TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sanyi da zafi page 15

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣5️⃣


Da gangan Munir yabar wayanshi awajen yadauke car key yafice, tashi Riyad yayi yawuce yasaka pajamas yadawo ya kishingida tareda lumshe idanu, wayan Muneer ne yahau ringing hakan yasa yabude idanu kadan yakalli screen din ganin Mom R yasa yayi shiru yana kallo wayan na dab da katse wa yasa hannu ya dauka yakai kunnenshi yaki magana daga ta dayan bangaren Mom tace “Son” ahankali yace “Mom ina yini” ijiyan zuciya Mom ta sauke she really miss him chan tace “sabida I questioned you zakai zuciya kabar gidan? Riyad when did you grow dahar zakabar min gida sabida namaka fada? Riyad I still see you as my little baby boy da I have to guide every step of the way, your are my purpose, you are the reason I become a Mom, did you really leave house yau kwana biyu sabida na tambayeka game da abu Riyad”? Mom tai maganan muryanta na tsinkewa kaman zatai kuka, Riyad yayi shiru Mom abin ya matukar bata mata rai tace “ko kakai 100yrs of being a man I will always see you as my little child, I will always tell you do this and that, I agree raina abace yake ranan datamin maganan dan kunnen nan and I wasn’t thinking clearly, but still inada right nai fada, Babanka yayi aure aure but tell me menene fa’idan hakan yanzu? Kullum gidanshi cikin rikici makirci da fada ake, kalli Baffan ka tunda yama Amaryanshi koran kare bai sake marmarin kara aure ba sabida yaga implications din gashinan shida Jummai are living peacefully and happily, wat I’m saying is mata dayawa masifa ne, bazan taba bari ka auro wata wacce ban sani ba ko ban aminta da ita kaman Haleematu ba kafin azo arabani da d’ana that is the reason namaka fada and asked you ranan, and gashi nakosa naga Haleematu tai ciki amman shiru, dakaina nakai yarinyar taga gynecologist ance she’s fine kaine dai baka cika nemanta ba, kuma ita Haleematun tagayamin yawanci koka nemeta ba rannan ovulation dinta bane saisa har yanzu batai ciki ba, mesa kakemin haka Riyad? Kai ba dan gidan nan bane bakaga yanda matan yayyinka ke haihuwa shekara shekara ba? Duk shirin da Babanku yakema yaranshi maza tun suna yara kaima an maka amman narasa mesa kakeda sanyi a harkan raya sunna” da sauri Riyad yacire wayan daga kunnenshi yanajin wani irin kunya da nauyi idan Mom namai irin maganganun nan, danna wayan kawai yayi a speaker ya ijiye agefense yana jinta. “Kap yaran family nan wlh basama matansu wasa kai har rama matan suke sabida yanda yaran Mai Martaba Baba Ali fire for fire ne akan matansu” wannan karan Riyad baisan sanda ya dafe kanshi yace “Mom can we change the topic please” cikeda bacin rai Mom tace “Kaci gidanku da change of topic Riyad, nabaka gobe come back home and continue kaga yanzu kayi skipping 2days babu abinda ya shiga tsakaninka da Haleema, kubani grandson nagaya maka saida safe” ta kashe wayan, ijiyan zuciya ya sauke yakoma ya kwanta tareda lumshe idanunshi.


Har Muneer yadawo a kwance yasameshi yace “ina tuki natuna wani abu daya faru dazu yanda dayar ma’aikaciyar yarinyar tace ma Masifaffiyar mamanta nada HIV” dagokai Riyad yayi yamai wani shegen kallo yace “and so”? Dan sosa kai Muneer yayi yace “bakomi kawai natuna abin ne” juyar da kansa yayi sai chan yace “HIV is just like any other ciwo, having it doesn’t mean you are bad ko karshenka yazo, stop with the stigmatization” dasauri Muneer yace “haba noo bana stigmatization sai kace Baffan mu da akace ya kori matarshi mai ciki da akace tanada shi, ko tana ina oho”? Tashi Riyad yayi yace “let’s eat” abinci suka shiga ci he ate alot kam yana gamawa yadauki laptop yafara aiki daman yunwa yahanashi yi.

Cikin bacci taji ana tabamata kai sabida tsabagen yanda bacci yau bai shigeta ba taba cikin tashin hankali firgigit ta farka.

Cikin dare sau biyu cikin dare Dr da Nurses sukazo duba Mama duk tana zaune bata runtsa ba harsaida Dr yace “kihau gado ki kwanta kusada ita mana ko ga babban sofa kihau” girgizamai kai tayi tana zaune kan yar kujeran dake gaban gadon, cikin sanyin murya tace “zan zauna anan” gyadamata kan Dr yayi yawuce harzai fita tace “ina bill dinmu?” Dan juyowa yayi yace “your bill has been cleared receipt duk suna cikin ledan drip dinta” yana maganan yabude kofa yafice from yanayin mutanen kawai yasan Mai Martaba taimakonsu yake.

Tashi tayi dasauri tawuce wajen ledan drip din da duk za’a sama Mama tabude taciro takardun receipt wanda na farkon na meal tagani 2 person breakfast 2person lunch dinner da snacks na 3days taga 270k, abincinta itada Mama kullum 30k for 3days 270k zaro idanu tayi takai hannunta tana dafa kirjinta, tadauki dayan receipt din single room dasuke dakeda gado sofa fridge da bayi is 25k per day kwana uku 75000, sai magungunan Mama gabaki daya da drip da allurai taga 497,250 wannan karan saida ta fada kujera ta zauna, duka kudin 842,250naira, kusan miliyan daya ta ina zata fara neman kudaded nan? No gobe zatasa a sallamesu, but ko an sallamesu sunyi kwana daya which is 25k daki, sai kudin magunguna 497,250 dole saita biya ta ina zata fara, hawaye taji sun zubomata sai kawai ta gogesu da sauri tahada duka receipt din ta linke tasa a jakanta tadauko kudinsu ta kara kirgawa duka savings dinsu kenan 150k tadade ahaka saita maida jaka ta kama hannun Mama ta rike har aka kira asubahi idanunta biyu tashi tayi tawuce bayi tayo alwala tafito tabude jaka ta ciro dadduma anyi alamun gabas aşaman dakin hakan yasa ta kabbarta salla ta idar tai azkar tana zaune kan dadduma Dr yakara shigowa dasauri ta tashi ta linke dadduma Dr yaduba Mama yajuyo yakalli Rashida datai zuru zuru yace “Alhamdulillah BP yasoma sauka, maganin zai saketa soon zata farka bada jimawa ba” gyadamai kai tayi, murmushi Dr yayi yace “Maman ki will be fine kinji” gyadamai kai tayi ahankali tace “thank you” wucewa yayi  yafita


Zama tayi har bakwai da rabi kallon Mama take sai alokacin tafara hamma sai kawai ta kifa kanta anan bakin gado ko 1min batayiba bacci yayi awon gaba da ita.


Wajajen 10 na safiya Mama ke bude idanunta ahankali bakinta dauke da kiran sunan Allah, saman dakin ta kalla sannan ta sauko da idanuwanta ta kalli drip da ake samata kafin ta sauke idanun kan Rashida dake zaune kan kujera ta kwantar da kanta bakin gadon kusada hannunta tana bacci, ijiyan zuciya ta sauke ahankali komi daya faru jiya na dawo mata, ta tuna yanda tagama magana da bawan Allah nan mai kirki tafara tafiya tafadi tabbas taga bawan Allahn hankali tashe yazo yana kiranta Mama Mama dishi dishi take gani bama ta iya magana dağa baya kuma taga shida security sun kaita mota daganan kuma bata sake sannin inda kanta yake ba, ahankali cikeda karfin hali irin nata ta cire drip din ta sauka tana tafiya da kyar tawuce kofan data gani ta bude ta shiga bayi ta dauro Alwala tafito ta sanya hijabi taje ta sauna kan dadduman data gani tai salla dağa zaunen datake tun magrib da isha’i tahada dana safiya sannan ta dawo ta lallabo ta zauna agadon jin jiri na neman yakara dibanta motsin da gadon yayi yasa firgigit Rashida ta bude idanunta ganin Mama zaune da hijab dinta yasa da sauri ta tashi tace “Mama kincire drip din” takama hannun Mama dasauri tashiga maida mata drip din tace “mesa baki tasheni ba har yanzu BP ki is high Mama, you can fall at any moment”


Yanda take maganan Mama take kallo kaman ba Rashida ba duk ta tsure harta rame idanunta sun fada ciki sosai, hannunta Mama takai ahankali ta kama habarta hakan yasa gently tadago fuskanta ta kalli Mama duk yanda taso taboye damuwanta takasa da duka zuciyanta tafashe da kuka sosai atsaye hawayen na sauka kan hannun Mama, cikin kuka tace “Mama dan Allah kiyakuri I keep causing you pain koda yaushe, Mama I know how sick you are but kullum kara miki damuwa nake Mama, akan mene bazanyi hakuri na dinga danne komi ba, komine sainayi fada akai, is because of me BP ki yatashi, Mama kiyakuri kiyafemin dan Allah” har sheshekan kuka take, zuwanshi kenan yakai hannu kenan zai knocking kofan yaji sautin kuka da maganan datake hakan yasa ya tsaya chak.


Ahankali Mama ta girgiza mata kai tace “shiiiiii don’t ever blame kanki for ciwo ba cus ba laifinki bane ko daya, stop crying to bagani nan naji sauki ba, gashi nan duk kin bata fuskanki jibi yanda idanuwanki sukai ja sabida kuka bari kiga” Mama sai kawai takama bakin hijabinta takai kan fuskanta tashiga sharemata ta shafa kumatunta tasake murmushi tace “I have the most beautiful yarinya wlh idan tai kuka sainaga idanun nata ma sunfi kyau” dan murmushi kadan tayi wasu hawayen na taruwa, Mama tace “ai kaga abin karki kukan ya isa nace, yanzu dai tafi gida ki shirya kitafi school idan zaki dawo saiki biya wajen gyaran wayanki” baki Rashida tabude zatai magana akai knocking kofar just once kallon kofan sukayi dukansu, Mama tace “jeki bude kofan muga ko likita ne natafi gida” but Dr direct yake bude kofan tai maganan aranta tasa hannu ta goge fuskanta tass sannan tawuce wajen kofan tasa hannu ta bude ido da ido tayi da Riyad dake sanye cikin wata shadda yau sky blue jumper kanshi ba hula tashin Kansa ya kwanta sidik tunda take bata tabajin kamshin turare mai dadin nashi ba, da sauri ta dauke kanta dağa kallonshi Mama hangoshi yasa tace “bismillah bawan Allah” anatse akamilance yashigo har gaban gadon yaje yaduka dasauri Mama tace “tashi tashi haba zauna ga waje” tabashi kujera ijiye ledan dake hannunshi yayına gefen gadon yace “ya karfin jiki Mama ina kwana” murmushi Mama tayi tace “jiki Alhamdulillah naji sauki, nagode da kulawa ka kawoni asibiti banda bakin maka godiya Allah maka Albarka” takalli Rashida dake tsaye wajen kofan tai folding hannu tace “baki iya gaisuwa bane ko akwai abu abakinki ne” dan juyawa tayi da kyar tace “ina kwana” baki Mama tasaki tana kallonta ganin baka yasa da kyar tace “mungode” dasauri Mama takalleshi tace “Ya sunanka ne?” Ahankali yace “Riyad sunana” daidai lokacin akai knocking tareda shigowa dakin wata ce tana sanye da uniform na ma’aikata tace “good morning Ma dazu nazo nakawo muku breakfast naga kuna bacci natafi dashi dan karyayi sanyi yanzu zanje nakawo muku” tawuce tafita daga wajen kofan akunbure Rashida tace “Mama kicemai yasa a sallamemu mutafi asibitin mu” dan juyowa yayi daga inda


Yake yazuba mata ido dauke kai tayi strictly yace “Dr yace 3days Mama zatayi anan and hakan ne zai faru” dasauri Mama tace “Riyad kaga ai dawainiyan zaiyi yawa ta ina zamu sami kudin biyanka? Dan Allah kasa asallamemu naje general dana saba zuwa kaji, Allah yamaka Albarka Allah yakara daukaka” daidai lokacin aka kawo abincin breakfast ne omlete da bread toast sausage tea dakuma bowl na fruits yarinyar ta saukar dama da Mama wajen ijiye abinci kan gado sannan takai dayan abincin kan table sannan takalli Riyad tace “Sir do you need anything”? “No thanks” yafadi atakaice, Mama ta kalli Rashida dake tsaye kikam har lokacin awajen kaman mai gadi tace “zokiyi kari kitafi school don’t even tell me bazaki ba” kaman zatai kuka tace “Mama ni banso naje wazai zauna dake natafi” “I will be here with Mama” dağa Mama har Rashida dukansu kallon Riyad sukayi, hakanan Mama kawai taji tanason natsuwan yaron, abin yana mata ma kaman tasanshi batason tai rubbing in his face hakan yasa tai murmushi tace “to kinji Riyad zai zauna yatayani hira zoki ci abinci kitafi school kinyi katti already banson kina fashi a school kije gida ki shirya kitafi” bataso taje school ba but abinda yafima damunta is wannan mutumin dayakeyi kaman irin ya sansu din nan ko su yan uwa ne saiwani shishigi yaje musu mutumin da shekaran jiya ta sanshi, batason tai gardama sabida Mama batada lafiya hakan yasa ta taho wajen gadon gefen Riyad ta ballama jakan abubuwan dayakawo harara karaf akan idanunshi sannan tadauki jakanta dake wajen ta taso tajuyo hada ido sukayi tadauke kanta tajuya Mama tace “abincin fa” akufule tace “ni bazan ci ba” tawuce wajen wardrobe na dakin taciro kayan jakan an Mama daya kawo ta maidasu ciki kudin taboye karkashin kayan sannan tawuce tai hanyar kofa  tace “natafi” tabude kofan tafice ijiyan zuciya Mama tasauke tasa cokali ta a abinci tace “I have a very stubborn yarinya Riyad” dan murmushi kadan Riyad yayi baice komiba, Mama tai shiru kaman mai tunani tace “she’s all abinda na mallaka aduniyan nan” saita dauki fruits takai bakinta tafara taunawa sai kawai tafashe da kuka as if she’s holding on to something ahankali Riyad yace “Mama stop crying she will stop being stubborn soon duk yarinta ne, zata dena nan gaba, stop crying kinji Mama is not good for you zai hanaki warkewa” ijiye spoon din tayi takai bakin hijabinta ta goge fuskanta tace “ciwo na bana warkewa bane, HIV gareni Riyad” tadanyi murmushi tace “I don’t even know why nake fadamaka nasan kariga kasani Rashida tacemin agabanku abokiyar aikinta tace inada shi” tai shiru sai kuma ta zufar da iska dağa bakinta tace “I’ve caused Rashida pain tun tana ciki na, yarinyar nan tayi girma cikin bullying din society yar fasika yar mazinaciya yar me HIV so sometimes I don’t even blame masifa da fadan da stubbornness nata society shaped her to be that way dole tai finding means na yanda zatai surviving.


Mama takara shiru saikuma tasa hannu tadauki bowl din fruit din tarike tadauki spoon tadau lemu zatakai baki is as if akwai so many things acikin zuciyanta dake damunta tace “wlh, wlh tunda nake arayuwana bantaba fasikanci ba, inada cikin 6months ina laulayi sosai aka kaini hospital akamin gwaje gwaje the next thing inada HIV, aka gwada Mijina baida shi, kishiyata ma baidashi babu wanda ya yarda da magana ta, Mijina ya koreni, yamin koran kare, nakoma garinmu dayake dagani sai yayana iyayenmu suka haifa shima ya koreni wai bazan jamai abun kunya ba yana babban mutun a kauye karnazo naraba ma kauyensu kanjamau, haka nai garari aduniya da ciki ajikina” Tasakeyin shiruuu tana kallon bowl na fruits din tace “har yau har yau bansan tayaya nakamu da HIV ba Riyad, haryau bansani ba” saikawai tafashe da kuka dayasa idanun Riyad sukai ja yasauke kanshi kasa Mama tabashi tausayi and wlh he believed her cus you can see honestly a maganan ta, her body language, maida bowl din tayi ta ijiye tace “cikin garari na haifi Rashida, komi nawa saida na saida just to sustained bata madara dan ban bata nono ba haka likitoci suka gayamin, ina zuwa clinic lokacin da karfina nafara aikace aikace ina goyata ahaka nasata school ta taso tanada ilimi  har yar baiwa ake kiranta lokacin, cikin wahala sosai Rashida ta tashi, ba gatan uba ba gatan yan uwa, just ni kadai takedashi, tun batasan menene HIV be sabida yanda jama’an unguwa ke constantly singing dinshi akanta tazo tasan menene shi, tana wajajen JSS1 karfina yasoma gasawa as small as that girl sai ita tasoma zuwa gidajen danake aikatau tanayi amadadina nina zauna agida sabida rashin lafiya tundaga lokacin kawowa yau Rashida dakake gani itace ci na, sha na, suturata, wajen zamana, magunguna na, kudin makarantan ta da komi, anywhere da zata samu aiki tayi she wants to go sabida batason taje taroki kowa yamana abu, ko an kawo mana taimako bata amsa, she’s 23 but she works like a 45yrs old man” Mama tai shiru tasa hannu ta share fuskanta chan tace “Riyad I’ve become a burden arayuwan y’ata, I’ve become a curse in her life, I believe idan na mutu she will enjoy life better….” “Mama!” Riyad yakirata da sauri, fashewa dawani irin kuka Mama tayi takalli Riyad tana bubbuga zuciyanta ta saman riga tace “I am hurt sabida I have the best daughter a duniya dabana iyama komi kawai nasata a wahala ne, I am selfish Riyad dan dana haifeta dazan iya kaita gidan marayu amman nace nizan raineta ta taso suffering, yara yammata irin ta suna gidan iyayensu akillace nawa na garari aduniya from morning to night bata airport, bata shagon abinci, bata hotel tana shara da wanke wanke da wanke bayi just to make ends meet, so I am selfish Riyad”  Mama tafara sheshekan kuka da kawai kasan matan nan ta tara abu dayawa azuciyanta ne tace “na zaman ma Rashida alakakai arayuwa, na zaman mata annoba, sabida ni kullum aiki take, kowace yar budurwa na gidan iyayenta na jin dadi iya yen na nemo abinci su bata taci ni tawa ke gararin duniya ta nemo tabani naci, I’ve burden my poor daughter, I don’t deserve to be her Mother wlh I do not!!” Tashi Riyad yayi ahankali yazauna bakin gadon dan kukan da Mama take is getting too much, calmly yace “Mama don’t say that, you are wrong Mama!” Ahankali yace “kinsan yanda yarki ke sonki kuwa?” Saikuma yasa hannu a aljihunshi ya ciro handky yamika mata yace “goge fuskanki Mama nabaki labari” da kyar Mama tasa hannu ta karba ta share fuskanta tass takalli Riyad da jajayen idanunta, dan murmushi yayi just to calm her down but jiyake kaman yamata kuka shima yace “Mama all abubuwan dakike tunani akan yarki is totally wrong cus I see complete opposite of abinda kika fada” dan shiru yayi kaman mai tunani chan yace “all I see a idanun yarki is you are her motivation, her inspiration, her strength, her confident, Mama kece dalilin dayasa yarka is strong! Fearless and resilient, bold, I witness how she fought with her soul sabida ke Mama!” Dan murmushi Mama tayi ganin haka yasa Riyad yace “Mama ke kinga yanda tayi ne ai harni namiji saida na tsorata kartazo ta hada dani” daidai lokacin Mama ta kwashe da dariya yanda yayi maganan was sooo funny, ganin tai dariya yasa cikedason kwantar mata da hankali yace “Mama karki taba tunanin ke burden ce arayuwan ta ko curse all I see is kece the whole entire reason na existence nata, Mama yarki na sonki fiyeda tunaninki and duk yaran dake son iyayenshi bata taba daukansu koya kallesu a matsayin wahala kowani abu trust me Mama” murmushi Mama tayi tana kallonshi har cikin ranta taji sanyi da maganganunshi yace “idan you want her to keep being her ki warke kiji sauki sabida hankalinta ya kwanta Mama inba hakaba rashin lafiyanki will shatter her tiny little heart I’m sure ko’ina take yanzu hankalinta rabi da kwata na kanki she might not concentrate ko a school right”? Gyadamai kai Mama tayi ahankali saikuma chan tace “nagode Riyad, you made me feel good” murmushi yamata yace “kici abincin ko zakisha yoghurt”? Gyadamai kai Mama tayi freely kaman ta sanshi da dadewa kawai saiya sauka daga gadon yabude ledan daya kawo yaciro komi yakawo ajuwa dates, ruwan Zamzam babban gora dakuma yoghurt, cup ya dauka na tea da aka kawoma Mama yaje ya zubar Mama sai binshi da kallo take ta natsu da yaron kaman tasanshi da chan, yataho da cup din ya tsiyaya mata yoghurt din aciki yabata karba tayi ahankali tace “bani dabinon” dasauri yabude daya yabata ta karba yadawo ya zauna tashiga sha tanacin dabinon wlh haka ya zauna da ita sai hira suke kaman sun san juna har Dr yashigo yadubata yadan shiga hiran shima na 5min kafin yawuce yatafi wajajen zuhur yafito yatafi masallaci ana idarwa yadawo yazauna Mama tace “bakaci komi ba” cikinshi yataba yace “kuma yunwa nakeji sosai Mama tea kawai nasha dazan fito” dasauri Mama tace “tashi kaje gida kaci abinci dan Allah” zaiyi magana aka bude kofan dakin da sallama Rashida ce tana sanye dawani material ja dogon riga ne har kasa ta yafa gyale baki kayan sun mata kyau sosai ta goya jakan school abaya da pink crocs din nan akafanta sai wayanta dake hannunta tana gumi a goshi dan da kafa tazo gashin gaban kanta duk sun kwanta, ko kadan batasan zata ganshi ba ganinshi yasa ta hade rai sai kawai ta shigo ta ijiye jakanta kan kujera tazo ta gefenshi takai hannunta da sauri ta taba goshin Mama tace “Mama ya jikin meke miki ciwo yanzu”? Dauke kanshi yayi daga kallonta Mama tace “lafiya na kalau” da idanu ta nuna mata Riyad hakan yasa ba yabo ba fallasa tace “sannu” wayanshi yaciro yashiga dannawa Mama tamata dakuwa da hannu hakan yasa ahankali tace “ina yini” shiru yayi chan yace “fyn” sai shegen jiji dakai sabida yaga yanada hotel halama na babanshine ba nashi ba tafadi aranta, maida wayan yayi a aljihu yamike tsaye yace “Mama bari naje”dasauri Mama tace “nagode nagode Riyad Allah maka Albarka nagode kaji saika dawo agida Mama” “zasuji” yayi maganan yana juyawa yawuce yafita wucewa wajen wardrobe na dakin Rashida tayi taciro kudin tarike a hannu tace “ina zuwa Mama” kafin Mama takirata harta bude kofa tafita daga dakin dagudu tabishi abaya ita bama tasan sunanshi ba hakan yasa ta kasa kiranshi gashi wayanshi na kunne har parking space yabude mota ya shiga mota yana kokarin tadawa tai knocking glass din hakan yasa yasauke glass din kasa ya zubamata mayun idanunshi haka nan taji gabanta yafadi kawai saitaji muryanta ya makale, dan gyaran murya tayi kadan duk yana kallonta sannan tadago hannunta dake dauke da kudin ta mikamai yabi kudin da kallo da aka daure da lobari sannan yajaye idanunshi dagakan kudin yazuba mata manyan idanunshi still baice komiba aranta tace “amman anyi dan wulakanci anan” saikuma ta daure ganin kallon kudin me yake mata tace “150k ne nan, sauran kudin daka kashe I will pay you back small small” dauke kanshi yayi daga kallonta ya kunna motan kaman wanda akace dole yayi magana yace “keep your money ban bukatanshi” jitayi ranta yafara tafarfasa sabida yanda yayi maganan a wulakance ta kalleshi tace “nikuma ban bukatar taimakon ka ko angayamaka i need your help to take care of my mother ne”? Da kokarin yin reverse yake but jin maganan ta yasa ya dan dakata yakalleta yace “you need all the help Rashidahhh!” Faduwa gabanta yayi yanda yakira sunanta saikuma amsan daya maida mata yadawo mata wani irin sparking taji tanayi zatai magana taga yayi reverse abinshi yana kallonta yana saka wani bakin glass a idanu sannan yajuyar da kan motan yafice abinshi kaman ta kurma ihu takeji.



Post a Comment

0 Comments