TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

👬🏻 TAGWAYE 👭🏻 5 -7

      Free Episode




Episode Five : Adam


A bakin kofar makarantar jeka ka dawo ta gwamnati ta yammata, tagwayen ne a tsaye suna jiran abin hawa. 


"Kinga Sumayya, na gaya miki fa babu me napep din da zai dauke mu tun daga nan zuwa gida a naira hamsin, ai ba baban mu ne ya saya masa ba" Sumayya tace "kai Rukee, shekarar mu nawa muna tafiya gida daga nan a naira hamsin ɗin? Kullum ba goyo muke yi mu basu hamsin ɗin ba?" Ruqayyah ta fara tafiya tana barin bakin gate din tana cewa "a da kenan. Yanzu ƙatin ƙatin da mu zamu yi goyo? Ni wallahi na gaji ba zan iya da wannan abin kunyar ba, yanzu ni ina labor prefect kawai sai yara su ganni ina goyo a napep? Ke kina ganin hakan dai dai ne?" Sumayya tana bin ta a baya tace "to labor prefect, sai ki gaya mana yaya zamu yi? Hamsin din ce zata haifi wata hamsin ɗin ko kuma mune zamuyi aman wata hamsin ɗin" Ruqayyah ta ja hannuta suka yi sauri suka shige gaban wata taxi data tsaya a gaban makarantar da niyyar daukan dalibai. Wasu daliban duk suka shiga baya.


Sai da mai motar ya tayar ya fara tafiya sannan sumayya ta rada wa Ruqayyah "kudin mu fa ba zai kai ba, gwara mu gaya masa tun kafin muyi nisa in yaso ya karo wasu mu zauna tare, ko a cinyoyin mu mu dora su" Ruqayyah ta ture ta tana gyara zamanta tace "sai dai a dora miki a cinyarki ba dai a tawa cinyar ba. Bari kiji in gaya miki, hamsin din ma ni bani da niyyar bayarwa ajiye wa zanyi gobe in an bamu kudin motar sai mu hada da shi dan ya ishe mu" Sumayya tace "to shi wannan ta yaya zamu sallame shi?" Ruqayyah ta kalli driver din ta gefen ido sannan ta tabe baki tace da Sumayya "look at him, ba bahaushe bane ba. Dan haka duk baya jin abinda muke cewa. Muna zuwa gida sai mu nuna masa kamar mun yar da kudin a hanya bamu ganshi ba, sai mu bashi hakuri" 


Sumayya ta leka ta bayan Ruqayyah ta kalli driver din. Saurayi ne daga ganin sa bai dade da gama secondary ba, that's in yayi secondary din, kana ganin sa kasan ba bahaushe bane ba amma Sumayya ba zata iya tantance wanne yaren bane ba. Kuma a fuskarsa babu alamar cewa yana jin abinda suke cewa. Fari ne tas kuma jikinsa fes yake babu alamar wahalar duniya a tattare dashi dan haka daga gani kasan asarar naira dari ba zata dame shi sosai ba amma kuma a ranta tasan naira darin nan still hakkin sa ce, ta tuna da jerin waazin da Inna Ade take yi musu kullum akan cin haram, cin zali, daukan alhakin mutane, ballantana wannan bayan cin haram din ma kuma akwai karya, gaskiya zunubin yayi mata yawa. 


Ta dawo da dubanta kan Ruqayyah tace "Rukee babu kyau fa, kinsan babu kyau" ta harare ta "to shehiya malama Sumayya. Sai ki zaba, ko dai ki karyata ni ki tona min asiri ni yaruwarki kuma har abada ba zan manta ba ko kuma ki yi shiru kici zalin inyamurin da ba kara ganin sa zaki yi ba a rayuwarki. Ai ina sane muka shigo motarsa, sai dana kalle shi sosai na zabe shi sannan muka shigo" Sumayya tace "to yanzu in ma mun gaya masa haka, what if yaki yarda yace sai mun biya shi kudinsa? Idan ya fara yi mana hayaniya fa a unguwa ya zamuyi dashi?" Ruqayyah tayi murmushi tace "da zarar naga ya fara kokarin daga murya zan zunduma ihu ince ya rike ni yana tattaba ni" ta kare maganar da murmushin mugunta a fuskarta.


Sumayya ta sunkuyar da kanta kasa tana kallon hannayen su da suke cikin na juna ita da Ruqayyah. Tasan Ruqayyah kusan fiye da Inna Ade data haife su, tasan kuma zata iya aikata abinda tace ɗin, but it is not right, in ta biye mata ita ma ta zama irinta kenan kuma kamar ta kara encouraging dinta kenan. A hankali ta zare hannunta daga cikin na Ruqayyah ta juya tana kallon titi.


Luckily sai da duk aka sauke sauran passengers din sannan aka zo bakin layin su Rukee. Suka nuna masa inda zai tsaya ya tsaya sannan ya juyo sosai yana kallonsu yace "your money please, 100 for the both of you"


Ruqayyah tayi pretending as if tana nemo kudi a jikinta, sai kuma ta hau duba jakarta tana da bincike, in ka kalli fuskarta zaka iya rantsewa da Allah cewa da gaske neman kudin take yi, sannan ta dago kai tana kallonsa da budaddun idanunta da suke nuna alamar tsoro tace "I can't find it. I can't find the money." Ta sake shashshafa aljihunta sannan tace "I swear I put it inside my pocket. I must have lost it at school" ta langwabe kai "we are sorry sir. Please dash us the money".


Sai ya dauke kansa gefe yace "check again. Maybe you hid it somewhere" sumayya ta juyo tana kallonta tace "Rukee ki bashi hamsin din, sai mu roke shi yayi hakuri in yaki yin hakurin sai inje gida in karbo masa a gurin Inna Ade" Ruqayyah ta harare ta tace "chafdi, wallahi ba za'a bashi din ba, so kike Inna Ade ta saka mu a gaba da nasiha" 


Sai ta juya gurin drivern da fuskar tausayi tana ta shashshafa pockets dinta "I can't find it. It must have been stolen at school" ya juyo yana kallonta sannan ya kawo hannu kamar zai taba ta yace "let me help you check. Da azama ta rike hannun daya miko, idanuwa a waje, sai ya kawo daya hannun, Sumayya tayi saurin rike shi shima. Abin duk ya faru ne in seconds. A take kuma Ruqayyah ta bude baki da niyyar zunduma ihu, sai Sumayya ta saka hannu ta rufe bakin tana girgiza mata kai sannan ta juya tana kallon driver din tace "please, please sir, we are sorry, let me go and get you the money" 


Sai ya zare hannayensa daga nasu yana kallon Ruqayyah yace "ki bata hamsin din jikin ki sai ta karbo wata hamsin din ta kara akai" sai tsoron fuskarsu ya juye zuwa mamaki. Ya daga kafada yace "I might not be hausa, but ina jin hausa kamar jakin kano, dan haka you picked the wrong target" ya bude musu kofar motar yace "get out of my car. Da nayi niyyar ganin karshen drama dinki, but naji tausayin twin sister dinki dan naga kamar ita ta gari ce" a salube Sumayya ta fito daga motar, Ruqayyah kuma ta fito tana kumbura baki sannan ta juya tana kallon sa ta rike kugu tace "aikin banza aikin wofi, dan kana jin hausa kuma sai me? Dan kaji abinda muka ce sai me? Naira darinka din banza, drivern taxi kawai" 


Sumayya ta sunkuyo ta window tace "dan girman Allah kayi hakuri. Ni ka tsaya ma dan Allah in karbo maka kudinka a cikin gida, ta boye hamsin din kuma nasan ba bani zata yi ba" ya juya hannun sa yace "ki barshi kawai. Na bar miki, ita ma na bar mata hamsin din tayi arziki da ita. Sannan ki fada a gida a kara muku kudin mota in ba haka ba wata rana zaku samu wanda zai daki kudinsa. Sannan ki saka ido akan twin sister dinki, bata da kirki" ta gyada kanta da sauri yayinda Ruqayyah take neman irin zagin da zata yi masa, da sauri sumayya tace "dan Allah kar ka kulata" ya kalli Ruqayyah yana tayar da motarsa yace "I will not, am not her mate" daga nan yayi tafiyar sa.


Ruqayyah ce ta fara shiga gidan su a fusace kamar zata tashi sama. Inna Ade tana gaban murhu tana zubawa yan samarinta abinci wadanda suma dawowarsu kenan daga tasu makarantar.


Duk da cewa daga Ade har Yusufa basuyi karatun boko ba hakan bai hana su saka nasu yayanba, amma sai sun tabbatar cewa sunyi sauka kuma sunyi hadda. Hatta karamin su zunnur yayi hadda, duk iskancin Ruqayyah babu ayar da zaka bude mata ba tare da ta karanta maka ba. Bayan Alqur'ani kuma sun san sauran littattafan addini.


Bata ko kalli inda suke ba ta wuce su da sauri tayi hanyar dakinsu. Suleiman yace "kububuwa! yau kuma wanne mai tsautsayin ne yayi wasa da jelar damisa?" Zunnur ya kwashe da dariya. Inna Ade tace "Allah yasa ta jiyo ku, in ta kama ku tana jibga babu wanda zan ceta" Sumayya ta shigo da sallama, ta zarce kan baranda ta ajiye jakarta da robar abincin su sannan ta dawo inda suke ta gaishe da Inna Ade, Suleiman yace "wa ya taba Rukee ne yau" Sumayya tace "ina ruwanka? Bana son tsegumi" daga nan babu wanda ya kuma tambayarta dan sun san babu wanda zai samu amsa, sai dai ita kanta bata iya bin Ruqayyah zuwa daki ba sai tayi sallar ta anan sannan ta debi ruwa ta fara wanke musu uniform dinsu wanda zunnur ta aika ya dauko na Ruqayyah, sai data gama sannan ta daukar musu abincin su ta shigar musu dashi daki, tasan dai zuwa lokacin Ruqayyah ta sauko, dama ita saurin hawa ne da ita da kuma saurin sauka.


Ta tarar da ita a kwance tana karanta littafinta na makaranta. Ta zauna ta bude shinkafa da miyar da akayi har da yankakken salak a sama. Rukayya ta mike zaune tare da karbar chokali a hannun sumayya suka fara ci babu wanda yayi magana, sai da suka kusa gamawa sannan Ruqayyah tace a hankali "duk laifin Baba ne" Sumayya ta dago kai cikin rashin fahimta tace "laifin baba kuma? Menene laifin nasa? Shinkafar ko miyar ko kuma salak din?" Ruqayyah tace "talauci. Talaucin da muke ciki. Shine ai yake da alhakin kula damu, shi yake da alhakin nema mana abinda duk muke bukata a rayuwa amma kuma ya gaza, ya gaza sauke abinda yake dole ballantana abinda yake ganin ba dole bane ba" sumayya tace "kina da hankali kuwa Ruqayyah? Kin manta Allah? Ina karatun ki ya tafi? Shin arziki da rashinsa ba duk na Allah bane ba" Ruqayyah ta ajiye spoon din hannunta tace "Allah ba zai taba taimakon wanda ba ya taimakon kansa ba. Allah ba zai taba baka abu in baka tashi ka nema ba" Sumayya tace "amma kuwa in zaki yiwa Baba adalci ke kanki kinsan yana neman ai. Kinga yadda hannun Baba yake kuwa? Kanta ce fa a hannunsa saboda tsabar leburancin da yake yi. Shine aikin labura shine gini, har dako fa baba yi yake yi, kuma duk dan mu yake yi dan muci abinci muyi suttura muje makaranta. Tunda muke bamu taba kwana da yunwa ba, shin ba zamu gode Allah ba? Shinkafa muke ci da rana, gidajen masu hali irin na Baba nawa ne suke samun shinkafa a sati? Jiya fa ina jin Inna ade taji kina complain kin gaji da cin mai da yaji shine fa ta karbo wankau tayi na tabbatar kudin da aka bata shine ta siyo kayan miya da salak din nan tayi mana. Kuma duk dan kar muga gazawar sune a matsayin su na iyayen mu. Kar ki zama butulu mana" 


Duk maganar da Sumayya tayi abinda Ruqayyah taji kawai shine kalmar butulu, "nice butulun ko? Ni zaki kira da butulu ko? To ki jira, in dai nice muna nan dake zaki ga nayi kudi. Gabaki daya gidan nan sai na saka an rushe shi anyi mana sabo, an zuba mana kayan alatu irin na gidajen masu kudi. Inna Ade sai ta manta da cewa ta taba yin wani abu wai shi wankau ballantana har a goranta min a saboda shi" Sumayya tace "oh oh, Inna Aden ce zata yi miki gori? Kenan biyanta kike nufin zakiyi na hidimar da tayi dake? Duk kudin da zakiyi Ruqayyah kin isa ki biya iyayenki wahalar da suka sha a kanki? Ballantana ma baki da tabbas din zaki yi kudin" 


Nan take rigima ta kuma kachamewa. Inna Ade ta shigo ta tsaya tana kallonsu. "Ya ilahi, yaran nan ko hanjin junan su suke gani ne ni ban sani ba? Ba yanzu kuka gama wani fadan ba har kun sake wani? Kuma in an tambaye ku me ya hada ku ba zaku fada ba ballantana a sulhunta ku?" Ruqayyah ta mike zata fita daga dakin tana kunkuni. Inna Ade ta jawo hannunta "ke Ruqayyah ban hanaki in ana miki magana ki fita ki bawa mutane guri ba? Wato bama zaki tsaya kiji abinda za'a gaya miki ba ballantana kiyi aiki dashi ko?" Sumayya tace "kiyi hakuri Inna" Inna tace "ke ce bakinta? Ita bata da bakin magana ne?" A hankali Ruqayyah tace "Allah ya baki hakuri" Inna Ade ta sake ta ta fita daga dakin zuciyarta babu dadi.


Sai da suka yi sallar laasar suka yi wanka suka shirya sannan suka fito tsakar gida, yau thursday dan haka masu zuwa daukan karatu basu shigo ba sai Ruqayyah ta dauki tsintsiya ita kuma Sumayya ta harhada kayan wanke wanke suka fara gyaran gidan. Suna gamawa Sumayya ta hada wuta ta dora tuwon dare Ruqayyah kuma ta dauko dutsen guga ta hada wuta ta fara goge musu kayan gugar su daya taru. A lokacin Inna Ade ta rufe Alqur'anin da yake gabanta tana karantawa tunda tayi laasar, ta shimfida tabarma kusa da inda Ruqayyah take guga ta zauna. Kamar hadin baki sai ga Sulaiman ya shigo tare da Zunnur, suka zauna suka gaishe da Inna Ade suma bata labarin shagon da suke zuwa koyon dinki. 


A lokacin kuma Baba ya shigo, da sauri yan samarin suka mike suna karbar kayan hannunsa suna yi masa sannu da zuwa. Ya amsa yana zama akan tabarma kusa da Inna, Sumayya ta ajiye rariyar hannunta da take tankade da ita ta wanke hannun ta ta debo masa ruwa a randa. Ya karba yayi mata godiya, yasha ya ajiye kwanon sannan inna ta gaishe shi, yace "yauwa Sa'adatu. Ya gida?" Ta amsa da fara'arta, "ka dade yau baban biyu, har na fara tunanin in aika gidan maman Minal in aro wayarta a kira ka muji ko lafiya" Yace "wallahi na je gurin wannan neman aikin da na gaya miki ne, wannan sabon kamfanin da aka bude, *H & H* to naji sanarwa a gidan radiyo cewa sun fara daukan kanana da manyan ma'aikata shine naje ko Allah zai sa a dace su dauke ni ko aikin gadi ne inke yi musu, ko wani aikin dai daban, aikin dai da za'a ce mutum kullum in ya fita yana da aiki kuma duk wata zai samu albashinsa" Inna tace "insha Allahu muna da rabo a aikin nan. Mun gaya wa Allah kuma insha Allahu zai dube mu" yace "ameen" sannan ya jawo ledar daya shigo da ita yace "ga garin masara nan na auno mana uwar biyu, sai a lallaba ya kai mu wani satin" ta shafa ledar tana jin yawan garin tace "wannan baban biyu ai har wani satin zai kaimu in sha Allah. Mungode Allah ya kara budi, jazakallah bi khair" yace "ameen. Amma bance ake yin tuwo kadan ba dan kar gari ya kare, a yi isashshe wanda yara zasu ci su koshi da safe a dumama suci kafin su tafi Makaranta. Bana so suke zuwa makaranta da yunwa" Inna tana murmushi tace "lallai masu 'ya'ya" ya jawo wata karamar leda yace "wannan busasshen kifi ne na siyo dan ake saka wa a cikin miyar kaɗi, saboda yara suji dadin cin ta" Inna Ade tace "Lallai yara yan gatan baban su, komai dai ace dan yara, ni ba a yin komai dan ni" ta fada da sigar tsokana, Zunnur yace "ai sai dai kiyi hakuri Inna mum kwace miki power a gurin Baba" duk sukayi dariya banda Ruqayyah da take ta gugar ta kamar bata gurin. 


Inna ta tashi ta dauko masa abincinsa ta kawo masa, yana bude wa yace "lala, uwar biyu miya akayi mana haka harda salak? A ina kika samu kuɗi?" Ta dan bata rai tace "saboda nasan kana so shi yasa na danyi wani aiki na samu kuɗi nayi dan in faranta maka. Ni dan kai nayi ba dan yara ba" duk akayi dariya har da baban shima, sai kuma yace "to ai ke nasan baki da matsala, tunda ke kika zabe ni kika ce kinji kin gani, su kuwa yara basu suka zabi zama yayan mu ba, bana so suke sha'awar iyayen wasu suna cewa ina ma dai sune nasu" Sulaiman yace "haba dai Baba, ni da ace za'a sake haihuwa ta ace in zabi iyaye ai da ku zan zaba sau goma, kunyi mana komai sai fatan Allah ya saka muku da alkhairi ya bamu ikon yi muku biyayya da faranta muku".


Sai a lokacin Baba ya juya yana kallon Ruqayyah da take ta gugar ta kanta a kasa yace "Hassana. Baki ga na shigo ba ko gaishe ni baki yi ba?" Ta dago da murmushin yake a fuskar ta tace "na gaishe ka Baba, baka ji ni bane" ya girgiza kansa kawai ya fara cin abincin sa.


Sai da yayi nisa da cin abincin suna yar hirarsu da Inna sannan ya dago kai yana kallon Sumayya yace "Hussaina yaya jarabawar taku? Ana dai kokari sosai ko?" Ta rufe tukunyar data ke juyawa ta taho tana cewa "Baba alhamdulillah, ai mun kusa gama wa ma insha Allahu nan da sati biyu zamu kammala gabaki daya" Ruqayyah ta ajiye iron din hannunta wanda ta gama guga dashi tace "nan da sati biyu zamu gama Neco Baba, saura Waec" yayi shiru sannan yace "ita ce wadda ba'a biya muku bako?" Sumayya tayi saurin cewa "ai bata da wani muhimmanci Baba. Kaga Minal ita fa waccan shekarar ta gama amma har yanzu bata karbo waec dinta ba tunda taci duk abinda ake bukata a Neco" Ruqayyah ta zauna akan tabarmar tace "muhimmancin ta daya shine idan mutum bai ci Neco ba, ko kuma yaci rabi bai ci rabi ba, zai iya hada wa da waec sai ya samu duk abinda ake bukata a jami'a" Baba ya gyada kai kawai bai ce komai ba, amma fuskarsa ta nuna damuwa. 


Inna Ade tace "maganar jami'a fa naji kuna yi, ita minal din bata gaya muku uban kudin da mamanta take bani labarin an kashe kafin a saka ta a jami'a ba? Ita kadai ma ballantana ku biyu?" Baba yace "abin ai na Allah ne, insha Allahu, indai sunci wannan jarabawar kuma suna so zasu je. Ko ba zan iya turasu su biyu a lokaci daya ba sai in saka daya wata shekarar sai a saka dayar. Abin ai na Allah ne" 


Friday bayan sun tashi daga makaranta, suna tsaye a bakin titi suna jiran abin hawa sai ga wata taxi ta tsaya a gaban su. Ruqayyah ta sunkuyo da niyyar yi wa driver magana sai taga mutumin ranar nan ne, ta ja tsaki tare da komawa baya tana hade rai. Sumayya ta leka itama ta gashi zata matsa taji yace "ku shigo in kai ku" Ruqayyah ta leko tace "ko babu motocin haya a titin nan gwara mu tafi a kafa" ta kuma komawa baya ta tsaya. Yace da sumayya "ke shigo in kaiki" ta girgiza kanta "bazan iya tafiya ba tare da sister ta ba" yace "I understand" tace "mungode bawan Allah" yace "yes, ni bawa ne na Allah but sunana Adam" Ruqayyah ta leko "babu wanda ya tambaye ka sunanka saboda babu wanda ya damu daya sani" Sumayya ta kalle shi tana murmushi tace "Sunana Sumayya, yar uwa ta kuma sunanta Ruqayyah,".



Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu #500 ta account 

First Bank

Account Name : Alhassan Musa Sadiq

Account Number : 3189669587


Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin

09135803002


Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na ₦500 zuwa wannan layin

09135803002 


Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only👬🏻 TAGWAYE 👭🏻



By



Maman Maama



Free Episode





Episode Six : Chloroform


Hira tayi dadi tsakanin Hussain da gimbiyar sa, har lokaci ya tafi ba tare daya sani ba, tun suna kan kujera suna hira har suka sauko kan carpet suna ta magana cikin yiwa juna murmushi da dariya, kasancewar duk su biyun masu fara'a ne sosai. Suna cikin hirar ne alarm ya kada a wayar Fatima, ta dauka ta kashe tace masa "lokacin tafiyar ka yayi kar kayi missing Flight dinka" yana kallonta da mamaki yace "wai kina nufin har alarm kika saka min?" Ta juya idonta tace "nasan zamu iya mantawa, kuma tafiyar ka tana da muhimmanci, bana so inso kaina da yawa" 


Ya jinjina kansa yana jin soyayyar ta tana karuwa a zuciyarsa, sosai yake son yadda take gudanar da al'amuran ta, komai nata a tsare yake, komai nata a nutse take yinsa. Har airport ta kai shi sannan sukayi sallama a ransu suna jin kamar kar su rabu, Hussain yana ji a jikinsa cewa in sukayi aure duk tafiyar da zaiyi tare da ita zai ke yi tunda dai matarsa ce kuma babu abinda zata zauna tayi a gida.  


Cikin sauri yaje gida, ya tarar Hassan ya gama hada masa kayan tafiyar sa ya zuba masa a mota dan haka wanka kawai yayi ya chanza manyan kayan jikinsa zuwa ƙanana sannan ya shiga mota Hassan ya mayar dashi airport. A hanya babu wanda yayi magana har suka je, haka kawai Hussain yaji jikinsa yayi sanyi and for the first time tunda ya fara tafiye-tafiye yaji cewa baya son tafiya, yaji cewa baya son ya rabu da danuwansa.


Sai da Hassan ya karkada masa key a fuska sannan ya juyo yana kallonsa yana kirkiro murmushi. Hassan yace "what's wrong? Tsoron jirgin kuma kake yi yau ko me?" Hussain ya duba agogon sa yana noticing mintinan daya rage kafin jirgin su ya tashi, wata zuciyar tana gaya masa ya juya ya koma gida amma sai yayi sauri ya girgiza kansa yace da Hassan "take care of yourself bro. Bazan jima ba dan bana jin zan wuce sati daya. Duk abinda ya kamata ayi to ayi kawai kar ace sai an jira ni. Ka bawa Aunty hakuri kace tafiyar ta zama dole ne bana so auction din nan ya wuce ni" Hassan ya rike dariyar da take taso ma sa yace "Badan na sanka ba da sai ince kamar tsoro nake gani a fuskarka kuma nake ji a muryarka, amma na sanka kuma nasan Hussaini baya jin tsoron komai, shi jarumin jamurai ne" Hussain yayi murmushin da ya tsaya a lips dinsa yace "bana jin dadi ne kawai. Amma nasan kafin mu sauka zan ware" ya sake kallon abogon hannunsa sannan yace "take care of yourself bro" Hassan yace "you already said that bro" sai hussain yayi murmushi yana bude hannu yace "okay take care of everyone at home" sannan ya bude kofa ya fita.


Hassan ya bishi da kallo har ya shiga kofar departure hall, sai daya daina ganin sa sannan ya tayar da motar ya bar gurin yana jin part of him ya tafi tare da Hussain. Amma dama ya saba da wannan feeling din, kullum in basa tare da Hussain sai yaji kamar rabin sa ne a gurin rabi kuma yana inda Hussain din yake, tun suna yara haka yake ji, duk fadan su duk rigimar su amma duk duniya babu abinda yake so sama da Hussain, baya jin kuma akwai wani abu da zai raba shi da Hussain.


Direct gida ya koma, yana ta lissafin abubuwan da suke gabansa abubuwan da ya kamata ya yi kafin dawowar Hussain daga Beijing. Dazu dai yayi wa kananan ma'aikatan da za'a dauka aiki a sabon kamfanin interview kuma har ya riga yayi grading dinsu, sai ya zauna zai yi final zabe sannan sai a kira wadanda aka zaba din a sanar musu. Shi komai yafi so yayi a hankali, ya tuna yadda suka yi da Hussain a lokacin da suke maganar daukan ma'aikatan. "Kaga Hassan, don't stress yourself akan maganar nan. Kananan ma'aikata ake magana fa ba manyan ma'aikata ba, ba takardu zaka duba ba ba komai ba, kawai just look at their physique ka tambaye su akan past experiences dinsu shikenan. Wanda kaga ya dace ka bashi aiki kawai a take wanda bai dace ba ka sallame shi kace masa babu aiki dan kar yaje gida yayi ta saka ran zai samu" 


Hassan yace "so kake mu dauki baragurbi kenan mu bar masu kyau? Ai shi lamari na daukan ma'aikata a nutse ake bi ayi interview idan da hali ma sau biyu dan aga mai juriya, ni har medical certificate nake so suje suyi saboda in tabbatar da lafiyar su, sannan sai na zauna a nutse sai in tace wanda naga sun cancanta" Hussain ya mike tsaye yana bude hannu yace "do whatever you want. Ni dai abinda na sani shine, duk wanda Allah ya tsara yana da rabon samun aiki a *H and H* ko ka bashi yau ko kuma kayi ta delaying sai nan da shekara daya still dai sai ya samu. To gwara ka bashi ka huta shima kuma ya huta".


Hassan yayi murmushi yana kashe motar bayan yayi packing a compound din gidan su. Tun suna yara kusan kullum sai sunyi irin wannan musun kuma har yau babu wanda ya taba chanza ra'ayin danuwansa. 


Ya shiga gidan. A kan dining ya hango yar autar su Zulaihat da takardu a gabanta tana karatu, shirye shiryen ssce take yi dan yanzu haka sun kusa kammala neco sauran su waec. Dama ita kadai ta rage a secondary School sauran yammatan duk suna jami'a dan Hassana har ta kammala ta kuma yi service dinta, ta kuma samu mijin aure dan yanzu so ake yi ma a hada bikin nata dana Hussain.


Zulaihat ta amsa sallamar sa tana binsa da kallo sannan ta kalli bayansa da sauri sai kuma ta sake kallonsa "ina yake?" Ta fada tana kara kallon kofa. Ya jawo kujera a can karshen dining table din ya zauna tare da jawo food warmer din daya gani a gurin, yasan duk gidan sunfi son Hussain a kansa, sunfi sabawa da Hussain saboda ya fi shi faran faran da wasa da dariya, ya fishi kuma kashe musu kudi da shagwaba su, shima kuma yana taya su son Hussain din. Ta sake tambaya "yaya H1 ina yaya H2 yake? Bai dawo daga kanon ba?" Ya fara zuba abinci sannan yace mata "ya tafi China" ta bude ido da baki tana kallonsa sannan ta ajiye littafin hannunta ta tashi a guje ta tafi saman Aunty. Yayi murmushi yana cigaba da zuba abincinsa. Sai daya fara ci sannan yaji saukowarsu kusan gabaki dayansu . Duk suka taho inda yake, Aunty ta zauna a kujera tana kallonsa "ina Hussaini?" Ya dago kai shima yana kallonta yace "ya tafi China, suna kan hanya ma yanzu".


Ta fara fada "yanzu lamarin Hussain har ya kai haka Hassan? yanzu ni a gidan nan ban ma isa a gaya min in za'ayi tafiya ba ballantana in saka ran za'a nemi izini na kafin ayi? Yanzu har sai yayi tafiyar ma sannan zai aiko ka ka gaya min?" Bai ce komai ba har ta gama fadanta sannan ya ajiye spoon din hannnunsa yana kallonta yace "tsakanin ku ne Aunty, kun fi kusa. Nasan in ya sauka zai kira ki sai ki yi masa fadan. Nima sai dana gaya masa rashin dacewar hakan amma sai yayi min bayanin cewa in ya gaya miki hana shi tafiya zakiyi kuma in kika riga kika hana shi ba zai iya tsallake maganar ki ba, sannan kuma tafiyar mai muhimmanci ce sosai saboda injinan da za'a yi amfani dasu a sabon Companyn yin flour nan su zai siyo, in ya aika kuma za'a iya siyo masa fake shi yasa ya tafi da kansa. Kinsan halin Hussain, he settled for nothing less than the best"


Tayi shiru tana tunani, yayin da yammatan suka fara mita, Safiyya tana korafin ai yayi mata alkawarin tare zasu tafi kuma shine ya tafi ya barta. Aunty tace "yanzu yaushe zai dawo kenan?" Hassan yace "sati daya yace zaiyi" tayi ajiyar zuciya tace "Allah ya kaimu, ya kuma dawo mana dashi lafiya. Ni wallahi na ƙagu azo ayi bikin nan nasa ko zai rage wannan yawon, tunda naga yana son Fatima sosai dole zai ke son zama anan tare da ita" Hassan yayi murmushi yace "in yana son yawon zai iya daukan matarsa su tafi tare, menene a ciki?" Aunty ta bata rai "don't put that idea into his head" yayi dariya yana bude hannu "nayi shiru. Amma ina tunanin already idea din tana cikin kan nasa sai mu jira ayi auren mu gani. Hussain ne fa, bana jin aure zai saka ya zauna guri daya" 


Suka yi shiru gabaki daya, Hassan yana cin abincin sa amma kuma yana jin idon Aunty a kansa, take ya fahimci tunanin me take yi, sai yaji tace "kai kuma fa?" Ya gane me take nufi amma sai yayi keeping blank expression yace "ni kuma me aunty? Ni ma yaushe zan tafi chinan?" Ta hade rai tace "kai ma yaushe zaka yi auren? shine abinda nake tambaya, kai ko budurwar nan ma ta zamani baka da ita, kaki kula duk yammatan da suke sonka" 


Nafisa tayi saurin cewa "ai kuwa Aunty akwai wata course mate dina, baki ga yadda take son shi ba, kullum sai ta tambaye ni ina yake" ya harare ta yace "hala bata ga Hussain ba? Am sure tana ganin sa zata ce shi take so bani ba" Aunty tace "Hussain ai ya riga ya samu matarsa, a very good girl from a very good family. Family dinta is one of the best a duk fadin kasarnan. Kai ma ya kamata ka kara kokari ka samo wa Fatima yaruwa" ya shafa kai yace "za'a samo wa Fatima yaruwa Aunty, amma sai a hankali, kuma ba irin Fatima za'a samo ba dan ni bana son abinda yake all covered in gold and praises. Saboda nasan most of the books with good cover basu da good contents. Ni am more interested in the content" Aunty tana girgiza kai tace "ai kuwa ana samu Hassan, ana samun wanda yake da goodness in both the cover and the content, ko ita fatiman ai haka muke fata" ya girgiza kansa yace "I am not going to take that risk gaskiya, nafi son in nayi aure ya zamana har abada, mace daya in na samu irin wadda nake so ta ishe ni har abada. Nafi son in auri mace from a lower background than ours, yadda ba xata ke looking down on us ba, yadda zata ke girma ma ku iyaye na kuma ba zata ke yiwa sisters dina magana anyhow ba kamar yadda take yiwa bayin gidansu. Nafi son wadda duk abinda na bata, no matter how small zata yi appreciating ba zata raina ba saboda ta saba da wanda yafi shi. Nafi son me low life style irin nawa not extravagant kamar Fatima" 


Aunty tace "to Allah ya kawo mana ita, Allah yayi muku zabin alkhairi baki daya" ya amsa da ameen. Sun jima suna hira, yana updating dinta akan shirye shiryen bude sabon company, sai gata ta dauko masa wani dogon list wai daga Gombe aka aiko dashi inji uncles da auntys dinsu na mutanen da suke so a dauka aiki. Ya karba kawai yayi murmushi amma shi a ransa yasan babu wanda zai bawa aiki sai wanda ya cancanta sai dai duk abinda za'a ce ace.


Daga nan part dinsu ya nufa, ya shiga palo yana karewa luxurious kujerun da suka kawata falon kallo, amma last dawowar Hussain daga Japan yana shigowa palon cewa yayi "what? Wannan kujerun har yanzu ba'a cire suba? Wadannan ai sun zama old models yanzu sam ba'a yayinsu" Hassan yayi murmushi yana jin kewar danuwan nasa, Hussain sarkin rikici. Ya bude kofar dakinsa ya shiga, komai tsaf tsaf kamar yadda ya barshi. Yayi wanka ya chanja kayansa zuwa kanana sannan ya fito ya rufe dakinsa ya shiga na Hussain. Komai na dakin abin kallone, ko bakasan kudin kaya ba kana shiga dakin zaka san cewa tabbas an kashe kudi a gurin tsara dakin zuwa kayan da aka zuba a ciki. Sanda Hussain zaiyi renovating babu yadda baiyi da Hassan ba amma yaki yarda a gyara masa nasa dakin "ni dakina babu abinda yayi bana bukatar a gyara min shi, wannan ai almubazzaranci ne, Ni fa da ka ganni yanzu zan iya yin 10 years nan gaba ba tare dana chanza komai a dakina ba".


Sai dai Kamar yadda Hassan yayi tsammani a hargitse dakin yake, kaya sun kai set goma duk a baje a kan gado kuma yasan duk a kokarin shirin zuwa gurin Gimbiya ne aka hargitsa kayan. Yayi tsaki kawai ya wuce wata drawer ya dauko takardar da yazo nema, sketch ne na sabon companyn da ake gina wa wanda kusan an gama komai yanzu, finishing touches kawai ake yi. Ya dauka ya fita, a compound din gidan ya kira wani amintaccen yaron su Salisu, salisu tun babansu yana da rai yake gidan shi da babansa, bayan rasuwar baban nasa sai Hassan da Hussain suka cigaba da zama dashi a matsayin amintaccen su wanda shi kadai yake da access da dakunan kwanan su da abincin su da komai nasu da yake personal, yace "kaje ka gyarawa Hussain dakinsa, ni zanje site sai magrib zan dawo" sannan ya ja motar ya tafi.


Site din ginin ya tafi. So yake yaje yabi ko ina ya tabbatar yadda aka yi sketching din haka aka yi aikin. Dama sunyi waya da engineer dan haka already a can ya same shi sai dai ma'aikatan sun fara tafiya gida tunda magriba ta fara gabato wa. Haka suka yi ta zagayawa sako da lungu na gurin Hassan yana yi yana duba sketch din hannunsa a tsanake duk inda yaga kuma ba'ayi dai dai ba sai yayi magana sai engineer yayi masa bayani in bayanin ya gamshe shi shikenan in kuma baiyi ba yace a gyara. A haka har suka gama, engineer yayi masa sallama ya tafi shi kuma ya tsaya ya dan yi rubuce rubuce a takarda ya saka a cikin sketch din sannan ya fito. 


Sai daya fito sannan ya lura da yadda gari yayi duhu, masallatai ana ta sallah wasu ma har sun idar. Da sauri ya bude motarsa yana jin takaicin missing jam'i da yayi, ya ajiye takardar hannunsa a kujerar kusa da driver sannan ya zauna a kujerar driver yana zura key a jikin ignition. 


Wani abu mai sanyi yaji ya taba wuyansa, sanyi irin na karfe. Da sauri ya kalli side mirror sai idanunsa suka sauka a kan yar karamar bindiga da ake kira da pistol, bakin bindigar a rufe da silencer. Zai iya cewa bai taba ganinta a zahiri ba sai yau ballantana ya taba ta amma yana ji a finafinai cewa karfenta sanyi ne dashi sai gashi yau ya tabbatar, sai dai abinda basu fada a films din ba shine yadda sanyin yake wucewa har cikin zuciyar mutum. Ya runtse idonsa ya bude, yana tunanin Hussain, ko yaya zaiyi copping da labarin mutuwarsa?


Murya yaji dai dai kunnen sa, cikin rada amma kuma da kakkausan amo "take your hand of the ignition and place it on your head" a hankali yabi umarnin da aka bashi, ta gefen idonsa yaga wani ya bude kofar gefen driver ya shigo, bai juya ya kalleshi ba amma daga yadda motar ta amsa zaman nasa yasan cewa katon gaske ne, yasan ba zai iya tarar sa da fada ba ballantana kuma gashi su biyu ne da wanda ya saka masa bindiga a wuya. Amma yasan da Hussain ne da zai gwada, zai gwada ko da kuwa chances dinsa na winning is 1% in yayi failing ma zai sake gwada wa, amma shi ba zai gwada ba, shi yana analysing situation dinsa ne kafin ya gwada sa'ar sa kuma wannan karon baya jin akwai Sa'a.


Yaji alamar wani ma ya bude baya ya shiga, su uku kenan, yayi shiru yana jiran yaji instructions din da zasu bashi amma basu ce komai ba sai kawai ji yayi wani hannu rike da wani tsumma ya zagayo ta baya ya rufe masa hanci da bakinsa. A jikin tsumman ya shaki kamshin wani abu, kamshin da yayi bringing back memory din lokacin da suka je South Africa shi da Hussain, lokacin da suka je kallon namun daji a reserve dinsu, lokacin da wani tiger ya tsallake shingen da aka yi masa yana kisan sauran dabbobi sai aka watsa masa wani abu mai irin wannan kamshin. Ya tuno sanda ya tambayi mutumin game da abin sai yace masa dashi suke amfani dan suyi knocking down dangerous animals, sai ya gaya musu cewa "masu satar mutane ma dashi suke amfani su fitar da mutum daga hayyacin sa dan suji dadin satarsa" ya tuno sunan da mutumin ya gaya musu "sunan sa chloroform".


Da sauri Hassan ya dauke numfashin sa yaki shakar abin ya kuma fara amfani da hannayen sa dan ganin ya cire tsumman daga fuskarsa amma sai mutumin ya kara danna masa shi wanda ya zauna a gaban kuma ya fara kokarin rike hannayen sa, tunanin Hassan daya a lokacin, tsoron sa daya a lokacin shine kar su sace shi suyi amfani dashi gurin cutar da Hussain. Shi farko ya dauka robbers ne sai yanzu ya fahimci kidnappers ne. Yaji sunyi magana a tsakanin su amma bai fahimci mai suka ce ba sai dai kuma yaji muryar wanda yake bayan tamkar muryar wanda ya sani, wanda ya sani sosai amma ya kasa placing.


Sai yaga sun dauke hanky din daga fuskarsa sannan na bayan ya saka hannayen sa biyu yayi amfani da duk karfinsa ya shake wa Hassan wuya yana toshe masa hanyar wucewar iska zuwa huhunsa, Hassan yaji kamar zai mutu, kwakwalwar sa ta totse kirjinsa kamar ana hura wuta a ciki babu abinda yake so illa ya shaki iska amma sun hana masa, ya yi tunanin this is what suffocating feels like, this is the end of him. Regret dinsa daya a rayuwa shine baiyi aure ya bar yaya ba kamar yadda yake da buri, sai yaji cewa ashe Hussain is right akan kayi komai a lokacin da ka samu dama kar ka jira sai wani lokacin, sannan yayi wa kansa alkawarin indai har yayi surviving the first thing da zaiyi shine aure, duk yarinyar data fara kwanta masa a rai ita zai aura.


A lokacin daya gama saddakar da tafiya lahira a lokacin ne kuma suka cika masa makogwaron sa sannan suka yi placing wannan jikakken hanky din a kofar hanci da bakinsa. Farkon abinda ya fara kokarin yi shine shakar iska zuwa huhunsa da yake ji on fire, wannan yasa ya shaka da karfi, ya kuma shaki abinda baya so din har cikin huhunsa. Ya jima yana shaka, a kokarin sa na dawo da numfashin sa dai dai, a lokacin da numfashin nasa ya fara dawowa dai dai a lokacin ne kuma hankalin sa ya fara gushewa, a lokacin ya fahimci cewa ya shaki chloroform din.



Ga masu son siya zasu iya turo kudinsu ₦500 ta account 

First Bank

Account Name :Alhassan Musa Sadiq

Account Number : 3189669587 


Sai su turo shaidar transaction din ta hanyar WhatsApp zuwa wannan layin

09135803002 


Wadanda basu da account zasu turo katin MTN na #500 zuwa wannan layi

09135803002 


Dan girman Allah banda kira, WhatsApp only👬🏻 TAGWAYE 👭🏻



By



Maman Maama

Post a Comment

0 Comments