TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Nacina ya jawo mini page 61-62

*Daga alƙalamin* 


🖍️📚 *Narrnarhh Bukar*  📚🖍️





*Comments and share 🙏🙏🙏Fisabilillah*.



[5/28, 8:12 PM] Narnarhh Bukar: 


🏵️ *NACINA YA JAWO MIN* 🏵️






*Narrnarhh Bukar* 

( *The Amazing Pen* ✍️)




*TASKIRA WRITER'S FORUM*

*T.W.F*


*BOOK 2*




6⃣1⃣----6⃣2⃣




Washe gari da wuri suka karya kumallonsu tare da shiri cikin sauri saboda Uncle Hassan yanada ayyuka a gabansa,haka sukayi ma su Mairo da Na'ima sallama sannan suka fito wanda lokacin ƙarfe 9:12am na safe,suna cikin niyyar shiga mota saiga wani mai machine da mutum a bayansa ya goyo tare da fakawa a gefen motocin nasu,sauka yayi tare da biyan mai machine kuɗinsa,juyawan da zaiyi Karaf! idanunsa ya sarƙafe dana Umman Sa'eeda,nan take zuciyoyinsu suka bada Daramm!!! Damm!!! Dadammm!!! Lokaci guda Umman Sa'eeda ta rikice tare da nuna wannan mutumin,muryarta na rawa tana cewa





"Sssulaiman!!! "




Da ƙarfi tayi maganar wanda kowa a wurin saida yaji,Sa'eeda ce tayi saurin fitowa jin Ummanta ta ambaci sunan mahaifinta,ita ma da ƙarfi ta ce




"Abbana kai ne"



"Eh Sa'eedata ni ne,ina kuka shiga ne Sa'eeda nayi nemanku lungu-lungu layi-layi amma shiru, har islamiyarku naje nan ma ance ba'a san inda kuka koma ba,bacci gagarata yake saboda tunani da zullumin ina zan ganku,wani tunani ne yazo jiya da daddare akan nazo nan Damari ko zan samu labarin inda kuke,sai gashi nazo a sa'a" cewar Abban Sa'eeda


"Ƙarya kake munafikin Allah, babu wata sa'ar da kazo da ita,kamanta cin mutuncin da ka mana ni da ƴarka a lokacin da mukazo sanar maka Hussaina yayi accident" cewar Uncle Hassan


"Innalillahi Wa'inna Ilaihi Raji'un,ya hakan ta faru,wallahi bansani ba,sannan ni bansan sanda na maka cin mutunci haɗi da ƴata ba,to taya zan wulaƙanta ƴar da na haifa da ciki kuma wacca tafi soyuwa agareni"


"Ai haka zaka ce mana malam  wato kazo kayi mana daɗin baki ko,kamanta lokacin da kace Sa'eeda ba ƴarka ba ce koo......"


Sauri katse mishi magana Abban Sa'eeda yayi da cewa


"Wannan fa ƙarya ne,ni Sulaiman bazan taɓa cewa Sa'eeda ba ƴarta ba ce wallahi"


Har Uncle Hassan yayi niyyar ce masa wani abu sai Momin Sadam ta ce


"Kaga Hassan yanzu ba lokacin wannan surutun bane,ka bari idan mun koma gidanka sai ayi zanjen a can"


"Haba Aunty Ruƙayya taya zan bari wannan mutumin ya taka cikin gidana,bayan cin mutuncin da ya mana ni da Sa'eeda tare da wulaƙanta Hussaina, haba inaaa inaa wallahi"


"Hassannnn ka kwantar da hankalinka mu tafi dashi gidanka,zan maka bayanin komai Hassan na roƙeka da Allah karka musamin please"


Shiru Uncle Hassan yayi sai can ya buɗe motar ya shiga dama maganarsu ce tasa ya fito,kowa shiga motar yayi har da Abban Sa'eedan amma ba'a motar Uncle Hassan ba saboda ya ce shi bai yar da da Abban Sa'eeda ba. (Ohhh su uncle Hassan da zuciya tare da rashin mantuwa😂😂😂)


Su Baba da Gwaggo Ladi sai kallon ikon Allah suke babu wanda a cikinsu ya saka baki saboda basu san yadda maganar take ba,shiga motar sukayi lokacin da aka ce su shiga,nan da nan motocin suka ɗau hanyar barin ƙauyen zuwa Kaduna,kasancewar gudu suke sosai sai wurin 1:00pm suka iso Ƴan Majalisu tare da wucewa har cikin gidan Uncle Hassan, daman Uncle Hassan ya kira Dr. Nabila akan suna hanya sannan akwai baƙi don haka ta shirya musu girki,jin haka nan da nan Dr. Nabila ta shiga kitchen tare da mai aikinta Jamila suka fara girke-girke domin tarar baƙinsu,kuma koda su Uncle Hassan suka iso gidan har abinci ya kammalu sun saka a food warmers.


Shiga kowa yayi cikin falon tare da barin Gwaggo Ladi da kalle-kalle,sai faman ɗaga wuyanta take tana duba filin gidan tare da flowers din gidan,a haka har ta shiga cikin falon,Uncle Hassan, Baba da Abban Sa'eeda ne suka fita masallaci kasancewar koda suka shigo cikin Kadana har an fara kiraye-kirayan sallar Zuhr,suma matan sallah sukayi wanda a lokacin alwala saida aka sha dariyar Gwaggo Ladi saboda wai ita atafau baza tayi alwala a wannan bayin ba,taya ɗaki guda haka za'a ce mata tayi alwala a ciki,su Dr. Nabila da Umman Sa'eeda sunyi-sunyi da ita akan bayi ne ba ɗaki ba tayi alwalar a ciki amma taƙi,Momin Sadam ne tayi ta lallashinta akan daga yau bazata sake alwala a ɗakin ba tunda ta ce ɗaki ne,a haka  aka shawo kanta sannan tayi alwala tare da yin sallah, fitowa falon sukayi domin cin abinci, kasancewar an shimfiɗa babban curtain mai kyau irin wanda larabawa suke shimfiɗawa idan zasu ci abinci musamman idan ahali guda zasu ci abincin,kowa cin abincin yake cikin kwanciyar hankali, a ɓangaren Gwaggo Ladi hmmmm ba'a cewa komai domin sai brush take da shinyar dajjaja(kaza)kowa saida ya tashi ya barta a wurin tana faman lodan abincin.(Gwaggo Ladi  an daɗe ba'a haɗu da dajjaja ba😂😂😂)



Bayan sun kammala cin abinci sai Momin Sadam tare da Umman Sa'eeda suka kira Hassan gefe tare dayi masa bayanin matsalar Abban Sa'eeda, dayake Umman Sa'eeda ta sanar ma Momin Sadam komai akan zamanta a gidan Abban Sa'eeda tare da mallakar da Umma Kande tayi akan Abban Sa'eeda,shima zai yanzu ya fahimta saboda a lokacin da suka je shida Sa'eeda sanar masa Accident ɗin Umman Sa'eeda a yadda yake maganar zaka fahimta da wuya yana cikin hayyacinsa saboda kalaman da yake amfani dasu dole akwai alamar tambaya ga uwa-uba shegenta ɗiyarsa ta cikinsa,bayan sun gama tattaunawa ne sannan suka dawo cikin falon,tattaunawa sukayi ta fahimta akan komawa gidan Abban Sa'eeda cewa Abban Sa'eeda, amma Uncle Hassan ya ce,zata koma amma ba'a wannan gidan ba saidai za'a siya mata gida a wannan unguwan nasu ta dawo nan da zama bayan bikin Sa'eeda, daman a lokacin tattaunawansu sun mishi bayani akan auran Sa'eeda da Sadam,wanda yayi farin ciki sannan yace tunda har an saka ranar auren duk a can shi baida matsala sai aje ma can ayi bikin,nan Uncle Hassan yaji daɗin wannan karramawar da Abban Sa'eeda yayi hakan yasa ya ƙara saukawa daga fushin da yake.


Komawa maganar zuwa aikin Hajjinsu Baba da Gwaggo Ladi akayi, a nan ne Momin Sadam ta ce zata biyama Abban Sa'eeda aikin Hajji shikenan sai su tafi tare,murna iya murna Abban Sa'eeda yayi har ya rasa kalmomin da zaiyi amfani dasu wurin yi mata godiya, Umman Sa'eeda da Sa'eeda godiya suka shiga yi mata tare da Abban Sa'eeda, hira ce ta ɓarke a tsakaninsu,ana cikin hirar ne Umman Sa'eeda ta tambayi inasu Umma Kande da Maman Jummalo,ai kamar jira yake a tambayesa,bai tsaya ɓata lokaci ba ya fara rattafo musu labarin duk abinda ya faru bayan tafiyarsu dayake Iklima ta sanar masa komai akan abinda ya faru a lokacin da baya cin hayyacinsa,zaman auransu ne,mutuwar Zaliha da Musa ne,Haihuwar Maman Jummala da ɗa mai kan jaki  komai bata ɓoye masa ba har zuwa dawowar Nusaiba gida tana yoyon kashi da kwalemar da sukayi haɗi da fashewar wannan kwalbar da haukan mamanta,shima duk yadda ta sanar masa haka ya sanar musu,ai kan kace me ɗaki ya kaure da Salati tare da sallallami ana ƙara girmam sunan Allah musamman Gwaggo Ladi wacca ta ƙara tsarkake zuciyarta jin wannan labari mai ban mamaki da al'ajab ashe akwai wa'inda suka ci ubanta a wurin hassada tare da biye-biyan bokaye da malamai lallai Allah abin godiya da yayi saurin ankarar da ita,kenan da ita ma ƙarshenta ba kyau zaiyi ba.


Sosai abin ya bama Umman Sa'eeda mamaki da al'ajab wai yau Umma Kande ta hauka ce sannan Nusaiba na yoyon kashi Ya Rahman tabbas *Duk wanda baiji tsoron Allah ba yayi asara* yanzu ina Umma Kande mai nuna ita itan ce,ke duniya ina zaki damu,shiru tayi sai can ta ce


"Gobe sai muje mu gaisa dasu"


"Ina! Gidan zaki sake komawa su kassaraki" cewar Uncle Hassan


"Karka damu Hassan ai wacca ma idan naje zata iya kassaranin Allah yayi ikonsa akanta,yanzu ta kanta take,zanje ingansu kafin a gama yi masu Baba Visa zuwa gata sai mu wuce Kebbi"


Cigaba da hirarsu sukayi,washe gari Umman Sa'eeda,Dr. Nabila, Sa'eeda tare da Momin Sadam suka nufi gidansu Umman Sa'eeda na da,tunda aka shigo layin Sa'eeda take kalle-kalle ganin yawanci gidajen da ta sani duk an sauyasu gashi an kara gyara layin sosai,bayan sunyi parking din motarsu sai suka fito lokacin Abban Sa'eeda ya fito kenan daga gidansa daman jiya ba a can ya kwana ba ya dawo gida,da farin ciki ya tarbesu zuwa cikin gidan,da sallama suka shiga cikin gidan a lokacin su Maman Jummalo da Nusaiba sun fito da Umma Kande sai faman ihu yake, su  Iklima da Jummalo suna wanke ɗakin saboda kwana biyun da basu wanke ba gidan sai ɗoyin kashi ya ke haɗi da zarnin fitsari,su Umman Sa'eeda na shigowa gidan sukayi saurin toshe hancinsu saboda warin da gidan yake,da Sauri Dr. Nabila ta ce


"Jama'ah meke wari a gidan nan ko yasan shadda ake  muku,sai mukoma"


Sai lokacin su Maman Jummalo suka san da shigowar mutane gidan saboda ihun da Umma Kande take duk ya kaure ilahirin gidan,juyowa sukayi kasancewar sun ba ƙofar gidan baya,manyan mutane ne suka gani gashi basu gane kowa a cikinsu ba,Maman Jummalo ne tace


"Sannunku da zuwa manyan baƙi,don Allah kuyi haƙuri gyaran wurin da Umma Kande zata zauna muke shiyasa zaku ji gidan ya ɗume da wari"


"A'a babu damuwa wallahi" cewar Umman Sa'eeda tana ƙara kallon yadda Maman Jummalo ta rame tare dayin baƙi harda ma Nusaiba, Abban Sa'eeda ne yace


"Hala baku gane su ba" 


"Eh Baban Nusaiba bamu ganesu ba gaskiya,suwaye haka"


Girgiza kai yayi yana murmushi sannan ya ce


"To Hussaina ce da Sa'eeda tare da ƴan uwanta"


"Meneeeeee!!! Umman Sa'eedan dana sani da Sa'eeda!!! " cewar Maman Jummalo


Murmushi Umman Sa'eeda tayi dan tasan za'a rina saboda ita kanta tasan komai na jikin ya sauya  saboda hutu da kwanciyar hankali ba lallai su ganeta ba,magana ta fara cikin wannan muryarta ta da suka santa dashi 


"Eh ni ce Umman Sa'eedan da kika sani ga kuma Sa'eeda"


Nuna Sa'eeda tayi wacca take faman toshe hanci saboda warin da gidan yake,tare da cigaba da cewa


"Munzo muku ziyara ne tare da sanar muku da auran Sa'eeda bayan babbar Sallah da sati biyu"


"Allahu Akbar,lallai Allah da girma yake,Iklima! Jummalo! kuzo kuga su Umman Sa'eeda da Sa'eeda"


Da sauri su Iklima da Jummalo suka fito jin ance musu gasu Umman Sa'eeda da Sa'eeda daman sunata addu'ar Allah ya haɗasu dasu kosa nemi yafiyar abubuwan da suka musu a baya,Rayuwa kenan! Mamaki ne ya cikasu ganin Maman Jummalo na nuna musu Umman Sa'eeda da Sa'eeda saboda idan da za'a barsu ba iya ganesu zasuyi ba saboda kyau da hanken da suka ƙara ga wani irin sheƙi da fatan jikinsu take irin na jin daɗi da kwanciyar hankali,tsayawa sukayi suna kallonsu kamar sun samu television,murmushi Sa'eeda tayi tare da cewa


"Ƴan uwana ya kuke,ya bayan rabuwa"


"Rabuwa!!! Rabuwa!!!  Ai tana wurin Sankeru"


Sai yanzu Umma Kande ta fara magana bayan ta gama binsu Umman Sa'eeda da kallon ƙurilla,Sa'eeda ce taji magana tazo mata banbaraƙwai cewa tayi 


"Ina wuni Umma Kande"


"A'aa Ba Umma Kande ba Sarere ta Sankeru zakice hhhhhhhh!!!! Ni ce Sarere ta Sankeru!!!! "


Dariya ta tintsire dashi tare da cigaba da susar gabanta wanda yanzu wani irin ruwa mai yauƙi yake fita, ga wani iri  uban ɗoyi gaban nata yake duk da su Maman Jummalo suna iya ƙoƙarinsu wurin yi mata wanka a duk kwana biyu tare da wanke gaban nata amma still gaban nata fidda ruwa kamar ruwan gyambo,Maman Jummalo ne tace


"Kinga Sa'eeda daina biyewa maganar Umma Kande domin yanzu bata cikin hayyacinta,bara yanzu mukaita ɗaki tunda an wanke ɗakin mu kawo muku tabarma ku zauna"


"Babu damuwa" cewar Umman Sa'eeda wacca mamaki da al'ajab ya cika ta ganin Umma Kande cikin hauka,ga gashin kanta ya motse wanda kana gani kasan mahaukaciya ce,duk tayi baƙi ta rame,gashi duk wannan ƙibar da tayi ta zube,haka aka cicciɓeta zuwa ɗakin wanda su Iklima da Jummalo sun goge tare da saka turaran wuta a ciki,tabarma Nusaiba ta ɗauko musu,zama sukayi sannan suka ƙara gaisawa,Maman Jummalo cikin muryar damuwa ta ce


"Don Allah Umman Sa'eeda da Sa'eeda ku yafe mana laifukan da muka muku,wallahi munyi da nasanin biyema ruɗun zuciyoyinmu,munga iftala'i kala-kala kuma mun san Allah ne yake nuna sakayyarsa akan abinda muka muku,kunga yadda Umma Kande ta koma yanzu da idanunku wallahi wallahi wallahi duk sanadiyyar muguntar da muka muku ne,ni kaina ban tsira ba domin yaro na haifa mai kan jaki wanda sanadiyyar zuwa wurin boka na samu cikin,Don girman Allah ku yafe mana,kin gammu nan"


Nuna kansu tayi tare da cigaba da cewa


"Wallahi addu'a muke akan Allah yasa mu hadu daku domin neman yafiyarku saboda mun cutar daku a lokacin da kuke gidan nan,gashi Allah ya nuna ikonsa akanmu tun bamu je ƙiyama ba"


Wasu zafafan hawaye Umman Sa'eeda take zubarwa tuno da wahalhalun da suka sha a wannan lokacin,yanzu gashi Allah ya saka musu tun kan aje lahira, Allah kenan cikin sanyin murya Umman Sa'eeda tace


"Ni da ƴata mun yafe muku Allah ya yafe mana gaɓa ɗaya"


Farin ciki dukkaninsu suka shiga yi  har tausayi suka ba su Umman Sa'eeda da Sa'eeda ganin yadda suka  rame,godiya suka shiga yi musu akan yafiyar da suka musu,a nan suka kara sanar musu da bikin Sa'eeda wanda ba'a Kaduna za'ayi ba,a can Kebbi State za'ayi bikin,sunyi farin Ciki sosai tare da cewa idan lokacin bikin yazo in shaa Allah zasu je,murmushi Umman Sa'eeda tayi sannan ta ce


"Babu matsala zan turo driver har gida ya ɗauke ku zuwa Kebbi in shaa Allah, sannan magana ta gaba shi ne neman lafiyar Nusaiba"


Shiru su Maman Jummalo sukayi suna sauraronta,cigaba da cewa tayi


"A gaskiya bazaiyu Nusaiba ace ta cigaba da ruyawa da pampers ba,domin ba kowani namiji zai iya auranta ba"


"Hakane wannan amma likita yace bazata taɓa dawowa yadda take ada ba,sannan yoyon kashi bazai tsaya ba har illa maa shaa Allah,shiyasa ya bamu shawarar siyan pampers saboda shi yafi cancanta da ita a yanzun" cewar Maman Jummalo


"Maganar likita bazai kasance ɗari bisa ɗari ba domin ba'a je wani asibitin an tabbatar  ba,idan ta kama har zuwa ƙasar waje ne sai aje idan kwalliya zata biya kuɗin sabulu ai shikenan sai muje,in shaa Allah bayan bikin Sa'eeda zan waiwayo kan maganar lafiyar Nusaiba"


"Allah sarki Umman Sa'eeda *Mai sakanya sharri da alkhairi*  muna godiya sosai Allah ya saka da alkhairi"


"Babu damuwa Maman Jummalo, mu bara mu wuce daman cewa nayi bara mu gaisa"


Tana maganar tare da miƙewa,kowa miƙewa yayi har da su Maman Jummalo dasu Nusaiba suna ƙara mata godiya haɗi da amsar numbanta,ciro kuɗi tayi masu yawan gaske tare da miƙama Maman Jummalo akan sukara wurin siyan pampers da abinci wanda ni kaina saida na sake baki ganin wannan uban kuɗin masu yawan gaske ji nike kamar nima Umman Sa'eeda ta haɗa dani🙃🙃🙃😂😂😂.


Wurin ɗakin da Umma Kande take ciki suka nufa,tare da kallonta ta windon,ita kuma a lokacin tana ta faman ƙyaƙyata dariya haɗi da susar gabanta,ganin mutane a wurin windon ya sakata saurin miƙewa haɗi da cewa


"Yawwa kun shirya!!! Ni bara na shirya muje wurin Boka Sankeru!!! "


Sai wani gyara-gyare take kamar mai shirin fita,su kuma abin ma dariya ya basu,wucewa sukayi ba tare da sun biye mata.


Dawowa gidan Uncle Hassan sukayi wanda a lokacin har su Baba da Gwaggo Ladi sun dawo daga Immigration office,har gama komai abinka da kuɗi,Abban Sa'eeda kuma washe garin ranar aka yi mishi nasa.A ranar da aka kammala masa passport a ranar su Umman Sa'eeda,Sa'eeda, Momin Sadam haɗi dasu Baba da Gwaggo  suka wuce Kebbi State, sai washe gari Uncle Hassan ya bisu can.


Wata ƙwarya-ƙwaryar walima tanadar  masu Baba da Gwaggo Ladi tare da basu kyatuttuka masu yawa wanda har kuka saida Baba yayi,tabbas alkhairi danƙu ne gashi ta silar taimako ya samu abubuwa da dama wanda bai taɓa tunanin samu a rayuwarsa ba.Sati biyu sukayi sannan suka dawo Kaduna wanda lokacin bai fi azumi saura ƴan wasu kwanaki ba.


Haka dai rayuwa ta cigaba da gudana,tun ana kwanaki,aka koma satuttuka,sannan aka tafi watanni wanda yanzu har su Umman Sa'eeda su tafi aikin hajji tare dasu Baba, Gwaggo Ladi, Abban Sa'eeda, Momin Sadam da Sa'eeda,Alhamdulillah sun kammala aikin hajjinsu cin nasara da kwanciyar hankali wanda a can ma saida aka sha dramar Gwaggo Ladi, har Sa'eeda a can tayi mata videon abubuwan dariyan da tayi,bayan sallah da kwana uku suka dawo Nigeria.Su Abban Sa'eeda,Baba da Gwaggo Ladi suna nufo Kaduna,su kuma Umman Sa'eeda, Momin Sadam da Sa'eeda suka wuce Kebbi tare da fara shirya-shiryan gagarumin bikinsu Sa'eeda da Sadam,Shi gogan namu bayama ƙasar duk wannan tafiye-tafiyan da su Umman Sa'eeda suke tayi,saidai suyi waya da sahibar zuciyar wanda wannan kullum ne babu fishi.Wannan Kenan



       @@@@@@@@@@@@@@



*KADUNA*



A ɓangaren *LOVE BIRDS* 🕊️🕊️ wato Sauban da Maryam har da Khairat rayuwa na tafiya musu normal babu matsala sosai,zamantakewar kowacca tsakaninta da mijinta sai a hankali musamman Sauban da Maryam har yanzu sun kasa zaman lafiya kullum sune rigima tare da faɗace-faɗace kusan yanzu Sauban ne ke janta da faɗa musamman idan office bai mishi daɗi ba,sai ya sauke fushinsa a kanta,ita kuma babu haƙuri kamar zawo haka zata biye mishi suyita sa'insa,duk wannan rigimar baka taɓa jin Sauban da Khairat suna sa'insa saboda bata biye masa,daya fara janta da faɗa zata ce masa yayi haƙuri don tasan neman inda zai sauke fushinsa yake,idan taƙi biye masa saiya koma wurin Maryam wacca kamar jira take.


Har yanzu babu alamun ciki a jikin Maryam da Khairat daman a baya saboda baisan shike da matsalar ba shiyasa yake tada jijiyoyin wuya amma yanzu da yasan matsalar daga wurinsa take ai muƙus yayi kamar *Yaci shirwa ya sha ruwa*  Mominsa ma ta daina tada hankalinta akan rashin haihuwar matan nasa tunda yanzu tasan ba laifinsu bane,addua kullum take akan Allah ya kawo masa zuri'ah masu albarkha.


A kullum rigimar Sauban da Maryam na matukar damun Khairat saboda  batason matsalar da take afkuwa a tsakaninsu,tafison su kasance tsintsiya maɗaurinki ɗaya wanda zaman lafiya zai dawwama a tsakaninsu baki ɗaya.A yau Khairat ta shirya tunkarar Maryam da wannan maganar saboda abin naci mata tuwo a ƙwarya,kasancewar yau Saturday tana gida Maryam bata tafi wurin inda take bautar ƙasa,da sallama Khairat ta shiga cikin falon nata,lokacin Maryam na bedroom taji sallamar Khairat da mamaki ta amsa sallamar tare da fitowa,murmushi Khairat ta sakarma Maryam,ita kuma Maryam fuskarta babu yabo babu fallasa haka ta zauna a kujeara da take kullum inda Khairat ke zaune,shiru daƙin yayi na kusan minti ɗaya kowa na tunanin zuci sai can Khairat tayi gyaran murya tare da cewa


"Nasan zakiyi mamakin ganina a ɗakinki saboda ɓan taba shigowa ba,alkhairi ne ya kawoni wurinki Maryam ba sharri ba"


Taɓe baki Maryam tayi tare da cewa


"Hmmmm wai alkhairi ne ya kawoki wurina,daman kishiya na bin kishiya da alkhairi ne inba sharri ba"


Murmushi Khairat tayi sannan ta ce


"Of course kuwa,domin ba kowace take da mummunan hali ba,Maryam nazo wurinki ne akan rashin haɗin kan da mukeyi a baya don Allah mu daina,inaso mu zama tsintsiya ɗaya maɗaurinki ɗaya,Wallahi! Wallahi! Wallahi! Har a zuciyata kuma Allah shi ne shaidata bana jin daɗin rashin zaman lafiyar da kukeyi keda Sauban,koda kika ga bama faɗa bawai baya takalana bane a'a saidai bana biye masa muyi faɗan,Please Maryam Understand me wallahi from the bottom of my heart i never have any bad intention against you,da zuciya ɗaya nake zaune dake,bansato gidanmu naga iyayen suna bambamtamu ba,matan mahaifina uku ne amma wallahi idan kika je gidanmu bazaki taɓa gane yaran wance da wance ba domin kowani yaro a gidanmu yakan koma ɗakin ɗayar Umman tamu da zama,koni kaina ba'a wurin mahaifiyata na taso ba,zamansu na matukar birgeni shiyasa nace why not we should stop this battle and face the reality.Allah na saman na kallo ko rashin iya girkin da kike wallahi dumuna yake, saboda ni mace ce sannan ciwon ɗiya mace na ƴa mace ne,don Allah kiyi nazari akan kalamaina,kibi kowanne ki fahimta,pleaseeee! "


Shiru ɗakin ya kuma yi babu me cewa komai sannan baka jin motsin komai sai ƙaran A.C dana fridge.Tun sanda Khairat ta fara magana jikin Maryam yayi sanyi domin ita kanta bata jin daɗin faɗan da suke da Sauban take ba ƙarin daɗi haushin rashin iya girkinta na matuƙar damunta,batasan yadda zata bullowa wannan al'amarin ba,kamar yadda Khairat ta ce  tabi kalamata dalla-dalla haka tabi tare da fahimtar komai,sai can ta dubi Khairat wacca take zaune tayi ta gumi,ta ce


"Khairat nayi analyses din kalamanki sannan ta fahimci komai,ada ina miki kallon maƙiyiyata amma yanzu banga wacca ta fiki zama masoyiya a gareni ba saboda gaskiya kike faɗamin,haƙiƙa kin hankaltar dani abubuwan da ya dace ace na sansu tuni amma duk da haka lokaci bai ƙuremin ba,in shaa Allah daga yau zanyi iya ƙoƙarina wurin daina biyawa Sauban idan yazo da fushinsa sannan idan da hali ko zaki iya koyamin girki tare da wasu abubuwa na mata, a gaskiya i'm lacking them alot"


Murmushi jin daɗi Khairat tayi ganin yardarta a nan kusa,cikin farin ciki Khairat ta ce


"You are always welcome dear ko yanzu i'm free idan kisano,ina godiya sosai da fahimtana,ina roƙon Allah daya dawwamar da farin ciki tare da zaman tafiya a tsakaninmu,ya kore sharrin shaiɗan a tsakaninmu"


"Ameen ya Rahman"


Cikin farin ciki haka suka doshi kitchen ɗin Maryam tare da ɗora girki,tun daga ranar zaman lafiya ya fara wanzuwa a tsakaninsu, baka jin sirrinsu ko kuma faɗansu,Sauban ma abin mamaki ya bashi domin idan ya shigo gidan da fushinsa yanaso ya sauke fushin a kansu sai su manna mishi hauka,ga wani shegen haɗin kai  wanda yanzu suke,Momin Sauban ma tayi farin cikin wannan haɗin kan da suke a yanzu tare da addu'ar Allah ya kawoma kwaccansu haihuwa tare da yara masu Akbarkha

.


Bayan ƴan wasu watanni Maryam ta fara laulayin ciki mai shegen bada wahala,yawanci ayyuka Khairat take saboda zaman Maryam a asibiti kusan sau uku ne,Sauban ya shiga ruɗu saboda rashin lafiyar Maryam gashi bikin mai gidan  *CEO SADAM DAUDA GHALI MAI NASARA*  ya ƙarato baifi sati ɗaya ba,dole ya haƙura da zuwa Kebbi State  saboda rashin lafiyar Maryam. Damma Khairat na matuƙar ƙoƙari akan Maryam ɗin sosai wanda har iyayen Maryam suka daina jin haushin kishiyar da Sauban ya ƙarama Maryam saboda ɗawainiyar da takeyi da ita a asibiti. Suma da alamu sun ajiye makaman yaƙinsu a gefe.Wannan Kenan



          @@@@@@@@@@@@@@@



*KEBBI*



Tun bayan dawowarsu Umman Sa'eeda daga aikin Hajji suka fara shirye-shiryan biki,yanzu haka Umman Sa'eeda da Sa'eeda sun dawo family housa da zama,furnitures ɗin Sa'eeda a Dubai akayi ordering ɗinsu,wannan aikin sai *Hassan na Hussaina madubi sha kallo* wato Uncle Hassan,shi yace zaiyi wannan a matsayin gudummuwarsa,ita kuma Dr. Nabila duk kayan da Sa'eeda da Umman Sa'eeda zasu saka a wurin event-event ta ɗinka musu na gani na faɗa a matsayin gudummuwarta.Ƙara gyara Family house ɗin akayi tare da canja wasu abubuwa a gidan,hall ɗin kansa inda za'ayi tarurrukan saida aka sake gyarashi haɗi da ƙara faɗaɗashi saboda wannan bikin ba irin sauran bukukkuwan da akayi a baya bane wannan na musamman.


A ɓangaren Momin Sadam da dangin Daddyn Sadam sunyi matuƙar bajinta wurin haɗa lafiyayyan akwatuna ɗai-ɗai-ɗai har akwatina dozen biyu bancin dukiyar da aka kashe a wurin haɗe lefen irinsu gwala-gwalai,kayan shafa,laisussuka,atamfofi,shaddodi,jallabiyoyi,da dai sauransu duk kayan babu na talaka domin bikin Auta za'ayi *Autan Hajiya Rukayya matar Alhaji Dauda Ghali Mai Nasara* 


Tun ana saura kwana shida biki,baƙi suka fara yin sallama a family house,har ƴar ƙasashen waje wa'inda Sadam yake harkar kasuwanci dasu duk sun fara zuwa wanda hotel guda Sadam ya biya kuɗin ɗakuna har zuwa bayan bikin,Maman Jummalo, Iklima da Jummalo sun zo bikin tare da barin Nusaiba a gida don ta kula da Umma Kande (Wato Sarere ta Sankeru😂😂😂),Baba, Gwaggo Ladi dasu Mairo suna duk sunzo bikin,Iman aminiyar Sa'eeda itama tazo bikin,ƴan uwan Abban Sa'eeda ma na ƙauye sunzo Kebbi bikin,kai kai kai jama'ah da sukazo bikin nan a gaskiya basu ƙirguwa har da mutum Abuja Sunzo amma banda Fadila wacca har yanzu tana nan tana dakon soyayyar Sadam a cikin zuciyar duk da ta haihu amma har yanzu tana nan da ƙaunar Sadam a zuciyarta.(hmmm Fadila saidai kiyi haƙuri domin Sadam na Sa'eedarmu ce🙃🙃🙃💘💘💘)



Programmes uku za'ayi sai ɗaurin aure,wanda bayan ɗaurin aure da kwana ɗaya zasu wuce  *LAS🕊️ VEGAS🕊️*  yin honey moon ɗinsu acan,tun ana saura kwana huɗu biki aka fara events,tun daga dinner,reception,arabian night duk anyi,kowa ga gani a hall ɗin yasha kyau musamman amarya Sa'eeda wacca har glowing fatar jikinta yake saboda tsabar gyara,ga wani kamshi mai sanyaya zuciya wanda ke tashi a jikinta,hmmm har dani aka je Maiduguri wurin ɗauko ƙwararriya mai gyaran jiki da ƙamshi ciki da waje,tunda su Sa'eeda suka dawo daga aikin Hajji  ta daina fita saboda a lokacin ne mai gyara jikin ƴar maiduguri tazo,wanda har yanzu bata wuce ba,upon gyaran jikin harda gyaran ciki ake,nifa tsoro nake ji karfa suje su hauka Autan Momin a gaskiya irin wannan gyara haka🙃🙃🙃.



Alhamdulillah! Alhamdulillah! Alhamdulillah! An ɗaura aure lafiya sannan taro ma ya tashi lafiya, kasancewar har yanzu Maryam jikinta sai a hankali cikin na wahalar da ita shi ya hana Sauban zuwa bikin Maigidan Sadam tare da Amaryarsa Sa'eeda.Washe gari kuma baƙi na nesa suka fara tafiya gida tare da ɗumbi alkhairai kala-kala,Sadam da Sa'eeda a washe garin ranar jirginsu ya tashi zuwa U.S 



Taro ya watse kowa ya koma gidansa,Umman Sa'eeda ma ta kusa dawowa Kaduna da zama dayake Uncle Hassan yanaso ya siyan mata gida kusa dashi saboda bayaso ta ƙara zama a gidanta na farko.Wannan Kenan.




          @@@@@@@@@@@@@



*LAS VEGAS*



Haɗadɗan birni ne wanda yake a cikin U.S,ana yawan samun baƙi samu zuwa yawan shaƙatawa saboda kyau da haɗuwar garin,ga wurin ban sha'awa iri-iri,garin babba ne mai ɗauke da manya-manyan benaye masu kyau da tsari,kai kai kai in taƙaice muku Las Vegas duniya ne,domin garin ya haɗu kuma yana ɗaya daga cikin garuruwan da ake zuwa yawan buɗe ido................





*Mu haɗu a pages na gaba don cigaba da karanta wannan chakwakiyar✍️✍️✍️🔥🔥🔥*




*Koya amarcin Sadam da Sa'eeda zai kasance a wannan babban birnin???*.........




*Shin Nusaiba zata samu lafiya kuwa???*..........




*wai haka su Iklima zasu tsaya babu aure???*...........


*shin itama Khairat Allah zai kawomata ciki kamar ƴar uwarta Maryam???*........



*Da alama har yanzu Sauban baisan wace ce Mai gidansa ya aura ba,shin idan ya sani mai kuke tunani???*........




*haka zalika Maryam batasan waye Mai gidan mijinta ya aura ba,shin idan ta sani mai kuke tunani???*...........





*Kai! Kai! Kai! Abubuwa da yawa🙃🙃🙃,amsoshinku na nan tafe a pages masu zuwa,kudai  ku cigaba da zubo ruwa comments da reactions🌹🌹💖💖🌼🌼💘💘,ni kuma bazan gaji ba wurin suburbuɗo muku new updates zafafa* 🌹🌹🙃🙃💖💖🌼🌼💘💘😂🔥🔥🔥🔥🔥




*Ina ƙaunarku My Esteem Fans Lodi Lodi* 🌼🌼💖💖🌹🌹🙃🙃💘💘



 

Post a Comment

0 Comments