TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI page 3-4

3⃣


*Dedicated to SIS ZULAIHAT RANO*


Sannan tace "naji dadin wannan maganar Hjy kuma inafatan zasu fuskanci juna Allah ya tabbatar mana da abinda yafi zama alheri *


Hjy saratu tace "amin amin Insha Allah gobe zezo su gaisa daita din saboda baniso a dau lokaci"


Ummi tai murmushi "tom madalla zansamu faseelat da maganar"


Hjy saratu tace "ni tunda nashigo bangantaba nade san su Mubarak ana school"


Ummi tace" inajin bacci takeyi, bari natado miki ita "


Hjy tace "aa barta bari na tashi nawuce gida "


Ummi tace "tom nagode kigaida gida "


Suka fito ummi tayo mata rakiya suna fitowa tsakar gida sega faseelat ta fito zata shiga toilet wanka tana daure da towel ,tana ganinsu ta sunkuya ta gaida Hjy saratu dasauri tashige toilet, Hjy saratu ta bita da kallon birgewa sannan tawuce, 


Ummi wasai ta nufi kitchen ita kuma faseelat tai wanka tai brush sannan tafito neman abinci, tana shiga kitchen ta tarda ummi na aiki batareda tace komiba ta debi kunun tsamin daakayi tafita shaf shaf ta shanye ta dawo tace ummi ta bata tayi aikin, ummi tace "a,a barshi zan dan tayaki se muyi tare "


Faseelat tace "a, a ummi kibari nayi "


Ummi tace "to" tasamu wuri tazauna tace "miko min albasa da latas din na yanka miki "


Faseelat ta mikomata  ummi nayanka take magana, "faseelat! "


Faseelat ta juyo "naam ummi "


Ummi ta cigaba da cewa "Hjy saratu ce tazo da maganar tanason danta khalil ya aure ki shine ta zo neman izini zezo kugaisa kufahimci juna"


Faseelat tai kasak'e can zuwa tace "to ummi "


Ummi tace "gobe yana nan zuwa seki shirya sannan inaso Dan Allah badanniba ki saurareshi "


Faseelat takara cewa "to ummi "


Ummi ta cigaba da cewa "Hjy saratu mutunniyar arziki ce tun bayan dawowarmu daga saudiyya ta daukeni kamar kanwa tana sona da zuria ta baki daya, gashi hartanason hada jini dani, Allah ina rokonka kasawa abinnan albarka"


shiru faseelat tai ta cigaba da tsintar waken dake gabanta. 


itama Hjy saratu tana komawa gida tafadawa mijinta yanda Sukai yace Allah yasa haka shine mafi alheri .


se 2pm khalil yashigo gidan dakin Hjyar ya wuce yafada kan kujera "I'm very tired hjy "


Ta harareshi "se kace wanda yayi dako "


yace "Allah Hjy barci ne a idona sosai bari na tashi naje naci abinci na kwanta "

Har ya mike Hjy saratu tace "kai dawo kazauna"


Yace "to "yaxauna yana jiran mi zatace 


"dazunnan naje munyi magana da wata kawata zakaje kaga diyarta intamaka shikenan, tunda kai kakasa fiddowa da kanka gwara ni na zabarma, kashirya gobe kaje kaganta inka tashi kamin magana zanbaka address inafatan kagane? "


Tunda tafara magana yake kallonta "amma Hjy kinaganin ba matsala ni da kinkara min lokaci banfa isa aure ba gaskiya "


Hjy ta watsa mashi harara "tashi kaban wuri "


Ya tashi har ya kai kofa ya juyo "amma Hjy kinaganin ita yarinyar zata amince? "


Hjy saratu takara watsa masa harara 


Abinda yasashi juyawa kenan ya fita dakin yanajin duk ta takura masa aishi be tashi aure ba gaskiya shi ko kallon mata bayayi bare soyayya,kusanma tsoron matan yake ranar kwana yayi beyi bacci ba ya nata saka da warwara Karon farko da ze tunkari mace me zece mata?  Mi zasu tattauna shine tunaninshi kawai. 


Itama faseelat batai bacci ba will he be like her dream guy? gaskiya bazata taba yin aure ba harse tasamu muradin ta idan ya mata fine inbe mata ba bazata aureshi ba ko, 


Haka ta kwana sake sake, 


Washe gari 



Bayan tagama aikace aikacenta na yau da kullum sannan ta shirya tasa ka riga da sket ta yafa gyalenta ta zauna jiran tsammani dan ummi sunyi waya da hjyar tace karfe 11 zezo, 



agogo ta kalla taga karfe 11 saura ta zare gyalen tana tsoki ta kwanta kan bed baccin da bataiba ya dauketa 11 dede ya iso kofar gidan wata yarinya yasamu yace ta kira masa faseelat, gabanshi nata dukan goma -goma. 


Yarinyar nashiga ummi tace kice gatanan zuwa, tashiga dakin faseelat ta tadata"kitashi kigyara 

fuskarki maza "


shaf -shaf ta sauka daga gadon ta kara kallon madibi bata tsaya kara shafa komiba tafita she's eager to see him. 


tana fita kofar gidan ta diba hannunta na haggu taga roba -roba  fa ke ,cikin ranta tace oh God ko yar honda bedaita mtssssw. 


Tayi sauri ta juya hannunta na dama, se gashi tsaye yanata son ganin fuskarta tana waigowa ya zuba mata ido itama shi take kallo daga saman sa zuwa kasa. 

baki ne amma not that black idanuwansa a bit tiny hancinsa gajere with medium mouth kayan jikinsa kaftani ya taso hula gaba har kan goshi daf da ido tsawon shi takalla dogo sosai shantaly kenan 😂🙊zufar dole ce tashiga keto mata, 

*da akwai matsala fa*🤣

in next page zamuji ya firarsuzata kasance.

4⃣


*dedicated to sis ZULAIHAT RANO*


*All praise be to Allah*


Shi ko kallonta yake saboda ta tafi da hankalinsa tabbas faseelat mace ce da inka kalleta seka kara kallonta, kallon kallo suke wa juna and ita nata kallon tanayi ne kawai amma hankalinta baya tare daita magana ma take da zuciyarta ga abinda take cewa "allahumma ajirni fii musibaty wa aklifly khairan minha, to musiba mana gabadaya tunaninta ya Kare akan mamakin tsawon sa dama duniya a kuma Katsina akwai masu irin wanga tsawo haka? Ta cigaba da cewa ya Allah kaceceni mu rabu da bawannnan naka lpya. 


Shiko tashi zuciyar tuni ta kamu da kaunar faseelat  ,


Can zuwa ya tattaro natsuwarsa bakinsa na dan kyarma yace "Assalamu alaikum"



firgigit ta dawo hayyacinta still zufa na karyo mata se kace mejin kashi, 


Tana mazurai tace "sannu da zuwa shigo ciki"


Wani iri yaji jin muryarta yayi tsaye itakuma tashiga cikin zauren gidan ya bita zalalo zalalo kamar rakumi da akala. 


Har cikin zauren babban zaure ne dan already har an ajiye sit din roba biyu tai tsaye ta juyo sannan yakaraso tana nuna masa kujera tace" bismilla "


Ya haye ita kuma tasa gefen gyalenta ta share wata zufa data tsiyayomata ganin kafafunsa Sun dan baud'e kadan, 


jiki sanyaye taja kujera ta zauna ta dukar da kai sam bata kaunar ganinsa, beyi mata ba, mi zatayi da baki?dogo kamar ba samude sam baze yiwuba. 


Tunanin ta yakatse ne da yafara magana voice dinsa na vibrate saboda yadda yake jin tsoro yace "sannu malama faseelat, Da farko de sunana khalil shekaruna 35 ina teaching a all brighters academic, Hjy ta ta umarce ni nazo naganki mu dedeta ina fatan zamu fahimci juna ni da ke "


wata iriyar murya ce dashi gatanan de, ita kuma faseelat tana son miji me siririyar murya shi ko gata de, kamar wadda aka mara tashiga jijjiga kai, shiru ne ya biyo baya can ta tuna bata kawo masa drinks ba, ta tashi ta kawo masa dudu milk ta tsiyaya a cup ta mika masa, yayi kurba daya ya ajiye shiru beda abin fadi kanta na kasa amma duk dagowar da zatayi seta ga ita yake kallo, 


Can zuwa yayi karfin halin cewa "kibani no din wayarki "


Faseelat gabanta na faduwa tana inda inda tace "ni banda waya"


yayi shiru can yace" ba damuwa inafatan nasamu karbuwa? "


tai shiru can zuwa ta daga kai 


Yace "Alhamdullilah se na sake dawowa ko? "


Haushi ya kashe faseelat se tambaya yake kamar tsohon makaho ta dago tace "ihhhhhh"


Aiko yayi shiru ya tashi tsaye"ni nawuce "


Afili tace "tow agaida Hjy, a Zuci tace agayas "


yajuya yafita daga zauren takara bin bayanshi da kallo kuttt se yanzu ta lura rigarshi ta wuce gwiwa tsabar tsawo 


Ta kai minty 5 zaune sannn ta tashi tai cikin gida, 


Shiko Karon farko da yafara fira da mace dadi kawai yakeji yanda ya sameta ya tada babur dinshi yayi gida. 


Faseelat nashiga cikin gida da sallama ummi ta amsa, zuwa tai zata wuce ummi tashiga daki ta kwanta ko ta samu ta dawo dede, 


ummi tana kallonta tace "zo nan faseelat"


Tana daga kafa daya kan daya kamar wadda kafar taiwa dayi tazo gun ummi ta zauna, 


Ummi tace "ya kukayi"


Faseelat ta sosa kai tare da cewa "naam"

ummi ta harareta tace "eh "

Sosa kai faseelat ta fara labbanta na kyarma tace "ummi beyi kama da mijin da nikeson aure ba "

ummi tarika jifanta da mugun kallo can tace "dan ubanki har wani kalar mijin da kikeso kika tsara? wallahi faseelat ki shiga hankalinki tom,"


Faseelat ta zumburo baki gaba "wlh ummi bani sanshi baki ganshiba beda kyau ko kadan "


ummi ta rike haba "faseelat? Dan kina ganinki fara shine zaki ce haka, ke kekikayi kanki haka hala? To kamar yadda kike haka fara shima haka Allah yayishi baki kuma haka yakeson ganinshi "


faseelat ta matso hawaye "Allah ummi ni banisonshi "


ummi tace "rufemin baki kar in mazgeki, dan kinsamu ze temakamiki ma wa yataba cewa yanasonki? Dankawai ze rufa miki asiri? To barikiji wlh inkinga baayi aurennan ba to abbanku ya binciko wani mummunan hali atare dashi ne ko in Allah ya kaddara

Ke ba matarshi bace amma ina tabbatarmiki se anyi bikinnan "


Faseelat ta dora hannu akai "nashiga ukkuna ummi dan Allah ki temakamin "


Ummi tace "temakon da zanmiki knan in aurar dake "


Faseelat tafasa kara tana kuka sosai ummi ko tatashi tabata wuri tace "ai seki tayi "


"wayyo Allah na ni wlh bansonshi "

Hardasu majina saboda kuka sallamar abbansu ne yasa ta gudu wurinshi ta rungume "abba dan Allah banisonshi karku auraminshi "


cikin mamaki yace "share hawayenki diyata "


Tasa hannu ta goge still wasu na biyowa yace "bawanda ze miki auren dole kinaji ki wuce kije ki kwanta "


Faseelat ta wuce sundum sundum ummi tafito daga kitchen "amma de alhaji kasan bazanji kunya nai magana biyu ba nariga na amsa musu yanzu mi kakeso nacema uwarsa ince bata sonshi? "


Abba cikin sanyin murya yace "haba asiya kibi komi sannu mana, wai ma duka Nawa faseelat din take ne? Duka fa yanzu shaekararta biyu da graduate, kibari komi asannu akebinshi ai yau suka fara haduwa may be su dedeta zuwa gaba"


Faseelat dake labe tace "wlh aa banisonshi bazan so sa ba harabada "sede  bawanda yajita dayake ta Shiga daki 


Ummi tace "hmmmm"


Tashige kitchen 


Shiko abba ya shige daki yana girgiza kai, yarasa daliin ummi da ta kagara ta aurar da faseelat. 


faseelat kan gado ta mike tanata sharar kwalla har bacci ya kwasheta. 


shi ko malan mudi da farin ciki ya isa gida, 


Bayan ya shigar da babur dinshi yawuce dasauri dakin Hjyarsu Hjyar na tsefe gashinta da rabi yafara zama furfura ya shiga, Hjy saratu ta dago tana kallon fuskar shi tagane yana cikin farin ciki, 

Ya zauna tare da cewa "Hjy kiniya zabe wlh tayi komi yayi dede, gata da kyau ga iya wanka "

Hjyar tai dariya" marar kunya kawai, aibaka isa aure ba "

Yayi shiru yana dariya "toya ita faseelat yanayinta ta amince? "

yace "eh Hjy "

"to yaushe Zaka koma? Kukara ganawa, kafin atura su kawu "

yace "gobennan Hjy "

Hjy tace "hmmmm Allah ya kaimu, sede dan Allah ka natsu kuma ka rika yimata kyautuka saboda takara sonka sannan kuma ka san maganar da zakurika yi "

Yace "to "

Yakagara gobe tayi



Post a Comment

0 Comments