TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sarauniyar kyau page 9-10

 *ⓟⓐⓖⓔ 9&10*


🄺🄰🄽🄾


    

🅹🅸🅴🅳🅳🅰🆁🅷♥︎🅚🅞🅜🅐🅘♥︎🅝🅐🅚🅐


A gurguje take shirin tana jin Humaira na ƙwala mata kira zasu tafi airport ɗauko "ABBA" zai dawo daga ƙasar Australia. Da sauri ta ƙara murza Jan baki a laɓɓanta tana kallon kanta a dress mirror saida tayi juyi sannan ta ɗauki wayoyinta  da handbag ɗinta ta fito tana yafa scarf ɗinta.


A palo kuwa Humaira ta cika tayi fam fam domin kuwa saura kaɗan ta fashe, da sauri ta ƙarisa saukowa downstairs ɗin da sassarfa ta ƙariso wajen Humaira bata tsaya jin abunda Humaira za ta ce ba ta jawo ta tana faɗin "afuwan my sis zo muje" ba yanda Humaira zatayi haka tabi bayan Jieddarh suka fita dan tuni Auntie tana jiransu a mota ita da Heesham da yake shi zai kaisu airport ɗin.


***

Sun isa airport lokacin saura five minutes jirgi Yayi Landing, dan haka suka tsaya jira basu wani daɗe suna jira ba jirgi ya sauka, a hankali fasinjoji suke saukowa duk gabaɗaya su jieddarh sun bada hankulansu suna jiran fitowar sa.


A hankali farin dattijo wanda akalla bazai wuce shekaru Hamsin zuwa da uku ba yake taka mattatakalan jirgi yana saukowa, Humaira ce ta fara hango shi aikuwa da sauri ta ƙarisa gurin shi bata tsaya jiran wani Abu ba ta rungumeshi tana faɗin "welcome Abba we miss you highly."


Murmushi kawai yake saki yana bubbuga bayan ta, lokacin ne su Jieddarh suka ƙariso gurin fuskar ko wannensu ɗauke da walwala.


"To ae saiki sakeshi ya huta ko, kin wani maƙalƙale shi, Like a baby girl!, Jieddarh ta faɗa cike da barkwanci dan kuwa duk, wanda yasan Jieddarh yasan ta da barkwanci,She`s flirting girl.


Dariya Humaira tayi tana faɗin "nayi kewar ABBA obaa highly shiyasa", ta faɗa lokacin da take sakin shi.


A haka dukansu suka yi hugging ɗin shi cike da farin ciki da Nishaɗi, Auntie ce ƙarshen yi da akazo kanta sai taƙi yin hugging ɗinshi wai tayi fushi saida aka gama da yara sannan za'a tuna da ita?.

Dariya sukayi dukansu hadda Abba Jieddarh ta ce "haba Auntie ae yanzu ba take akeyi ba tamu Abban mu yake ke kinyi tsufa kalli yadda kike tafiya kamar zaki yi kasa fah,  habah Auntyn mu kinyi zamanin ki fah wannan ƙarnin mune fah."


Dukan wasa Auntie ta kai mata da sauri ta ɓuya a bayan Abba tana dariya qwafa Auntie taja tana faɗin "zan kama ki ae fitinanniyar Yarinya kawai hmm hmm."


Dariya Abba yayi ya ce "ba ganewar da zatayi ae gaskiya ta faɗa dan haka a qyale min ɗiyata.


Heesham ya ce "da kunzo antafi gida a ƙarishe drama ɗin acan." 

"Aikuwa dai da zaifi armashi" cewar Humaira Ita ma.

Gabaɗaya suka ɗunguma gurin mota suka ƙarisa Heesham ya shiga mazaunin driver, Humaira kuma a gefan mai zaman banza, Yayinda Jieddarh dasu Auntie suke a kujerar baya Jieddarh tana nanuƙe da Abba a Haka har Gida.


     


           


   ⒶⒷⓊⒿⒶ


🅷🅰🅻🅴🅴🆂🅰🆃♥︎🅜🅐🅘♥︎🅚🅨🅐🅤


Bayan fitan su Lailah school ɗaki ta koma kai tsaye Wayarta ta ɗauka ba tare da Wani ɓata lokaci ba, ta lalubo lambar xixi na ƙasar faransa ta danna kira, Sai dai a kashe wayar take.


 Yanzu ma Bayan tsawon mintuna Talatin, ta kuma kiran tana mai addu'ar Allah Yasa xixi ta ɗauka, saboda akwai maganar da take so ta mata, shin ko akan meyasa takeson dawowa Nigeria da karatunta bayan kuma ita ta zaɓa karatu a Abroad.


Cikin sa'a kuwa wannan karon xixi ta ɗaga kiran.


Wata nannauyar ajiyar zuciya Haleesat ta sauke tana mai zama akan Royal bed ɗinta.


"Hello!! xixi," Haleesat ta faɗa Cike zaquwa.

On the Other hand ƙasar faransa, xixi ta amsa da....

"Hello!! Aunty leesat ya kike?"....

"Am so Normalcy," "kefah naji muryar ki kamar ta mai kuka meke faruwa?", aikuwa kamar ta ce ma xixi ta ƙara volume ɗin kukan ta ne, ƙara sautin kukunnata tayi, cikin kukan take faɗin "Aunty leesat ni gida kawai zan dawo na gaji da wannan ƙasar ta faransa,muguwar ƙasa,ni kawai Nijeriya zan dawo soon.


cikin rarrabewar murya Haleesat tace "xizzixi! xixi!! calm down just relax, natsu ki faɗamin abinda ya sameki kinji,"

Still cikin muryar kukan xixi ta ce "ni kawai gida nakeso na dawo, na gaji da wannan muguwar ƙasar wallahi." ta ƙarishe maganar  tana mai fashewa da kuka higher.


"Tofah" Haleesat ta faɗa tana furzar da huci tunda taji xixi na kuka tasan abin ya cutura, a hankali cikin muryar lallashi ta ce "xixi shiga video call kawai domin zamufi enjoying na maganar okay!!."


"Tom" xixi ta ce tana kashe wayar sannan ta shiga video call ɗin ita ma Haleesat kan sofa ta koma ta zauna sannan ta shiga video call ɗin ita ma, nan take wata kyakyawar matashiyar budurwa ta bayyana wacca ba za ta wuce shekaru goma sha tara ba, tana kwance saman royal bed jikinta sanye da top red color da wando jeans pencil dogo black color ta ɗaure dogon gashin kanta da red nd black Ribbons tayi style in ponytail idanun nan nata kuwa sun koɗe sunyi jajur, fuskarta ta kumbura alamar dai taci kuka ta godewa Allah, dogon hancinta shima har wani ja, yayi saboda matsan da yasha. pillow rungume a chest ɗinta ta ƙanƙame shi cikin muryar kuka ta ce "Aunty leesat!".


Zaro ido Haleesat tayi tana bin xixi da kallo ganin yadda duk tabi ta rame tayi zuru zuru da ita. "xixi kece kuwa?"xixi Menene meke faruwa dake haka ne duk kinbi kin rame". Haleesat ta tambaya cikin shiga tsananin violence.


Qara ƙanƙame pillows ɗin dake ƙirjinta xixi tayi ta rufe bakin ta da duka hannayenta ta kasa cewa komai saima kukan dake ƙara taho mata.


"Okay natsu kwantar da hankalinki sai kimin magana" Haleesat ta faɗa tana ƙara waro ido tana bin xixin da kallo gabaɗaya ta fita hayyacinta kamar ba ita ba, ajiyar zuciya ta kuma saukewa a karo na babu adadi sannan ta kira sunanta.


A Hankali "xixi! faɗamin abinda ya faru kinji?, kodai baƙyajin daɗin zaman gidan Uncle Yunus ne?, girgiza kai xixi tayi alamar a'a, "to menene ko a school ne?", nanma girgiza kanta ta kumayi alamar dai a'a. "to kin gaji da paris ɗinne kinaso ki dawo Nigeria gurin mu?.


Girgiza kai tayi, sai kuma da sauri ta ɗaga kanta alamar eh Hakane, murmushi Haleesat tayi sannan ta ce "wato kewar mu kike yi ko?", eh xixi ta faɗa tana sauke ajiyar zuciya to yanzu me kike nufi Haleesat ta Tambaya tana jiran amsa.


Dan kuwa tasan xixi ɓoye mata kawai tayi wannan dalilin bashi zaisa ta rame haka ba akwai dai wata a ƙasa.

"Okay kinsan menene ki daure ki kwantar da hankalinki ki samu ki ƙarisa wannan term ɗin kinga yanzu kina level one going to level two ki daure ki ƙarisa kin san dai daddy baya tolerating nonsense ki daure ki ci gaba karatun ki nasan ba gaskiya kika faɗamin ba amma na miki uzuri duk time ɗin da kikaga ya miki zaki iya faɗamin abinda ke damun ki, kinji ko Tawan," Da to xixi ta amsa tana sakin murmushin ƙarfin hali.


"Okay to sharre hawayen naki kinji baby xixi na Autar momy kuma Autar gidan mu daga ke ba ƙari ko anaso ko ba`aso," Fashewa da dariya xixi tayi, ita ma Haleesat ɗin dariyar takeyi.


Muryar Labiba taji ta bayanta da sauri ta juya tsaye take, ta harɗe hannayenta ta baya tana sanye cikin Turkish gown riga doguwa milk color bata sa mayafi ba sai veil da ta yafa a kanta  fuskar nan nata a ɗaure tawau.


Qarisowa tayi saman gadon ta zauna sannan ta ce "Aunty leesat karki bi ta wannan yarinyar tunda ta iya zurfin ciki tun one week da ya wuce take wannan kukan anyi lallashin duniyar nan ta faɗa abinda ke damunta taƙi faɗa," Labiba ta ƙarishe tana hararar xixi.


Dariya Haleesat tayi sannan ta ce "ae kunfi kusa ko kin manta saboda ke ta dawo nan ƙasar da karatunta ta barmu Anan,"


Dariya Labiba tayi ta ce "gashi kuma taƙi faɗamin abinda ke damunta gabaɗaya na shiga damuwa,"  "ae rabu da ita kawai idan taji wuya zata faɗa ne" Haleesat ta faɗa tana murmushi, "ke dae Aunty Leesat barta kawai karma ta faɗaɗin zamuga wanda zai bari ta dinga yin ƙunci a gidanan," Labiba ta faɗa tana ƙara tamke fuska alamar bada wasa take bah, nan dai Haleesat da Labiba suka ci gaba da fira tsakani,ita kuwa xixi idan taga dama ta saka musu baki idan kuma bata ga dama ba sai dai tabi su da ido, sun ɗauki lokaci suna wayan kafin suyi sallama Haleesat ta kashe wayarta a hankali ta lumshe kyawawan idanun ta.


Tunani ta faɗa lokacin da xixi ta kammala secondary school ɗinta, lokacin xixi dagewa tayi sai ta koma paris da karatu wajen Uncle Yunus ɗinsu wai tare takeso su ci gaba da karatun tareda Labiba ɗiyar Uncle Yunus a paris dayake, Age mate Suke Labiba taba xixi wata biyu a duniya, alokacin har ciwo ta kwanta dan daddy ya hanata zuwa paris karatu saida ƙyar aka samu ya barta ta tafi shine yanzu wai kuma zata dawo itama tasan ba'a take dan daddy ba yarda zayyi ba har saita kammala degree tukunna, murmushi Haleesat ta saki a fili tace xixi rigima silly girl kawai kuma autar gidanmu😝


Tashi tayi ta faɗa wanka takai tsawon mintuna talatin kafin tafito ɗaure da towel White color.

Gaban dress mirror ta tsaya tana busar da dogon gashinta da handDrier saida ta busar da gashin, sannan ta aje Drier ɗin a mazaunin shi.


Shiryawa tayi cikin indian dresses gown iya gwiwarta pink mai adon stones purple da wando jeans pencil dogo pink and purple shima, ribbons tasa ta tufke sumarta da ƙyar don yawan da sumar take dashi domin kuwa kaf gidan daga Zaynerb sai Haleesat sune masu tsayi da yawan gashi over highly,ita dai Afeefah sai dai ta nuna musu yawan gashi sosai domin gashinta akwai yawa sosai don ya wuce gadon bayanta ya sauka har mazaunanta.

Ɗaukar mayafin kayan tayi ta yafa akanta ba tare da tasa hula ba tana shirin ɗaukar wayarta domin kiran Wata Maryam classmate ɗinta domin su tattauna akan Bikin maryam ɗin daya kusa, Ta tajiyo muryar momy a palo tana ƙwala mata kira.

Palon ta fito ta sama guri ta zauna a saman two siter ita ma momy Rafi`at ɗin guri ta samu ta zauna tana fuskan tar Haleesat ɗin "Haleesat".


Momy ta kira sunan ta ba tare da ta ɗago daga latsa wayar da takeyi ba ta amsa da "na'am momy akwai wani abune?"


Gyara zama Momy Rafi'at tayi bata damu da yanayin yadda Haleesat ta amsa mata ba ta fara magana.

Haleesat ki natsu magana mai muhimmanci nakeso muyi dake Yanzunnan.

Mayar da wayar dake hanunta gefanta Haleesat tayi sannan ta fuskan ci momy Rafi`at ɗin "Yeah! inaji wata magana ce wannan ?".

"Haleesat yanzu haka zamu saka ido a Gidannan wannan shegiyar Yarinyar nan ta dinga juya kowa yadda takeso kamar wasu bayinta ki duba ki gani ɗazu da zata fita a gaban mu taba wancan kucakar House maid ɗin can  sa'adah dubu ɗari biyu, to wallahi idan muka bari irin haka ta ci gaba da faruwa tofa wata rana Gidannan sai yafi ƙarfin mu gashi ɗazu naji wai ana maganar an zaɓe ta a gasar 𝐒𝐀𝐑𝐀𝐔𝐍𝐈𝐘𝐀𝐑 𝐊𝐘𝐀𝐔 matakin jaha kuma naji ana maganar saura one month.....

Ɗan tsagai tawa da maganar Momy Rafi'at tayi tana kallon yadda Haleesat ta mayar da hankalinta gabaɗaya kanta tana sauraronta.


Murmushin gefan fuska Tayi sannan ta ci gaba da cewa "Kuma tana cin gasar nan nasan ba za ta tsaya ba saita je na ƙasa daganan kuma saina duniya,mu kuma Zuwa Lokacin baƙin ciki Ya kashe mu"😱


"Yanzu na yanke shawarar kota halin qaqa bazan bari taci gasar nan ba gobe zanbi  Flight zuwa China gobe."

"Na Rantse da Allah Mai girma indai ina numfashi a duniya bazan bar yaran haajarah su huta a duniya ba yaran da mijina ya fifitasu sama da nawa yaran" ta ƙarishe maganar tana huci kamar wata kububuwa..


Miskilin murmushin gefen baki Haleesat tayi sannan ta ƙara gyara zaman ta akan Royal sofa ɗin kana ta fara magana, momy kenan wani lokacin kina bani mamaki saiki dinga abu kamar yarinya yanzu wannan ƙaramar alhakin ne saikin Tafi har can China akanta, irinsu makirci ma kaɗai ya ishesu yanzu ga YaYarta Zaynerb duk da bansan ko Menene ainihin abinda ya sakata a Halin shayashaye ba amma nasan da saka hannunki ciki sabosa nasan wacece ke sama da kowa right, ɗan shiru Haleesat tayi yayinda suka shiga kallan kallo tsakanin ta da mahaifiyartata Momy Rafi`at,wai akuya ta mari kura, wani ƙayataccen Murmushin gefan fuska Halessat ta kuma saki sannan bata damu da kalar fitinannen kallon da Momy Rafi`at take mata ba ta ci gaba da cewa,  "Ae koshi kaɗai ya ishesu a Rayuwa ma ba sai an ƙara musu da komai ba,Haleesat ta ƙarishe maganar tana kuma sakin shu'umin murmushin gefen baki...


Wata Kalar Dariyar Bosawa Momy Rafi'at ta fashe da ita tana tafa hannu tace yanzu nasan na haifa ƴa duk sauran yarana duk wawayene yanzu nasan na haifa Yarinyar da zata maramin baya a duk shirina. Haleesat ɗiyata Allah Ya suburbuɗa miki Blessed highly highly kuwa.


Dariya Haleesat tayi ita ma harda ba momy hannu suka tafa kamar wasu yara ba ƴa da uwa ba { T⨳o⨳f⨳a⨳h⨳ T⨳o⨳ A⨳l⨳l⨳a⨳h⨳ y⨳a⨳ k⨳y⨳a⨳u⨳t⨳a⨳ }


A hankali Zaynerb dake laɓe a bakin ƙofar bedroom ɗin ta fara Ja da baya tana rufe bakin ta da duka hannayenta jin wani irin kuka nason qwace mata, Yayinda gabaɗaya Jikinta babu inda baya rawa na tsananin tashin hankali data shiga, Da gudu ta shige ɗakinta ta rufe da key.


Ta faɗa saman bed tana sakin wani marayan kuka ta na ƙarajin mamakin hali irin na Momy Rafi'at, ita batasan me ita da ƴar uwanta suka tarema matar nan ba tabi ta tsanesu a Rayuwa duniyar su, share hawayenta tayi ganin ba kuka ne abin yi ba tashi tayi ta zauna a saman bed tana ƙara tuno yadda taji firan Momy Rafi'at da Haleesat ɗin, Farkon Abin ta fito da niyyar tafiya ɗakin Haleesat suyi magana akan matsalar xixi taji magana ƙasa ƙasa shine ta tsaya dan taji me ake cewa dan ita da farko ta ɗauka Haleesat ɗince take waya da ƙawayenta ashe abin ba haka bane, Gashi taji abinda yafi ƙarfin tunanin ta ashe Haleesat kallon kishe akema rogo muguwar makira ne ba'a sani ba, murmushi tayi sannan a fili furta China ko zanga yadda za'aje china kuwa, Ubangiji Allah ya kaimu goben da rai da Lafiya😇.


Miƙewa Tayi sannan Takai dubanta ga agogon dake ɗaure a tsintsiyar hannunta ƙarfe ɗaya da kwata na rana.


Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta nufa gaban dress mirror ta cire agogon hannun ta sannan ta shiga bathroom, Alwala ta ɗauro ta fito ta shimfiɗa sallaya sannan tayi sallar azahar bayan ta iddar da sallar ba tare da ta cire hijjab ɗin da tayi sallah ɗin ba ta fito daga bedroom ɗinta, kai tsaye kitchen ta wuce Auntie sa'adah ta samu tana aikin abincin Rana, Da murmushi ɗauke a fuskar ta ta ce "Auntie  sa'adah sannu da aiki baki wuce ba kenan?",  Ita ma murmushi tayi ta ce "sai zuwa ƙarfe uku na rana zan wuce insha Allah.


"Okay aunty akwai wani Abu na musamman a kitchen ɗinnan kuwa wanda mai ƙaramin ciki zata iya buƙata na marmari?".


Murmushi Auntie sa'adah tayi sannan ta ce "eh mana Zaynerbu Abuuu akwai, baza`a rasa ba. "Yawwa Auntie a haɗomin akwai mai buƙata cewar Zaynerb tana murmushi, "Ae inaga zatafi son kwaɗo ko bari nayi  ma ta shi kinsan mai ciki akwai son kwaɗayi, "Aikuwa dai Auntie sa'adah ita wannan cikin nata wata huɗu ne shigan na biyar, Zaynerb tayi maganar tana zama a ɗaya daga cikin chairs ɗin dining da aka qawata kitchen ɗin dasu.


Aikuwa kwaɗon dafaffen zogale da quli yaji kayan hadi tayi sannan ta zuba a kula ƴar daidai taba Zaynerb dake kallonta tana murmushi ta ce "gashi an kammala" Amsa Zaynerb tayi tana yima Auntie sa'adah godiya sannan ta fita daga kitchen ɗin.

Auntie sa'adah ta bita da kallon tausayi dan kuwa sosai take tausawa Rayuwar Yarinyar ita da ƴar uwanta Afeefah basu da wata matsala saina Rashin uwa ga mahaifin su shiba mazauni ba gashi sun haɗu da kishiyar uwa mace mai son kanta da Yawa, kai kurum ta girgiza sannan ta ci gaba da aikin ta tana mai musu addu'ar samun ingantaciyar Rayuwa cikin zuciyar ta.


{𝔗𝔬𝔣𝔞𝔥 𝔍𝔞𝔪𝔞'𝔞 𝔐𝔢𝔫𝔢𝔫𝔢 𝔄𝔟𝔦𝔫𝔡𝔞 𝔐𝔞𝔥𝔞𝔦𝔣𝔦𝔶𝔞𝔯 𝔰𝔲 𝔄𝔣𝔢𝔢𝔣𝔞𝔥 𝔱𝔞𝔶𝔦𝔴𝔞  𝔪𝔬𝔪𝔶 ℜ𝔞𝔣𝔦`𝔞𝔱 𝔫𝔢 𝔡𝔞 𝔷𝔞𝔣𝔦 𝔥𝔞𝔨𝔞, 𝔡𝔞 𝔱𝔞 𝔡𝔞𝔲𝔨𝔦  𝔞𝔩𝔴𝔞𝔰𝔥𝔦 𝔪𝔞𝔦 𝔤𝔦𝔯𝔪𝔞 𝔥𝔞𝔨𝔞 𝔞𝔨𝔞𝔫𝔰𝔲 𝔷𝔞𝔶𝔫𝔢𝔯𝔟 𝔡𝔞 𝔄𝔣𝔢𝔢𝔣𝔞𝔥, 𝔄𝔫𝔶𝔞 𝔨𝔲𝔴𝔞 𝔨𝔲𝔫𝔞 𝔱𝔲𝔫𝔞𝔫𝔦𝔫 𝔴𝔞𝔫𝔦 𝔞𝔟𝔲,𝔨𝔲𝔴𝔞 𝔨𝔬𝔡𝔞𝔦 𝔫𝔞 𝔟𝔞𝔨𝔦𝔫 ℌ𝔞𝔩𝔢𝔢𝔰𝔞𝔱 𝔡𝔦𝔫𝔫𝔢,𝔐𝔬𝔪𝔶 ℜ𝔞𝔣𝔦`𝔞𝔱 𝔱𝔞𝔫𝔞 𝔡𝔞 𝔰𝔞 𝔥𝔞𝔫𝔫𝔲 𝔞 𝔰𝔥𝔞𝔶𝔞𝔰𝔥𝔞𝔶𝔢𝔫 𝔡𝔞 𝔷𝔞𝔶𝔫𝔢𝔯𝔟 𝔱𝔞 𝔱𝔰𝔦𝔫𝔠𝔦 𝔨𝔞𝔫𝔱𝔞 𝔠𝔦𝔨𝔦 𝔨𝔲𝔪𝔞 𝔱𝔞𝔨𝔢𝔶𝔦 𝔱𝔬 𝔨𝔬 𝔪𝔦𝔶𝔢 𝔞𝔪𝔰𝔞𝔯 𝔡𝔲𝔨𝔞 𝔴𝔞𝔡𝔞𝔫𝔫𝔞𝔫 𝔗𝔞𝔪𝔟𝔞𝔶𝔬𝔶𝔦𝔫 𝔰𝔲𝔫𝔞 𝔠𝔦𝔨𝔦𝔫 𝔴𝔞𝔫𝔫𝔞𝔫 𝔡𝔞𝔡𝔡𝔞𝔡𝔞𝔫 𝔏𝔞𝔟𝔞𝔯𝔦 𝔪𝔞𝔦 𝔰𝔲𝔫𝔞 🅢🅐🅡🅐🅤🅝🅘🅨🅐🅡♥︎🅚🅨🅐🅤  𝔨𝔲 𝔟𝔦𝔶𝔬 𝔞𝔩𝔨𝔞𝔩𝔞𝔪𝔦𝔫 𝕋𝕙𝕖 ℕ𝕒𝕚𝕟𝕒𝕣𝕙 𝕂𝕕 𝔡𝔞𝔫𝔧𝔦𝔫 𝔴𝔞𝔫𝔧 𝔦𝔯𝔦𝔫 𝔡𝔞𝔯𝔞𝔰𝔦 𝔩𝔞𝔟𝔞𝔯𝔦𝔫 𝔶𝔞𝔷𝔬 𝔡𝔞𝔰𝔥𝔦, 🄺🄷🄰🄳🄴🄴🄹🄰🅁🅃🄷 🅂🄰🄱🄸`🅄 🅈🄰🄷🅈🄰🄷, { 𝕋𝕙𝕖 ℕ𝕒𝕚𝕟𝕒𝕣𝕙 𝕜𝕕 ✍️👑👸📲 }♥︎💖💝 }


Zaynerb bedroom ɗinta ta koma ta canza hijjab iya gwiwa fari dama doguwar rigar pakistan ne a jikin ta blue black sai wando shima na pakistan Red color mai adon stones blue black, kular ta ɗauka sannan ta fito daga gidan gabaɗaya ta nufa gidan maƙwabciyar su mai suna ⓈⓊⓃⒶⒾⓃⒶⓇⒽ!.


🅛🅐🅘🅛🅐🅗♥︎🅜🅐🅘♥︎🅚🅨🅐🅤

  


Ɓangaren Lailah kuwa suna zaune a lecture Room suna ɗaukar lecture ita da Afeefah ne bencinsu a gaba sai bencin su zahrah a bayan nasu sai kuma sauran student, nan wayar Lailah Tayi ƙara alamar shigowar kira waƙar mawakiyar korean  "J.Fla" na Tashi mai taken { Attention }


Gabaɗaya hankulan mutanen dake cikin lecture Room ɗinne ya dawo kanta hadda lecturer ɗin dake musu lecture gabaɗaya sun zuba mata na mujiya har Afeefah dake gefenta suna kallo, Da sauri tayi checking excuse. Lecturer ɗin ya bata dama sanin wacece ita da kuma mahaifinta badan haka ba a ƙa`idar makarantar ba`a zuwa da phone idan ba aiki da ita bane ya taso,amma sanin waye mahaifinta a ƙasar yasa, ba ko musu bai mata ba,balle kuma kallon banza ya bari ta fita ɗaga kiran, kuɗi kenan😇


Fita daga lecture Room ɗin tayi tana sauke ajiyar zuciya tana shirin ɗaga wayar kiran ya tsinke tsuka taja Cike da Takaici, To dama da unkown number aka kirata,don batasan ko waye ba,To koma ta sani indai Laila ce,ba bin kiran zatayi bah.


Zata koma wani kiran ya ƙara shigowa wayar sai dai wannan karon momy ne mai kiranta ba wancan ba.

Ɗaga kiran tayi da sallama.

Daga can Ɓangaren Momy Rafi'at dake zaune saman Royal sofa nata ta kira sunan ɗiyartata "Lailah!", amsawa tayi da "na'am momy da wani abu ne ina class Yanzu please zan kiraki anjima Bye bye, Love you, Bata tsaya jin mai momyn zata ce ba ta katse kiran tana jan tsuka sannan ta kashe wayar gabaɗayanta.

Sannan ta koma Lecture Room ɗin basu daɗe ba Lecturer ɗin ya fita dama daga shi ba wani sai kuma gobe, dan haka fitowa sukayi suka nufo Gida Gabaɗaya.


A mota Afeefah sai tsokanar Lailah takeyi dan tasan bazai wuce sabbir bane ya kirata😇


Ita dai Lailah bata kulata ba driving ɗinta kawai takeyi tanajin yadda Afeefah ke tsokanar ta taƙi kulata har suka iso Katafaren Gidan nasu Wanda Ya gaji da haɗuwa ta kowani ɓangare securities ne..

Horn tayi gate man ya wangale musu wagameman gate ɗin gidan, sannan Lailah ta cusa hancin motar cikin Katafaren Gidan a parking lot tayi parking sannan suka fito dukansu a gajiye suke, Don Haka koda suka shiga cikin palon bajewa sukayi saman Royal sofa's da aka qawata qaton palon dasu kuma sukayi ƙyau.


Zaynerb kuwa tana fita Gidan Kai tsaye Gidan wata Neighbor ɗinsu sunainah ta nufa, Da isarta ƙofar wagameman gate na gidan ba tare da ɓata lokaci bah.


Knocking ɗin ƙaramar ƙofar gate ɗin Tayi, sannan mai gadi ya buɗe mata bayan Na`urar tsaro dake jikin gate ɗin ta gama bincikarta, fuskar sa ɗauke da fara'a yake amsa gaisuwar da Zaynerb ke mishi domin kuwa Ya santa highly, ah ae dole yasanta sosai kodan na ce fa ne datake bashi huh🤣😂😅.


Shiga cikin Gidan Tayi sannan ta tura door ɗin palon a buɗe yake dan haka shiga palon tayi da sallama saidai ba kowa ciki..


A tsakiyar palon ta tsaya tana ƙwaɗawa matar Gidan kira, faɗi Take  "Ummyn farhana", "Ummyn farhana!",  Da sauri wata ƴar dattijuwar mata wacca ba za ta wuce ƴar aikin gidan bane ta fito daga kitchen. Da sauri ta ƙariso gurin Zaynerb.....

Ganin ta Yasa Zaynerb ta sauke ajiyar zuciya sannan ta ce "Yawwa Babah dije matar Gidan tana nan kuwa?", Zaynerb ta tambaya Babah dije data fito daga Kitchen na Palon, ,Eh madam ki sama guri ki zauna bari na kira ta inaji Bacci ne ya ɗauketa kinsan masu juna biyu sai da hutawa", Babah dije ta faɗa tana nufar wani korido dazai sadata da bedroom ɗin matar Gidan.


Zama Zaynerb ɗin tayi tana latsa wayar ta kafin matar Gidan ta fito ilai kuwa bata daɗe da zama ba, Babah dije ta fito tana faɗin "gatanan zuwa bacci ne ya ɗauketa, amma fah batayi nisa ba domin kuwa ina magana ɗaya ta farka duk nisan bacci  irinna masu ciki,"  cewar babah dije lokacin data ƙariso gurin da Zaynerb ɗin take, Godiya Zaynerb ta mata da sauri dan ta fahimci tsohuwar shegen surutu ne da ita,dan wannan surutun da tayi ya fahimtar da Zaynerb ɗin haka domin ita ɗin ɗalibai lauyanci ne kuma zaqwaqwura don tasan makamar karatunta shiyasa da zarar ta haɗu mutun mai surutu ko wani abin take fahimta.

Ita kowa babah dije ta koma kitchen ta cigaba da abinda takeyi.


Zaynerb tana zaune can saiga wata ƙyakyawar mata wacca ba za ta wuce shekaru ashirin da bakwai ba, ta fito tana faɗin "ah ah Yau manyan baƙi ne a gidan namu ashe"  Ta faɗa tana zama a three sieter, Dariya Zaynerb tayi ta ce "uwan Triple yau kuma mune baƙin kodai cikin ne yasa ba'a gane mutane Yadda Ya kamata?"..

Dariya ita ma tayi sannan ta ce "ras nake gani kece dai kikayi nisa kinfa kai one week baki zo ba wallahi, Afeefah tafi ku kirki dukanku harsu Lailah ɗin don tafiku son zuwa nan alamu yana nuni da nan gaba ma saita fiku rike zumunci Yarda ya kamata.


"Okay tuba muke uwan Triple" Zaynerb ta faɗa tana miƙa mata kular hannun ta, Karɓa tayi tana faɗin "harda su tsaraba ne Allah yasa dai na'iya ci,"  Ta faɗa tana buɗe kular aiko tana arba da kwaɗonnan ta fara suburbuɗawa  Zaynerb godiya tana faɗin "dama yau da Wani irin kwaɗayin zogale na tashi gashi Allah ya aikomin ke Zaynerb ɗiyar Albarka dashi.


Ita dai Zaynerb latsa wayar ta take tana dariyar kwaɗayin masu ciki, "Ae kigama min dariya Allah kaimu ranar da zangan ki da ciki zan rama nima," sunainah ta faɗa ganin yadda Zaynerb ke mata dariyar kwaɗayi.

 

Da sauri Zaynerb ta ce "tuba nake Ummyn farhana kinsan Waya ne a hannuna, Don Haka ita ce ta bani dariya obaa  highly bawae keba."


Sunainah bata kulata ba ta ƙwalawa Babah dije mai aikinta kira, Da sauri dattijuwar tazo tana faɗin gani maman Ferhane!!😝😝.


Dariya Zaynerb tayi ta ce "babah dije ba "Ferhane" ake cewa ba "Farhana" ake cewa." 

Dariyar ita ma Babah dije tayi tana faɗin "ae wannan suna sai ku ƴan zamani ni ina zan iya cewa wani ferhane."

Sunainarh tana dariyar maganar Babah ta ce "Babah rabu da Zaynerb kawai, Plate zaki ɗaukomin a kitchen",  "To" Babah dije ta ce sannan taje kitchen ta ɗauko special plate ta kawo mata aikuwa ta ansa ta juye kwaɗonnan a plate ɗin nan ta hauci kamar ba gobe, Hannu baka hannu plate, Saida ta cinye tas ta sha Ruwa tana mai miƙa Appreciation to Allah.


Da mamaki Zaynerb ke kallon ta ganin ko minti biyar ba'ayi ba harta cinye,  "Lallai "Ummyn farhana" wannan ci haka anya ba Triple bane bamu sani ba," Zaro ido sunainarh tayi ta ce,  "Triple kuma Zaynerb na kaisu ina? ɗaya ma ya aka ƙare balle kuma har ƴan uku.


Dariya Zaynerb tayi ta ce "ainaga cikin minti biyar harkin cinye Kwaɗo cikin plate ba dole nace ƴan uku bane."

Murmushi sunainarh tayi ta ce "idan ma ƴan ukunne Allah ya bada masu albarka, ae Albarka ake nema ba wani abu ba." Zaynerb ta amsa da ameen, nan dai suka ci gaba da fira irinnasu na ƙawaye.


IN BRIEFLY 

Zaynerb dai ba ita ta bar gidan ummyn farhana na ba sai wajen biyar na yamma acan tayi la'asar sai da taga mijin sunainarh ɗin ya kusa dawowa sannan ta mata sallama ta nufi gida.


🅆🄰🄲🄴🄲🄴_🅂🅄🄽🄰🄸🄽🄰🅁🄷_?

    


Sunainarh dai itaɗin makwabciyar su Zaynerb ce, Kuma  asalinta ta kasance ƴar bauchi ce, Aure ne ya kawota Abuja "Sohail" Shine sunan mijinta ɗan gidan ministan ilimi ne shiɗin, haihuwar ta ɗaya sunan Yarinyar FARHANA shekaran ta uku a duniya, Shiyasa Zaynerb take ce mata "Ummyn farhana" suna mutunci obaa highly da Zaynerb harda ma su Afeefah.


🆆🅰🅽🅽🅰🅽 🅺🅴🅽🅰🅽.




Post a Comment

0 Comments