TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Yadda Kaddara taso page 50

 *BABI NA HAMSIN (50)*


TAFIDA POV.

“Ki fito ga ni na zo”

Yana faɗin hakan ya aje wayar sa kr kare a kunnensa, yanzun kusan ƙarfe shida ne na yammma, dan yau kusan yini ya yi a asibiti.

Tun da suka doso motar yake kallonsu ita da wata da besanta ba har suka iso wurin motar.

Ƙofar gaban ya buɗe ya fito, gaisawa suka yi da wadda ya gansu taren.

“Sundar ƙawata ce, sunanta Hafsa”

Tafida ya juya ya kalli Hafsa.

“Sannu ƙawarmu ya kike, ya al'amura”

Hafsa na washe baki tace.

“Wallahi komai lpy”

A hankali ya gyaɗa kansa sannan ya kalli Maryam.

“Muje Miriam”

Daga haka kuma ta yi sallana da Hafsan sannan ta shiga motar ya tayar suka tafi, sai ta ga ya ɗauki hanyar unguwar kantin waje.

Har suka kai wani gida bata ce masa komai ba. A parking lot ya yi parking suka fito a tare.

“Gidan Mairama ne, ƙanwar mahaifi na”.

Sun kusan kaiwa minti goma zaune a makeken falon gidan, kafin wata hamshaƙiyar mata ta fito tana taku cike da isa da ƙasaita, kallo ɗaya Maryam ta mata ta gano kamarta da me martaba.

Cike da girmamawa Maryam ta duka gaisa da Maryam, kafin tasa a yiwa yaranta magana suka zo suka gaisa da Maryam ɗin, wata ce wai ita Asiya ta bi Maryam da kallon raini sannan ta miƙe zata bar falon.

“Ke Asiya, ba ki gaida matar wanki ba”

Asiya ta juyo tana wani yatsina fuska.

“Sbd Allah wannan zan gaisar ?, jibeta fa, wata villager da ita...”

“Asiya bana san iskanci, ke da da aka ce ki aure shi ba ƙi kika yi ba, se yaunzu za ki zo kina wa mutane iyayin banza da wofi, ki bata haƙuri yanzun nan”

Ba haka Asiya ta so ba,amma koda wasa basu isa musu da Mairama ba,dan haka tace.

“Sorry”

Daga haka kuma ta juya, Mairama ta sallami sauran yaran nata sannan ta dubi Maryam.

“Ki yi haƙuri takwarata”

Maryam ta girgiza mata kai.

“A'a ranki ya daɗe babu komai ”

°°°

Maryam da ke kallon window ta ji hannun Tafida ya riƙo nata, ta juyo ta kalke shi.

“I am sorry Miriam, ba ta san wacece ke ba shi yasa tace haka, ita fa ƴar uwata ce, kwanaki aka ce ta aureni, amma tace ita bata san monster”

Sai kuma ya yi murmushi me sauti.

“A time ɗin ban ji haushinta ba, amma yanzu na ji, sbd nasan ni ba monster ba ne, Tafida Eshaan ɗin Miriam ne”.

Maryam ta yi murmushi, wato yanzu baya san sunan da yake kiran kansa da shi a da, se de a cikin ranta ta ayyana irin wannan abun da take gudu tun sanda aka ɗaura aurenta da Tafida. 

“Kuma duk da ina monstern, amma ke naga kina so a haka”

Dama ita tasan da walakin, dan bisa ga dukkanin alamu sun nuna cewa Asiya fa kishi ta ke. Bata cemasa komai ba kawai ta ci gaba dakallonsa.

Fada ta ga su nufa, kuma ta ji daɗin hakan dan ko ba komai zata je ta ga Fulani da Nadra.

“Nadra bamu waje”

Wannan Muryar ta Fulani ta faɗi a sanda ta shigo falon da Maryam da Nadra ke ciki, Nadra ta saka Maryam a gaba se zance take mata.

Sim-sim Nadra ta fice daga falon. Fulani ta nemi kujera ta zauna kusa da Maryam tana mata murmushi.

“Babu abinda zance da ke Maryam se godiya, dan sosai na ga canji a tare da ɗana, naga har wata ƴar ƙiba ya yi”

Maryam ta yi dariya tana sunkuyar da kai.

“A'a ranki ya daɗe, ba ni ya kamata a godewa ba, Allah zamu godewa, kuma akwai wata magana da nake so na miki.....”

Fulani bata ce komai, ta yi ahiru tana jinjina hankali da tarbiyar yarinyar.

“Ranki ya daɗe ya kamata a ce kina jansa a jiki, ciwonsa yana buƙatar ja a jiki, yana buƙatar ya samu wanda ze riƙa faɗawa damuwarsa, yana san a ja shi a jiki sosai, ta haka ne ze faɗa miki duk wani abu dake damunsa”

Fulani ta kasa cewa komai, ta kafe Maryam da ido kawai.

“Salamu alakimu”

Sallamar Tafida da ga waje ta katse musu hanzari.

Ya shigo ciki ya zauna.

“I dan kun gama zamu iya tafiya?”.

“Muna ƴar hirar tamu zaka ɗauke min sirikar tawa”

Ba Tafida ne kawai ya yi mamakin sakewarta ba, harda Maryam da ta bata shawara, bata tab'a zaton zata ɗauki shwarar ta haka da sauri ba.

“A'a kawai dr naga dare ya yi ne, shi yasa nace zamu koma”

Bisa ga mamakinsu sai suka ji ta yi dariya.

“Babu damuwa, zaku iya ta fiya, ammam dan Allah ku dawo gobe”

Muryarta a sake kuma cikin raha, Tafida xai iya rantsewa da Allah bai tab'a jin muryarta cikin wannan yanayin ba.

*Unguwar Garko*

*12:00pm*

“Da Allah wace zan samu ta min lalle idan zamu tafi ?”

Cewar Maryam yayin da take saka alkakin da Maanmu ta saka aka mata a cikin leda.

Yau kusan satinsu ɗaya a haɗejia, kuma suna sa ran tafiya zuwa jibi, ta yi ziyara sosai, dan har dangin Abban su seda suka je, hatta da gidan kawu usman da da bata san zuwa sbd ƴaƴansa da suke mata kallon reni, dan ita bata san a renata.

Amma kuma wannan zuwan da ta yi haba-haba aka riƙa yi da ita, gaba ɗaya mutanen gidan sun sauya mata, bata ce ga dalili ba, amma wata ƙila dan ta yi aure ne, ko suna mata dan ta auri me kuɗi, ko kuma ma dan matsayin wanda ta aura ɗin.

“Ga Ummi me funkaso, ai har yanzu tana yi” 

Hafsa ta amsa mata tana tayata kwashe al'kakin.

“Ni fa ɗan gam nake so”

“Duka ta na yi, zan mata magana se ta zo har gida ta miki”

“Yaushe kenan ?“

“Gobe ya yi ?”

“Allah kaimu goben to”

“Amma ba za ki yi kitso ba ?”

Cewar Maanmu dake aje musu bokiti cike da dubulan, dan takanasa ra kano ta sa aka yiwa Maryam ɗin dubulan da al'jaki, dan ta san tana san su.

“A'a Maanmu banda kitso.....”

Caraf Hafsa ta yi tace.

“Ina ita in yin kitso gashin kanta ya koma irin na indiyawa”

Maryam ta girgiza kanta, Iya Ummi bazafa tab'a sauyawa ba.

“Yaya ga farar”

Maryam ta kai hannu ta karb'i ledar da Muhsin ke miƙa mata, dan ita ta aike shi ya siyo mata fara, sbd tana san fara sosai.

“Yauwwa Autan Iyarsa, na gode”

“Maanmu, Hafsa, Anti Hanne fara ”

“Wa ?!, ni jikar Haruna, kin tab'a ganina naci wata fara?“.

Cewar Maanmu.

“Miƙo min na ci”.

Hafsa ta faɗi tana tsane hannunta daga cikin bokitin dibulan.

“A'a alhamdulillah“

Anti Hanne ta faɗi a sanda take kunna gas, dan yanzu sun ma bar aiki a ice a gidan.

TAFIDA POV.

Yau be samu dama ya je ya ɗauki Maryam ba, dan tace masa lalle za'a mata, kuma shima abubuwa sun masa yawa ga shi gobe zasu bar garin.

Ko abinci be samu ya ci ba, haka ya dawo gidan cikin sa fanko, gashi a gidan babu abinci. Kwanciya kawai ya yi a falo yana saƙe-saƙe.

Jin an turo ƙofar yasa shi miƙewa zaune, Maryam ce ta shigo bayanta biye da masu gadi sun ɗauko mata kaya, ita ta nuna musu inda zasu aje mata sannan ta musu godiya suka fita.

Kallonsa kawai take Tana san gane meke damunsa.

“Me ya faru ?”

Tatambaya a sanda take zama kusa da shi, tare da aje flask ɗin hannunta. Ya furzar da iska.

“Wallahi yunwa nake ji”

“Allah sarki, kaga kuwa na taho maka da abinci, dan nasan yanzu ba samun damar ci kake ba”

Ta ƙarashe tana janyowa flask ɗin ta buɗe.

“Muga lallen”

Ya kama hannyenta data riƙe murfin flask ɗin da su, ya shiga jujjuya hannun yana kallo lallen, da aka tsantsaramata shi, wanda ya kwanta a kan farar fatar ta.

“Ya yi kyau sosai”

Ta ɗanyi murmushi.

Janta ya yi zuwa cikin jikinsa, wannan abun da ya saba kai kawo a cikin kan Maryam ya shiga aikinsa.

“Bani abincin to”

A hankali ta kai hannunta ta janyo flask ɗin, sannan ta shiga bashi abincin tana masa hira.

*11:30*

Maryam na jere kayan sakawarta a cikin jakar da ta zo da ita. Ƙofar ɗakin a ka turo, kuma ko bata kalle shi ba tasan shine, dan haka bata kalle shi ɗin ba, ta ci gaba da jera kayan.

Tana jin takunsa har ya tsaya a bayanta, kuma shima be jira komai ba, ya saka hannayensa biyu ya ɗaga ta sama, yay mata ɗaukan bride style.

Maryan ta zare ido tana kallonsa, sannan ta cilla ɗankwalin atamfar da ke hannunta cikin jakar.

Tafiya ya fara yi da ita har zuwa kan gado, ya kwantar da ita yana shirin rufa mata bargo. Ta yi sauri ta miƙe zaune.

“Kaya fa nake haɗawa....”

“Sshhhhh, ki kwanta kawai sai da safe”

Ya faɗi yanaa ƙara kwantar ta, Maryam ta ƙara miƙewa.

“Idan na ce sai gobe makara zan yi”

Shima kuma ya ƙara kwantar da ita, sannan ya kwanta a gefenta, ya motsa hannunsa ya kashe wutar ɗakin.

Maryam da kanta ta murgina kusa da shi, dan gwara ko motsinsa ne ta ji a cikin duhun nan.

“Baki dena tsoro ba har yanzu ?”

Ya tambaya yana motsa kunnensa. Yana jin kanta da ta girgiza masa, shima kuma se ga gyara kwanciyar tasa yana sakata a cikin jikinsa.

“Ina nan tare da ke, hmmmm?”

Ta kuma gyaɗa masa kai.

HARIS POV.

“Kai Uchenna aiki na kyau“

Cewar Falaƙ, a sanda suke duba comments ɗin masoyan waƙar sa ta biyu da ya saki, waƙoƙinsa yanzu sune ke zagaya duniya baki ɗaya. A cikin wattanin ba ƙaramar shahara ya yi ba.

Albarkoki daga ko ina zuwa suna ta zuwa, yazu ya sauya musu gida, amma kuma a cikin cosgrove ɗin ya sauya, kawai de ya bar nasa na da, ya koma wanada ya fishi, hatta da Babansa ya sai masa gida. Babu abinda zai ce sai dai ya godewa Allah dan waƙa ba ƙaramin karb'arsa ta yi ba.

“Muna tayaka murna Uche”

Djn studio ɗin ya faɗa. Ya miƙa masa hannu suka gaisa, sannan ya shiga gaisawa da sauran abokan aikin nasu.

Wajejen ƙarfe 8pm ya koma gida, a falo yaga Arya shi ɗaya yana wasa.

Aryaan na ganinsa ya shiga daga masa hannu, alamun ya ɗauke shi, Uchenna ya masa dariya yana ɗaukansa, tare da dan ƙa masa chocolate ɗin da ya shigo da shi.

Ya san cewa war haka Hanam tana kitchen, dan haka kai tsaye ya wuce kitchen ɗin, a nan kuwa ya sameta tana ta faman haɗa girki.

Bata ma san da shigowar su ba sai da ta ji hannu ɗaya ya yi hugging ɗinta ta baya, se da taja wata iska, sannan ta juyo tana kallonsu, dan tasan ba shi kaɗai ba ne.

“Kufa bakwa jin magana, so kuke se kun sa na makara a girkina”

Haris ya yi dariya.

“Yau makara ta nawa kuma ?, takwas fa ta yi, amma baki gama girki ba”

“Ku min shiru ni, kuje waje ku jira ai na kusa gamawa”

Memakon su fitan kamar yanda tace, sai suka zauna a kan kitchen island, ya shiga yi wa Aryaan wasa, yana yi yana bawa Hanam labarin nasarar da aka samu.

Har ta gama abincin ta juye musu a kwano ɗaya, dan yanzu duk rintsi a kwano ɗaya suke cin abinci su duka ukun.


*House No.122, B3, Alaro city lekki, Lagos*

MARYAM POV.

Hannunta ya saka riga ta ƙarshe a cikin wardrobe ɗinta. Sannan ta rufe wardrobe ɗin.

Dawowa ta yi ta zauna a kan gadonta, tana ɗaukan wayarta, ji ta yi zuciyarta na ta shi, hakan yasa ta miƙe da gudu ta yi banɗaki.

Ta shiga kela amai kamar zata ƙarar darm ruwan dake jikinta. A galab'aice ta miƙe tana kunna famfon sink, ta wanke bakinta, sannan ta fito.

Kusan karo na biyu kenan tana amai a yau ɗin nan. Yau da safe suka sauƙa a lagos, bayan sun tsaya a abuja, sannan suka iso lago ɗin.

Kuma suna dawowa Tafida ya tafi shopping shi da David, ba zata ce ga takamemen abinda yasa take aman ba, amma kamar tana tunanin pizzar da suka ci a air port ne, sai da tace ba zata ci ba amma Tafida ya takurata se da taci.

Ita tasan dama cikinta ba san baƙon abu yake ba. Ji ta yi ma zaman ɗakin ba ya mata daɗi, dan haka kawai ta fita, kuma bata tsaya a ko ina ba se saman gidan, dan tana ganin wata ƙila zata samu daddaɗar iska a wajen.

Ta ɗan jima zaune a waurin tana shan iska, kafon ta hangi shigowar motar Tafida, dan haka ta miƙe ta sauƙa.

Tana tsaye a falo ta ji sanda ya buɗe ƙofar kitchen ta baya. Bayan ɗan wani lokaci kuma ya shigo cikin falon ta ƙofar gaba.

Yana ganinta ya buɗe mata hannayensa biyu, alamun ta taho ta yi hugging ɗinsa, kunya tasa ta sunkuyar da kanta ƙasa.

Shi kuma be ce mata komai ba har ya ƙarsa inda ta ke, kuma yana isa inda take ya ja hannunta ta faɗa jikinsa sannan ya ƙanƙameta, kansa ya sauƙa a kan kafaɗunta.

“Ke biki yi kewata ba ko ?”

Mamaki ya kama Maryam, dan be wani jima da fita ba. Ya saketa yana kallon fuskarta, a hankali Maryam ta tsirawa idonsa ido, ganin yanda yake ƙifƙifta shi, kuma se da abinda baya so ɗin ya faru. Wato ƙwayar ta koma ja.

“Ba yanzu ka fita ba?”

Se ya ɗauke hannunsa da ga ƙugunta, ya dawo da shi gefen fuskarta yana motsa shi a hankali.

“Baki sani ba ne Miriam, ko da da minti ɗaya idan na matsa daga kusa da ke kewarki ce ke kamani, bana san na yi nesa da ke ko kaɗan”.

Maryam ta kwantar da kanta a hankali a kan ƙirjinsa, tana jin sautin bugun zuciyarsa a kunnuwanta.

Ji ta yi ya yi pecking kanta sannan ya ƙara riƙeta cikin jikinsa.

“I love you, Miriam”

Maryam ta kewaye hannyenta biyu a bayansa.

“I love you too Shona(sweetheart).




Post a Comment

0 Comments