TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sanyi da zafi page 6

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

  ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 6️⃣

Wallahi kanshi ma sarawa yafarayi jin maganganun da Mom kemai, first of all duk wani abun na sarautan su bayaso saisama baya iya zama agarin, baison hayaniya baison how they do things cus is always fighting, makirci and politics, and baijin tunda ya girma yatabayin cikakken 2months like good 60days agidan ba bini bini yabar country, lokutan salla ne yasan dole yake dawowa sabida yanda Baba ya maida abin mandatory yanason duka yaranshi to be home sabida hawan salla and other activities na al’adu, shi mutum ne da baisan mulki he prefer business nashi, he derive joy a business, it gives him purpose, for aure kuma dudda yasan culture nasu ne amaka aure abaka mata but shi kwata kawata baitaba sanin Mom zatamai hakaba cus Mom is highly educated and expose, itama bata cika biyema culture ba saisa ma take barinshi to live his dream life, ko kadan bai shirya aure ba cus bayason commitment for now, his plan is nan da 2yrs zaiyi aure yanzu kawai aure baya lissafinsa, dukawa yayi ahankali gaban Mom yadafa kafanta kaman zaiyi kuka yace “Mommmmm” ahankali itama Mom tana kallonshi tace “Riyaddddd! You don’t have to say abinda zaka fadi kasan nasanka sama da kowa aduniya ko?” Gyadamata Kai yayi Mom tace “I know how you despise sarauta, mulki infact bakamasan komi akaiba, I know for auren zakace baka shirya ba bakasan damuwan mace da sauransu” sai kawai takai hannuwanta tai cupping face nashi cikin tattausan lafazi tace “dama akwai abinda zan taba so aduniyan nan dabaza ka iyamin ba Riyad”? Ahankali Mom tace “I thought nine number 1 dinka like you always say”? Dasauri cikin raunin murya Riyad yace “Mom u are my number 1 kema kin sani” kai tsaye Mom tace “inhar nine number one din naka then karka karamin gardama kan maganan nan it’s an order allow me to do everything am I clear?” Yadade yana kallonta yanda take kallonshi babu wasa kan idanunta yasa ya sauke kanshi kasa alamun dai baiso but baice komiba, baya iyama Mahaifiyarshi gardama, cikin fushi Mom tace “kamin shiru? Ban isa dakai bane ko ban isa nace maka haka nakeso kayi kayiba”? Tai maganan tana shaking leg in anger, abu yahadiye awuyanshi har saida taga motsin adam apple nashi asanyaye yace “okay” tsayarda shaking leg din tayi tai murmushi sai kawai ta matso ta mannamai peck agoshi tace “I wish kowacce uwa zata sami d’a mai mata biyayya kaman Riyad dina data zama very very lucky, Allah maka albarka kaji, Haleema is a good girl tana matukar sonka tun tana yar yarinya, she will keep my son happy I’m sure of that, so karka damu, zancen sarauta kuma I will teach you everything and you will do well kaji”? Gyadamata kai yayi zuciyanshi duk ba dadi duka duka kwanan Babanshi nawa da rasuwa but kowa is after kujeranshi, look at matayensu kaman ba mazajensu ne suka rasu ba dukansu kokarin daura yaransu kan Sarautar suke sunma manta da rasuwan shima yanzu yazama sarkin one day haka matarshi zatayi kenan itama yana mutuwa all focus dinta will be yanda danta zai gajeshi bamatada lokacin yimai addu’a tashi kawai yayi yajuya yayi kofa.


Mom tabishi da kallo ranta fess, dolema Riyad dinta yadinga intimidating kowa, yafi duka yaran sarki kyau ga kwarjini ga haiba ga natsuwa, ga jan aji, ga kudi, ga rashin magana, ga rashin shiga mutane, gashi baida kallon mata shi kadai keda qualities na sarki and bazata hutaba saita maidashi sarki wannan alkawari ne!.


Dakinshi yashiga Munir dake danna laptop yabishi da kallo ganin yanda mood dinshi ya chanza tashi daya,   Wucewa yayi yafada gado yakife cikinshi tareda lumshe idanu Munir baicemai komiba yacigaba da abinda yakeyi abinshi.


Yana fita Mom ta daga wayanta takira matan Waziri da ake kira da Mariya ringing daya ta daga wayan tace “ranki shi dade Uwardakina, Allah yaja zamaninki Umman Riyad” dan murmushi Mom tayi kafin cikeda isa da jiji dakai tace “dole gobe Haleematu zata koma makaranta ne”? Dasauri Mariya tace “ai Uwardakina ko makarantan kikace karta kara zuwa saita zauna” jinjina kai Mom tayi tace “tom inaga bazata tafi goben ba dan zan turo Riyad yazo ya ganta inaso nahada su aure inyaso bayan yaganta zata iya tafiya” wani ihu Mariya tayi cikin waya saikuma ta zube kaman tana gabanta tace “nagode nagode Uwardakina da wannan karamci naki, kidubi kowa na gidan nan amman kuka zabinma Yarima Riyad Haleematu nagode, namiki alkawari bazaki taba samin matsala damu ba, I will forever be loyal to you, Haleema zata bautamiki Uwardakina, kuma da yardan Allah kujeran sarautan nan ta Yarima Riyad ce ai naji jita jita, da yardan Allah shine magajin sarki” dan murmushi Mom tayi tace “Waziri ya shigo yakirani” tana maganan ta katse waya wani ihu Mariya tayi tamike da gudunta tafice zuwa dakin  Haleematu kai tsaye tabude kofan yarinyar na zaune sanye da rigan bacci tana kokarin hada kaya Maman kawai ta dagata tana juyawa tana rawa abinma saiyasa Haleematun dariya tace “Mommy menene kike murna haka”? Cikeda jin dadi tace “yanzun nan Sarauniya Maryama takirani tace tanason hada aurenki da Yarima Riyad gobe ma zata aikoshi gidan nan” wani kalan zaro idanu Haleema tayi she can’t believe abinda taji tun tana yar yarinya takeson Yarima Riyad yahadu ne over wlh, lips nata rawa suka fara farinciki yahanata magana tace “Mommy mekikace? Yarima Riyad mene? Dan Allah maimaita”?Kyalkyacewa da dariya Mama tayi tace “dalla cewa nayi za’a aura miki Riyad zaki zama matan sarki dan ina mai tabbatar miki shi za’a bawa Sarautan” ihuuuu tayi tareda wani kalan tsalle ta rungume Mamanta sai kawai tahau tsalle sosai lekowa dakin Waziri da shigowan shi kenan yayi ganinsu yayi murmushi waya na kunnenshi Mama zatamai magana yadaga hannu yace “inajinki ranki shi dade” wucewa falo yayi yazauna Mama da Haleema suka biyoshi a speaker yasaka wayan dashi da Mom ke magana suna shirya komi kaman ba mutuwa aka musu ba, planning auren da yanda zasu sami kujeran suke hankali kwance.

**



Wuraren 10 yafito daga dakinshi yana sanye cikin wani farin yadi da akamai dinkin jumper yamai kyau sosai sai kamshi yake zubawa kaman zaije gasan turare, binshi da kallo Mom tayi tana murmushi tace “Son katashi? Munir yashigo yakai sau uku nacemai bai isa yatasheka ba, bayan kunyi sallan asuba tare a mosque” karasowa yayi yazo kusadab da ita yazauna ahankali yace “morning Mom” as usual pecking nashi tayi a goshi tareda shafa kumatunshi tace “morning Riyad, yaya jikin? Zakai breakfast yanzu ne”? Girgiza mata kai yayi alamun no, dasauri tace “to maza je Gwaggon ku ta aiko dazu akiraka kadawo saikai breakfast kafin kafita fada ko”? Dan gyadamata kai yayi yatashi ahankali yayi kofa haryasa hannu zai bude kofan tace “idan tamaka maganan auren Haleema kai naam” dasauri yajuyo da kanshi ya kalli Mom dauke kai tayi kafinma yamata wani maganan, dan jim yayi sannan yabude kofa yafita ma’aikata fada sun cika wajen yawanci Mom bata barinsu falo so anan waje suke yashe kaman kaya, gaishe gaishe da kirari sukahau mai ya wuce abinshi ko kadan baison zuwa wajen Gwaggo shi kadai hakan yasa yaciro wayanshi daga aljihu dailing number Munir yayi ringing daya yadaga yace “kana’ina”? Daga dayan bangaren yace “ganinan daure da towel wanka zan shiga” dan yatsine fuska yayi yace “be fast to” ya katse wayan baiso ya koma ciki dan baiso Mom tasan baijeba kuma baison yayita tsayawa awajen hakan yasa yawuce flat din su Munir wanda da dan tafiya sai gaidashi ake bai amsa kowa har gaban flat din tsayawa yayi jimmm awajen sai chan yasa hannu yabude kofan da sallama ahankali hada idanu yayi dawata mata dake zaune a falon sanye da hijab da charbi a hannunta kaganta kaman ita tai kakinshi ta tofar sunyi kama sosai, itama tanada haske kaman shi, sauke kanshi yayi kasa da sauri sannan ahankali yashiga ciki tareda maida kofan yarufe yama kasa magana, tadade tana kallonshi sannan tasauke kanta kasa tace “Munir nasama kaje ka sameshi” gyadamata kai yayi sai chan kaman me tsoron magana yace “ina kwana Mami” batare data kalleshi ba tace “yajikinka dafatan basu maka komi ba”? Dan dago kanshi yayi yakalleta ganin kanta akasa yasa shima ya maida kanshi akasa yace “I’m fine” daidai lokacin Munir yaleko daga sama daure da towel yace “ina fitowa daga bayi naji kamshin turarenka wlh daukomana breakfast kataho dashi” mugun kallo yamai saikuma kawai yawuce dinning din yazauna yana bude warmers din saman table din,  ganin shayi dayaji kayan kamshi mai zafi dasauri ya zuba a cup ya debi waina da pepper soup yadade rabon dayaci traditional food kawai yahauci bini bini Mami na dago kanta tana kallonshi dudda yabama falon baya, sosai yakecin abincin dan yanada ci yana cikin ci wayanshi yahau ringing ganin Mom yasa yahadiye wainan bakinshi da sauri yakai wayan kunnenshi kafin yayi magana cikin kakkausan murya strictly Mom tace “kana ina Riyad?” Kasa magana yayi yay shiru cikin masifa sosai Mom tace “okay sabida na barka tareda Munir shine yanzu gidansu kake zuwa kasan nida matan nan bamayin juna but you keep going there kana ganin gidan nan kowani yaro najin maganan uwarsa ni ban isa kaji nawaba ko ai shikenan kayi duk yanda kakeso…..” “Mommm!” dip ta katse wayan dasauri yatashi yajuyo sauke kanshi kasa yayi cikeda girmamawa yace “Mami bari naje in Munir yafito yasameni awajen Gwaggo” ahankali Mami tace “okay” kofa yayi dasauri yabude yafita tabishi da kallo sai kawai ta sauke ijiyan zuciya, wajen Gwaggo yawuce, Babban flat ne uwa gari guda, ga hayaniya ana shiga da fita masu aiki sai gaidashi ake kaman anga sarki amman ko kallon mutum daya baiyiba harya shiga dankareren falon Gwaggo, dudda dakin yacika da mutane yana shiga Mai Babban daki ta sallami kowa falon yarage daga ita sai shi yawuce wajenta yazauna yayi shiru, fuskanshi Gwaggo ta taba sannan takama hannunshi tabi da kallo tana dube dube tace “yaro jiki uwa na baturai kai kenan baka isa kaga kazanta ba” murmushi yayi ya fizge hannunshi yace “Gwaggo ni na warke kidena dubamin jiki dan Allah” tsuki tayi tareda hankadeshi tace “kaga shashasha” Hararanshi tayi tace “ni shiga dakina ka dauko huran dana dama maka daga babanka sai kai kap cikin jikokina keson furana” jikinta yayi sanyi shima haka sai yayi shiru ganin yanda yayi yasa da sauri tai murmushi tace “bance kamin fuskan mara lafiya ba, Allah shiya bani babanku kuma shiya amsa Alhamdulillah d’ana yayi abubuwan alkhairi da dama aduniya yayi shukoki daban daban, ya gina makarantu, rijiyoyi, gonaki dan haka banda nadama Allah ubangiji yakai haske kanarinsa jeka dauko” tashi yayi ahankali yadauko kwaryan fura yazo yazauna yafarasha anatse tana kallonshi harga Allah itama zatazo Riyad yazama sarki cus yarone mai tausayi mara hayaniya ga kwarjini ga biyayya sannan ga kwazo, baida sa ido, shine yaro na farko kap yaran sarki daya fara neman nashi da kanshi, tun ana gulma ana cecekuce but marigayi yace abarshi yayi abinda yakeso dudda kalan kudi dayake dashi baitaba raina wani ko yadingaji yafi kowaba gashi da tausayi ya tsani yaga wani na fushi ko kunci sanadiyanshi dan haka itama Riyad ne zabinta daman tariga ta jefamai kuri’a. Ahankali tace “zabinka ne diyar Waziri ko zabin Mamanka Maryama dan nasanta da tsinannen taurinkai, dason saka kabi ra’ayinta sabida taba Allah ya yoka me biyayya, kaika zabi Haleematu”? Abu yaji ya tsayamai awuya but ya daure ya gyadama Gwaggo kai batare dayayi magana ba, Gwaggo tace “ai shikenan za’ai magana idan anyi bakwai na babanka muji, zanma Baffan ka Muji magana nama kirashi daman” daidai nan Munir yashigo yana zama akai sallama Mujitapha yashigo yana sanye da manyan kaya daya fito da katon teban daya ijiye sai kyalli shaddan jikinshi yake kana ganinshi kasan yasha kudi ya koshi waje ya samu ya zauna hakan yasa daga Munir har Riyad suka gaidashi atare. “Ina kwana Baffa” binsu yayi da kallo shikebin mahaifinsu yanason yaran wanshi baida matsala dasu, yanason ya gaji sarautan but then again idan baisamu ba no big deal idan any of yaran wanshi suka samu, adai dauko wani sarki ne daga cousins nasu da sauransu shine bazai yarda ba, anatse yace “kai yajiki? Kasami lafiya?” Gyadamai kai Riyad yayi Baffa yace “har yanzu ana kan investigation koma su waye sukai kokarin kasheka za’a kamasu, so don’t worry, it’s good zakai aure koda bakai maganan ba ma yana cikin plan dina nace kafito da mata you need to settle down shi lokaci baya jiran kowa mutuwa ake kullum” Munir ya kalla daketa sunnar dakai yace “kaikuma fa yaushe zaka fito da taka matar?” Dasauri Munir yadago kanshi saikuma ya nuna kanshi foolishly yace “Baffa ni” akufule Baffa yamai dakuwa yace “a’a ni” Gwaggo ta zubamai rankwashi tace “dan kaniyanka kaima kafito da mata akace” kabar da hannun Gwaggo yayi yana turo baki yakalli Baffa yace “toh Baffa zan fara nema daga yanzu” gyadamai kai Baffa yayi yace “kutashi kuje toh lemme speak to Mama” tashi sukayi suka fice daga dakin.

Direct dakin Mom yayi yana bude kofa Mom tace “get out Riyad” gaban kofan ya tsaya yace “sorry Mommy please Munir naje kirafa yarakani wajen Hajiya”



Cikin fushi Mom tace “tell me Riyad akwai abinda kataba so daban maka ba? You showed me duk cikin yan uwanka Munir kakeso dudda ban shiri da mahaifiyarsa but nabarka dashi but na gayamaka kadena zuwa side dinsu banso banso yare nake maka daka kasa fahimtata eh?” Ahankali yafara tafiya yakai inda take sai kawai ya rungumeta ashagwabe yace “I am sorry Mommyyyy bazan karaba kinga banda lafiya karki fushi dani please am missing Dad already abin zaimin yawa” shiruu tayi saikuma ahankali tace “okay nahakura but baka ba ita that woman is the reason har Babanku ya rasu baya shiri dani she come between ni da shi, allow me to plan your wedding and coronation in peace kaji” sakinta yayi sai kawai ya daura kanshi kan cinyanta ahankali yace “Mom kimin auren na yarda but please Mommy banson nazama sarki dan Allah I am too young to be Sarki, Mom I want to tour round the world with my wife in peace” cikeda fada tace “kaje sama da 58 countries wani tour round the world ne yarage bakayi ba? Is time kayi taking responsibility naka Riyad, you are royalty Riyad, kai Royal blood ne ba normal samari out there ba, duk wanda aka haifa a royal family akwai high possibility zai iya zama king so accept your calling, and Babana zai turo bodyguards dazasu dinga binka anywhere and everything” dasauri yatashi yace “Mom banso wlh banso” wani kalan kallo tamai tace “did you even know su waye da waye ke kokarin kashe ka?” Kallonta yayi yace “suwaye?” Tana kallonshi tace “I don’t know but my gut is telling me Yayanku from the way yake eye service dan he’s everywhere, da yarinyar nan bata cecekaba I don’t know what would’ve happened” dan ijiyan zuciya Mom tasauke cike da damuwa tace “kullum bana baccin dare sabida tunanin wasu out there are trying to kill my son” dan lumshe idanu Riyad yayi ahankali yace “Mom lemme see the footage” iPad dake gefenta agadon tadauka ta bashi daidai lokacin akai sallama yar aiki ta gayamata tai baki tashi tayi tawuce tafita shikuma ya kwanta ahankali kan gadon tareda playing footage din da aka samo daga airport din yana kallo kusan footage biyar ne daban daban tun na shigowan shi arrival hall dana elevator saina bayin wanda shine na ukun, tsare cleaner yarinyar da ido yayi, a lokacin da abin yafaru bai wani kalleta ba dan yana cikin tashin hankali sai yanzu yake kallonta on this footage dudda is not that clear video karkar dinnan but yanda ta turashi cikin sharan yakala da yanda tarufe da how she handled everything ahankali yace “who is this feisty gurl”? The way takebin music yake kallo, he was actually watching the footage to see kozai gane criminals din but yana fara kallo attention nashi kawai yadawo kan cleaner, har footage data kaishi wajen dumping shara yakala da yanda take tafiya sai kawai yayi pursing video tareda zooming face nata yace “who are you? You saved my life.”




Post a Comment

0 Comments