TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI page 7-8

7⃣


Dedicated to *SIS ZULAIHAT RANO*


Abba na zuwa ummi ta kama faseelat da temakon kaninta abul saboda ko tafiya bata iyayi ga zazzabi ga ciwon mara ga tension abun da yawa, har cikin mota akasakata, babansu yana da mota amma ta kwana biyu sede batayi tsufa can can ba ,yayan abba wanda sunansa salisu suna kiranshi baba babba ummi kuma na kiranshi alhaji babba mutum ne me kirki da arziki duk da de bawani arziki ne me yawa ba amma ba laifi tunda yana da zuciyar temakon yanuwan sa shi yakai su ummi hajji ya siya wa abba mota shine ya dauki nauyin karatun ya umar, kuma a gidansa yake zaune a Niger Republic din da yake shi alhaji salisun shima dan kasuwa ne yana yawan zuwa can shine yayi aure kuma yabar matar a can kasar. 




Shi kuma abba tuni ya dena zuwa Niger din iyakar shi nan gida Nigeria duk da ummi can duk ilahirin dangin ta suke amma alhaji be bari ya zauna a wani gida ba se a gidanshi wannan kenan. 



Asibiti suka kaita da zuwan su aka sa mata ledar ruwa, bayan allurai da aka mata, 


Se bayan laasar ta farka likita ya shigo yana tambayarta mike damunta yanzu, 


Jiki ba kwari tace "ciwon mara da nan "

Ta fada tana nuna setin zuciyarta likitan ya dan kura mata ido ta glass sannan yayi yan rubuce rubuce, 


Ya juya wurin ummi da ke tsaye tanajin duk abinda ke faruwa yace "Hjy ire iren ciwon marannan inba aure akayiwa yaranba zeyi wuya ya barsu, sannan batun ciwon heart din rashin cin abinci ne da isashshen bacci wannan kesa ulcer ke kama mutum wuf daya, se akiyaye duk abinda na fada banda abu me tsami ko yaji ko mai da yawa arika bata abinci akai akai "ya juya bayan ya gama jawabin yana kara kallon faseelat, 


ummi tace "insha Allah zaa kiyaye, kuma ankusa yin bikin ta ma "


Likitan ya Mike tsaye yana gyara ta kaddun hannunshi, shi da har ya fara tunanin ya samu ta ukku, matanshi biyu, ya killace a gida dukansu farare ne tass dan yanada gurin ajiye fararen mata kuma dukansu a asibity suka hadu daya ma kauye take daga amai da gudawa ya aure ta. 

Fita daga dakin yayi yana fadin ,"Allah ya sawwake, "


ko da abba ya dawo hospital din samu yayi an sallame su dan lokacin kusan 6:40 ya biya Bill suka wuce gida. 



Bakin wani pharmacy suka tsaya abba ya Shiga ya siyo magungunan da aka rubuta musu sannan suka wuce .


suna isa ummi takama faseelat suka fito har zuwa dakin ta ta kwantar daita malt da milk ta hado mata tasha tasha magunguna ta kwanta baadade ba bacci ya dauketa. 


Can ana kiran sallan ishai se ga Hjy saratu kamar daga sama tana sallama ummi da fitowar ta wanka kenan ta amsa tana mata marhaba Hjy saratu ta shiga ummi tai mata iso har daki, 


bayan sun gaisa take tambayar ummi ya me jiki? 


ummi tace "dasauki dazunnan ma aka sallamomu daga asibity dan seda suka saka mata ruwa"


Hjy saratu tace "Abu beyi dadi ba Allah ya sawwake ya bata lpy ai tundazun naso zuwa se kuma na makara wajen fitar diyar kanwata ta haihu shine muka tafi suna tundazu inata so na taho se yanzu Allah yayi ina rokon Allah yabata lpy "


Ummi tace "amin"



Hiya saratu tace "tunda Khalil ya koma naga ne ba lpya ba dan kamar kwai ya fashe masa a ciki haka yayi "


Ummi tai dariya "khalil kenan ai dazun da yazo ya cika faseelat da abun arziki harda su waya a cikin kayan, Allah de ya kara budi na alheri "


Hjy saratu tace "amin amin,bari naje na dubata na wuce gida"


Suka mike suka fita zuwa dakin da faseelat ke kwance, 

Har lokacin tana bacci ummi tace "bata tashiba kila cikin drugs da aka bata akwai na saka bacci ciki "


Hjy tace "to ni zanwuce Allah ya kara bada lpy "


Ummi tace "amin "


Ta na mata tattaki zuwa bakin kofa seda suka kai can ummi ta dawo ta shige daki ta'ida shiryawa, sannan tafito. 



Ana gama isha'i duk suka hallara ummi takawo masu babbar cooler datake zuba musu abinci se plates da spoons suko sunbaje akan tabarma, kowa ya dibi nashi suka fara ci, Mubarak yace "ummi ni de nakoshi tunda yaya bata lpya"


Ummi tace "haba dan auta na, ka daure kaci ga faseelat can tana cin Nata itama "


Yace "dagasske ummi? "


Tace "eh kai sauri ka gama cika cikin ka se kaje wurinta yace to "yafara buga loma. 



Su ummi basu dade da barin dakin ba tafarka ba laifi massaran ta sauka tun asibity ciwon ma ya lafa, sede ciwon da zuciyarta ke mata, baa jima ba taji wayarta na vibrate taja dogon tsoki kamar ba marar lpya ba afili tace "dan wahala"


Hjy saratu na'isa gida take bawa khalil labari tace "ashe haka faseelat ke jin jiki ?umminsu tace dazun har seda aka kwantar dasu asibity"


Yace "Hjy suna asibitin yanzu? "


Tace "a, a an sallamo su agida na samesu "


Ya tashi tsaye daga shi se jallabiya ga zungureriyar casbahar shi yana ja yace "bari na dawo hjy "


Hjy na kallonshi tace "kai dawo nan ina zaka? "


yace "yanzu zan dawo fa hjy gidansu zanje "


Tace "Kai  baka da hankali da zaka je gidansu yanzu? "


Kawai ya juya "sena dawo "ya fice 

Niko nace hjy barshi kinsan dogo dama be cika hankali ba 🤣🙊



Ya fidda babur dinshi yaja akan hanya ya tsaya wata supermarket ya siyi chivita da hollandia da malt da short cake da big biscuits gefen shagon ya siyi fruit irinsu orange, banana da pineapple 


 daya wuce gidansu, lokacin kusan karfe 10pm dan har Sun kulle gida ya yi parking machine dinsa ya fara kwankwasa gidan, 


Be dade da fara kwankwasawa ba ishak ya fito bema sanshi ba hakanan yace masa "inayini "


Khalil yace "lpya lau, ya me jiki? "


ishak yace "dasauki "


Khalil yace "Allah shi kara afuwa, ga wannan ka kai mata "


Ya mika masa ledar ishak ya amsa yace "injiwa? Za a ce?"

Yace "khalil "


ishak ya juya yasaka sakata ya shiga cikin gidan abba da yake zaune shi ma yace "waye ne ?"

Ishak yace "yace khalil ne kuma yabada wannan yace abata "

Abba yace "kai ma ummi tana can wurinta 

Ya juya zuwa dakin ummi kadai ya tadda tana gyara wa faseelat gado ita kuma tana toilet yace "ummi gashi inji khalil yace yana gaida me jiki "

Ummi tace "oh cikin darennan ya taso to kawo "

Ta amsa ta ajiye shi kuma ya fita baa jima ba faseelat tashigo dakin, 

Wajen wardrobe dinta tawuce ta kimtsa kanta sannan ta dawo ta zauna kan bed. 

Ummi tace "ga kayan marmari ankawo me zakisha? "

Faseelat tace "nakoshi ummi ruwan zafi kawai nakeso insha "

Ummi tace "to bari in je inhada miki amma ki tashi ga ayaba nan kici ko kadanne kinsan tana rage menstrual cramps "

Tace "to "

Ta amsa ta bare tana ci tana yamutsa fuska.


8⃣

Dedicated to *ZULAIHAT RANO*


Lokacin da ummi ta dawo har faseelat taci biyu, mika mata tea din ummi tayi tana fadin "bansa sugar ba amma nasa miki citta da yawa saboda tana koro jini da wuri "


Faseelat ta amsa "Nagode ummi "


Ummi ta zauna tana kallon faseelat tace "dazun Hjyarsu khalil tazo kina bacci tana gaidaki da jiki "


Faseelat tai shiru bata ce komi ba, 


Ummi tace "baki tambayi wanda ya kawo miki fruit dinnan ba "


Faseelat ta kurbi tea tace "nayi zaton abba yakawo "


Ummi tace "a, a khalil ne ya kawosu yanzu da darannan "


Kuts-kuts ta zubdo tea din bakinta wani kuma ya sarketa tafara tari, 

Ummi tace "kibi a sannu mana inya miki zafi kibarshi ya huce tukun "


Faseelat ta goge gefen bakinta taajiye copyn tea din tai shiru tana mamakin wane irin mutum ne khalil itade ba sakarmishi fuska take ba sannan bawani sabawa sukai ba ballatana ya dinga yi mata wadannan abubuwan, 


Ummi ta katse mata tunani da cewa "kind ace da miji faseelat alamu duk sun nuna haka yaro me kunya da tarbiyya, duk dade bansan halinsa ba amma ina mai kyakykyawan zato, Dan Allah faseelat ki saki jikinki sosai naga tunda yazo kike ciwo bansaniba ko hakanan kika amsamin amma baki son auren shi "


Faseelat tace "ummi gaskiya na amince ne saboda kawai kiji dadi ba dan inason shi ba "


Ummi tace "ai nangaba zakiso shi "


Faseelat tace "hmmmmm "


ummi tai dariya "kiyi magana mana nasan nangaba ko ance auren hadi akai muku mutane bazasu yarda ba danni nasan nabaki many lessons daga tasowarki zuwa yanzu Wanda ko bankara da komi ba sunisheki zaman gidan miji, kuma kina da komai da zakija hankalin namiji dashi inde har kinmeda hankali mallake namiji baze miki wuya ba ,zaki so shi ki haifa masa yara Kema kizama uwa me koyarwa kamarni"ummi ta'ida maganar da murmushi fuskarta. 


faseelat batace komi ba batasan komi ze faru nan gaba ba amma bata tunanin zataso khalil ko ta so shi bawani so sosai ba, saboda tadan fahimci wasu abubuwa dangane dashi. 


Ummi ta katse shirun da cewa "ga kayanda ya kawo ki dauki abinda kikeso na kaiwa yanuwanki sauran "


Faseelat tace "ni nakoshi ki tafi dasu kawai "


Ummi tace "to ki sha tea din kar yayi sanyi kuma "ta dauki ledar tai waje 


Faseelat ta yi tagumi ji yadda komi ya jagule mata lokaci daya saboda kawai ummi ta kamata tana wankan janaba inda bataganta ba bazata matsa mata haka akan aure ba, faseelat sede taji hawaye Sun zubomata anata abubuwa kamar gobe ne auren why? 


ita tai kanta haka ne haka Allah ya halicceta mata nawa ne irinta? Maza nawa ne Irinta suma haka iyayensu ke matsa masu akan aure ko se ita dantana ya mace tilo gun mahaifiyarta? Ta share hawayenta tana daga kai cikin zuciyarta tace bazan kara zubda hawaye na akan batunnan ba zanyi kokarin hakan. 


(yo anya zata iya?) 



ummi nafita ta kaiwa abba kayan ya gani tace "me zaabaka? "


ya dauki hollandia yace "wannan yayi "


Ta tashi su ishak nata fira abul na gefe yana duba handout ummi ta zauna tsakiyarsu tace "Mubarak kawo wuka"


Ya tashi domin daukowa, 


Abul ya kalli kayan "wai ummi waye ya kawo kayan nan "


Tace "kubakusan antinku aure zatayi ba? "


Ishak yace "wannan kai "


abul yace "yaakayi ne"


Ishak yace "lokacin da na bude gida naganshi tsaye ya bani tsoro dogo ne sosai nazata ma aljani ne "


Ummi ta rumtse masa baki da hannuwanta tace "ubanka so kake ka kara tunzura yayarku"ta juya tana kallon wajen dakinta 


Abul ya kece da dariya ,"ummi kibarshi ya ida mana"


Ummi ta harareshi "kayi dede Allah yayi maka albarka "


daya daga cikin sirrin ummi ko wane laifi zaaimata sede tace Allah yayi albarka bata taba cewa komi fiye da wannan sede harara. 

Mubarak ya dawo da wuka hannunshi yana mita wai wukar can karkashin kwandon wanke wanke ya ganta ummi tace "to me kauda kayan bata lpya se inta tashi tukun "ta yanka kayan marmarin suka fara sha sunayi suna labari. 



Hjy najin motsin mashin din khalil tafito waje seda yayi parking tace "kai dogore seda kaje dinko? "


alhajinsu ya leko tunkan khalil yayi magana "ai gwara da yaje zasu kara ganin yadda take da mahimmanci a wurinshi "


Hjy ta rike haba "ah to yayi ka ganta ko? "


Yayi shiru ya shige daki.like mother like son wajen shegiyar tambayar yaya akayi aka haifi uwarka. 


The following day.......

Post a Comment

0 Comments