TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

RAGON MIJI PAGE 61

 6⃣1⃣







Wlh nayi nadamar abunda nai maka kai da mahaifinka, kullum cikin dana sani nake, kayi hakuri plsss kadawo gareni wlh duk cikin diyana nafison ka, bansan yadda zangyara kuskuren da na maka ba,amma ka tausayamin  ,na azabtu da rashinka ina bukatar kulawar ka my son.. "ta tsagaita saboda kukan da yazo mata , but she's very surprised yadda ya dauki wayar yatsaya saurare don baya daukar wayarta inma ya dauka da yagane itace yake kashewa duk yayi saving numbers dinta don yarika avoiding kiranta, 


Jikin faseelat kyarma ya dauka jin abinda umma ke cewa jin sautin kukanta hawaye suka zubomata zuciyarta na bugawa da karfi magana takesonyi bakinta yakasa fitar da maganar , 


Jin shiru umma tace"plssss ka yafemin, kayi hakuri nasan nacuce ka "


Hawaye sharrrr suka zubo ma faseelat jin uwace kewa danta kuka begging for his forgiveness, muryarta na rawa tace "ya ...fita... masallaci..."


Sanin Aisha bata shiga lamarin tace "faseelat ce? His bride? "


Faseelat ta shanye kukanta tace "ni...ce umma"hawaye na cigaba da kwaranya a fuskarta 


umma tayi murmushin jindadi wanda har faseelat seda ta jishi,murya a raunane tace "I'm very happy da naga pictures na bikinku, ina tunanin zaki temakamin wurin shawo kan fahad, na mishi laifi babba na wulakantashi nabarsu shi da mahaifinshi saboda son zuciya ,amma nayi nadamar abinda nai masa tunda dadewa, mahaifinshi be bani damar koda ganinshi ba, after his death na kira fahad nayi zarya gidanshi da office dinshi nabashi hakuri Amman he dont even listen to me,na tura malamai da dama gunshi  he didn't look at them, I once come to his wife itama bata saurare ni ba, I don't know what to do, kamar yadda nagani yana sonki sosai dan Allah ina rokonki ki shawomin kanshi ya yafemin tun kafin na bar duniyar "


Faseelat tace "karkice haka umma fahad ze yafemiki ze so ki kamar yadda kowane da yake son mahaifiyarshi kiyi ta masa addua umma Allah ya sanyaya mishi zuciyarshi adduar ki kar babbace, kuma ina rokon karki fushi dashi "


Umma tace "ina ta addua faseelat amma shiru, kuma bana fushi dashi ko kadan don nasan duk ni najawo hakan, Nagode kwarai dagaske "


Faseelat tace "ki kara hakuri umma komai ze zama labari watarana "


Umma tace "Allah yasa Nagode da kika saurareni se anjima "


Ta kashe kiran tana tunani da dama, 


Faseelat har suka gama wayar tana hawaye, jikinta ya mutu murus zuciyarta na cigaba da harbawa, wayar na rike hannunta takasa ajiye ta sanin irin balain da fahad Ke ciki tafasa kuka zuciyarta cunkushe numfashinta har daukewa yake,


Bayan fahad ya dawo masallaci dakin Aisha yawuce ya same su sunata labari da amira, shima ya zauna akai tayi don ya debewa Aisha kewa , karfe biyar da wani abu ya fita ya nufi dakin faseelat, 


Ya tura ya shiga faseelat da har lokacin tana zaune wurin takasa tashi ta juyo idanunta dake jawur ta zuba su akan fahad tarika kallonshi kamar yau tafara ganinshi, 


Abun yabawa fahad tsoro ganin idanuwanta jawur a kumbure ga gashinta dake zube koina gaba da baya, 


Dasauri yaida shiga dakin ya isa wurinta yaje ya zukunna gabanta yana gyara mata gashi da hannu yana kallon fuskarta yace "what's wrong with you? Ehimm? "


Hawaye suka gangarowa faseelat tana meda kukan dake niyyar kufcemata tace "Ankira wayarka "


Fahad ya kalli wayar dake hannunta batare da ya damuba yace "answer me first meke damunki kike kuka "


Kanta a sunkuye ta dago tana kallon kwayar idonshi tace "it's the phone "


Fahad yariga yasan baya wani abun banza da wayar shi atata in zata ga abin tashin hankali befi hotunan Aisha da suke birjik ba wasu ma half-naked, aranshi yayi tunanin ko wani Yakira yafadi wani abun tashin hankali, ya anshi wayar daga hannunta ya shiga call log, number bad woman ce sama kuma sunyi kusan 10mnt suna magana, 


Kafin ma ya dago faseelat tace "it's bad woman"


Fahad ya dago ranshi bace yace "who ask you to pick my call? Miye ruwanki da kiran da akemin da har zaki dauka eyee?"


Faseelat jikinta mace batare da ta bashi amsa ba tace "hero! Kaine kake kiran ummanka bad woman? Umma ce fa wadda ta dauki cikinka wata tara tai nakudar ka tabaka nononta kasha itace kake avoiding kiranta kai watsi daita just because she did a small mistake? " ta ja ajiyar zuciya ta cigaba da cewa "kasan halinda kake ciki kuwa? Haba hero banyi zaton haka daga gareka ba "



Fahad ya mike tsaye yace "don't interfere in this faseelat stay away from this matter, kuma daga yau karki kara daukarmin waya"


Ya juya zebar dakin ranshi bace, 


Faseelat tace "hero mahaifiya ba abar yadda wa bace ba ,kome tayi kuwa, ankarbo daga Abdullahi dan mas ud wani mutum yazo wurin manzon Allah (S. A. W) yace ya manzon Allah man ahakkan nasi bi husni sahabatiy?se maaiki yace mishi ummuka yace summa man? yakara ce mishi ummuka yace summa man?yace abuka "


"Hero yanzu kai ba maganar kyautatawa ma ake ba ka saurare ta ma ka ki baka tsoron fushin Allah? manzon Allah yace yardar Allah na tare da yardar iyaye fushin Allah na tare da fushin iyaye ,hero kar idanka ya rufe ka gaggauta zuwa wurin mahaifiyarka ku dedeta, ayoyi nawa ne a alkurani sukai magana akan yiwa iyaye biyayya saboda mahimmancin yiwa iyaye biyayya awasu wurare da dama daga kadaita Allah se yiwa iyaye biyayya agaba , duba suratul israi daga aya ta 23 da ukku zuwa da 4, suratul ahkaf aya ta 15 zuwa da 17 da suratul...."


Fahad ya daka mata tsawa ta fiddo ido waje tana kallonshi rai bace yace "kimin shiru bana bukatar waazin ki akan wannan matar, ta cuceni ta wulakanta ni saboda son zuciyarta ta rabu dani lokacin da nake bukatar ta har yau kunne na yakanyi ciwo time to time saboda marin da tamin, ita ki naganin tayi abu me kyau kuma ta tursasa mahaifina ya saketa don son zuciya kawai? ki fidda kanki cikin maganar nan faseelat, Aisha shekarar mu nawa tare amma bata taba shiga maganarba hasalima tafini jin zafin wulakanta ni da matar tayi ,idan har baso kike raina yarika baci ba to ki fidda kanki aciki "


Faseelat daketa zubda hawaye tana kallonshi tace "bazan dena nuna maka gaskiya ba umma tayi maka laifi kuma tayi nadama ta nemi afuwarka seka yafe mata wai shin baka yiwa Allah laifine amma kuma ya yafemaka, itama fa mutum ce mace tanada rauni yakamata kamanta baya ka rungumi mahaifiyarka ko zaka samu rabauta "


Idanunshi jawur ranshi bace ba abinda yake tunawa se labarin da mommy tabashi na cewa "bata sonka ko kadan bata kula da kai daddynka shine komi naka shine wanke maka tutu shine wanka shine dariyarka shine duk gatanka "


Jijiyoyin kanshi duk Sun fito zuciyarshi na zafi yace "bakijin magana ta kenan nace kibar maganar ta I'm warning you this is the first and last time karki kara maganar matar nan acikin gidannan inba haka ba I will do something bad "

Ya fita yabar mata dakin, faseelat ta kara fashewa da kuka yanzu idan ya mutu yau fa me zece wa Allah bayada wata hujja akan abinda yake yi, 


Fahad gidan yabari gabadaya yana tuki yana fidda huci, 




Hjya cikin dabara kar jamila ta kaita karshe ta kira khalil ya dauka da sallama ta amsa tace "khalil kazo ka dauki jamila ku tafi gida kasan baason me ciki na kai Maghreb awaje "


Yace "to hjya ganinan zuwa "


Hjya takashe kiran ta shiga ta samu jamila dake bacci hjya ta bubbuga gefen kujerar jamila ta bude ido tana kallonta hjya tace "ki tashi ki shirya gashinan zuwa zaku tafi gida "


Jamila ta tashi tana ya mutsa fuska ta shiga toilet, 


Hjya tace "oh ni saro na daukowa kaina jidali yarinya ba kunya kokadan duk tabi ta fitsare kafarta  to Allah ya kyauta "


Jamila kau tunda ta riga tagama gano halin hjya ta kuduri musguna mata, 


Gab Maghreb khalil yazo ya dauketa suka koma gida, 



Fahad wurinda suke hutawa da friends dinshi ya nufa sabeer se shakiyanci yake mishi sede yayi murmushi,


bayan faseelat ta yi sallar Maghreb ta shiga kitchen ta masu vegetable soup and white rice, 


Tana gamawa ta kai musu dining ta koma daknta tayo wanka tayi salla ta saka doguwar riga dark purple ta zauna gaban mirror tarika kallon kanta ta madubi har yanzu jikinta be dawo dede ba idanunta sunkum, 


Kasa yin kwalliyar tayi ta fesa perfumes ta koma ta zauna a cushion, 


Hakanan taji kewar ya umar dinta ta dauki waya tayi dialing number dinshi  ya dauka tana shagwaba tace "ni nayi fushi da kai yaya"


omer yayi dariya cikin muryarshi me sanyi yace "sorry kanwata me nayi ne"?


Tace "shikenan kamanta ni ko? "


Yace "amin hakuri to ni ban isa namanta rabin raina ba "


Faseelat tai dariya tace "I'm missing you"


Yace "nima ina missing dinki sosai "


Fahad da ya dawo yanzu dakin faseelat ya nufa dan kiranta suci abinci yaji tana waya da omer tana ta shagwaba ,kishi ya taso mishi be tsaya ida jinsu ba yajuya ranshi bace, 


Yakoma dining yace wa Aisha tai sarving dinsu faseelat ta koshi, Aisha tai sarving dinsu suka fara cin abincinsu, Aisha daga yanayin shi ta riga tagano akwai abinda ke damunshi don ko abinxin yaki sakin jiki yaci, taja plate dinta ta matsa tafara bashi abaki tana mai labari, 


Faseelat data gama waya ta zo saukowa ta hangesu ta juya takoma daki ranta cike da kishi, 



bayan sungama cin abinci a falo suka baje sunata kallo kan Aisha a jikin fahad yana wasa da gashin kanta, 


Amira ta tashi ta shiga dakin faseelat, faseelat nata tunani amira ta shigo dan dole ta kirkiri faraa tana rungume da amira tana ta mata labari har bacci ya dauke amiran, ta dauketa ta kaita dayan bedroom dinta ta shiga toilet tayi wanka tasaka sleeping dress kwata kwata takasa shan ko wani abu me sanyi ta hau bed ta kwanta tana tsoron tafita takara ganin abinda ze tarwatsa mata zuciya har bacci ya dauketa, 


Fahad beko leko dakin faseelat ba yawuce dakinshi yayi wanka ya kwanta yanata tunani yatsani  duk namijin da faseelat zatai magana dashi ba kamar omer da take sakarwa jiki sosai, 


Aisha ta riga fahad tashi donhaka batasan yana cikin dakinshi ba, ita tabawa zuciyarta shawara taje dakinshi ta kwana maybe ihun su baze tada ta ba, tagama kwalliyarta around 11pm ta nufi dakinshi, 


Ta bude ta shiga dakin da deem light ne kawai akunne bata lura said fahad da ke kwance ba ta haye gadon ta kwanta, 


Fahad da dama yaketa tunanin yadda zaai ya kwana haka, ya matsa ya rungumo Aisha jikinshi, tai sauri ta bude ido tace "yaya dama kananan? Bari natafi I thought kana dakin faseelat "


fahad da yafara rikita mata lissafi yace "u r not going anywhere anan zaki kwana "


Aisha tace "faseelat fa? "


Yace "she send me out kamar ba ango ba "


Aisha tai dariya takara shigewa jikinshi suka lula sama, 




can 12am faseelat ta farka ta laluba gefenta taga wayam ba fahad, ta tashi zaune ta dafe kai tana tambayar kanta wace irin zuciya gareshi haka harda kaurace mata, 


Ta sauka daga gadon ta bude kofa tafita, 


Direct dakinshi ta nufa bata tsaya komi ba ta murda handle zata shiga ciki, through haske me duhu dake dakin taga abinda ke wakana Aisha akan fahad suna sex, 


Dama bata ko Saki handle ba Cikin sauri tajawo masu kofar ta ruga da gudu dakinta tana kuka tafada kan bed tai tayi, 


Dukansu da fahad da Aisha sun ganta amma hakan be hanasu ida abinda suka fara ba, seda suka gama fahad ya rungumo Aisha yanata sa mata albarka yana fada mata sweet words dan sosai ta samar mashi natsuwa, atare sukai wanka suka dawo suka kwanta like da juna, 


Ba dadewa bacci ya dauke Aisha, fahad ko yakasa bacci zuciyarshi nabashi faseelat na can na kuka, 


har 2am ya daure ya janye Aisha ya nufi dakin faseelat, 


Ya tura kofa ya shiga tana kan bed har tayi kuka tagaji tai shiru tana zaune kan bed tana ta wasa da hasken dakin ta kunnashi red ta kunnashi green, 


ya rufe kofa jikinshi sanyaye yazo ya zauna kusa da ita har ya zauna batako kalleshi ba yazo ze jawota jikinshi tace "don't toch me "


ya tsaya yana kallonta duk tayi zuru zuru, yace "I'm sorry honey for what I did to you .."


Ta daga mishi hannu tace " karkacemin komi hero ashe da bansan kowaye kai ba yanzu nema nafara saninka, me na maka da zaka kauracemin Ka dauki kwanana ka kaiwa wata eyee haka ake adalci? ko kanaso kazo ranar kiyama barin jikinka a shanye? An Kar6o daga *Abi-Hurairah (ra)*, *Annabi* Yace: *“Duk Wanda Ya Kasance Yanada Mata Biyu, Sai Ya Karkata Zuwa ga Daya Daga Cikinsu, Zaizo Ranar Kiyama 6angaren Jikinsa a Shanye”* annabi be gushe ba yana adalci a tsakanin matanshi bayan ya raba musu kwana kuma yarika cewa...  *“Ya Allah Wannan Shine Abinda Na Aikata Cikin Abinda Nake da Iko, Kada ka Zargeni Cikin Abinda Ka Mallaka Wanda  Ban Mallaka ba* kaide tunba aje koina ba ka nuna bazaka iya adalci ba "tana magana cikin fada idonta nakara haskomata yadda ta gansu. 




fahad sammm baya daukar raini saboda albarkacin amarci🤣ya hadiye fushin shi ya mike tsaye yana zaro mata ido yace "ina daga miki kafa karki crossing limit dinki wlh inkika kaini karshe bazakiji dadi ba, kuma daga yanzu I don't want all ur waazi ki rike abinki karki kara jawomin hadisi ko wata aya idan muna magana idan kunne yaji...."be tsayawa idawa ba ya fita yabar mata dakin, faseelat zuciya awuya kamar zata fashe tabi kofar da kallo, kuka ma yaki zuwa mata se wani gumi da yarika keto mata tsabar kishi, ta tashi ta shige toilet ta dawo ta kabbara salla tana addua tana kuka tana rokon Allah ya shiryar da fahad don in ya daure haka duniyar shi da lahirarshi duk bazasuyi kyau ba, 



Bayan sallar asuba suka yi karatu da amira sukai wanka ta shirya ta ta tura ta ta gaida mommy ta haye gado tai kwanciyarta, 


Suma su fahad abinda sukai kenan seda sukafito yin breakfast wayam bakomi, shaf shaf shi da Aisha suka shiga kitchen sukai frying egg sukai toasting breadi suka fito, 


Sunata labari suna dariyarsu dukda de fahad tunaninshi na can gun gimbiya, 



Suna cikin cin abincin faseelat ta fito tazo ta zauna tafara hadawa kanta tea fuskarta tamau, 


Fahad don yabawa faseelat haushi ya tauna bread ya sakawa Aisha a baki kamar zasuyi kiss Aisha ta rumtse ido tace "hummmmmm yummy dadi wlh let me give u mine "

Itama ta tauna ya kanga baki ya amsa,haka sukaita shirme idanun faseelat cike da hawaye taki ko daga ido ta kallesu dan karsu zubo, se kurban tea take da zafinshi har yana kona mata baki, 


Fahad ya kalli faseelat ya meda kallon wurin Aisha yace "heartbeat yau ina cikin farin ciki yau zan dawo gareki "


Aisha tai murmushi ta dan kalli faseelat tace "a, a yaya nakara maku kwana sati zakai mata "


Ya bata fuska yace "haka zamuyi duk zumudi na? "


Tace "sorry haka yakamata ai "


Yace "to baniso taso ma muje nagwada miki wani abu "yakashe mata ido daya 


Tace "OK "ta mike suna hawa step ya dagata sama, 


Suna tafiya faseelat ta ajiye copyn hannunta ta Duke tafara kuka, 


Amira ta matsa ta tabata tace "anty kuka kike? Ki dena kuka karki sani kuka"


Faseelat ta goge hawayenta ta dago taiwa amira murmushi tace "I'm not crying ai babba baya kuka "


Ta tashi tafara gyara gidan don ganin baai komi ba, 



Ita tayi musu lunch jellop rice with chicken nuggets ,


har suka gama lunch din bata kalli fahad ba yanata so su hada ido taki kallonshi, 


Shi yariga kowa tashi ya haye sama, 


Dayake yau Aisha keda girki suna gamawa ta wuce kitchen tai wanke wanke sannan Takoma sama tana charting, 



Karfe 4:30 anty salma Ta danna door bell faseelat suna cikin karatu da amira tana koya mata hand writing ta dauki remote ta latsa, 


Anty salma ta shigo tana taunar cingum tai tsaye tana kallon su faseelat data kadaddabe amira kamar diyarta, 


Can zuwa faseelat ta dago ta Kalli anty salma ta kakaro faraa tace "yi hakuri dan Allah bari naje nakira maki ita "


Anty salma tai dariyar rainin hankali zatai magana Aisha ta sauko tana cewa "maraba da anty kishigo kintsaya kamar bakuwa "



Anty salma ta zare glass din idonta tace "baride nagama kallon ikon Allah yar matsiyata ansamu wuri waini zataiwa iso "


Aisha tai dariya tace "hmm anty kenan aikin san basuiya samun wuri ba muje ciki de akwai labari "


Anty salma takara rafkawa faseelat harara suka haye sama, jikin faseelat har rawa yake saboda bacin rai samm bata ciwa mutum mutunci kuma baaisa aci mata ba, 


Arikice ta cigaba da nunawa amira hannunta na rawa ,


Acan sama anty salma kayan mata ne birjik takawowa Aisha takara daura mata darasi se 5:40 suka fito sunata labari kamar wasu friends gabadaya yau Aisha bata da damuwa ko kadan, 



Suka zo zasu fita anty salma tace "amma de ki kama diyarki kar ai wata kissa daita "



Aisha tace "kuma fa anty ai bata da zuciya ne namata warning taki barin tabamin diya da yake ba zuciya "


Anty salma tace "kide kama yarki kar akoya mata muguwar dabia "


Suka fita duk faseelat najinsu har mota Aisha ta raka anty salma seda ta bar gidan ta dawo ciki, ba tsaitsayawa tai wurinsu faseelat ta janyo amira faseelat ta rike ta ta tashi tsaye itama don ranta yagama baci, 


Aisha ta kalli hannun faseelat data rike amira ta meda kallnta gun faseelat tace "sakarmin diya, tunda bake kika haifamin ita ba "


Faseelat tace "ai bake kadai kika haifi diyar ba nima diyata ce tunda diyar mijina ce "


Aisha tace "da Allah gafara can marar kunyar banza harni zaki kalla kice wai diyar mijinki, mtswwwww na fada miki ki bar ta bamin diya kar agoga mata dan hali mutum da aurenshi yanabin namiji "


Faseelat tai murmushi tace "wannan shine kuskuren da natabayi a rayuwata kuma ni nakasance mai tuba ga Allah akowane yini inada tabbacin ya yafemin, kuma ma miya kawo wannan maganar ne cin fuska? "



Aisha taja tsoki ta harari faseelat up and down tace "towa yasani ko kema awurin ta gida kika koya abu aduhu "



Idanun faseelat jawur dan ba abinda bazata iya juraba amma banda zagin iyaye batare da bata lokaci ba ta dauke Aisha da mari, tasss!!! 


Aisha ta dafe kumci tana kallonta abun yazo mata un expected, amira tasa kuka, 


fahad fitowar shi kenan yagama aiki a laptop dinshi zeje office hankalinshi na kan wayarshi ya ji karar mari yayi sauri ya daga ido yaga hanun Aisha dafe da kunci faseelat kuma na huci ga hannun amira kowa yarike da alama akanta suke fadan taf tafffff taff yafara saukowa daga step dasauri, 


Dukansu suka meda kallonsu gun wurin har ya karaso rai bace ya dauke faseelat da mari, 


Ta dafe kunci hawaye suka ziraro mata ta zuba mai ido tana kallonshi, Aisha ta saki karamin murmushi tana tuno marukan da tasha saboda faseelat ,


fahad rai bace yace mata "kada ki kuskura ki kara gigin tabamin mata, bata girmeki ba? Tsarar ki ce ita da zaki mare ta oya apologize to her"


faseelat hannu dafe da kumci take kallonshi baki bude, bawani bincike ya dauketa da mari, 


rai bace da tsawa yace"nace kibata hakuri "


faseelat gani tayima ya rainata ta ja karamin tsoki ta sauke hannunta kasa tace "bazan bata hakurin ba, kuma wlh ko yanzu takara zagarmin mahaifiya sena dauketa da mari "



Yafara kwance belt dinshi yace "bazaki bata hakuri ba?" zuuuu ya zuge belt din, 


faseelat tasaki hannun amira ta kwasa aguje yabi bayanta tana shiga daki ya shiga ta haye saman bed tana yarfa hannu ido rufe yafara lafta mata belt kotaina, tarika ihu tana sosa jiki, 



Aisha na tsaye jin ihun faseelat da sautin duka tai dariya  tace "yanzu kika fara gani yarinya "taja amira kan kujera tana rarrashi,


amira daketa jin ihun faseelat takiyin shiru ta cigaba da kuka, 



seda yama faseelat lilis sannan ya wurgar da belt yawuce dakinshi ya sake wanka yazo yawuce su Aisha dake zaune falo yabar gidan ,


faseelat na sheme kan bed tana ta kuka tunda take baataba dukanta da belt ba.




Post a Comment

0 Comments