TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI PAGE 49

 4⃣9⃣




*dedicated to those lovable group's*👇🏾


*RAGGON MIJI FANS*

*RAGGON MIJI FANS 2*

*RAGGON MIJI FANS 3*

*UMMYN YUSRAH NOVELS GROUP*

*MUKARU DA JUNA BY MOMYN SAUBAN*

*NOVELS ZAFAFA BY DR FATEE*

*MY FORUM GOLDEN PEN WRITERS ASSOCIATION*

*MOMMY'S NOVELS GROUP BY SHALELE*


*THIS PAGE IS ALL YOURS FRIEND'S ACIGABA DA COMMENTS KAWAI*⛹🏻‍♀




*MANZON ALLAH (S. A. W) YACE :-lalle Allah ya rubuta kishi akan mata, da jihadi akan maza wadda tai hakuri acikinsu tana da lada kwatankwacin wanda yayi shahada.*




Yanajin wani irin ciwo a zuciyarshi, jintana ta kuka ya dagota yafara duba jikinta duk yayi ja abunka da farar fata ga gashinta duk Aisha ta yamutse shi cikin jin tausayi yakara rungumeta yana shafa bayanta, 


Kwata kwata kuka yaki zuwa ma aisha tazuba mishi ido tana ta kallonshi ganin yadda ya kwakume faseelat kamar ze medata ciki yasa ta sauke hannuwa daga kumatunta tai hanyar kitchen da gudu ko seconds goma baaiba ta fito da sharbebiyar wuka ahannu tai kukan kura zata sokawa faseelat a baya, fahad yayi sauri ya rike kaifin, 


Aisha tafara jujjuya wukar tanaso ta kwace ta sokawa faseelat shi kuma ya rike kuma still yana rungume da faseelat daketa kuka, 


Dandanan jini yafara diga Kasa kan farar hijab din faseelat, ganin jininshi yana zuba amma yaki sakin wukar Aisha ta saki wukar ta dora hannuwa biyu akunne ta kwara baki ta saki kuka tai saman bene da gudun tsiya, 


Fahad ya Saki wukar tafadi kasa ya bude tafin hannunshi yana kallon yankan da ke jiki, 


Faseelat ta zare jikinta tana kallonshi cikin tausayi ta duka ta dauki kallabinta dinta ta kama hannun fahad tana nannada mishi tana kuka, shi ko kallon fuskarta kawai yake yana ganin wautar ta na zuwa gidan a yanzu, 


Suna haka aisha tafito tana kuka sabe da amira awuya tafita tabar gidan, duk sukabita da ido, 


Seda tafita faseelat ta medo kallonta gareshi tana sheshsheka tace "I'm sorry bansan haka anty take ba nazata zata saurareni ne dana sani banzo ba "


Ya riko fuskarta da hannu biyu yana kallon cikin idanunta yace "aisha zata iyayin fin haka, karki sake irin gangancinnan cutie yanzu da bani nanfa? Wlh aisha har kashe ki tana iyayi saboda gabadaya ta haukace,"


Ya riko jikinta "jibo yadda taimiki da jiki"


Faseelat takara zubo da hawaye dan ta jibgu ba karya ,


Ta riko hannunshi tana fadin "it's hurting ko? "ta kalleshi cikin jin tausayi, 


Ya rungumota jikinshi yana kwantar mata da gashin kanta yace "it's not idan nahadashi da zafin dukanki da Aisha tayi "


ta kwantar da kai kan kafadarshi tana hawaye, 

Yana ta shafa gashin kanta tai breaking hug din tace "zan tafi gida "


Ya jawo hijab dinta da take dauke da drops na jininshi yasaka mata, sannan ya kalli jikinshi daga shi se boxer ya dago ido yace "bari na dauko key na kaiki "


Ya juya ya haye bene few minutes ya dawo cikin jallabiya da keys a hannu ya kamo hannunta suka fito daga cikin gidan ya bude mata motor ta shiga ya zagaya yaja sukabar gidan ,shide baba tsoho yanata kallon ikon Allah yadda yaketa ganin Aisha na ficewa da kuka yasan akwai matsala, 



Suna kan hanya yana tuki da hannu daya hannunshi daya kan cinyar faseelat, tunda suka fito take ta kara zubda hawaye, 


Ya kalleta ya meda kai kan titi yace "kiyi hakuri cutie ki dena kuka ,Aisha bata isa ta hanani aurenki ba inasonki sosai fiyeda yadda zaki harsaso, ki kwantar da hankalinki aisha zata sauko insha Allah "


Faseelat zuciyarta zafi kawai take yadda Aisha ta wulakantata ga zafin yankan da taiwa fahad da takeji kamar ita akaiwa, 

Ta Kalli hannunshi dake kan cinyarta 

Tasa hannu ta rufe fuska jin kukan da ya taho mata tafarayi tana jan numfashi, 



Fahad ya dauke hannun daga kanta ya shafi kanshi zuwa sajenshi ya fitar da iska me zafi daga cikin bakinshi gabadaya Sun caza mishi kai yace "cutie ya kikeso nayi ne? Yanzu kina ganin zan bari kitafi gida kina kukannan? Kiyi hakuri plsss"


Ta daga kai ta jawo hijab dinta tafara share hawayen dake zubomata tana sharewa wasu na zubowa, 


Ya girgixa kai ,har suka kawo kofar gidansu, Ta bude zata fita yace "kode nakaiki asibity ne ko akwai inda ke miki ciwo? "


ta girgiza kai cikin muryar kuka tace "thank you "ta bude tafita ta shiga gida dasauri, 


Yakara murmuxa gashin kanshi kanshi na zafi sannan ya tada motar ya nufi gidan mommy, 


Faseelat dasauri ta shiga gida ummi da tundazun ta duba bataga faseelat ba ta ga wulgin faseelat dasauri tafito daga dakin abban tabi bayan faseelat da kallo kayan jikinta a cumumuye ga jini saman kan hijab din zuwa kasan hijab din, 


Hankalinta ya tashi tabi bayan faseelat, lokacin faseelat ta yaye hijab din tahaye can karshen gado ta hade kai da gwiwa tana kuka, 


Ummi ta shigo dakin tana kallon gashin kanta cumimiye tace "kee daga ina kike "


Faseelat ta dago tana raba ido tafara nazarin me zatacewa ummi, 


ummi tace "dan ubanki ba magana nake miki ba? "


Faseelat ta fara yarfa hannuwa tana kuka, 


cikin zafin rai ummi ta haye kan gadon ta shakarota cikin tsawa take cewa "bazaki fadamin ba ne dan ubanki daga ina kike? "



Abba yafito daga daki jin kakari da fadan ummi yayi sauri ya shiga dakin ummi ganin ta shakare faseelat yayi sauri ya je ya janye faseelat din yana kallon ummi yace "haba asiya kibari mana aibata haka zaki tambaye ta ina tajeba "


Ummi tace "alhaji yarinyarnan harta san takwasa taje wurin saurayi? Yaga ma tumurmusarta ta dawo tana kuka, jibi hijab dinta "ummi tajawo hijab din tana nunamasa tace "duk jinine jiki wlh faseelat ta iskance tunda har taiya bashi kanta kafin aure "


Faseelat ta dago tana zare ido jin abinda ummi ke cewa, 


abba cikin mutuwar jiki yakebin faseelat da kallo duk ta harmutse, 


ummi tace "nikam nagaji alhaji dan Allah kasamu yaronnan kace ya turo tunkan ta jawo mana abun kunya"


Abba bece komi ba yabar dakin ummi tazo zata kawowa faseelat bugu faseelat ta kauce tana zare ido tace "wlh ummi banyi komi ba, naje bawa anti hakuri ne, shine ta yankeshi a hannu amma wlh baai komi ba "



Ummi cikin rashin yarda tace "gafara can da Allah ni zakiwa karya, ko ni makauniya ce? ke kikasani dan wlh ko aurenki yayi bazaki wata daraja ba sakarai kawai yo miki so hauka ne da zaki je kibashi kanki, kin kyautawa kanki ai "



Fuuu tabar dakin faseelat ta fashe da kuka ta jawo pillow ta danne kanta dashi ta cigaba dayi, 




ummi nafita bataga abba ba har yabar gidan takoma dakinta ta buga tagumi zuciyarta na zafi, tundazu maganar da sukeyi da abba akan faseelat ne don yaji abinda yafaru jiya Sunata neman mafita sega sabuwa ta billo, 



Aisha nashiga cikin gida takara sakin kuwwa da mommy dasu ramlat sukayo waje, sadiya tai sauri ta amshi amira daga hannunta, 


Aisha ta rungume mommy tana kuka, 


Mommy tace "wato Aisha bazaki bi shawarata ba ko? Yanzu mi yakawoki da safennan?"


Aisha na kuka tace "faseelat dince wai tazo bani hakuri shine nahauta da duka ina cikin dukanta shine yazo ya mareni shine na dauko wuka zan soka mata shine yarike da hannunshi duk yaji ciwo ahannun "


Hjy tace "wato de bakijin magana ta kenan ko? yanzu da kin kasheta fa? Kema ba barinki zaaiba, nace kiyi hakuri kibar lura da abubuwansu kinki, inaji miki tsoron ya sake ki dan masu irin wannan haukan da saki suke karewa, kinga shikenan se ita wasila take kowa tasami yadda take so"


Aisha tace "wlh bataisa ta rabani dashi ba "ta cigaba da kuka, 


Ramlat dake gefe tace "kinyi dede anty gwara da kika ci ubanta da kyau "


Mommy ta banka mata harara tace "tashi kiban wuri "


Ramlat tatashi tabar wurin dama sadiya bata zauna wurinba tunda ta amshi amira ta wuce daita ciki ta kimtsata, 


Mommy ta medo hankalinta kan Aisha taja ta tazaunar daita kan cushion tace "haba Aisha inafada miki abinda yakamata kiyi kina kaucewa, kiyi hakuri kibari ayi auren karkimanta fahad a tafin hannuna yake ya daukeni tamkar uwa, ba abinda waccan zata fiki awurinshi inde zakibi shawarata "


Aisha takara saka kuka mommy nata ban baki amma taki denawa, 


Seda fahad yafara zuwa hospital akai mishi dressing sannan ya taho gidan mommy, 


Yana shigowa ya gansu main pallow yaude fuskar mommy ba walwala dan taji zafi da ya mari diyarta akan wata, 


Yazo ya zauna gefen kujera Aisha ta dago ido tana kallon hanninshi da bandage ta cigaba da kuka kanta kan cinyar mommy, 



fahad yace "Aisha kiyi hakuri kizo mutafi gida banso na dakekiba "



Aisha batace komi ba mommy na kallonshi tace "inaganin kabarta anan ta danyi kwana biyu tadan samu natsuwa sannan se ta koma don naga duk tafita hayyacinta, kayi hakuri daita da duk abinda zatayi anan gaba, nide namata duk nasihata taki ji "


Fahad gabanshi ya fadi don be tunanin zeiya 2days batare da matarshi ba wannan nema yasa yake tafiya daita duk inda zashi, 



Cikin rarrashi yace "Aisha kiyi hakuri mukoma gida, kinsan bazan iya kwana nikadaiba "


Ta dago fuska ta watsa mishi harara ta meda kai kan cinyar mommy, 



Mommy ta canza maganar tace "dama inadawowa daga gidan kawunku se gata ai naso nakiraka tazo ta hargitsamin lissafi, naje nasameshi munyi magana yace kaje kuyi maganar kasameshi a office "


Aisha tatashi ta haye bene dagudu jin abinda mommy tace 


Fahad Yace "Nagode mommy bari naje nasameshi "


Ya tashi yafita yaja motar zuwa gidan kawunshi rabiu, 



Yana fita mommy taja tsoki, tace "dole fa intashi tsaye kar abinda na raina yazo yafi Karfina "




Fahad har cikin office din alhaji rabiu ya shiga ya zauna suka gaisa alhaji rabiu yace "danbaba mommynka tazo mun da maganar kanaso ka kara aure, naji dadi sosai ka girma kazama babban mutum ai karin aure sunna ce kuma mutum nakara girma,sede bata fadamin gidansu yarinyar ba nace ta turoka muyi maganar"


fahad yayi murmushi yace "Daddy sunanta faseelat gidansu a kofar durbi yake bazawara ce babanta sunanshi alhaji maaruf "


Alhaji rabiu yayi dariya yace "ai zawarawannan ma sunfi hankali da dadin shaani yanzu yaushe ka ke ganin zanje na musu maganar mommynka tace bataso bikin yafi wata amma inaso naji ta bakinka "


Fahad yayi dariya yasan kawunshi dama da barkwanci yace "yau nikeso inde akwai damar hakan, kuma su zasu zabi tym sede banson komi daga garesu kuma inaso ayi komi kamar auren budurwa "


alhaji yayi dariyar manya yace "to maganar kudi fa? "


fahad yace "zan rubuta maka chek kaje kacire yanzu de kafara zuwa tukun, anjima zan kawomaka kudin "



Alhaji yace "to yayi Danbaba Allah yasa ayi damu "


Fahad yace "amin se nazo anjiman ya tashi yafita "




Shiko abba gidan baba babba yawuce dan suyi shawara dan bayayin komi seda shawarar shi, 



bayan an mashi iso ya shiga alhaji yace "lpya kake naganka somehow kamar kana cikin damuwa "


Abba yace "tunda safe asiya tazo takecemin bataga faseelat ba se yanzunnan gata tadawo jikinta duk jini wai taje wurin yaron sunyi lalata inaga, ni tundazunma muna ciki muna tattaunawa da ita akan batun saboda jiya matar yaran takira ita faseelat taci mata mutunci d daddare har mungama yanke shawarar tirsasata ta rabu dashi sega wannan abun "



baba babba yace "subhanallahi ashsha abu be dadi ba "



abba yace "shine nayi shawarar fadama yaron ya fito amma yakace? "



Baba babba yace "hakane dede ayi mishi magana yafito inda gaske yake, tunda gashi har yayi mata fyade, tunda ai tataba aure this means dakarfi ya kwata "



abba yace "to Allah masani nima abun ya dauremin kai amma tunda tana sonshi zanmasa magana yafito ayi musu auren suje can su cinye kansu tunda da kafarta tabar gida ai "


Baba babba yana jimami yace "Allah ya kyauta "suka cigaba da labari, sannan sukai sallama abba yawuce wurin kasuwancinshi. 


Kafin sha biyu zazzabi da ciwon kai me zafi ya rufe faseelat, ummi Takoma dakin da niyyar takara cin ubanta ta sameta cikin bedshit dukunkune taja tsoki tafita tana ta maganganu ita kadai ta dora bagaruwa da karamfani da dankumasu da ganyen magarya saman wuta ta dahu sosai ta tace ta cika uwar robar wanka takai toilet tazo ta yaye zanin gadon da faseelat ta rufa dashi tace "kitashi ki tube muje nagasa miki jiki in Iskanci dadi ne gobe seki kara zuwa sakarai wadda batasan ciwon kanta ba, "


Faseelat dakyar jikinta yayi tsami ta mike zaune tafara jijjiga kai, zataiwa ummi magana, 


Ummi tace "karki cemin komi anan kitashi ki abinda nace "



faseelat ta sunkuyar da kai cikin tausayin kanta ta tashi ta daura zane tana dafa bango zata fara tafiya ummi ta kamata tajata har cikin toilet ta zame mata zane cikin bacin rai tace wa faseelat ta shiga ciki, 


Faseelat tafara matso kwalla ganin yadda ruwan ke suraci, 


Ummi ta daka mata tsawa jiki na bari ta shige ta zauna ciki tanata cije lebo Tana rumtse ido saboda zafi. 


Bayan 

wani lokaci 

Ummi tajawo karamin towel ta rika tsomashi tana mammatsa wa faseelat jiki tanayi tana mata fada hawayen azaba yarika wankowa daga idon faseelat .



Team faseelat kuje ku fadawa ummi ba abun bane tukunna 😂



Post a Comment

0 Comments