TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI page 9-10

 RAGON MIJI 


9⃣


Ta kama ran Friday salla day awurinmu musulmai, bayan ya dawo daga masallaci da asuba ya shiga ya gaida Hjy ta amsa ciki -ciki yace "Hjy lpya? Ko nayi miki wani abu ne? "


tai shiru ya kara memetawa 


Tace "da Allah tashi kaban wuri "


"Hjy dan Allah kiyi hakuri innayi miki laifi bada sani naba "


"bakasan laifin da kayi ba kenan? Jiya ban hana ka zuwa gidannan ba da daddare amma seda kaje, tunda kaje kaga yarinyar nan shikenan ba saura ba kingi duk ka zauce, aka gaya maka haka akeyi ? ko dama can kana santa bansaniba?"


Maganganun hjy sun matukar bashi mamaki yace "haba Hjy kefa kikayi wannan hadin ni ina zan santa ma bare na so ta, kuma ni wlh hjy banga wani abinda nikeyi ba dede ba, jiya kuma Banyi tunanin tafiya ta zata bata miki rai ba, kiyi hakuri "


Tace "to naji why kake ta kashe kudi har haka danna ce kai mata kyauta aiba cewa nai kaita kashe kudi ba .


Shiru yayi kanshi duke tambayar kanshi yake mi yasamu Hjyarsu. 


can zuwa yace " bawani kudi bane fa sosai waya kawai na siyo mata se cosmetics that's all "


Ta Harare shi "eh ba kudi bane masu yawa tashi kaban wuri, ai gwara ayi ai auren ko kasamu kanka, ni wlh dama kauye naje nasamo maka yar yarinya"


ya tashi tsaye ya shafi sumar kanshi can zuwa yace "Allah yabaki hakuri "ya fita 


Tace "amin"


Khalil kusan Karo sukayi da alhaji yayi saurin zukunnawa gaida shi alhaji ya amsa ya wuce ciki. 

Khalil ya tashi ya tafi saboda shirin makaranta .


Alhaji yana shiga yafara wa hjy fada "wato de sararu bazaki bar halinki na banza ba ko? saboda nasan halinki fa shiyasa ban kara aure ba danna san duk wacce na aura kashe ta kadai ke bakiyi, yanzu kuma ga matar danki zaki koma, to kibi Ahankali wlh tun kafin yaronnan ya fahimci manufarki "


komi batace ba ta tabe baki a ranta tace "aini ma bansan haka yake ba nazata ze cigaba da halinsa na rashin son auren. 


7:30 khalil ya fito da shirin shi yau kam yayi kyau wani yadi ne ash color yasa mishi bakar hula da bakin takalmi rigarde tazarce ce da alamu duk haka dinkunansa suke hular ma tayi gaban goshi sosai shima da alama haka yake saka hular shi, ya leka kitchen hjy se diminiya take dan kawai karyayi kalacin danwake ne zatayi amma tai nan tai nan batare da ya damu da rashin hada kalacin ba yace "Hjy natafi "


Tace "Allah ya bada saa "fuskarta ba yabo ba fallasa. 


Ko damuwa beba ya bar gidan se sannan hjy tagama danwaken, 


karfe 9 siyama ta shigo gidan tareda yaranta biyu "Fatima da farida "


hjy saratu tace "oyoyo oyoyo yan albarka "


siyama tana fara'a tace "hjy ina kwananku "


"lpy lau ya jikin kwana biyu da kikai ba lpy kamar kin kwana goma wajen sunan ramla se tambayarki suke "


Tace "eh wlh hjy amma jiya na aika mata da sako kuma Bayan kwana biyu zanje gidan na gano takwara, ai wlh naji jiki hjy danbana iya komi, abdulkadir ke komi har girki "


hjy tace "Allah yasa kaffara ne,"


siyama tace "amin su yaya ana makaranta "


hjy tace "uhm antafi ai yayanki ya kusa zama ango "


siyama na murna tace "dan Allah Hjy wacece yarinyar "


Hjy saratu tace "eh ba wata bace se faseelat "


Siyama tana murna tace "faseelat de wadda nasani Hjy? "


"itafa "


siyama tace "gaskiya naji dadi hjy Allah yasa alheri ai faseelat full option ce komi yaji, tana dariya tace "finally yaya zaayi aure "


Hjy tai dariya siyama ta mike tsaye "Hjy mi zaa dafa muku yau ?"


Hjy tace "komi kikayi yau de jumaa komiye de da miya zaki "


"ayi taliya da miya NE? "


Hjy tace "a, a kide yi shinkafa kinsan khalil beson taliya gwarama in anyita da safe shima se anci saa kawai kiyi shinkafar se ki dafa masa wake, dan kinsan shinkafar ma baya sonta ita kadai "


Tace "to "tai hanyar kitchen. 




Khalil ko school ya wuce ,jss classes yake koyarwa duk jiki mace yake komi maganganun hjy nata mashi yawo yanata kara nazarin su,, ga rashin lpyar faseelat data dameshi. 


12:30 aka tashi saboda sallan jumaa direct supervision store yawuce ya siyi su peak milk , bournvita,cornflakes,block sugar, golden moon da tea bag, da different sweet , kusa da wurin akwai oasis bakery ya saye big bottle ice cream da snacks ya nufi gidansu faseelat .



yana isa yayi dede da dawowar Mubarak daga school , Mubarak se kallonshi yake, khalil ya jawo shi "abokina zo mugaisa "


Mubarak de yayi tsaye yana kallonshi khalil hannunshi ya kamo yasaka a nashi yace "ummi na gida?"


Mubarak ya daga kai 


Yace "yayar ku fa ya jikinta "


Mubarak yace "dasauki dan dazun naganta tafito zatai shara ummi ta hanata "


Yace "good kaje kafadawa ummi cewa khalil yazo yana so ze shigo ya gaidata "


Mubarak yace "to"

ya shige gida seda yafara shiga dakinsu ya ajiye jikkarsa sannan yaje ya fadawa ummi, ummi tarike baki "Allah sarki yaron kirki ,jeka ce ya shigo "har ya tafi tace "Mubarak dawo jirani "


tashige dakin faseelat, faseelat taji sauki sosai dan wayar da yabata tasaka wa tsohon sim dinta, tai checking balance babu kudi ciki tanayin Wanda ya kawo taga 1000 ta tabe baki ta siye data tayi download what's up tai installing messages sunata shigowa ummi tashigo ,"ke ki tashi ki kimtsa ga khalil nan shigowa "


faseelat tace "khalil ?"tana zaro ido 


Ummi tace "eh ki tashi gashinan shigowa "ta juya Tabar dakin faseelat tace "mtssww shikenan fa khalil khalil maganar kenan ta kalli riga da wandon dake jikinta fakistan tace "ni shirye nake danban kara irin gayunnan saboda shi "


Ummi nafita tace yashigo tashige daki ta sako hijab. 


Tare da Mubarak suka shigo yana dauke da katuwar bakko, 

Har bakin dakin ummi yayi sallama ummi ta amsa tace "maraba ka shigo "


ya dan sunkuya dukda tsayin kofar ya shiga memakon ya zauna kan kujera ya xube kasa, a sannu ummi ta saci kallonshi tace "kambuu da wannan ne faseelat ke kushewa ina laifinsa yanda mazannan sukayi tsada, 


Ummi tace "a, a katashi kazauna saman kujera "tana sunkuyar da kai na surukai, 


Yace "ina yini, "batare da yakoma ma waccan maganar ba. 


Ummi ta amsa akunyace yace "ya me jiki? "


Ummi tace "dasauki "


yace "Allah shi bata lpy dama zuwa nai nagaisheku"kanshi a kasa shima kunyar yakeji 


Ummi tace " amin angode kwarai "


Dama da shigowar shi ya jingina bakkon jikin cushion hannunshi ya cusa cikin aljihu ya zaro kudi a kalla sunkai 10 ya ajiye sannan yace"ni zanwuce "


Ummi tace "to angode bari na kira maka faseelat din "

Bece komi ba ummi tafita Mubarak de na zaune ummi nashiga tacewa faseelat "ki tashi ki shiga ku gaisa "


faseelat da tunda taji sallamar shi taji zazzabi ya fara rufeta ta tashi tafita kamar me koyon tafiya, 


Ummi tace "yar rainin hankali har ciwon ya dawo ko "


Faseelat ta shiga da sallama bakinta, wani sanyi ya mamaye zuciyar khalil ya dago kananun idanunsa ya zuba mata, kallo daya ta masa ta samu kujera ta zauna. 


Yace "inawuni malama faseelat,"faseelat ta kalli zungure riyar hijab din dake jikinta tai shiru, 

yanata kallonta yace "ya jiki?"


ta lumshe ido ta bude tace "naji sauki ai "


Yace "da sauki zaki ce de, tunda baki warware ba "


Tai shiru 


Yace "to Allah yasa kaffarane "


Tace "amin "kasa-kasa 


Ta dago ta saci kallonshi Sukai 4 eyes seda gabanta ya fadi ta rasa wane irin kallo yake mata, shiko kallon luv ne yakeyi, to da yake de sabon shiga ne se kallon yayi kama da kallon ruruwa🤦🏻‍♀Inajin harda kallon luv se kun koya mishi 🤣


Faseelat ta kauda kai sannan ta dago ta kara kallonshi lokacin ya dauke ido yana magana da Mubarak harda kudi ya bashi, wannan ya bata damar kallon dressing nashi a zuciyarta tace not bad, 


Ya mike tsaye yana jifanta da wannan kallon yace "ni zanwuce "


tafara wasa da hannunta,


yace "ba bankwana?"


Tai shiru yace "to natafi amma plss ki rika daukar kira na i have called you several times but you don't pick my calls why? "


Faseelat seda murmushi ya  kufce mata saboda jindadi atleast de yana iya kwantar da murya wajen pleading kuma ya iya turanci daya daga cikin abunda take so wajen mijinta. 


akan idonsa tai murmushin wani farinciki ya mamaye shi ganin smile a fuskar ta, 


Yace "I'm pleading I hope you will accept my request "


kawai ta girgiza kai dariya tazo kufcemata ta jawo hijabinta ta rufe fuskarta. 

yayi dariya yafita ummi bata waje danhaka yawuce har kofar gida Mubarak ya rakashi khalil nata masa labarai,. 


Yana wucewa Mubarak ya shigo gidan dede fitowar faseelat daga dakin taci dariyarta se kuma daga karshe ta dinga buga tsoki, 


sukayi kicibus da ummi. 


Mubarak yace "gaskiya ummi yana da kirki sosai jibi kudinda ya bani "ya fiddo yan 200 guda biyar da yabashi sabbi fill 


Ummi batabi kan maganar shi ba hankalin ta na kan faseelat daketa murmushi ummi tace "wai lpya kike ta dariya ke daya "


Faseelat ta daure fuska "bakomi "tashige daki da sauri 


Ummi tace "hmmm Allah ya shirya ki "


Ta Shiga dakinta, tana zare hijabin jikinta ta jawo bakkon ta bude kaya niki -niki, ta fiddo Ice cream da snacks din ta ajiye gefe guda, 


Kudin da ya ajiye ta kirga nera dubu goma ciff ummi tai murmushi ta jawo wayarta tace "bari na kira hjy saratu nai mata godiya "

RAGON MIJI



🔟





Ringing biyu Hjy saratu ta daga bayan  gaishe gaishe ummi tace "yanzu khalil ya fita yashigo har gida mungaisa, mun gode da abun arziki "


Hjy saratu tana ta faraa kamar duka knan tace "ah bakomi wlh ai anzama miye aciki "


Sukai bankwana ummi Nata godiya sede bata fada mata yakawo wani abu ba Hjy saratu tace "hmmm yanzu haka wani abun ya kai musu, kowa na haramar tafiya masallaci shi yanata surukai," taja dogon numfashi "nasan abinda zanyi komi zezo karshe "


Shi ko khalil masallaci ya wuce daga gidansu faseelat, hankali kwance, gabadaya jiyake kamar bashi ba, soyayya ta fara sauya masa rayuwa. 


Faseelat kau seda ta shiga daki ta kara jan tsaki "komiye na mishi dariya ma?  Nan fa se yayi tunanin tafara sonshi ne "ta kara jan tsoki, 


Ta jawo wayarta messages sungama shigowa abinda ta lura groups dinta Sun ragu dama inka dade baka online groups fita suke, bin groups din tafara yi taga wadanda suka fitar daita, 


Taga kusan group bakwai ta fita, se tafara bin numbers dinta tayi wa friend dinta magana a medata wasu ,akwai wani group sirrin mu mata, shi ta fara shiga saboda tanajin dadin group din, messages din wasu Sun bude wasu basu bude ba, tatura sallama ,suka amsa tace "plss masu group suyi adding dina ko abada number ta asani nadade bani online ne "


Se akafara mata reply da welcome masu turo sticker na turowa, wata me suna maman amira tace akwai wani group amma se kinbiya 500 ake adding naki ana karuwa sosai ciki,


faseelat tace "anayin share and self? "


Maman amira ta turo mata "eh anayi,  Ko kati ko BTU ko transfer "


Faseelat tace "kiban no din admin zantura mishi through share and self saboda banda kudi "


maman amira tace "ayya zan biyamiki asaki ki dan jira "


Faseelat tace "amma de Nagode aunty Allah yaraya amira "


maman amira ta turo mata smile face. 




daganan faseelat tai taganin new groups na matan aure wasu na novels ana sakata, 



Seta bi maman amira PC tana mata godiya maman amira tace karkidamu sister sunanki kawai ya burgeni ,faseelat tace zan'iya adding number dinki? 


maman amira tace"yes zakiiya nima zanyi adding taki "


Faseelat ta tura mata thanks you" (the Fateful relationship just begun) 


Ko minti 10 baaiba akayi adding nata ta tura" slm "


Maman amira taturo "you are highly welcome friend "


Faseelat tace "I'm grateful "


Fitowa tai a group din tafara bin status daya bayan daya sannan ta sauka online,


fitsari ne ya matseta ta tashi tafita waje dasauri, 


Ummi tagani tafito daga kitchen hiyaki ya korota, tai sauri tashige toilet ta biya bukata ta dawo, ta tafi gun ummi "ummi for god sake miyasa kikeson wahalar da kanki nace naji sauki kibari nayi "


ummi tace "ai gwara narinka shiga ciki ko na saba tunda tafiya zaki kibarni ni daya "


Faseelat tace "eh naji amma bari nashiga inbani nan kyayi din "

Ta kutsa kai kitchen din duk da hiyakinsa inda sabo ta saba .


Hjy saratu kau alhaji ta dannawa kira, bayan ya amsa yace "lpy de ko kira gab Shiga salla "


Tace "eh dama so nike ince maka inason zamuyi magana inka dawo "


yace "To saurin mi akeyi da antaso masallaci zanshigo gidan "

Ko to batace ba ta yanke kiran, 


Siyama ta fito daga kitchen tana kai abinci daki har ta gama sannan ta zauna tana "wash Allah na "


Hjy ta kure ta da ido tace "wannan dan aikin? To ko de ciki gareki "

Siyama tai murmushi batare da tace komi ba, 


Hjy tai dariya "to Allah ya raba lpy "


Siyama tai tsit can tace "bari naje nai salla "


Hjy tace "har lokaci yayi ne "


Tace "eh karfe 1:40pm"


Hjy tace "bari mutashi muma "



Ana saukowa masallaci alhaji ya taho gida yana shiga da sallama bakinsa yaran siyama suka gudu suka tarboshi ya tallabo kawunansu sukayi ciki, yanata jindadi, 


Dakinshi ya wuce kai tsaye ya rage kayan jikinshi ya dan kishingida sega siyama takawo masa abincinsa suka gaisa ya mata ya jiki ta fita tareda yaran. 


Yana tsakiyar cin abinci Hjy tashigo ta zauna sannan tace "sannu da zuwa "


yace "yawwa yana Kai loma bakinsa "


yace "wai maganar mi cece da baajira na dawo "


Tace "dama bawata magana bace seta khalil da faseelat "


Ya ajiye cokalin hannunsa yace "inajinki"


Tace "nace mi zaihana akai kudin neman aurensu tunda de akwai su, bayan ansa rana se su cigaba da fahimtar juna kafin auren, nasan shima khalil din zeso hakan."


yadanyi nazari for some minutes sannan yace "yanzu de kifara yiwa mamanta maganar duk yadda kukai se inji saboda kamar abun yayi wuri "


Tace "haba bawani matsala amma bari na kirata "


ta kwalawa siyama kira tace mata ta miko mata wayarta, takawo mata ta juya. 



hjy tayi dialing number ummi 


Tadanyi ringing sannan ummi ta dauka da sallama, 


Hjy tace "kinga na sake kira ko,dama maganar yarannan ce to munyi magana da alhaji kiyi magana da abbansu in anbada izini zaaturo "


Ummi tace "to ba matsala nasan yanakan hanyar dawowa Inya dawo zamuyi maganar duk yadda mukayi zakiji "


Hjy tace "to Nagode kwarai se na jiki "

Ta yanke kiran 


Alhaji bece komi ba ya cigaba da cin abincinsa.


Khalil siyama nafita ya shigo tafara zaulayar shi, yana dariya yace "siyama bakiji ni kuma ake zolaya? Ni yayan. "


Tace "hmm yaya kenan ,yanzu de kabar number anty ta mufara gaisawa "


yace "zanbaki amma ba yanzu ba, kije ki daukomun abinci na tukun inna gama se muyi maganar "


Ta kawo masa abincin yafara ci dan mutuminnaku be wasa da k'oto. 



Seda ummi tabari abba yagama cika cikinsa da daddadan abincin da faseelat ta dafa sannan tafada mishi yadda akai yace "kunde nace ga hadin nan auren hadi matsala ne dashi in aka samu sabani, "


Ummi tace "insha Allah bawata matsala"


Yace "to yanzu de su bamu lokaci kamar nanda sati daya, dan inaso nayi bincike, bama wannan ba ita faseelat din ta amince ne? "


Ummi tace "eh mana ko akirata ka tambayeta? "


Yace "eh kiramin ita "


Ummi tatashi ta fita kiranta daga can bata dawo dakinba, 


Faseelat ta zauna "gani abba"


ya kalleta sannan yace "kinji iyayen khalil zasu aiko me kikace? "


Faseelat gabanta ba karamin faduwa yayi ba tai shiru ta sadda kai kasa, 


Abba yace "kin amince? Yanzu kina sonshin? "


Kuka ne yazowa faseelat tai saurin rufe fuskarta da hijabin jikinta, 


Abba yayi tunanin ko kunya ce yace "to tashi kije? "


Ta tashi da gudu tashiga dakinta ta fara kuka me cin rai.

Post a Comment

0 Comments