,guda bakwai ta tsinka ta wanke tazubasu a jug cikin ruwa tamurje su ,ta bude kurani ta karance suratul bakara kafff aciki ta rufe tatsaya tunanin yadda zatai dasu tunda wankan dole se awuri me tsarki,dabahaka ba da a tanki zata bawa baba tsoho ya zuba kowa yaita wanka, ta tashi ta sa a fridge tana fatan in yadan fara dawowa dede tabashi yayi wanka dasu,


Kusan karfe5:40 tsit da alamu duk basunan ,


Tashiga kitchen tadora girki da man habbatus sauda da zaitun ta soya miya domin hadasu cikin na shafawar tahada tuwon shinkafa miyar ganye a wahalce tagama ta dora dining tahaye sama ta sake wanka tai Maghreb  ta dauko kwalin maganin da akace na hiyaki ta aje kwalin tafita dashi,


A falo ta jona burner seda tai ja sosai ta kwarara maganin falon ya turnuke da hiyaki ta dauka tana haki ta zagaye wurin dining dashi zuwa sama dataje dakinshi seda takara zubawa sannan ta kullo dakin ta fito ,


Takoma daki tana ta tunani kanta na matsanancin ciwo har akayi ishai tayo alwala tazo ta kabbara tana salla tana kuka ,


Bayan ishai fahad yadawo daga gun abokanshi har lokacin aisha bata dawo ba ,


Yana bude gidan yaji wani kalar kamshi badadi ko kadan kanshi yayi nauyi,dasauri ya haye sama ya bude dakinshi nan kuwa yafi koina samu yabude windows ya kure fanka shaf shaf ya shige toilet yayi wanka ,ya fito yasa boxer ya zauna bayason fita falon sega aisha tazo ta rungumeshi tana cewa"nadade ko ?im sorry"


Yayi shiru saboda tunda yashigo kanshi yafara matsanancin ciwo,


Tace"ya de?"


Yace"normal kikawo mana abinci anan sama plsss banason fita falon"



Tace"to shikenan"ta juya ta fita ta dauko abincin ta medo sama ,


Tayi serving dinsu a plate daya tafara bashi abaki tana cewa "kamar bakajin dadi?"


Ya samu ya hadiye na bakinshi dakyar yace"im not well"


Tazo zata kara masa ya kauda kai ya dauki jug ya tsiyayi sobo cikeda cup ya shanye ,


Seya fara jin juwwa juwwa ya tashi yana layi yafada saman bed nantake bacci ya daukeshi ,


Hankalin aisha yatashi taje ta birkito shi taga yana sauke numfashi ahankali yana bacci ta gyara mai kwanciya ta koma taci abincinta takoma dakinta tai wanka ta haye bed tana charting se 11 takoma taga har lokacin yana bacci ta juya tafita ,tana ta kalonshi wata zuciyar nabata takira likita wata zuciyar na cewa tajira yatashi,


Takoma daki ta kwanta se bacci ,


Faseelat kam yau kokadan bata rumtsa ba daga zaune take ta salla tana adduoi a sujud tana hawaye ,sosai takejin jikinta ya mata nauyi amma hakanan tadaure tai tayi,



Karfe 4am ya farka da faduwar gaba yanajin kamar.....




What i want u to understand asiri ma ciwo ne bayan addua dole se antashi tsaye da neman magani har Allah yasa adace ,Allah yabawa marassa lpy ,lpy amin.







Karkumanta da wakar kuma banda dariya 🤣



Post a Comment

0 Comments