TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sarauniyar kyau page 55-56

 *💋SARAUNIYAR KYAU💋*

*Takun Farko*



______________________________________________________________________💥👑𝑻𝒉𝒆 𝑮𝒍𝒂𝒎 𝐐𝐮𝐞𝐞𝐧👑💥____________________𝑩𝒚:𝑻𝒉𝒆 𝑵𝒂𝒊𝒏𝒂𝒓𝒉 𝑲𝒅____𝑲𝒉𝒂𝒅𝒆𝒆𝒋𝒂𝒓𝒕𝒉.  𝑺𝒂𝒃𝒊'𝒖.  𝒀𝒂𝒉𝒚𝒂𝒉🤙



☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆

💦𝑳𝒂𝒇𝒂𝒛𝒊 𝑾𝒓𝒊𝒕𝒕𝒆𝒓'𝒔 𝑨𝒔𝒔𝒐𝒄𝒊𝒂𝒕𝒊𝒐𝒏💦🤙


☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆☆




🎀🎀ϝιʋҽ ʂƚαɾ'ʂ ɯɾιƚҽɾ'ʂ🎀🎀


ᵀᴴᴱ συɾ σɾԃιɳαɾყ  ᴼᴺᴳᴼᴵᴺᴳ ᴮᴼᴼᴷ'ˢ



1:ȥαɳ ʝιɾα ƙα

       ɳα

A'isha Alƙali

            /ɱɾʂ αყʂιႦ/



2:ιɳ Ⴆα ƙαι

         ɳα 

Fateemah .M. Kabeer

               /συɱ αϝɾҽҽɳ/




3:ɾαʂԋιɳ ʂαɳι

             ɳα

 Fatahiyya Moh'd Yakasai

                  /συɱ ყαʂɱҽҽɳ/



4:ʂσɳƙι ɳҽ ƙαԃԃαɾα ƚα

                   ɳα

          Fateemah Abdullahi

                    /Ⴆαƚσσʅ ƙαɱႦα/



5:ʂαɾαυɳιყαɾ ƙყαυ

                ɳα

 Khadeejarth Sabi'u Yahyah

                   /ƚԋҽ ɳαιɳαɾԋ ƙԃ/








Page *55&56*




Tana fitowa daga bedroom ɗin ta kai tsaye bedroom na mijinta Abubakar Mai Kyau ta wuce batare da tayi knocking ba, dan a tunanin ta yanzu kuma shikenan sun haɗe.



Tasa hannu ta tura ƙofar a hankali, ta shiga, baya nan a palon bedroom ma  hakan.


Can ciki ta wuce a hankali ta tura kanta ciki tana leƙen sa.



Zaune ta hangoshi saman wata doguwar sofa mai mazaunin mutum biyu dake manne da bed ya ba ƙofar yaba, domin kuwa yana kallon bed ne, ga waya manne a kunenshi.



Shiru tayi tana so ta fahimci hanyar da wayar da yake yi ta nufa, duk da cewa a nutse yake yi daɗi da ƙari kuma a hankali yake abin sa.

Amma wannan bai hanata jiyo abin da yake faɗa ba.


Abin ya gigita ta sosai, sannan yasa ka dukkanin jikin ta ɗaukar rawa kamar mazari


Duk da yanayin tashin hankali da maganar da taji suna fitowa daga bakinsa suka je fata, hakan bai hanata gyara tsayuwar ta ba, tana kuma jin maganar da yake fitarwa waɗanda suke nema su saka zuciyarta ta tarwatse, ba tare da ta shirya ba.






"Haba dai, ya zaki dinga faɗar hakan bayan kin san cewa baku haɗa iyaye da ita ba, kodai bakya sona ne?."






Ɗan shiru ya yi domin ya sama damar jin abin da zata ce.

Ajiyar zuciya ya sauke sannan cikin ƙara ƙasa da murya ya kira sunan ta




"Haleesat Rashid Rayyan..!'


Bai jira ta amsa ba ya ci gaba da cewa "Muddun kin yarda da ƙaunar da nake miki, kuma kema ɗin kina sona.! To kawai ki bari na turo magabata na  nanda five months, nasan zuwa lokacin na gama duka wasu shirya shiryen da suka kamata sannan idan ma bakya so ku zauna a gida ɗaya da 'Rafi'at, wannan ba damuwa bane zan iya a je ki a ɗayan gidana."





Shiru ya kuma yi sannan ya ciro wayar daga kunen shi yana dubawa.

"Ta kashe wayar da gaske fa. Katse min kira tayi fa."


Ya faɗa a fili kuma yana sauke hucin ɓacin rai.




Ganin yana shirin juyowa ne yasa Rafi'at da tayi suman tsaye, tun a lokacin da taji ya kira sunan 'Haleesat Rashid Rayyan'.

Saurin rufe ƙofar tayi ta juya da sauri sauri tabar bedroom ɗin.





Tana fita daga bedroom ɗin a maimakon tayi hanyar bedroom ɗin ta, bin hanyar ɗan ƙaramin kitchen ɗin dake anan upstairs ɗin tayi, ta shiga ciki.

Zama tayi a d`aya daga cikin kujerun dining dake kitchen a maimakon taji hawaye sun zubo mata kamar yadda tayi tsammani.

Neman su tayi ta rasa ashe dai hawaye ma rahama ne a wasu lokutan, domin ita gashi yau tana neman su ruwa a jallo amma ta rasa.






A kalla takai mintuna goma a haka bata sani ba, ta riga da ta faɗa a duniyar tunanin yadda zata yiwa tufkar hanci.





Ajiyar zuciya ta sauke tana sakin murmushin nan dai nata mara tabbas.



Ganin zama a wurin babu abin da zai ƙara ma ta illa ciwon kai, yasa ta miƙe ta fito daga kitchen ɗin.




Bedroom na mijinta Abubakar mai kyau Abin ƙaunar ta a kullum ta kuma komawa sai dai wannan karon tsayawa tayi cak a bakin ƙofar sannan ta saka hannun daman ta tayi knocking, kusan sau uku sannan yazo ya buɗe ma ta, murmushi tayi sannan cikin tsananin girmamawa da ƙanƙan da kai ta ce.



''Good evening Mister, dama cewa zanyi ne Dinner ya kammala a Dining room…"




Shiru tayi bayanta faɗan haka tana jira taji abin da zai ce.



"It's okay je ki ina zuwa."




Ya bata amsa a yayin da yake komawa ciki.


Rafi'at ji tayi tamkar ya watsa ma ta ruwan zafi a duka jikin ta, amma sai ta daure ta shanye kamar yadda ta sha alwashi.



Murmushin takaici ta saki a fili cikin ƙasa da murya ta ce



"Zaka shigo hannu ne, duk ranar da ka sake ka shigo hannuna. Ni Rafi'atu Rafiq Rayyan. Na Rantse da Allah mai girma zaka ɗanɗani kuɗar ka..."




Ta kumayin dariyar bosawa Like a zararriya, sannan tayi gaba Downstairs ta sauko ta ƙarisa Dining room ta ja kujera ta zauna, kana tayi saving kanta duk abin da zata buƙata shima tasa masa abin da ta fahimci yana so.




Komawa tayi ta zauna sannan ta ɗauki fork tana caccakar pounded Yam dake gabanta tamkar ta sama Haleesat Rashid Rayyan take gani.


Ta ɗauki tsawon mintuna biyar a haka, sannan ta jiyo sassayan ƙamshin turaren sa yana hallartar duka ƙofofin hancinta.



Kana daga baya mamallakin wannan sassayan ƙamshi mai haskaka zuciya ya bayyana cikin kyakyawar shiga.



Murmushi tayi sannan cikin kashe murya ta ce Bayan ya zauna ke nan "Barka da ƙari sowa Mister Mai Kyau."





"Yauwa Barkan ki dai fatan kin wuni lafiya?."



"Lafiya qalau Wallahi."




Ta bashi amsa cikin sauri, ya kuma tambayarta


"Ya baƙunta kuma?."




Murmushin jindaɗi tayi kana ta amsa da


"Awesome."




Ci gaba da fira sama sama sukayi, suna cin Dinner ɗin su, har suka kammala a tare, tashi ya yi ya bar wurin da alama bedroom nasa zai koma.





Kallon murmushi tabi bayansa dashi bayan ya ƙule tayi dariya a fili ta ce "Abubakar Sameer Lamiɗo mijina Mai Kyau, ni kaɗai ba tare da wata mace ba, muddun kuma wata mummunar makauniyar kaddara ta saka wata mace tayi kuskuren zama mata a gare shi, hmn hmmm hhhhh ina tsoron kaina, dan ban san abin da zai biyo baya ba Wallahi..."🔥






Tayi maganar tana kuma sheƙewa da dariyar bosawa Like a zararriya woman.😅



Sai da ta kammala gyara Dining table ɗin tsaf sannan ta kwashe plates da suka yi amfani dasu, kana ta wuce kitchen ta wanke su gaba ɗaya ta jeresu a ma'ajiyar su."





Fitowa tayi ta haye Up kai tsaye bedroom nata ta nufa, tana shiga kamar yadda tasa barwa kanta bathroom ta shige tayi wanka da Brush da alwala sannan ta fito, cikin ƙaramin lokaci ta shirya cikin sleeping dress.





Sannan ta hau saman mattress, ita batayi bacci ba, ita batayi wani abu ba.


Kawai dai tunanin mijinta take duk da cewa basu taɓa kasancewa a tare ba, amma tunanin shi takeyi sosai.

Wani lokaci?. A'ina?. Da yaushe?. Saboda wani dalili?.


Gaba ɗaya bata sani ba, abu ɗaya kawai ta sani shine tana son mijinta Abubakar Mai Kyau. tana ƙaunarsa da duka zuciyarta.


Tana masa son da batayi wa kanta, tabbas ta sani ƙaunar da take masa tayi yawa, ta sanie tana masa son da yafi a kira shi da, 'MASEEFAR SO' sai dai a kira shi bala'in ƙauna.


Tana ji a ranta da duka zuciyarta zata iya yin kisa akan shi, idan ta ce "Kisa tana nufin kashe mutum ɗan Adam har lahira."🙄





Tana cikin wannan tunane tunanen ne ta jiyo knocking a hankali sama sama.


Kasa kunenta tayi a domin taji shin da gaske ne, ita ake wa wannan knocking haka?.


Ilai kuwa tabbas ƙofar bedroom nata taji ana bugawa, du ba agogo tayi ƙarfe sha ɗaya na dare. Ta ga agogon ya nuna.






Saukowa tayi daga saman mattress ɗin kana ta nufa ƙofar ta buɗe.

Tsuru tayi tana kallon mutumin dake tsaye gabanta sanye cikin sleeping dress na maza, hannayen sa, gaba ɗaya cikin trouser pocket ɗin sa.




Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta bashi hanya ya shiga ciki.


Ita kuma ta mayar da ƙofar ta rufe, saman bed ya zauna yayin da ita kuma ta zauna daga saman wata doguwar stool, tana kallon shi cike da mamaki can ƙasan zuciyarta kuwa ba za ta iya kwatanta irin farin cikin da take ciki ba.






Ajiyar zuciya ta sauke tana kuma kallon sa cikin ƙasa da murya take faɗin



"Mister Mai Kyau, me kazo yi nan, a wannan daren, kuma a daidai wannan lokaci wurina?."




Ta jero masa tambayoyin tana zuba masa manyan idanunta.

Murmushi Mai Kyau ya yi kamar yadda shima yake Mai Kyau kana Yace 

"Wai ni kam, wannan sunan ba za'a canza min bane, ko dai har yanzu ba'a ɗaukeni a matsayin miji ba ne?."



Shi ma ya yi maganar yana zuba ma ta kyawawan idanun shi yana kallo.




Ɗan murmushi tayi, Aha lallai ba shakka, sai yau, kuma yanzu sannan dai dai wannan lokacin ta yadda cewa Namiji ba shi da kunya ko kaɗan kuwa, domin ko bata tunanin mijinta Abubakar Mai Kyau yana da kunyar, mutumin da ya gama waya ɗazu ɗazunnan da ƙanwar ta yana faɗa ma ta irin son da yake ma ta amma yanzu saboda lokacin da ake raba kunyar yana kwance saman royal bed, shi ne zai zo ma ta da wani ƙauli da ba'adi.

Ita sai yanzu ma ta fahimci abin da yake nufi.

Wato dai wannan Bawan Allah yana nufin yace haƙƙin sa yazo karɓa.🙃





Murmushi tayi, ita ba shashasha ko kuma sakaryar mace ba ce, tunda haƙƙi yazo nema aikuwa zai sameta sabuwa fil a leda, shi zai ɓare abin da. 🤐









A fili kuwa ƙasa tayi da kanta wai kunya kana cikin kashe murya da kisisina ta ce





"Toh ni kuma mai zance?."



Tayi maganar kamar wata sakarya, murmushi Abubakar ya yi sannan yace "Ki zaɓa mana, ga sunaye nan kala kala."


Qara ƙasa tayi da kanta tare da faɗin "To My Lawful..."





Wani haɗaɗɗe kuma ƙayataccen murmushi ya kuma saki sannan Yace "Okay aikuwa naji daɗin wannan suna da aka sakamin, wato Your halal. To yanzu dai your lawful yana da buƙatar SARAUNIYAR KYAU ta shiga bathroom tayo alwala a domin suyi sallar godiya ga Allah. Ya yi maganar ne cike da zaulaya kamar... 🤓



Da sauri ta miƙe ta shige bathroom tana rufe fuska wai kunya, tana shiga a maimakon tayo alwala ta fito a'a, tsayawa tayi tana kallon kanta a jikin madubi dake a bathroom ɗin, dogon tsaki taja tana sakin murmushi kamar ta zare, cikin hura hanci ta ce "Wani wai sallar godiya ga Allah."



Ta kwaikwayi muryar shi, taja qwafa sannan ta fara alwala, bayanta kammala ta fito tana rufe da fuska, hijabi ta ɗauka dogo ta saka sannan ta shimfiɗa musu sallaya a wurin da aka tanadar domin yin sallah, kana yaja su Raka'a biyu kamar yadda addini ya hukunta.




Bayan sun idar kamar yadda aka saba tambayoyi ya yi ma ta akan addininta ta bashi amsa fi ye ma da tambayar sa, murmushin jindaɗi ya yi sannan sannan...🔥


Daga wannan Ranar, daga wannan dare, daga wannan lokaci sabuwar Rayuwar Aure suka buɗewa juna, duk da cewa ba wani soyayya da kulawa yake nuna ma ta ba.


Amma kuma a kullum kwanan duniya a saman faffaɗan ƙirjin shi take kwana, Rungume da juna sannan kuma a bedroom ɗin sa.🙄


    







   





 __*BAYAN_SATI_BIYU*

    

    

    

   



A Ranar da suka cika sati biyu da Aure Abubakar Mai Kyau shi da Amaryarsa Rafi'atu suka je gidansu Rafi'at a domin duba iyayenta.


A  Ranar kuwa Hajiya Zinaru mahaifiyar su Rafi'at da kuma Alhaji Rafiq Rayyan mahaifin su Rafi'at ba ƙaramin daɗin ziyarar da suka kawo musu suka ji ba, daɗin daɗawa ganin yadda Rafi'at har wani haske na jindaɗi tayi.


A Ranar duk wani motsin Haleesat Rashid Rayyan da Abubakar Mai Kyau a idon Rafi'at yake faruwa, tana kallon yadda Abubakar yake so su haɗa ido da Haleesat, amma ita kuma taƙi bashi dama.


Qwafa taja kawai tana ƙara matsawa jikinsa sosai, ta yadda zata fahimci idan Haleesat Rashid Rayyan tana son mijinta Abubakar Mai Kyau.


Aikuwa ta fahimci komai, dan kuwa tashi Haleesat Rashid Rayyan tayi ta bar musu wurin idanunta sun cicciko da qwalla.



Bayan barin Haleesat Rashid Rayyan  wurin ne Alhaji Rafiq Rayyan yake faɗa musu cewa, "Ai ita ma Haleesat ta sama miji, kuma sunansa Abubakar yanzu ma yana shirin zuwa gidanne a domin su ganshi daga nan a saka biki.


A ranar ba ƙaramin farin ciki Rafi'at tayi ba jin cewa Haleesat Rashid Rayyan ta sama mijin Aure ke nan dai zata rabu ma ta da mijinta ta huta, a Ranar har suka koma gida cikin farin ciki take.




Post a Comment

0 Comments