TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

DABI'AR ZUCIYA ❤ page: 41 - 42

 41



Tunda suka tafi hankalinsa naga titi,tuqinsa kawai a hankali cike da nutsuwa har suka kawo gidan amaren,jama'ar daya debo suka fita,saidai mubina ta kasa koda motsawa,saboda yadda kan mata ciwo ainun,ya kuma qaru ke ciwon saboda saraki,wanda baisan meke faruwa ba,don suna zuwa bayan ya kashe motar ya fice daga ciki shima.


Baisan tana ciki ba sai sanda zasu koma,da yake wadanda ya debo din ba komawa zasuyi ba,amiru ya bude gaban da niyyar shiga ya ganta,ya shaidata don haka ya tambaya,da qyar ta iya amsa mishi


"Please saraki ka daure mu ajeta koda pharmacy ne ta amshi magani,daga nan ta kira wani ko daga gida ne ya maidata gida" yace da samir sanda yake tada motar,shuru ya masa bai amsa masa ba,ya fara tuqinsa abinsa.


A bakin wani madaidaicin private hospital ya tsaida motar,yayi horn sau biyu mai gadi ya taso ya bude masa ya saka motar ciki


"Ho samir" amiru ya fada a ranshi,bai tsammaci ma yana da niyyar yin abinda ya sakashi ba,duk da yasanshi sarai,yana da matuqar tausayi da kulawa,mutum ne kuma shi mai tausayin mace qwarai.


Nurse ce ta fito ta kamata zuwa ciki saboda yadda take tafiya da qyar saboda ciwon da kan nata yake mata.


Mintina qalilan ta gama ganin likita,amiru na zaune yana waya yaga shigowarta,ba jimawa samir din ya shigo shima ya tada motar suka wuce.


Bakin wani pharmacy ya tsaya,ya wurgawa amiru dake zaune a baya takardar hannunsa ba tare da yace masa komai ba,ya dauka ya duba saiya saki qaramar dariya,ya fuskanci kamar bisa dole yake duk wannan hidimar,kuma yasan dama baiso zuwa kai amaryar ba,shi ya tattagoshi,don haka baice komai ba shima ya fita,ba jimawa ya shigo da ledar magungunan,samir din ya kuma tada motar suka wuce.


"A wacce unguwa zamu saukeki,zamu wuce gia dare na dada yi" lallausar muryarsa ta sauka a kunnenta ta sake haifar mata da kasala,saita lumshe idanu,murya can qasa ta gaya mishi sunan unguwar,tana kallonshi ta gefan ido.


Nutsuwarsa da jan ajinsa sunyi yawa,komai nashi bisa salo me qayatarwa,abinda ya fara fusgarta akanshi kenan tun karon farko.


Dai dai sanda zasu wuce ta wani waje taji amiru ya sako masa hira kan wajen,wanda dukka maganar tasu kan kasuwanci ne,sai tayi fakare tana sauraren yadda muryarsa ke fita da haruffa a jere masu cike da nutsuwa da kamun kai,hakan ya sake dulmiyata cikin wata duniya,har batasan sun shigo unguwar tasu ba,tadai ji amiru na tambayar number gidansunta gaya masa.


"Na gode sosai,Allah ya saka da alkhairi,na gode" ta fada cikin raunanniyar murya,tana wassafa yadda zata samu number dinsa cikin sauqi.


Sai a sannan ya kalleta,ya gyada kai kawai yana kauda fuskarsa,tadan leqa baya kadan tana yiwa Aamiru godiya sannan tayi hanyar gida.


Shigowar kira wayarsa ya sanyashi waiwayawa ya dubi Aamiru


"Pls karbi driving din nan" sai ya fito suna qoqarin musayar sit,yana shiga wani yaro ya fito da hanzari daga cikin gidan,dai dai sanda amiru ke fitowa shima don shiga gidan driver,yana amsa wayar,baiji abinda yaron ke cewa ba,har sai daya gama wayar,dai dai sanda suka dauki hanyar barin unguwar


"Ta aiko a bata phone number din ka zata maka godiya idan ta samu sauqi"


"Kai kuma saika dauka ka bata kenan?" Samir ya tambayi amiru ba tare daya waiwayo ya dubeshi ba,yana qunshe dariya ya amsa masa


"Tunin ma,mukasan inda rana zata fadi,tunda kaine a kasuwa ai gwara a bata,mu mun riga da mun sayar" harara ya balla masa


"Idan ban girgide maka auren ba kace bani bane"


"Tuba nake the giant saraki" ya fada yana daga hannayensa sama alamar surrender,saiyayi qwafa kawai,bai sake ce masa komai ba.



***********Gefanta ta ajiye wayar kana ta miqe tsaye,goye da hannayenta a baya ta soma kai kawo da alamun zuzzurfan tunani.


Wayar landline dake dakinta ta daga kai ta kalla,kana ta isa wajen da hanzari ta zauna daga gefan gadon,ta fara kiran sashen masu aiki.


Bugu biyu aka daga


"Turomin saratu" ta bada umarni sannan ta kife wayar,taci gaba da xama a bakin wayar,har zuwa sanda taji ana knocking qofar bedroom din nata.


Zamanta ta gyara sannan ta bada izinin shigowar,cikin daqiqu kadan matar ta bayyana,kakkaura ce baqa,bata da tsaho sosai,saidai da alamu shekaru sun fara zuwar mata,duk da ba wani masu yawa bane amma tayi qaura daga gurbin quruciya zuwa na manyance.


"Zauna saratu" mummy ta bata umarni tana bin saratun da kallo,saidai abinda ta kirata dominshi har a sannan bataji nutsuwar hakan cikin zuciyarta ba.


Bata saba saka kowa cikin sabgar ba tsahon shekarun data dauka tana gudanar da al'amuranta a sirrance,to a yanzun ma batason ta soma sanya kowa gudun cabewar lamura,duk da cewa saratu amintacciyarta ce,saidai bata sakar mata ragamar komai ba,ta barta ne tasan iyakar abunda taso ita saratun ta sani


Dan tsakin da batasan ya fito ba ta saki,saita dubi saratun


"Jeki abinki" har ta isa qofa tunaninta yakai mata ga yarinyar


"Ki kiramin wannan baquwar me aikin"


"Kaltume?"kai ta gyada


"Eh ita"


"To hajiya" ta amsa mata tana ficewa daga dakin.


Karamar ajiyar zuciya ta saki,bata kaisu shekaru ko wayewa ba,bare aje ga batun wayo ko gogewa da sanin rayuwa ba,hakanan tafiya da itan zai sake zama mata tamkar wani tsani izuwa wani bigire. Kanta ta sake gyadawa tana sake tabbatarwa da kanta hakan yayi.


Daga karatu kaltum din ta shiga bawa jawahir labarin qauyensu,bada labarin a wajen kaltume dai dai yake shawagin ruhinta cikin qauyen,tana jin nishadi har tsakiyar zuciyarta duk sanda zata bawa jawahir labarin,kamar yadda jawahir din labarin ke burgeta,tana jin kalar wata rayuwa ta daban da batasan da wanxuwarta ba.


Dai dai nan saratu ta shiga dakin,ta kuma shaidawa kaltum kiran mummy,gabanta ya fadi,suka hada ido da jawahir,sai jawahir din ta miqe


"Muje na rakaki" kanta ta girgiza


"A'ah....tunda batace kizo ba tabbas ni kadai takeson nazo din,ki zauna kada mummy tayi fushi,yanzu zan dawo" jawahir din batace komai ba har suka fice daga dakin zuwa katafaren sassan mummy,bisa jagorancin saratu.



Tun daga yanayin dakin kaltum ta tabbatar da cewa lallai akwai qatoton bambanci,akwai kuma izza da jin isa bisa ga komai na lamarin hajiya jiddan.


Binta take da kallo tare da qoqarin sake karantarta sanda take tunkaro inda take,duk wani motsi nata da yanayin dabi'unta ta gama karanceshi,tun a farkon xuwanta ta gama gane cewa,bata da rawar kai,yawan surutu ko kuma shishshigi


"Kaltume" mummy ta kirata sanda ta zauna a cure waje daya


"Na'am momi" ta amsa mata a nutse


"Inaso zaki rakani anguwa gobe,ki shirya kamar gobe na safe,banason ki wuce haka,hakanan banason ki gayawa kowa batun zuwa unguwar,ni mutum ce mai son sirri,banason mutum mara sirri kin fahimta ai" kai ta gyada mata,sannan ta bata umarnin tafiya.



Har takai bakin qofa ta kirayi sunanta


"Hatta jawahir banason taji,don ba inda zanje da ita" kai ta gyada tare da ce mata


"To"


*********Goma na safiyar washegari har da mintuna goma sha biyar ne,daya daga cikin motocin dake farfajiyar gidan,wadda take mallakin hajiya jidda aketa zubawa kaya a booth tari guda.


Hamshaqiyar mota ce wadda ta lashi kudade masu yawa kafin ta mallaketa,amma duk wanda zai kalleta koda baisa kudin abun hawa ba yasan motar taci kudinta.


Cikin shiga ta qasaita dake nuna ainihin zallar alfarma da cikar arziqi da dukiyar mutumin da take aura ta fito,tana taku ɗai ɗai tare da qarewa farfajiyar kallo sanda ta tsaya tana jira a bude mata mazauninta.


Daga can wata shiyya dake mahada da sassanshi na gidan shima yake takowa,cikin shigar suit na alfarma ,hannunsa riqe da wani file dake cike da takardu yana budawa daya bayan daya,yana takowa ne cike da sassarfa,gefansa umar ne yake masa wasu bayanai,wanda da alama sun shafi takardun hannunta.


Ita ta fara hangoshi,saita dan gyara tsaiwarta,sam idan zatayi irin wannan tafiyar bata qaunar su hadu kafin fitarta daga gidan,duk kuwa da cewa yawa yawan siyayyar da take fita daga gidan zuwa wancan wajen tana fitowa ne daga aljihunsa.


Rufe file din yayi ya miqawa umar kana ya masa magana kadan,sai umar din ya juya zuwa mota,shi kuma ya qaraso inda take tsaye


"Barka da safiya" kamar ko yaushe,cikin kallon dake nuna qauna da kulawa tace


"Barka kadai my son....za'a fita kenan"


"In sha Allah" ya amsa mata yana kallon kayan da ake zubawa a booth din motar,kayane masu yawan gaske na amfanin yau da kullum,tun kafin ya gama mallakar hankalinsa take zuba irin wadan nan kayan take fita dasu zuwa duba gidan marayu,wannan tshohuwar dabi'arta ce da kaf gidan sunsan da ita.


Yana tsaye harta shiga motar,shi da kansa ya rufe mata murfin motar,yana jin kyautatawarta data shaida masa zata fita ne da kaltume,hakan yana shaida masa cewa ta soma sakewa dasu cikin gidan kamar yadda yakeso.


Duka duka tafiyar bata wuce ta minti arba'in ba suka isa wata unguwa,akwai gine gine wanda suke a tsare,saida akwai qarancin zirga zirgar jama'a qwarai da gaske.


Qofar wata babbar katanga mai tsaho motar tasu ta tsaya,sai a sannan kaltume dake zaune gaban motar ta daga kanta tana bin katangar da kallo,tun shigarta motar bata motsa ba,saboda tsoro rashin sabo da kuma hada muhalli da mommyn karo na farko,duk da cewa tunda suka shiga motar mummyn ke waya,wadda ko abu guda daya kaltumen bata fahimta ba cikin hirar da takeyi din.



Babu wanda ya tanka ko ya motsa,har zuwa sanda mummyn ta daga wayar,ta kuma shaida isowarta,ba'a rufa mintuna biyu ba wani kakkauran mutum dogo baqi ya fito ta qaramar qofar gate din,fuskarta dauke da madaukakiyar fara'a ya qaraso dab da motar,sannan ya fara bawa dirvern mummyn wucewa zuwa qofar da zuwa yanzu aka wangale mata ita.


A hankali ta zuro qofafunta da suka fara rawa.


,kallon farko ta yiwa asibitin ta tabbatar asibitin masu rangwamen hankaline,duba da yadda suke ko ina bajaja a farfajiyar asibitin,kowa yana sharafin gabansa.


Tunda take bata taba tsintar kanta a muhalli makamancin wannan ba,hasalima ita din mugun tsoron mahaukaci gareta,jakar mummy dake hannunta da qyar take ruquwa,ji take kamar ta kama mummyn ta ruqunqumeta amma tasan batayi wannan isar ba,ta dubu drivern mummyn da matashin da suka taho tare,wanda sai da aka jirayi zuwansa daga wani waje da batasan ina bane sannan suka taho,saita fuskanci hankalinsu kwance yake,babu wani tsoro ko fargaba irin nata tattare dasu.


Cikin mintuna qalilan wasu mutane maza biyu mace daya suka iskosu,sunfi kama da likitoci dake kula da marasa lafiyan saboda yanayin suturar jikinsu,cikin wani irin girmamawa suka tarbi mummyn.


Sakin ajiyar zuciya kaltume tayi sanda taga sun durfafi wata qofa da babu yawan jama'a sosai,tsoron dake cike fal a zuciyarta ya ragu,don tayi tsammanin zasu kewaye marasa lafiyan ne kamar yadda tasan anayi idan mutum yakaiwa marasa lafiya ziyara.


Babban office ne me kyau ba laifi,su suka jawa mummy kujera daya don ta zauna,saita girgiza kanta


"Ai banga ta zama ba,muje na ganta tukunna,inga in akwai matsala sai a san matakin dauka tunda wuri"


"To ba laifi,amma yau da wannan zaku shiga?" Ma'aikacin daya tarosu ya fada yana nuna kaltume dake tsaye riqe da jakar mummyn da hannu,sai a sannan ta waiwayo ta dubu kaltume,batasan tana biye da ita ba da alama


"Ki koma can wajensu alasan ki zauna" ta bata umarni,saita gyada kai tana hade yawun tsoro,ta juya zuwa wajen motar tasu tana addu'ar ta isa lpy.


Qofar motar ta bude ta shiga saboda tsoro,tana bin harabar asibitin da kallo cikin nazari,wato ta karanci wani abu a rayuwa,shi mai lafiya duk inda yake dan gata ne,duk wanda Allah ya bawa kyautar lafiya ya gode masa,babu wata ni'ima data kai ta lpy dadi,gasu dai wadan nan bayin Allah,Allah ya amshe ni'imar hankali daga garesu qila badon sun masa wani laifi ba,sai don haka nan yaga damar ganinsu......



Tunaninta ya yanke da sautin qarar wayar mummy data bari cikin motar,kafin tayi wani motsi alasan ya zuro da kansa yana duban wayar


"Ko zaki dauki wayar ki miqawa hajiya?, professor ne yake kira,kuma fada take a irin haka idan ya kira ba'a kai mata ba,shima kuma bayaso ya kira ba'a dauka din ba" tabbas tsoro takeji sosai,amma babu yadda ta iya tunda ya buqaci hakan,saita ajjiye jakar hannunta,tasa hannu biyu ya dauka wayar tana kallon irin kyan da wayar ke dashi,duk da hankalinta ba'a nan yake ba,ta buda murfin motar ta zura qafafunta ta fito.


Tana tafe tana waige hara ta dawo office din,saidai wayam babu kowa,sai wani mutum guda dake tsaye yana rubuce rubuce cikin wani file.


Muryarta nadan rawa alamun tsoro da rashin sabo take tambayarsa mommyn.


"Tare kuke?" Ya tambayeta bayan ya kafeta da idanu,kai ta gyada,kamar bazaiyi magana ba,sai kuma ya nuna mata wata siriryar qofa hanya


"Ki shiga ta nan,daki na can qarshe hannun hagunki" kai ta gyada masa sannan ta nufi qofar.


Tsoro ne sosai ya kamata saboda yanayin duhun wajen daya bambanta dana waje,duk da haka bata fasa saka kai ba,saboda yadda wayar dake hannunta kiran yaketa shigowa yana yankewa,a haka harta isa dakin daya ce mata,saidai kuma qofar kamar a kulle take,sai qaramar taga dake bude,ta yanke shawarar ta leqa ta nan ko wani ta bawa ya miqawa mommyn wayar.......



*_KO KUNSAN DA YAWANMU LAIFUKAN DA MUKA YIWA 'YAN UWANMU KE HANKADAMU WUTAR JAHANNAMA?_*


*_ZAGIN MUSULMI,CIN ZARAFIN MUSULMI,WULAQANTA MUSU,CIN HAQQIN MUSULMI,TOZARTA MUSULMI,YI DA MUTUM,RASHIN BASHI HAQQINSA NA KARE HAQQINSA DAKE KANKA,WATO KARE MUTUNCINSA DA ADDININSA,DA YAWA ABINDA MUKE RAINAWA MUKE GANIN BAIKAI YA KAWO BA,YA KUMA ZAMA JININ JIKINMU SHIKE KAIMU WUTA,Allah ka bamu dacewa_* 👏🏽👏🏽👏🏽👏🏽



*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*


*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*


*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*


*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*


*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*


*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*


*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*


*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*


*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*


*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*


*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU AKAN KUDI NAIRA 1K KACAL*


2👉🏾400

3👉🏾500

4👉🏾700

5👉🏾1000


*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*


09134848107


*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽

#team zafafa biyar






42


Window din yadan kerewa tsahonta,don haka ta danyi dage don takai ga bakin window din.


Dakine fetal dake malale da siminti,babu komai cikin dakin da zaka iya hanga,sai wani gado guda daya mara kyan fasali,daga gefan gado kuma saman daben simintin dakin kana iya hangen wata mace zaune jingine da bango,fuskarta ta nuna tarin shekaru sosai,tana sanye da wasu tufafi da ba lallai ka gane ainihin kalarsu ba saboda tsufa da rashin wadatar haske,kanta na lullube da mayafi da yayi kalar kayan,fuskarta na fuskantar window din,saidai bashi take kalla ba, mommy dake tsugunne gabanta ta zubawa idanu


"Me zaki gayamin?" Mommy ta furta tana ci gaba da kallonta,kamar yadda itama matar ta zuba ma mummyn idanu,kallon dake ratsa jiki da jijiyar mommy,kallon da zata iya cewa bata taba ganinsa a idanuwanta ba irin yau.


Shuru ne ya biyo baya,sai kallo dai da take binta dashi,irin kallon da zaka iya kiranshi da kallon qurilla.


Sake tashin ringing din wayar mummy dake hannun kaltume ya tsoratar da mutum hudu,mummy da mutane uku da suka shigo dakin tare,wanda suka juyo zuwa window da hanzari,sai kuma kaltume datayi saurin xamewa daga dagen datayi,ta sake daga wayar tana duba me kiran,tare da qoqarin hada alphabet ta karanta sunan me kiran dadan guntun karatun data fara samu.


Kafin takai ga aikata haka dukka sun fito


"Me kike a nan?" Mummy ta dakawa kaltum tsawa tana dubanta cikin fushi,kafin kaltum din ta bata amsa ta sake jefa mata wata tambayar


"Wa ya baki izinin biyoni?,bakiga yanayin wajen ba?,ko su kike su miki illa?"


"Mommy,ki haquri,alasa ne yace wai furofesa yana kira,shine yace na kawo miki kada kiyi fada" da hanzari ta tako,ta fusge wayar daga hannunta ta soma duba kiran,kafin takai ga kiran kuma wani ya sake shigowa,saita daga da hanzari tana kaiwa kunnenta,gami da yin gaba ta soma barin wajen,bayan ta yiwa kaltume nuni da idanu kan tayi gaba.


Professor ne ke shaida mata cewar yana hanyar dawowa daga yanzu zuwa yammaci


"Naje duba marasa lafiya,amma ina hanyar komawa gida yanzu in sha Allah" ta fada cikin salo na kwantar da kai,basu jima ba a wayar sukayi sallama,ta katse wayar,ta juyo tana duban mutanen da take tare dasu.


"Miqomin jakata" ta bawa kaltume umarni tana jifanta da harara,a ladabce ta miqa mata jakar,sannan ta wuce ta koma bakin motar inda su alasan ke jiranta suma.


Fuskarta cike da yanayu na bacin rai tace

"abunda mukayi magana dakai a kanshi ni ba ganshi ba,ban sani ba ko kunnenka ne yayi maka gizo,amma abinda nakeso guda daya shine,aci gaba da sanya kula ta ninka ta baya,gaf zuwa sanda hali zaiyi,saidai abu daya zan sake maimaitawa,banason matsala,na tsaneta,hakanan bansan kalmar sakaci ko kuskure ba,nafi yarda da ganganci" kai kawai yake gyada mata namijin,da alama maganar tata na shigarsa sosai


"Yadda matsala bata gifta ba tsayin shekarun da suka shude,bana jin a yanzu da komai ya riga da yayi nisa matsalar zata faru" macen ta maida amsa.


"Haka nake fata" ta amsa musu cikin yanayin izza da isa,sannan ta sanya hannu cikin jakarta bayan ta zugeta.


Kudi ta irgo kudi masu yawa ta miqa musu


"Duk sanda kuka karanci wani abu da bai muku ba komai qanqantarsa,bana buqatar jinkiri a shaida min"


"In sha Allah.....sai batun kaya"


"Nakune kamar ko yaushe,amma kuna iya cirar wani abu a ciki da zai iya amfanarta ku san mata" da wannaj furucin ta soma takawa zuwa waje,suka rufa mata bata,haka ta keta tarin marasa lafiyan har zuwa bakin motarta.


Sai data shiga sannan suka rufe mata motar,sukayi sallama suka juya, driver yaja motar suka bar gidan.


Waya taci gaba dayi,kafin ta isa tana bada umarnin cewa a tsaida komai dake gudana cikin gidan,a shiga aikin tarbar professor da dukka abinda ya dace,gata nan a kan hanya.


Kaltum na daga zaune,ko qwaqwwaran motsi ta gaza yi,hakanan takejin jikinta a mugun mace,ba abinda ke kai kawo a idanunta sai bayin Allan nan dake fama da lalurar tabin hankali,lokaci lokaci kuma fuskar waccar matar na dawo mata a kwanyarta,shin da wannan tsufar lalurar ta sameta?,ko kuma tun quruciya ne?,me yasa take tsare a nan?,ta fara samun sauqi shi yasa ba'a hadata da sauran ba ko kuwa?,duka ko daya cikin tarin tambayoyin nan bata da amsar kowacce.


"Dakata" muryar mummy ta sauka a kunnen kaltume,baya driver ya tsaida motar ya kasheta,harma shi ya fice daga motar.


A sanyaye ta tsaya daga qoqarin daukar mata jakar da takeyi


"Kamar yadda na gaya miki,karki sake kada kuma ki yarda naji wata magana data danganci inda mukaje daga bakinki,kome kika ji ko kika gan,kiyi kamar baki ji ko bakiga komai ba,wannan ni shine doka da qa'idar xamana cikin gidan nan,kowa da kika ganshi akwai tashi dokar,toke taki kalar dokar kenan,kin fahimta?"


Tun tasowarta tasan cewa biyayya ga uwar miji a tasu karkarar dolene,tunda itace mahaifiya ga mijinta,to binta ya zamar mata dole,kamar yadda zata bi wanda ya kawota gidan,don haka ta gyada mata kai gami da cewa


"Eh in sha Allahu" saidai ta shiga cikin gida cike da saqe saqe,da kuma tuna tunane masu tarin yawa,tunani da hasashe masu toshe basira da qwaqwalwar mutum,duka kanta ya kwance,duka iya yanda taso ta dora lamarin bisa wani mizani da zatayi masa duba na tsanaki abun ya gagareta.

 

A iya sani da ganinta,kai bama ita kadai ba,ganin dukka mai hankali,tattakin da mommy tayi aikine na alkhairi,wanda tasan mutane masu halin qwarai gami da dattako ke yin aiki irinsa,to amma me yasa batasan 'yar cikinta ma tasan taje wajen?,ko kuma wani zuhudu ne da gujewa riya?,wadda ke rusa aikin bawa?,tayi kuma tafiyar ruwa da dukka wani lada daya cancanci bawa ya samu?,ko ita take gudu?.


Ta samu gidan kuwa ya dauki harama kamar yadda mummy ta bada umarni tun kafin isowarta,itama tana ji da daukar kanta a matsayin me aikine kamar yadda taji uwar mijinta na kiranta da wannan sunan da batasan daga ina ta samoshi ba,don haka ta shiga cikinsu,ta karba aikin biba,matar da take jinta tamkar mahaifiyarta,saboda sunan ummanta da take dashi,uwa uba kuma yadda ta damu da al'amuranta,take kuma kulawa da dukkan komai nata.


Tana bala'inson ta shiga cikinsu ana aikin girki,tana matuqar qaruwa da abubuwa masu tarin yawa,wadanda batasan dasu ba a duniyarta sai a yanzu,duk da cewa wasu abubuwan da yawa idan aka dafa din bata iya ci,wani abun ma ko kwata ci ma batayi,sabida tana ganin bazai ciwu din ba,duk da yadda jawahir ke mata dariya gami da ciwon baki.


*_7:00 pm_*


Zaune yake cikin qawataccen falonsa,sanye da da jallabiyya ruwan makuba me santsi.


Kallo daya zaka masa kasan cikakken dan boko ne kuma dan siyasa,wanda ya wadatu da ilimi da kuma gogayya ta sanin duniya.


Daga gefansa najwa ce zaune,ya bata dukkan hankalinsa,da alama wata magana take dashi mai matuqar muhimmanci,saboda kana iya ganin yadda fuskarsa ta wadatu da murmushi.


Dai dai sannan hajiya jidda ke shigowa falon,cikin kwalliyar wani dandaqeqen lace maroon,kai baka ce safiya bace,bayanta jawahir ce ita da kaltum,wadda jawahir din ta tada tun safiya kan zasu shiryawa daddyn abun kari,kasancewar jiya bai shigo gidan da wuri ba,so kusan dukkan abinda aka tanada masa ma bai sami ci ba ya kwanta saboda gajiya.


Sallamarsu kawai ya amsa yana ci gaba da kallon su sanda suke shigowa,har fuskarsa ta fada kan baquwar fuskar kaltume.


Saida jawahir ta aje farantinta ta gaida daddyn ta koma gefansa ta zaunsa sannan kaltume ta qaraso.


Cikin nutsuwa da tsantsar ladabi,saboda duban da take masa na uba a idanunta ta duqa ta ajjiye kayan nata hannun,sannan ta zube har qasa tana gaidashi,saiya amsa yana dorawa da tambayar wacece?.


Najwa daketa hararar kaltum kamar ta hadiyeta tayi saurin bashi amsa


"Me aikin da ya samir ya kawo kace ya maidata kafin ka dawo"


Gyara zamansa yayi sosai sanna ya dubi kaltum


"Tashi kije" a sanyaye a kuma salube ta miqe ta fice daga falon,sai a sannan ya maida dubansa ga mummy,cikin yanayi na bacin rai yace


"Ban gayawa samir ya maida yarinyar mutane ba kafin na dawo?,rainin dake tsakanina dashi har yakai na bashi umarni yaqi bi?" Cikin taushi bisa salo na kissa mummy tace


"Kayi haquri professor,don Allah kada ka bari qaramin abu irin wannan ya bata ranka,abunda ka riga ka sanshi ne ka kuma saba dashi,meye baqo a halin samir a wajenka?" Banbarakwai maganar ta yiwa jawahir aka saita maida dubanta ga daddyn sanda yake cewa


"Duk wani iskancin samir da daurin gindinki yake yinsa,rashin uwarsa a gidan nan ba hauka bane da zan dinga shinfida doka yana takewa,har ya zamana cewa qanwar bayansa ta zama kusan itace makwafinsa,tanayin fiye da abunda ya kamata ace shine yayishi,sannan kice naci gaba da qyaleshi jidda....to ya fara isata".


Idanu mummyn ta lumshe kana ta bude cikin sakannin da basu wuce biyu ba,yayin da najwa ta saki wani boyayyen murmushi sannan tace


"Kayi haquri daddy don Allah ka qyaleshi,amfanin haifar yara da yawa kenan,idan wannan bai share maka hawaye ba wancan sai ya share maka,pls ka manta dashi daddy,haka ya zabawa rayuwarsa"


"Ke banson shirmen banza,waya sako bakinki a nan?,wa shin bama fita zakiyi ba?,tashi ki bama mutane waje" mummy ta fada cikin hade rai,don sam har yanzu najwa bata hau saiti yadda takeso ba,batason ta soko wani zancan daban


"Bamu gama da daddy bafa"


"Naji abinda kikace,anjima idan kin dawo zamu qarasa maganar,kafin lokacin nayi magana dashi"


"To daddy" ta fada tana miqewa,fuskarta na nuna zallar annuri da farincikin data samu.


"Daddy....don Allah kayi haquri ka fuskanci ya saraki,kome yayi saraki yayi idan ka tsaya ka duba sosai....yanayin abinda ya dace ne,kawai don dai baka fuskantarsa ne,amma yaya samir yana da zuciya me kyau......"


"Wa yasa dake kema?,me yasa kuka son shiga maganar manya ne?,tashi ki bamu waje kema ko na sabar miki" mummy ta fada cikin hade rai tana duban jawahir,wadda ta tattabe fuska kamar zata saki kuka. Har ga Allah ta saba da kaltume adan taqin,tana fuskantarta irin fuskantar da 'yar uwarta ma bata taba yi mata irinta ba,tana fahimtarta sosai,tana zama ta saurari hirarrakinta wanda ko mummy bata samu wannan sakewar da ita ba,tana son zamanta tare dasu,saboda ta hangi tarin baiwa masu yawa tattare da ita


"Um...um,qyaleta ta qarasa" professor ya samu kansa da fadin haka,najwa tafi kowa bin tsari da ra'ayinsa cikin gidan,amma kuma sau tari yakanji nutsuwa a zantukan jawahir,da kuma dadin saurare


"Daddy kaltum bata da gata,yaya ya daukota ne don ta samu gata,ba shi ya gayamin ba,na fuskanci hakanne a hirarrakin da mukeyi da ita,da labaran da take bani,sunashan wahalar rayuwa abba,idan ka riqe kaltum lada zaka samu,ya samir bai bijirewa umarni da ra'ayinka ba,yasan tsarinka,bisa hakanne ma ya sanyani nake koya mata karatu,yanxu haka cikin satin nan zata zana placement zata tafi ss one" shuru yayi yana farfasa zantukan jawahir,shurun daya jefa hajiya jidda wani tunani na daban,ya akayi jawahir tasan dukka wannan ita tana zaune?,yayin da jawahir din kuma ya bata qwarin gwiwar bawa daddyn labarin yadda kaltumen ta iya zane abun mamaki,hakan yasa ma ta bata shawarar ta zabi fannin zane tun daga nan har zuwa gaba idan Allah yayi zata din.


Nan ta zage tana bawa daddy labarin zanen datayi wanda ya bata mamaki sosai


"Idan ka biyewa shirmen jawahir ba zaka ci komai ba prof,tashi ki tafi hirar ya isa haka,Allah ya bada lada" mummy ta fadi tana miqewa zuwa gaban kwanukan da suka ajjiye tun dazu.


Kallon da mummy ke aike mata yasa ta miqe tana yiwa daddyn sai anjima zata kawo masa zanen.


Murmushi ya saki

"Duk da jawahir auta ce,amma tana da hangen nesa da nutsuwar da batayi kama data autoci ba" baki mummy ta tabe sanda take maida murfin tea flask din data zubawa daddyn zazzafan shayi.


Cikin nutsuwa yake takowa zuwa cikin gidan,sanye da wasu blazers ruwan sararin samaniya,sunyi matuqar haskashi da qara masa kwarjini,jikinsa na fidda qamshin turarensa da koda yaushe,zatinsa na tsaho da murjajjen jiki ya fito sosai,hannunsa daya dauke da wasu takardu dake qunshe cikin files dinsu.


Cikin lallausar muryarsa yayi sallama cikin falon,daga can inda take tsaye gaban katafaren teburin cin abincinsu da taje dinan kofunan da biban tace ta kawo ta jiyo kamar muryarsa,duk da bata tantanceta sosai ba,saita waiwaya a hankali tana amsawa.


Amsawarta yaja hankalinsa yakai duba inda take,saita tako a hankali riqe da kofunan,ta iso gabansa ta durqusa qasa tana gaidashi,cikin yanayin kulawa yace


"Lpy alhmdlh,ya karatun?" Dan murmusawa tayi kadan,karon farko da yaga fara'arta tunda yake ganinta


"Alhamdulillahi" ta amsa masa


"Ina jawahir" sai data kalla sashen dakinsu sannan tace


"Tana ciki"


"Kiramin ita" ya fada yana dan zama hannun kujera,tace to tana miqewa da hanzari.


Da sallama ta tura qofar dakin,tsaye ta samu jawahir gaban tarin kayan shafarta,hannunta riqe da wata zungureriyar roba,ta amsa tana ajjiye robar.


Tun kafin tace wani abu jawahir din ta soma magana


"Fada kawai kikeso muyi dake kaltum,kayan nan har yanzu banga kina amfani dasu bafa,yanzu man wanke kan nan banga alamar kin taba amfani dashi ba" dan murmushi tayi,batasan me yasa ta damu da lamuranta da yawa haka ba


"Kiyi haquri jawa,ki fara zuwa wajen....."sai kuma tayi shuru,don batasan da wanne suna zata kirashi ba,daga bisani ta yanke tayi kiransa da yaya kawai


"Ok,ina zuwa" ta fada tana juyawa ta nufi qofa da sauri.


Sai data fice itama tabi bayanta don kaiwa biba kofunan.


Kamar ko yaushe ta gaida samir din cikin girmamawa,ya amsa mata shima cikin kulawa


"Idan baki komai ki shiga ki gyaramin sashe na"


"To yaya" ta amsa tana masar muqullin bangaren nasa,shi kuma ya wuce zuwa sassan daddy.


Kitchen ta duba bata samu biba ba,saita wuce zuwa dakinta don ta gaya mata takai.


A nutse ta daga labulen dakin,idanuwanta suka fara sauka kan biba dake tsaye riqe da wani dan qaramin hoto a hannunta,wanda bata iya hango wanda ke ciki saboda da kadan ya wuce girman passport.


Sallamar kaltum yasa ta soma qoqarin boye hoton,a hankali ta qarasan gaban biban tana cewa


"Nakai kofunan kitchen,amma saina taras bakya nan,nama wanke na mayar dasu inda suke" kai ta gyada mata ba tare da tace komai ba,sai kaltum ta lura da hawayen dake idanun biban da take qoqarin gogesu,cikin mutuwar jiki tace


"Baki da lafiya ne?"kai ta gyada mata


"Kaina ne yake dan ciwo kadan,shi yasa na taho na huta" duka sai kaltum taji babu dadi


"Ayyah,sannu,Allah ya sawwaqe,gwara ki huta kam,Allah yasa kaffara"


"Amin"ta amsa tana sake goge idanunta da kyau,tayi kamar zata zauna tare da ita,amma biban tace babu komai taje,itama yanzu zata fito,tunda ciwon ba sosai bane,bai matsa mata ba.


*_SHIN KINSAN CEWA AKWAI RAMUWAR SALLA A KANKI ME JININ AL'ADA?_*


________________________________


*_WAIWAYE......ADON TAFIYA inji masu salon iya magana_*


*ZAFAFANKU BIYAR 🔥🔥🔥🔥sune suka sake dawo muku da wasu nau'in QAWATATTU kuma TSARARRUN LABARAN,masu dauke da SABBIN JIGO na MABANBANTAN LABARAI masu tsuma ZUCIYA*


*_SANIN HALI.....yafi sanin kama,indai kasan TAFIYAR ZAFAFA babu dana sani ko nadama cikin zuba kudi wajen siyan litattafansu,koda jin sunan ma kasan cewa tafiyar ta dabance_*


*GWADA IDAN BAKI TABA BA!!!,HAUSAWA SUKACE SAI AN GWADA AKAN SAN NA ƘWARAI,burinmu kowa ya shigo cikin tafiyar a dama dashi*


*JERIN SABABBIN LITATTAFAN NASU NA WANNAN KARON SUNE*


*_DEEN MARSHALL👉🏾 Mamuhghee_*


*_HALIN GIRMA👉🏾hafsat rano_*


*_TAKUN SAƘA👉🏾billyn abdul_*


*_SO DA ZUCIYA👉🏾miss xoxo_*


*_ƊABI'AR ZUCIYA👉🏾huguma_*


*DUKKAN WADAN NAN LITATTAFAN ƊAI ƊAI HAR BIYAR...ZAKU SAMESU A KAN KUDI NAIRA 1K KACAL*


2👉🏾400

3👉🏾500

4👉🏾700

5👉🏾1000


*Zaku saka kudinku ta wannan asusun bankin*

6019473875

MUSAA ABDULLAHI SAFIYA

keystone bank


Saiku tura shaidar biyanku zuwa ga wannan number


08184017082


*IDAN KATIN WAYA NE KO VTU,SAIKU TURA ZUWA GA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYANKU*


09134848107


*_HAR KULLUM MUNA MARABA DA ALFAHARI DA MASOYANMU_*🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽🤝🏽

#team zafafa biyar

Post a Comment

0 Comments