ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»
TEAM----ZAFAFA BIYARπ₯ππ₯°π
ALLAH ka gafartama iyayenmuπππ».
*_LITTAFIN nan na kuΙi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haΖura domin ALLAH karki karanta_*.
No. 26
..............Cike da jin haushin Yoohan Nu'aymah ta fito daga sashen hajjo. Hakan yayi dai-dai da shikuma Yoohan Ιin zai koma dan ya kammala wayar.
Karo sukayi, goshin Nu'aymah ya bugu da sarΖar Cross Ιinsa. Da sauri tai baya saboda azaba. Shima bayan yaja kaΙan yana wani yamutsa fuska idonsa a kanta. Kasancewar Nu'aymah bata taka Ιan step Ιin Ζofar falon hajjon dai-dai ba lokacin da tai baya sai ta sake yo gaba zata faΙi.
Yoohan ya tabbatar idan ya barta ta faΙi zataji mugun ciwo ne, dan haka da saurinsa kuwa ya tarota ta faΙo jikinsa. Sai kuma ta firgice saboda tsoratar da tai najinta kwance a Ζirjinsa, ta wage baki zata tsala ihu yay azamar Ιora lallausan tafin hannunsa saman bakin nata ya rufe ruf.
Cikin tashin hankali Nu'aymah ta fara mutsu-mutsun kwatar kanta, jikinta sai rawa ya ke yi. Shikuma yaΖi sakinta dan ya tabbatar yana sakin nata faΙuwar daya gudar mata a farko sai tayi wadda ta fita a yanzu, cike dajin haushi ya daka mata tsawa, dan jiyayma kamar ya saketa ta faΙin ma yaga Ζarshen rashin kunya.
Duk da tsawan da yay mata bata nutsuba, sai ma cigaba dayin mutsu-mutsunta nason Ζwacewa takeyi, tuni hawaye kuwa sun fara bimata kumatu, dan a rayuwarta da hankalin kanta kuma hakan bai taΙa faruwa da itaba. Ko hannu bata yarda samarin gidansu wani ya riΖe mata balle akai ga runguma irin haka. Sai gata yau kwance a Ζirjin Ζaton kahiri, da ko yayunta basu taΙa aikata haka a gareta ba. gashi ya rufe mata baki babu damar magana. Kuma Ζarfi ba Ιaya ba.........
Jin ya manneta da bango sai tashin hankalinta ya Ζaru, dan ta zata wani abun kuma zai aikata mata, ta kasa nutsuwa ta fahimci taimakonta yayi. hannayenta duka biyu ta saka tare da dukan Ζarfinta tana ΖoΖarin ture masa hannunsa daya rufe mata baki da shi. Ko gezau baiyiba, saima wani shegen kallo da yake binta da shi tamkar ya manta a inda suke, ga fuskarsa a matuΖar Ιaure balle kai tunanin da biyu yay hakan, sai dai shima zuciyarsa wani irin harbawa take da sauri-sauri.
“Ouch!!” ya faΙa da sauri yana janye hannunsa da ya toshe mata baki da shi, dan kuwa daddagewa tayi ta gasa masa cizo a tafin hannun. Yaja da baya yana yarfe hannun nasa da faΙin, “Are you mad?!”.
Nu'aymah da har yanzu jikinta bai bar rawa ba ta galla masa harara tana share hawayenta. “Eh banda shi. ALLAH ya isana kuma, wlhy ka sake gigin taΙani saina fasa maka kai, danni ba Ζ΄ar iska baceba!”.
“Silly girl! Waye Ιan iskan?” ya faΙa da turanci kamar yanda ta faΙa itama yana galla mata harara tare da cafkota, iya Ζarfinsa ya fisgota tayo baya ta sake faΙawa jikinsa. Mannata jikin bangon ya sakeyi, ya toshe mata baki da Ιayan hannunsa. kafin ya Ιago Ιayan hannun ya kalli inda ta cije sa, yamutse fuska yay ganin yanda shatin haΖoranta suka fito masa, ba wajen data ciza Ιin kawaiba, tafin hannun gaba Ιaya yayi jaa abinka da ba'asan wahala ba...
Nu'aymah ta rikice iyakar rikicewa yanzun kam, dan ta yarda a ranta da gaske Yoohan son cutar da ita yake. Ζilama abinda ya kawosa gidan kenan. Sake kaima Ιayan hannun cizo tayi. Yayi saurin janyewa ya maye gurbin hannun nasa da bakinsa. Shi kansa baisan yaya akai hakan ta faru ba, ya tsinci kansa ne kawai da haΙe bakin nasa da nata ya shiga kissing Ιinta.
Yanda take kuka da turesa da yakushinsa ne ya sashi janyewa daga gareta da sauri. Duk da halin daya ganta na Ζololuwar shiga ruΙani da tashin hankali hakan bai hanashi kallonta ba, tare da zazzaro mata manyan idanunsa da suka sauya kala zuwa ja.
Harga ALLAH Nu'aymah ta tsorata yau kam, dan ta tabbatar tunda har ya iya mata wannan abun a cikin gidansu to lallai zai mata duk abinda yazo masa rai. Tunda tasan su basu Ιauki keta mutuncin mace a komai ba. Amma tsabar Ζarfin hali irin na mutuniyar taku ana sakar mata baki sai ko ta murguΙa masa bakin da sake zuba masa harara. iya Ζarfinta ta turashi dan har yanzun yana manne da ita ne a bangon, amma ko gezau baiyiba balle tasa ran samun hanyar kuΙuta. Waige-waige take gudun kar wani ya fito ya gansu a haka, tana kuma hawaye, cike da tsiwa cikin harshen turancin data san yafi fahimta sosai tace,
*_“Dama ku babu abinda kuka iya sai son taΙa mata da Ιata musu rayuwa, ALLAH ya isana Ιan iska kawai. shiyyasa wanda baya salla an haramta ma sa jin daΙin duniya. Sannan zai gamu da wahalhalu a wurare guda huΙu: A nan duniya, da ranar mutuwa, da cikin Ζabari da ranar hisabi. A duniya ana Ιebe ma sa albarka, a cire ma sa kwarjini daga fuska, a sa ma jama'a Ζyamar sa. A ranar mutuwa zai mutu da wulaΖanci da yunwa da Ζishirwa. A cikin kabari ALLAH zai Ζuntata ma sa, a hura ma sa wuta a cikin sa, a aika ma sa kumurci a tsakanin fatar jikinsa da namansa. A ranar hisabi za a baΖanta fuskarsa, a yi masa hisabi dalla-dalla, sannan a haΙa shi da zabaniyawa da za su wurga shi cikin wuta. Lallai, sallah ita ce ginshiΖin addini. Idan kaΖi gaskiya zaka faΙa Ιata. Idan ba ka ji nasiha ba, zaka yi da-na-sani. Wanda baiji bari ba ya ji hoho!......”_*
Ta Ζare maganar da sake turashi da Ζarfi. Yanzun kam da kansa ma ya matsa ya bata hanya, da gudu tabar wajen kuwa tana kukanta har yanzun.
Cike da takaicin kansa ya rumtse idanusa da Ζarfi, tare da Ιora hannunsa a goshi yana murzawa da abaton “Oh lord!, mina aikata?!”.
★★★★
A wani Ιan lungun sashensu Nu'aymah ta maΖale tana sauke tagwayen shashshekar kuka, har zuwa yanzu jikinta baibar rawa ba, sai faman waige-waige take tamjar ance mata Yoohan Ιin biyota yayi.
Ta ΖanΖame jikinta lokacin da abinda ya farun ya sake dawo mata a rai, yanda gashin jikinta ke wani mimmiΖewa zai tabbatar maka da tsigar jikinta tashi takeyi.
Da sauri ta saka hannu tana share hawayenta saboda jin tahowar mutum. ‘Na shiga uku ya biyo ni’ ta faΙa a fili zuciyarta na wani irin zallo tamkar zata faso Ζirjinta ta fito........
“Nu'aymah lafiya na ganki anan? Mi kikeyi ne haka?”.
Duk da ganin Aunty Kubrah ce ba Yoohan Ιinba hakan bai hana Nu'aymah sake rikicewa ba, ta shiga inda-inda jikinta na tsuma. “A..Aunty babu ko.. Komai”.
Kubrah data kafeta da ido taΙan murmusa, sai kuma ta juya bayanta tana faΙin, “Ki kwantar da hankalinki ai ba biyoki yayi ba, na tabbatar kuma babu wanda ya ganku a gidan nan”.
Wani muguwar faΙuwa gaban Nu'aymah ya sakeyi daboda jin furicin Aunty Kubrah. Cikin rawar harshe Nu'aymah tace, “Aunty Kubrah wlhy ni.......”
“Kinga kwantar da hankalinki Nu'aymah babu maiji, indai nice ko Hajarah baza taji wannan zancenba balle wani a gidan nan. Amma inason ki faΙamin gaskiya, yaushe kuka fara wannan abun ke da shi?”.
“Innalillahi! Aunty wlhy bamu taΙa yiba, yau ma na rantse shin......”
“Kinga ya isa. Share waΙan nan hawayen idan baso kike ki tonama kanki asiri ba da kanki”.
Nu'aymah duk ta sake rikicewa, tama rasa fahimtar inda maganganun Aunty Kubrah suka dosa saboda tashin hankali. Duk da ta share hawayen sun gaza tsayawa. Hannunta Kubrah ta kama har lokacin fuskarta da murmushin da Nu'aymah ta gaza fahimtar na minene. “Kinga muje sashenmu, idan ba hakaba Umm sai ta fahimci abinda ya faru, ko kinfi buΖatar hakan?”.
Da sauri Nu'aymah ta shiga girgiza mata kai, “A'a wlhy Aunty, banason Umm ta sani dan zata kasheni, dan ALLAH karki faΙa mata, wlhy kuskurene ba kuma laifina bane ba, na rantse da ALLAH Aunty ban taΙa yiba, ko hannuna Namiji bai taΙa riΖewa ba”. Ta Ζare maganar da rushewa da wani irin kuka maiban tausayi.
Komai Kubrah bata sake cewaba ta kama hannun Nu'aymah suka nufi sashensu. Ta Ζofar baya tabi da ita, dan Ζannen Addah su Aunty Basira suna falo zaune dasu Addah suna hira. Batare data bari sun gansu ba ta shige da Nu'aymah bedroom Ιinsu. Zaunar da ita tayi sannan itama ta zauna a kusa da ita. Har lokacin kuma Nu'aymah kuka takeyi, zuciyarta na Ζarajin tsanar Yoohan matuΖa........
“Ko shine Ameer Ιin Saurayinki?”.
Da sauri Nu'aymah ta Ιago tana kallon Kubrah, sai kuma ta shiga girgiza mata kai, “Aunty dan ALLAH ki yarda dani, wlhy Ameer ba saurayina bane. Wannan kuma bama musulmi bane ba, baΖone yau na fara ganinsa”.
HaΙe fusaka Kubrah tayi tamau tana kallon Nu'aymah Ιin. “Karkimin Ζarya Nu'aymah, inba hakaba wlhy na fasa rufa miki asirin, a yau da daddare zan sanarma Hajjo da Baba malam da Umm komai. Ki faΙamin tun yaushe kuke tare? Sau nawa kuma yay amfani da ke?”.
Duk sai Nu'aymah ta sake daburcewa, dan tama rasa wace amsa zata bama Aunty Kubrah, gaba Ιaya ta kasa fahimtar manufar Kubrah.......
Kamar Kubrah tasan tunanun da Nu'aymahn keyi, sai ta sassauta fuskarta tana gyara zama. Ta Ιan rage kaushin muryarta kuma ta koma magana cikin lallashi. “Nu'aymah kinsan dai yaya nake a gareki, duk abinda zan iya gani gasu Hajarah raina ya Ιaci idan nagani daga gareki dolene naji zafi, Ιiyar Ζ΄ar uwar mahaifiyata ce kuma ke, dan kuwa Umm tamkar Ζ΄ar uwar Adda take, tamafi min wasu Ζ΄an uwan Addan. Yanzu Nu'aymah da wani ya ganki a gidannan Ζaton banza yana lalubeki mikike tunanin zai faru?, idan ma iskancin zakiyi ai gara kuyisa can a waje wani bai gankiba ko, amma a cikin gidanku? Babban gida mai daraja irin wannan? Wane kallo kikeson aima iyayenki maza damu kanmu Nu'aymah?”.
“Dan ALLAH kiyi haΖuri Aunty Kubrah, wlhy bazan sakeba wannan ma Ζaddara ce da kuma kuskure”.
“ALLAH yasa hakane to”. Kubrah ta faΙa tana wani Ιauke fuska da ΖyaΙe baki.
Nu'aymah na kuka tace, “Wlhy da gaske nake Aunty. Dan ALLAH ki yarda dani”.
“Nu'aymah idan ban yarda da ke ba minene amfanin musawar to?, tunda idan kunbar gabanmu ALLAH kaΙai yasan mi kuke aikatawa, masu iya magana fa kance rana dubu ta barawo, Ιaya tak ta mai kaya. Yau Ιinma ai bakiyi tunanin zan ganku ba”.
Ζasa Nu'aymah ta zube tana kuka tamkar ranta zai fita, ‘Ita mizata faΙama Aunty Kubrah ta fahimceta ne wai? Wane rantsuwa zatai mata danta yarda ba da yardarta kafirin nan ya aikata hakanba a gareta?’.
Sai da taci kuka sosai, Kubrah na zaune na kallonta kafin ta Ιagota ta rungumeta, “Kukan ya isa haka, aina yarda ba laifinki bane. Na miki hakane kawai dan kisan baki dai-dai ba”.
“Na gode da kika fahimceni Aunty, kuma namiki alΖawarin hakan bazata sake faruwa ba insha ALLAHU”.
Ζagota Kubrah tayi ta share mata hawayen tana murmushi, “Shikenan naji, kuma na miki alΖawarin babu maijin zancen nan a gidan nan kinji, kije bayi ki wanke fuskarki kizo ki sake shafa hoda dan karma wani ya zargi wani abun kuma kinji ko. Ki kuma saki jikinki inba hakaba Umm zata gane, kuma kinsan halinta. Zatabi duk hanyar data dace dan tasan gaskiyar abinda ya sakaki kukan”.
“Insha ALLAHU bazan bari ta gane ba Aunty, bara ma na wanke”. Ta Ζare maganar tana miΖewa da sauri ta nufi bayin su dake cikin Ιakin. Tana wanke fuska tana kallon bakinta a mirror. Wasu hawayen sai sake ΖoΖarin zubowa suke tana dannesu da Ζyar. A fili tace, ‘Na tsaneka mugu Ιan iska mai suffar samudawa, bazan taΙa yafe makaba wlhy”. Ta Ζare maganar da fashewa da kuka.
Taja kusan mintuna biyu tana kukan kafin ta wanke fuskar ta fito. Fitowar tata tayi dai-dai da shigowar Hajarah da wayar Kubrah a hannu. Da mamaki Hajarah take kallon Nu'aymahn, dan ita dai bataga shigowarta sashen ba.
“Nu'aymah yaushe kika shigo ne? Gashi kamar kinyi kuka?”. Da sauri Nu'aymah ta girgiza mata kai, sai kuma ta kalli Inda tabar Aunty Kubrah dan tana zaune a wajen, tana jinsu kuma amma ko kallonsu taΖi tayi balle ta nuna alamar tasan mi sukeyi ma. “Babu komai Aunty Hajarah, kaina ne kawai ke Ιan ciwo”.
Ζarasawa inda Nu'aymahn take Hajarahn tayi, ta Ιago fuskarta cike da nazari........
“Wai miye hakane? Tace miki babu komai kanta ke mata ciwo miye na damunta ne kuma?”.
Baya Hajarahn taja kanta a Ζasa tace, “Kiyi haΖuri Aunty Kubrah, ga wayarki dama Alhaji ne ya kiraki”. Ta matsa inda take cike da girmamawa ta bata wayar.
Tana amsa ta nuna mata Ζofa da ido. Da sauri kuwa Hajarahn ta fice.
Kubrah ta maida dubanta ga Nu'aymah dake a tsaye har yanzu. “K kuma ki bada himmar tonama kanki asiri kinji ko, ki wuce ki shafa hodan, idan kuma sokike wani ya sake shigowa to”.
Gaban Mirror Nu'aymah ta Ζarasa. Ta shafa mai da hoda harda kwalli, duk da dai hakan fuskar dai babu walwala.
Amma sai Kubrah batace mata komaiba suka fito falo inda su Hajarah ke hira tare. Zama tayi kamar yanda Addah dake kallonta ta Umarceta. Su Aunty Basira nata tsokanarta da faΙin ina tsarabarsu ne?.
Tun tana noΖewa dai harta Ιan ringa amsasu, amma ta gaza sakin jikinta yanda ya kamata sosai. Duk motsinta Hajarah da Addah na lura da shi, sai dai babu wanda ya iya cewa komai a cikinsu.
___________________________
A Ιangaren Yoohan kuwa duk yanda su Hajjo sukaso ya zauna jiran dawowar baba malam ya gaza hakan. Yace musu zai dawo da safe yanzu yanada wani uziri.
Badan hajjo taso ba ta barshi. har Ζofar gida su Yah Ahmad sukai masu rakiyya shi da Manager. Inda su Solomon ke jiransa a mota. Kasancewar basu iske baba malam ba yasa bai shiga dasu cikiba. Yace su jirashi a waje. Dan da Ζyarma Su Ahmad suka lallaΙashi ya shiga cikin gidan. Da farko ya ce zai koma tunda baba malam ya fita. Dan dama yaso yin surprise Ιinsa ne shiyyasa bai sanar masa shigowarsa kanon ba ma.
Har drivern sa ya tada mota ya tsaidashi. KuΙi ya ciro a cikin jakarsa rafa guda na Ιari biyar sabbi Ζal ya miΖama malam Ζarami yana faΙin, “Please a bama yarinyar nan barka da salla. Na manta ban bata ba”.
Malam Ζarami da ya fahimci Nu'aymah yake nufi sai yay murmushi. bai musa ba ya amsa yay masa godiya, dan suma daya basu sukaΖi amsa a ciki Ιata rai yayi, wai basu Ιaukesa Ιan uwansu ba. Hakanne ya sakasu amsa tunda yace barka da salla ce.
Duk abinda ke faruwa Solomon na saurarensu. Dama cike yake da haushin sake zuwa wannan gidan. Ya kuma Ιauki alwashin suna komawa wannan karon sai ya sanarma madam Chioma. Dan tsaf ya fahimci waΙan nan mutanen zasu iya jan hankalin Ogan nasu tsaf, musamman yanda suke masa hidima kamar wani sarki. Yanzu haka a gabansa aka saka babbar leda a booth wai kayan barka da salla ne aka bama Yoohan Ιin a cikin gida. Ya cije bakinsa yana satar kallon Yoohan daya kwantar da kansa jikin kujera ya lumshe idanu kamar mai barci ta mirror.
Babu abinda kema Yoohan kai kawo a zuciya da ruhi sai kalaman Nu'aymah. Kalaman sunyi masifar tasiri a ransa fiye da zaton mai karatu. Sai faman tisasu yake dalla-dalla kamar mai bitar karatu. Duk da ac dake aiki a motar bai hana zufa tsatstsafo masa a goshi ba. Mafarkin da yayi shekaran jiya da baba malam ya kuma sake maimaita shi yau da safe ya shiga tariyowa shima.
ya sauke wani irin nannauyan numfashi yana sake tariyo mafarkin nasa da yayi a karo na biyu kenan,
*Ya kanga kansa a mafarkin a gaban wani kogo Ζaton gaske, cikinsa akwai wani irin wuta dake ci mai ban tsoro, dan duk iya hasashensa ya kasa kamanta Ζarfin wutar da zafinta a zahiri. Aduk lokacin da yake a gaban wannan kogon dake zuwa masa a mafarki, ya kan tsinci kansa cikin matsanancin mawuyacin hali da ruΙu, sai dai kuma abin mamaki sai ya ga baba malam acan gefensa cikin shiga ta kamala, a wasu irin korayen ciyayi masu bada ni'imtaccen yanayi yana masa murmushi da miΖa masa littafin nan na musulmai (Al-Qur'ani), yakan ringa ce masa_______*
*_“Yoohan wannan shine zancen ALLAH, littafi dake Ζunshe da kowane irin sirri, littafin da aka aiko MANZONMU ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) da shi. kanada sauran daman riΖo dashi domin ka samu tsira daga wannan narkon azabar dake gabanka. Kazo gareni, zan nuna maka hanyar sanin UBANGIJINA kamar yanda ya aiko MANZONMU ANNABI MUHAMMADU (S.A.W) a garemu ya nuna mana muma, ya kuma koyar damu. Ni Sooraj bin Hashim, na rantse maka da ALLAH, babu wani addini na gaskiya sai musulinci, babu wata hanya ΖyaΖyΖyawa sai ta bin UBANGIJI, babu wani abin taΖama da riΖo sai MANZON ALLAH. Inhar kabi ALLAH, kai koyi da koyarwar MANZON ALLAH, ka riΖe gaskiya da amana, ka tsare gangar jikinka daga saΙama ALLAH, ka nema dukiyarka ta hanyar halak, kaji tsoron zalintar mutane, ka kiyaye jinka da ganinka daga haramun, ALLAH bazai jarabceka da shiga wannan taskar azabar dake a gabanka ba. Domin UBANGIJI ya tanadi gidaje guda biyu, WUTA DA ALJANNAH, ya kumayi alΖawarin cikasu da mutane. Dan haka Yayha kazo gareni, kazo ka karΙi kalmar LA'ILAHA ILLAH, MUHAMMADURRASULULLAH (S.A.W)._*
A wancan ranar da yay wannan mafarki ya wayi garine a yanayin sanyin jiki, da tunane tunane kala-kala. Ya kuma yini zuciyarsa na rinjayarsa da amsa wannan kira. Sai dai daya tuna wani gagarumin al'amari sai yay azamar ΖwaΙar kansa harma da alΖawarin nisanta kansa da su baba malam Ιin. Dan yau Ιin nanma da Ζyar manager ya lallaΙa shi sukazo nan Ιin. duk da kuwa yana a cikin kanon yau kwanansa biyu kenan ma.
Kafin su Ζarasa hotel Ιin daya sauka sosai ya tsinta kansa cikin ruΙanin kalaman Nu'aymah da mafarkinsa. Sai Ιunbin takaici da dana sanin abinda ya aikata ma yarinyar yakeyi, wanda sam ba halinsa bane yin hakan, amma yasan ita da duk wanda zai iya ji ko ganinsu a lokacin bazai taΙa yarda da shi ba. Ya Ιan ciza leΙensa na Ζasa da Ζarfin tsiya, Ζirjinsa na sake masa zafi.
Motocin na tsayawa baiko jira an buΙe masa ba ya buΙe da kansa ya fice. Daga Solomon har sauran guards Ιinsa tsaye kawai sukai suna kallonsa cike da mamaki da tsoron yanayin nasa. Da sauri Solomon yabi bayansa shima dan yasan ba lafiya ba dai. Gashi key Ιin Ιakin Yoohan Ιin yanama a hannunsa ne.
Ζan gudun da yayine ya sakashi cimmasa. Dan haka suka Ζarasa Ζofar Ιakin tare. Solomon ya buΙe masa tare da matsawa ya bashi hanya dan ya shiga.
Batare da yace masa komaiba ya shige, shi ma Solomon Ιin sai ya bisa yana faΙin, “Sir lafiya kuwa?”.
Cak Yoohan ya tsaya da ga yunΖurin shiga Bedroom Ιin da ya keyi, batare da ya juyoba ya Ιagama Solomon Ιin hannu da masa alamar ya barsa.
Da baya-baya Solomon ya rinΖa tafiya harya fice da ga Ιakin, yaja masa Ζofar a hankali gabansa na faΙuwa da yanayin ogan nasu.............✍
π€π€πΆπ»Tofa, Dr Yoohan yaya dai?πΆπ»
0 Comments