TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sanyi da zafi page 30

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 3️⃣0️⃣



Faduwa gaban Riyad yayi sosai jin abinda Mama tace, ahankali Mama tace “gidan nan gave my life tabo dabazai taba goguwa ba, gidan nan yasa y’ata is like this, ranan nan i told you karka shiga maganan nan sabida Jummai can hurt you Riyad basu da imani, look at yanda suka maida rayuwana yau, look at how far they’re willing to go tana kulle innocent yarinya a police cell” Mama tafashe da kuka tace “jibeni kaman tsinke nida keda kiba and Riyad nobody stood for me yayi defending dina, tsoro ne, menene oho but kowa stood there and watch me being humiliated, Riyad those people hurt me! An min sheri anmin kazafi, na wahala sannan poor child dina ta wahala look at Rashida, all her life washing plate da washing bayuka daban daban in different organizations takeyi just to feed me and sponsor school nata” Mama tai maganan tana fashewa da kuka dayasa Riyad yatashi daga kan kujera soyake yama cema Mama sorry yakasa saikawai yajuya yafita da sauri ya shiga sauka kasa yana karasa sauka beben yana cin karo da Munir dake kokarin hayowa rikeda Basket na abinci da sauri yakama hannun Munir yashiga tafiya da sauri da sauri Munir yabishi hankali tashe yace “Riyad what happened you’re scaring me, Meya faru?” Saida sukaje jikin mota Riyad ya tsaya tareda dafa kanshi Munir dasauri yace “Riyad menene wai”? Fuzar da iska Riyad yayi ahankali saikuma yakalli Munir yace “Rashida is our cousin! Yarinyar Baffa ce!” Dawani irin sauri Munir yace “wait wait, wat”? Ya ijiye basket na hannunshi yana kokarin connecting dot din yace “Mama ce daman matar Baffa daya kora me ciki?” Gyadamai kai Riyad yayi dasauri Munir yace “but ai ni nataba ganinta sau daya tazo gaida Ammi tanada kiba could it be sabida pregnancy ko maybe lokacin ban wani yin wayau nayi ba sosai ba I think ina around 10yrs lokacin saisa ban gane ta ba?” Lumshe idanu Riyad yayi yadafa mota yana sauke ijiyan zuciya sannan yadago yakalli Munir yace “Munir Mama don’t want anything to do with our family and I’m here na auri Rashida without knowing su waye su? I want to tell Mama wayeni!” Da sauri Munir yace “idan tace ka saki Rashida fa?” Dasauri yakalli Munir saikuma yakasa magana yadan duka ahankali awajen yayi shiru even though wani bangare na cemai karya fadama Mama yanzu yabari a sallameta but another part na zuciyanshi na cemai gwara yafada mata here and now she deserves to know waye ke auren yarta, tashi yayi yakalli Munir dake kallonshi yace “let’s go” Munir baicemai komiba yabi bayanshi suka tafi ahankali yabude dakin ya shiga yaga Mama na bacci peacefully.

Ijiye abincin Munir yayi yace “she’s sleeping zomuje muyi salla” fita sukai salla by 2:00PM Rashida ta dawo ganin Mama na bacci yasa ta duddubata tai murmushi tazauna tana kallon kulan abincin tadauki plate tabude kulan jellof rice tadeba kadan cikinta harya saba bata iyacin abinci she’s really missing her phone hakan yasa ta faraci tana cikin ci aka bude kofan Riyad ne hada ido sukayi da sauri ta dauke kanta ya kalli abincin dake plate din datakeci saikuma yakaraso ya ijiye wani waya wanda ga dukkan alamu sabo ne but bai bata kwalin ba ya ijiye gefen gadon ahankali yace “be using this ur sim is inside” kallon wayan tayi iPhone ne dudda batasan iPhone nawa bane dan bata saba dasu ba bataso ta karba but kuma batasan yanda zatai rejecting wayan ba, abu tahadiye a wuyanta murya chan kasa tace “thank you” juyawa yayi haryakai kofa yace “bari naje if anything comes up call me my number is inside” gyadamai kai tayi ahankali sannan yabude kofa yafice itakuma ta tsaya tana kallon wayan kafin chan tasa hannu tadauka tana taba screen din yabude gallery tafara shiga taga all pictures nata na yar vivo nata na wajen wanda yawanci hotunan pages na textbooks datake karatu dasu a library ne sai few pictures nata da lab coat da picture nata da Mama saikuma tashiga wajen waka taga songs dinta duka akwai murmushi tasakeyi sai kawai ta ijiye plate na abincin da duka baifi 3spoons tayiba ta kwanta jikin Mama tana kallon hotuna ahaka har akai magrib Mama tadan tashi taci abinci saikuma tasake komawa bacci magungunan ta da alluran dama suna sata bacci sabida abun ka da mai BP.


Zaune suke cikin mota wuraren 8 nadare gaban A&E, bude bayan motan akayi aka shigo Jummai dataci lafiyayyen shadda tadago kai takalli officer data shigo tana murmushi tace “thanks for coming Grace” Grace tace “you’re welcome Hajiya but wat is so urgent dakika kirani asibiti” bandage dake saman hancin Grace Jummai ta kalla tace “I want to end this mutanen da yarsu tamiki this but I want to confirm something are you sure Sarkin Kano ne yazo yayi bailing yarinyar Grace?” Dasauri Garce tace “100%, Oga yafadi mana haka fa kinga yanda jikinshi ke rawa ne daya budeta” mamaki yakara kashe Hajiya Jummai tace “how did Riyad know Zainab? Lokaci da aka kori Zainab Riyad was maybe around 13 yrs, yanzu duka dukanshi he’s 36, Riyad da baya zama gida how ya sansu haryake ma’amala dasu?” Saikuma ta kalli Grace tace “yasa kayan sarki dayazo?” Dasauri tace “no Ma, nothing shows he’s a king banda bodyguard dake binshi” shiru Hajiya Jummai takarayi saikuma tadauki wayanta cus takasa yarda Riyad ne taciro hoton Riyad ta nunama Grace tace “shine?” Shiru Grace tayi bata wani kalli fuskanshi ba lokacin dazata shiga Rashida take kallo but kaman shi hakan yasa tace “eh kaman shi but I’m not sure kinsan da daddare yazo and bana officer dasuke fitowa ne nikuma nake shiga” gyadakai tayi tace “okay” sannan tadauki wata bakar ViVa leather tabata tace “use this hold body I will look for you soon when it’s time to cook the girl up” murmushi Grace tayi tana hango how thick ledan looks da kudi ta karba tace “Hajiya I will remain loyal forever and ever thank you Ma saida safe” tabude motan tafice ta maida ta rufe Hajiya Jummai takalli wata mata dake gaban motan bakakirin da ita fuskanta sai uban muni ga kujera tace “kin shirya aikin ki Yar Mussa?” Da sauri matan tace “kwarai Hajiya! Rayuwata taki ce” Hajiya Jummai tai murmushi tana kada kafa tace “sauka kije ki tabbatar kin zuba ko a abinsha ko a abin ci, saikinzo gida” Dasauri tace “toh” sauka tayi anan parking space tawuce tana gyara hijabin jikinta sannan tawuce ta shiga cikin A&E tana sunnar da kai kasa, dakin cleaners tawuce dinsu tawuce anan ta dauki roban mop ta cire hijabi tasaka wani green riga da wando uniform sannan tafito ward tashiga gogewa tass kafin tawuce sama first floor lokacin 9:00 knocking gaban kofan 211 tayi but shiru hakan yasa tabude tashiga ciki Mama na bacci ga drip ga komi na aiki, Rashida itama tana zaune kan kujera but ta kifa kanta kan gadon takama hannun Mama tana bacci tana minshari kadan kadan dan bata gaji sosai yau ba, maida kofan Yar Mussa tayi tarufe tace “laaa nazo goge goge suna bacci” ta tsaya takalli dakin tass babu CCtV, bude idanu Mama tayi kadan dan ta dade tana bacci da sauri Yar Mussa ta juya taciro mop tashiga goge gogenta, dan tari Mama tayi jin wuyanta ya bushe sosai murya chan kasa tana kallon mai moping tace “dan taimakamin da ruwa” ijiye mop din Yar Mussa tayi ta juyo da sauri ta taho tace “to” dukawa tayi tadauki bottle water guda daya daga jakan bottle water dake wajen tanajin dadi azuciyanta tace “perfect opportunity” tabude goran tana tura hannu a aljihunta da sauri taciro wani syringe dake dauke dawani substance ta matsa da sauri aruwan tana jijjigawa, ahankali Mama dataji shiru tace “bakiga ruwan bane ko Rashida ta chanza musu wuri ne? Bude fridge kika dan Allah” Da sauri ta taso tana murmushi tace “a’a nagani” tamikama Mama goran tana ijiye marfin goran saman gadon sannan tajuya tacigaba da moping din da sauri da sauri, sosai Mama tasha ruwan thirsty kusan rabin goran tasha sannan tadauki marfin ta rufe, Yar Mussa  tagama moping tazo gaban gadon takalli ruwan da Mama tarage tace “dan Allah dan bani Insha nima kishin nakeji” Mama tace “kidauka karkisha ragowana” dasauri matan tasa hannu ta fizge ruwan har saida gaban Mama yafadi hakanan hakan Yar Mussa tace “nadau sabo bazan shanye ba wannan ya isa karmuyi asara bari naje kiyi bacci abinki” tana maganan tayi kofa bayan tadauki mop da bucket tabude kofan tafita tashiga next room tacigaba da aikacenta.


Mama tabita da kallo saikuma tace “hala batasan inada HiV ba” saikuma takalli Rashida da yau bata minshari sosai sabida batai aikin wahala sosai ba tashafa kanta tana murmushi tace “Amaryan Riyad” knocking akayi aka shigo office din Dr Bugaje ce sanye da scrub tana kallon Mama tace “kinga sai yanzu nafito daga surgery nan dana gayamiki wlh nace nadubaki kafin natafi, akwai wani abu dake miki ciwo?” Tayi maganan tana makala stethoscope dan duba heartbeat na Mama, Mama tace “lafiyana kalau wlh kaman ki sallame ni gobe ma naje nafara shirye shiryen bikin Rashida” dan dariya Mrs Bugaje tayi tace “mother Inlaw of the year Mama” kafafun Mama ta kalla da sun sabe kusan rabi tace “Alhamdulillah Mama kin sami lafiya sosai Welldone Mama, you’re a superwoman, wannan hartai bacci” tanuna Rashida, Mama tace “ai Rashida gatada nauyin bacci kamanme” Mrs Bugaje tace “tom bari naje Mama saida safe, banda tunani kinji ko” murmushi Mama tayi tace “to nagode, a gaida yara” juyawa Mrs Bugaje tayi hartakai kofa Mama tace “Doctor” juyowa Mrs Bugaje tayi Mama tace “ina alfahari na sanki, nasan ko bani Rashida nada wata uwa da mentor, thank you for everything” dan blushing tayi tace “Mama stop thanking me ki warke sabida ki koma gida nan da jibi ko gata” Mama tace “shikenan a kiyi tuki ahankali dare yayi” “toh” tafadi tana fita Mama kuma tashiga shafa fuskan Rashida har bacci yasoma kwasheta kafin chan bacci yayi nasaran dauketa.


Jijjiga da bed keyi up and down yasa cikin nauyayyen bacci Rashida tadan bude idanunta sabida yanda motsin ke mugun damun kanta, kafin chan motsin yayi yawa tabude idanun gabaki daya tana tashi zaune, Mama tagani tana wani bankarewa tana kama cikinta tana. “Hasbunaallahu wa ni’imal wakeel, Lailaha illallah wayyooo cikina wayyooo cikina” dawani irin sauri Rashida tai ihu. “Mama” daidai Mama tawani irin mirgino zata fado daga gado Rashida ta tareta takamata ajikinta tama rasa mezatayi, bata taba ganin Mama in this pain and agony ba cus tanada dauriya na ban mamaki, kankame Mama tayi datake abu kaman zata tashi ga kafafunta basa motsi tsabagen azaba tace “Rashida cikina wayyooo Rashida cikina, Rashida cikina” “somebody help me Doctorsssss!” Rashida tai wani irin ihu daya dauka ako’ina daidai lokacin kawai hancin Mama yafara fitowa da jini dayasa tasake buga wani uban ihu. “Doctors” daidai nan Dr Mumina dawasu nurses suka shigo ganin Rashida da Mama akasa yasa tace “meya sameta”? Jikin Rashida kawai rawa take bamata iya magana ba, kankame Mama tayi a hannunta Dr Mumina tashiga saka handglove hakama Nurses din wasu Drs ma na shigowa aka daga Mama daga jikinta aka daura akan gado Rashida na wani irin kuka tace “wat happened to her? Why is she bleeding daga hanci” Dr Mumina tama Nurse alamu tafita da Rashida wayanta Rashida ta dauka Nurse tafita da ita, rawa jikinta yake tana tsaye awajen Doctors sai zuwa suke ana shiga dakin da Mama ke, tanajin wayyyoo Allah cikina, cikina abinda Mama ke fadi kenan, tunda ta taso bata taba ganin Mama tai ihu tana kururuwa for ciwo ba sai yau, chan Rashida taji ana call Professor call him fast, taga nurses sun fito da gudun gaske sai kawai taji kafafunta na lankwashewa ta zube akasan wajen flat hannunta ya shiga rawa tabude wayan nata tashiga contact taga Riyad hakan yasa tai dialing number.


Yau sabida damuwa yamai yawa koda yagama abinda zaiyi da Haleema anan kan gadon ya kwanta bayan yayo wanka, wayanshi yahau kara hakan yasa yabude ido is so odd akirashi da night wayan yatashi yadauka Rashida tafito jikin screen din dayasa kawai yaji gabanshi yafadi fita yayi daga dakin yasauko kasa daidai wayan na katsewa yayi dialing number back yana ringing ya daga. Anatse yace “meke faruwa?”Nunfashinta kawai yakeji bata iya magana da kyar tace “zan…..zan mutu” katse wayan kawai yayi yakoma sama yashiga saka kaya Haleema na tashi dan tun ringing na wayan ta tashi tace “ina zaka Baby”? Ahankali yace “sleep fita zanyi” zatai magana yadauki car key yafita da sauri yashiga motanshi yana danna remote gate yabudu yaja motan aguje  dayake dare ne wlh cikin 5 good minutes ya iso asibitin sama yahayo aguje, tana zaune a inda take akasa ta hangoshi yana tahowa yana kallonta she felt as if her strength is coming towards her, dawani irin gudu cikin kuka ta tashi tai wajenshi batai wata wata ba tawani irin fada cikin kirjinshi ta kankameshi gamgam kaman wani zai rabata dashi tana wani irin kuka tama kasa magana, ahankali yasa hannunshi on her back yariketa yama kasa magana sai breathing fast, suna ahaka saiga Mrs Bugaje da hijabi tana gudu sosai tawuce su tai dakin kawai his mind tell him something hakan yasa yayi hugging nata so tight tareda manna mata peck a wuya, cikin wani irin murya na lallashi yace “stop crying Jewel, come” yadagota hannu yasa ya sharemata fuska yace “I’m here now Mama will be fine kinji”? Gyadamai kai tayi yakama hannunta saiya sauka kasa da ita yayi wajajen wasu kujeru ya zaunar da ita yaduka agabanta yace “stay here bari naje sama naga meke faruwa” gyadamai kai tayi yatashi yajuya yakoma sama gabanshi faduwa kawai yake non stop, direct yabude kofan dakin daidai lokacin da babban professor kecewa ke daga hannunshi yana kallon wristwatch dinsa yace “Time of death 4:57AM” chak Riyad ya tsaya kanshi na wani irin making bell sound yashigabin kowa na dakin da kallo tundaga kan Mrs Bugaje datai mutuwan tsaye tanama Mama wani irin kallo da idanunta ke kallon sama ga jini a hancinta da bakinta na gangara har lokacin, kafin ahankali Professor yakai hannunshi dake sanye da glove ya rufemata idanu sannan yaja farin zanin gadon yarufeta.



 

Post a Comment

0 Comments