TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI page 29-30

 RAGON MIJI


*Bismillahirrahmanirrahim*


*K'auluhu ta'ala:-faman yaamal misk'ala zarratin kairan yarah, waman yaamal misk'ala zarratin sharran yarah.*




*Gawasu de ankara samu, double power, kongy capsule ,extra large sizetablet,,gamyka herbal powder*






Yana haka wayarshi tafara ring ya dauka dasauri ganin hjya ce, ko sallama batai ba tace "ka koma gidan? kadauki diyarsu ka meda musu kar ta mutu nan, dan ummi takirani tace zatazo ta dauketa yanzu "


jikinshi nantake ya mace yace "ai har ma  Sun zo suntafi da itan "


Ummi tace "to yayi ai hakan ne dede kaga kaima yanzu seka cigaba da yan hidimomin ka "


Yayi shiru yana tunanin yadda ze kwana shikadai batare da faseelat ba, hjy ta yanke kiran, tana jan tsoki. 


Ko zama beba yajuya ya tafi gidan nasu lokacin har sun'isa faseelat na kwance kan kafar ummi tana ta kuka ya shigo gidan da sallama, 


Ummi ta amsa mishi ya zukunna ya gaisheta yafara tambayar ya mejiki? "


Ummi tace "gatanan de, ai da tuntuni ma kamedota gida irin ciwace _ciwacennan na masu ciki beda ranar warke wa "


Yayi shiru yana tunanin maganar ta kenan tunani take ciki gare ta, 


Ya buda baki yace "munsami likita yace tana fama da typhoid ga magungunanta nan acigaba da bata"


Ya ajiye ledar maganin da kazar da ya siyo mata da yoghurt 


Ummi tace "ai typhoid batajin maganin bature yanzu tunda ta na nan zaa samar mata na gargajiya "


Yace "Tom mungode ummi ga wannan kunsiya magani "ya ajiye masu dubu goma, 


Ummi tai godiya ya tashi tsaye yana kallon fuskar faseelat itama tun dazu shi take kallo dan tunda ummi tai maganar ciki takafeshi da ido tana so taga yanayinshi yace "Allah ya saw wake faseelat natafi "


ya juya ya fita jikinshi a mace gabadaya jiyayi kamar anraba shi da duk kuzarin sa, ya ja mashin dinshi ya tafi, 


Yana tafiya ummi tace "cikin wata nawa ne dan insan maganin da zaabaki "


Faseelat ta zumburo baki dukda bata lpyan can ciki ciki tace "ummi nifa banda komi yanzu haka ma mens nakeyi "


Ummi ta rike haba duk zumudin ta ya koma tace "aure wata 6 amma shiru, ke kuma taki haihuwar me jinkiri ce "


Faseelat tace "hmm" kasa-kasa inama zata iya fadawa ummi matsalar ta amma bazata iya ba ,


Ummi tace "to Allah yasa jinkirin alheri ne aini har nafara murna zansamu jika me tayani wasa "


Faseelat batace komi ba, suna haka sega abba ya mata ya jiki yana tausaya mata, ummi tafada mishi abinda ke damunta yace bari yaje wajen wani me bada maganin typhoid ya amso mata .



Yaje ya amso maganin akafara bata da na wanka da na sha dana suraci, ko da akai mata da rana da marece da dare segashi faseelat tadan fara jin sauki, 


karfe bakwai wayarta tafara ringing ta dauka tana murmushi ganin maman amira ce, 


maman amira tace "momyn twins rashin lpyar ce ta boye minke har yau "


Faseelat ta saki murmushi "anty kenan wlh ban lpya sosai inama gidanmu aka medoni dazun "


Tace "ayya banji dadi ba, babyn mu nata baki wahala, tun shekaran jiya da kikace min baki lpya nashiga damuwa nata kiran wayarki kashe "


Faseelat tace "eh ni kaina bansan ina nike ba se yanzu ne naji dan dama na kunna wayar "


Maman amira tace "ayya Allah yabaki lpy naso nazo dubaki to gashi kuma gobe zamu tafi London zamuyi one week sede in mundawo zanzo "


Faseelat tace "bakomi anty Allah yakiyaye ya bada saa"


Aisha tace "amin "


Faseelat tace "agaidamin amira I'm going to miss both of you "


Maman amira tace "don't mind bazamu dade bama ki kula da unborn dinmu bye "


ta kashe wayar faseelat tai murmushi ita kadai ta dora hannu akan cikinta tana shafawa tace "inaso inganni dauke da cikin my love naji ya masu ciki sukeji, "tai shiru canzuwa tace "Allah amin "



Bayan isha khalil yaje gidan hjya cin abinci ta zubomasa tanata jan shi da labari yana meda mata amsa sama sama abincin ma bawani ci yakeba gabadaya bayajin dadin jikinshi, 


Hjya talura dashi tace "wai yau lpya kake de naga ko abincin ma bakaci sosai "


yana yamutsa fuska yace "banijin dadi ne hjya "


Tana tabe baki tace "to dama ya zaai kaji dadi gimbiya na can gidansu ba lpya "


daga jin maganar yasan gatse take mishi, 


Ya dan matsar da plate din gabanshi yace "hjya bari natafi gida nasha magani Kaina ke ciwo "


Hjy tace "to aita himma "ta tashi ma tashige daki saboda takaici, 


Khalil ya girgiza kai ya fita gidan, 


Bayan yaisa yayi wanka ya haye gado gabadaya kewar faseelat ta cikashi, hanunshi kan gefen da take kwanciya yana ayyana da yanzu itace gun, 


Ya dauko wayarshi ya diba time karfe 9 da rabi, duk dade dare yafara yayi dialing no din faseelat ko yaji muryar ta ya rage zafi, 


Faseelat na kwance dakinta kiran ya shigo ta mika hannu ta dauka ta kara wayar akunne with out saying something, 


Yayi sallama ta amsa can kasa yace "ya jikin? "


tace "dasauki "


"Kinci abinci?"


Tace "eh "


Yace "faseelat na kasa bacci saboda rashin jinki kusa dani"


Faseelat tai shiru cikin ranta tace "dan rainin hankali kada kai baccin ni anan nafisamun natsuwa "


yakatse shirun da cewa "ina kewarki sosai"


Tace "nima haka seda safe "


Yace "to Allah yakaimu "

Dif takashe kiran tai kwanciyar ta, shima yagama tunaninshi ya kwanta, 


da safe ya koma wurin aiki, ana tashi yatafi gidansu faseelat, haka taita jinya kullum yana gidansu ya siyo mata wannan ya sai mata wannan, ummi sosai takejin dadin yadda taga yana kula da diyarta, 


Bayan 5 days faseelat ta warware abba da kanshi yace faseelat ta shirya takoma gidanta aragewa khalil zarya, ummi tace "dama anbarta tayi koda sati ne "


yace "kina gani de yaronnan a takure yake gara takoma yafi "


ummi ta yadda da shawarar abba tace amma se gobe zata tafi, 


ranar ummi tabawa faseelat magani yafi 5 dana matsi dana sha da dubara faseelat batai gangancin amfani da ko daya ba, 


wanshe kare da yake weekend ne wajen karfe 11 khalil yazo ya dauketa suka tafi, seda suka biya gidan hjya sannan suka wuce dan hjyar tata zarya dubiyar faseelat din, 


Suna zuwa gida dakin ya harmutse ba masaka tsinke cikin jin haushi faseelat ta hau gyaranshi. 



Tun kafin dare ma ta tanaji lemunta ta dafa ta zuba a flask dan tasan yau akwai bidiri. 



hakan ce tafaru ko tana ganin yayi bacci tasamu ta sauka ta hau shan lemon dinta tana sha tana tunanin khalil saboda yau so biyu yana attempting shigarta amma yakasa saboda wani irin son yara yakeji yanzu, niko nace malan khalil se anbada himma fa 🤣




ranar litinin faseelat takira maman amira dan tana tunanin sundawo, tai saa ta sameta tana dauka tace "patient ya jikin dazunnan muka dawo insha Allah gobe zan zo inga ya unborn ya medaki "


Faseelat tai dariya tace "to anty se kinzo inafatan de kundawo lpy? "


Aisha tace "lpya lau diyarki na gaidaki inafatan de kinkoma gidanki? "


faseelat tace "eh na koma "


Maman amira tace "se nazo to kimun wainar filawa irinta rannan"


Faseelat tace "ba matsala "




Tunda safe faseelat takara gyara gidan komi yayi fess tayi abincin rana shaf shaf ta gama ta soya wa maman amira wainar sannan tayi wanka ta zauna jiranta, 



Karfe 4  faseelat taji knocking dinta taje tabude mata tai sauri ta dauki amira tana jindadi , sika shiga ciki maman amira na zama tace "kai amma unborn be kyauta ba kinga yadda kika rame "


Faseelat tai dariya "Allah anty babu komai typhoid kawai ce, kinsan bazan tsaya boyemiki ba "


Tace "to naji ayi sauri de a samarwa amira kane aikun shana da yawa 6 month kuna jindadi? "


Faseelat tace "hmm anty ni bansan wannan dadin ba haryanzu "


cikin rashin fahimta maman amira tace "zaki sanshi ne "


Suka cigaba da fira sannan faseelat takawo masu wainar su da zobo da tayi da ruwa maman amira naci itakuma faseelat tana bawa amira suna labari har suka gama, 


Maman amira ta tashi tafita wanke hannu, jin karar toilet yasa faseelat matsawa ta dauki wayar ta dake ajiye gefen kujera luckily ba password ta shiga call log direct ,batare da shan wuya ba taga an rubuta heart beat ta shiga cikin contact din ta karance number tsaf, dandanan ta hardace ta, 


tana rike da wayar maman amira ta shigo ta zauna faseelat tana jujjuya wayar maman amira tace "gaskiya anty wayar ki nada kyau "


Aisha tai dariya "eh kuma tana da dadin amfani "


faseelat ta latsa wayar tace "laah anty bakisa key lock? "


maman amira tace "a, a ai daddyn amira bayason locking waya cewa yayi seyaga kamar da wani abu shiyasa nadena sakawa don shifa time to Time yana checking wayata yaga me nake daita "

Faseelat tace "koda naji "


Aka cigaba da labari can zuwa maman amira ta bude Jakarta ta fiddo wata riga me kyau cikin kwalinta ta mikawa faseelat tace "gashi aiwa ango khalil kwalliya "


Faseelat ta amshe tana kiran "Wow tayi kyau anty kamar kinsan best color na purple ne "


maman amira tace "to yayi kyau bari muwuce se kinzo ko? "


faseelat tace "insha Allah "


Maman amira ta mike ta yafa gyalenta amira tafashe da kuka itafa batasan wannan ba haka tajata suka tafi faseelat Nata masu waving da hannu har suka bace, 


Takoma gida ta zare hijab din jikinta ta jawo wayarta cikin tsananin farin ciki ta rubuta numbern fahad tai saving dinta da my hope. 




🤦🏻‍♀ yar uwa ki kula da number mijinki wlh saboda tunaninki baze taba hango miki wadda, zata cutar dake ba harse aikin Gama ya gama, wata makwabciya kullum kullum intazo gidana number da mijinta ke kiranta ba suna, nace wai ke shi ogan baa saving number dinshi tace kam a,a ai tana cikin brain dina kinga ko no need in yi saving harwata taji dadin kwasa, nai dariya ina mamaki don nide nayi saving no din abuna,.

RAGON MIJI


*Bismillahirrahmanirrahim*




*k'ad aflahal muuminun....... Wallazina hum li furujihim hafizun, illah ala azwajihim au mamalakat aimanuhim fainnahum gairu maluumin*






Ta tashi tanajin dadi takai kyautar ta daki ta dawo ta gyara wurin ta koma ta sheme kan cushion, 


Ta dauki wayarta ta bude data ta turawa maman amira message "anty Nagode kwarai da duk abunda kikemun Allah ya barmu tare harabada, ina amira ta fatan ta hakura, ya gajiya?inafatan kun'isa lpya"


she's offline dan haka ta wuce tana responding to friends nata, tana gamawa seta bi numbers dinta na what's up, suddenly taga number fahad shima yana chart kenan ta shiga number tana son ganin last seen dinshi amma yasa shi privacy don haka bata samu gani ba, tai shiru tana nazari can zuwa ta fara mishi message kamar haka "aslm yaya ya kake ya aiyuka Allah yabada saa, kullum kana raina my yaya kuma Kana cikin adduoina a kowace salla, fatana Allah yakara tsaremin kai ,ina sonka, tareda kewarka data addabi zuciyata  a kowace dakika "


Ta tura masa ta tsaya tana tambayar kanta "ai yayi ko? Kar in saurin tura mishi hot message yaje yayi blocking dina, gradually de zamu kai gun "


Ta fito ta shiga dp nashi pic din flower ne  purple jiki an rubuta "i like purple like no other color exist in the world "


Tai murmushi tace "that's why i started loving the color although my best color was maroon"


Hakanan taji tana son bude instagram and facebook da tanayinsu amma tunda khalil yabata waya batai ba  tana fatan fahad nayinsu nan danan tai installing dinsu ta shiga facebook ta tura mishi friend request, ta shiga instagram tai following dinshi,  tana ta jindadi, ana haka akai kiran sallar Maghreb ta kashe datar ta tashi tayi alwala tai salla ta dauki kurani tana karantawa har akayi isha'i tai isha i ta tafi tai wanka ta saka sleeping dress dinta ta dawo ta zauna, ta dauki wayar ta bude data, 

Cike da burin ganin reply na fahad, 


Tabi messages luckily har da na fahad tai sauri ta shiga ga abinda ya turo mata "thanks for your duas May Allah accept it, all thought I don't recognize you, who are you ,you are not familiar"


Tai murmushi tace "u will know me very soon "


Ta tura masa "I'm ur lover and sister to you also "


Fahad ya bude message din don maman amira ma is busy chatting with her friends, 


Ya dade yana kallon message din duk tunaninsa ya kare ne akan yaruwassa ce ko bangaren momy ko cikin dangin ummanshi, 

Ya dan ja tsoki bazata fadi sunanta ba kenan?kamar ya shareta se kuma ya tura mata "plss may i know you? "


Tai dariya ta tura mishi "sure, but u have to promise me that, zaka cigaba da charting dani bayan kaji kowacece, kuma baza kai blocking dina ba "


Yace "yeah "


Ta tura masa "sunana faseelat shekara ta 21 going to 22 ,kuma ni yaruwarka ce tunda ni musulma ce, nadade ina kallon pictures naka bana da sukuni inban Kalle suba, nafada sonka batare da na shirya ba, inafatan zaka bani dama "


Yana karanta wa yace "rubbish "


ya fita daga chart dinta, 


Shiru shiru ba reply gabanta ya fadi karfa yayi blocking dinta, 


tai sauri ta tura mishi "a good believer always fulfill his promise "


Yana charting da friends nasa besan ya shigo ba, dan haka be mata reply ba, 


faseelat ta hura iska daga bakinta ta rumtse ido tana tunanin pictures dinshi da tagani a instagram, 


Cikin ranta tace "I have to do something kar ya shareni kamar bola "


Tai sauri ta bude gallery tanabin pictures Nata daya Bayan daya ta tsaya kan wani picture da abul ya dauketa tana tsaye ta dan juya baya kadan tana sanye cikin riga da sket atamfa, tana murmushi, 


Ta kara kallon pic din ko ita kanta tasan yayi kyau, ta dora shi a dp nata,


Sannan ta koma ta cigaba da charting dinta, 


Fahad se da yagama duk abinda zeyi sannan ya bude message dinta saboda yanaganin she's insane da har zatai tallan kanta gareshi,


Yana ganin abinda ta rubuta yayi murmushi yace "young girl "


Yana fita message din yaga akwai dp hakanan yaji yanason sanin kowacece, ya shiga dp din, yana kallon pic din yayi shiru, "yeah she's beautiful amma ban tunanin na taba ganinta ko aina ta sanni ne? "

Yaja tsoki ya fita daga what's up din gabadaya, yayi zama abroad yaga mata kala kala wasu ma half naked donhaka pic din faseelat be kai pic din da ze tsaya yana wasting time akanshi ba, 



Khalil na dawowa ta turawa fahad "tunda ka shareni seda safe ka shafamin kan diyata amira "


ta sauka online ta kawo mishi abinci yana ci yace "kinsan siyama ta haihu? "


Tace "a, a me aka samu? "


Yace "namiji "


Tace "Allah yaraya kace zarya gidan jego ta gammu "


Yayi dariya kawai tai shiru tana kallonshi, wai shi baya ganin mutane na haihuwa ne? Ko a tunaninshi a romance kawai ake samun ciki ? Nace maybe 🤣


Yana Gama cin abinci ya jawo faseelat kan cinya yana shinshina ta yace "muma nangaba zamu samu yara Masu kyau kamarki "


Faseelat tai shiru cikin ranta tace "ai da yake a ruwa akesha "


Anan yaita romancing dinta sannan ya jata zuwa bedroom yau ma yayi attempting shigarta sede ina abun yaki shiga, faseelat jitai kamar Andora mata leda da ruwa cikinta kan prvt part dinta, 



da safe bayan ya tafi tagama aiyukanta ta tafi gidan jego tana zuwa se nan nan daita suke suna mata surutu wai uwar biyu aiwa babynsu hakuri yana bata wahala sede tai murmushi kawai, in tazo yin aiki suce aa karta wahalar da baby, maganganunsu ma takaici suke bata, 



kullum se faseelat ta turawa fahad message na addua tareda nanata mishi tana sonshi, 


Kuma yana budewa bayade yin reply, 



Ranar suna aka sawa yaro fawax su faseelat sunsha kyau dan anko sukayi, 



Da daddare har ta kwanta ta tuna bata turawa fahad message ba yau, ta tashi har khalil yayi bacci ta dauko wayar ta tura mishi "sorry yau bakajini da wuri ba ammin haihuwa ne muna wurin suna thanks for ignoring my texts "

Ta tura mishi pic din da aka dauketa cikin pitet gownt, 


tana cikin turawa khalil ya tashi yana kallonta tana latsa waya yace "faseelat dare ne fa ki ajiye wayar nan ki kwanta"


Tace "to "Tana turo baki ta kashe wayar tana gunguni tunda kai bakasan dadin charting dinba ai inkaga anayi se ka zuba wa sarautar Allah ido "shi khalil naganin chart is just wasting time shiyasa bayayi, 




da safe tana cikin aiki taji wayarta na ring tana dibawa taga maman amira ta dauka tana murna "anty kece? "


maman amira tace "eh, wai yaushe zaki zo kinsan fa ankusa fara azumi "


Tace "anty yaushe kikeso nazo? "


maman amira tai dariya "yau nikeso "


Faseelat tai dariya "to  yaude kinga marece yayi kuma banfadawa khalil ba amma gobe zanzo "


Maman amira tai dariya "bake kikace yaushe nake so ba, any way sena ganki goben "


Faseelat tace "thank you "



Suka yanke kiran, faseelat tai murmushi tana jin dadi fatan ta de taga fahad eyes to eyes she don't care yasan kowacece ita. 





Yau tunda safe ta shirya 11 tana bakin gate din gidansu dan yau yini takeson yi musu, me gadi ya budemata ta shiga tana gaidashi ta wuce ciki. 



Tana isa ta danna door bell sau biyu fahad da ke zaune falo Yana aiki da system dinshi ya jawo remote ya latsa kofar ta bude, 


Ganin kofar ta bude faseelat ta kutsa kai ciki tana ta faraa, 


Tana shiga tace "assalamu alaiiiii.... "takasa kara sawa ganin fahad zaune taja tai tsaye gabanta na bugawa, 


tanayin sallama ya dago ya kalleta ya meda fuskarshi kan system jin ko sallamar baakara sa ba anyi shiru yasa shi ya dago ya zubamata ido, yana kallonta from head to toe,

Post a Comment

0 Comments