TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

DABI'AR ZUCIYA ❤ page: 49 - 50

 49



Wani mummunar faduwa gabanta yayi,saita dakata da bin saurayin,wanda sam shi baima kula da abinda akeyi ba,saboda ci gaba yayi da tafiya yana zuba kayan,har yakai gab da samir daya soma takowa shi kuma inda take yana ci gaba da kallonta.



Gab da ita ya tsaya,taku kadan zai qara su hade da juna,numfashinta kamar zai dauke tayi qas da idanunta,ta kuma qame waje daya tana runtse idanuwanta sanda taga ya daga hannunsa zuwa gareta,daga bisani ta budesu a hankali lokacin dataji motsin daukar cart din dake ajjiye gefanta.


Kusan lokaci guda kowannensu ya sauke boyayar ajiyar zuciya sanda ya kama tsintsiyar hannunta ya riqe,ya fara takawa a hankali riqe da ita suka fara daga farkon layin.


Mamaki ne ya cikata sanda taga irin kayan da yake zaba,kusan duk abinda ya taba ya daukoshi yayi mata choice dinta ne,kaya yake zubawa kamar baisan mutuncin kudinsa ba,tsoro ya kamata,amma daga bisani saita dan sake data tuna maganar da suka tabayi da jawahir sanda ya taba siya mata wani set na man shafawa


"Allah dai ya biya ya saraki,Allah yaci sunansa,ba don yayana bane da tuni nayi wufff da abina,harso nake mu fita shopping dashi,bayajin komai ko meye zaki zaba,ba kamar mummy ba da zata yita mitan zamu qarar mata da lalitarta,yana da kyauta kaman ba gobe,babu ruwanshi"


Nauyinsa ya cikata sanda ya sakar mata hannu,ya bata damar ci gaba da zabar ra'ayinta,shi kuma yana tura cart din kamar wani me aikinta,ya ilahi,ta kasa gano ainihin halinsa,wani lokaci kamar zazzafan mutum,wani lokaci kuma sai taga sauqinsa da sanyinsa yayi yawa,har yayi kamarma ba kowa bane shi.


Sun gama da inda suke suka shiga bangaren undies,kamar ta nutse a waje taji sanda suke ratsawa ta sakanin panties da braziers,sai ta dinga tafiya da sauri da sauri don sunyi su fice a gun.


Danqo hannunta taji anyi daga baya,ta tsaya cak kana ta waiwayo,idanunsa akanta,ya mata nuni da wani abu,saita maida ganinta zuwa abinda yayi mata nunin dashi.


Brazier ce a hannunsa,daburcewa tayi tana dauke idonta,bakinta na dan rawa tace


"Ni...bana sawa" baisan sanda qaramin murmushi ya qwace masa ba,ya yadda da abunda jawahir ta fada,da gaske pretending takeyi,shi yasa zakayi tunanin bata da komai din.


"Wanne size kike sawa?" Dagowa tayi a dan diririce,saiya lumshe idonsa cikin second daya ya bude,saboda wani kyau da yaga sunyi masa a karon farko,sunyi haske sosai,dama can kuma suna da hasken yasan da wannan,amma a wannan karon sun sake kyau saboda girma da suka dan qara yi.


Kai ta sake girgiza masa


"Bana sa......"

Bata ankara ba taji ya fusgota a tausashe,sai gata dan dashi,wanda motsi kadan zatayi ta hade da jikinsa


"Idan na auna da hannuna zan gane ai" ya fada yana daga hannayensa,hijabinta taga ya fara tattarawa tare da qoqarin zura hannayensa ciki,batasan sanda ta cafki hannun nasa ba ta riqe,a rude kuma ta gaya masa number din tana jin yadda mararta tayi wani mugun murdawa,da alamu kuma tsoratar da tayi ya kawo hakan.


Murmushi ya saki ganin yadda gaba daya ta wani rude,sai ya janye hannayen nasa ,amma duk da haka baija baya ba,saiya qara ma matsowa,hakan yasa ya hade gap din dake tsakaninsu,jikinsa na gogar nata,baisan sanda ajiyar zuciya ta kubce masa ba


"Na zaci kinmin qaryar size ne......but ki daina takurewa haka,suna iya lalacewa ko su zube tunda wuri.... brazier is necessary for you tunda kinkai shekarun"



Ji tayi inama qasa zata tsage ta shige ciki ta huta,jikinta ya dauka rawa ta rigashi ja da baya tana dafe mararta data sake murdawa kamar ta tsage,har sai data dan sunkuya


"Are you okay?" Ya tambayeta muryarsa na shaking kadan,dagowa tayi yana gyada masa kai,saiya juya yana duba size din data gaya masan,ya saka iya yanda ya kamata,tana kallonsa ya hada harda pad.


Da qyar take takawa zuwa motar,ta bude seat dinta ta zauna,tana jin sanda ya qaraso shima ya bude ya shiga,baya an saka musu kayan a booth ya tada motar suka fara tafiya,saita cure waje daya,tare da dora fuskarta saman cinyoyinta,tana jin yadda pain ke tasowa daga mararta har zuwa qafafuwanta,wanda dauriyarta ta fara qarewa,harta fara motsi kadan kadan wai ko zataji sauqin radadin.


"Are you okay?"ya sake tambaya karo na biyu,bayan ya fuskanci yadda taketa motsawa,saita gyada masa kai,saidai suna gab da isa gida juriyarta ta qare ta soma fidda qaramin sautin kuka.


"Marata" ta amsa masa


"Ya salam" ya fada yana tsaida motar


"Kin gama shan magungunanki?" Kai ta gyada masa


"Ok...." Ya amsa yana dauko wayarsa,number din dr labaran ya laluba ya kirashi,cikin sa'a kuma ya sameshi,ya masa bayani


"Babu komai,dama hakan na iya faruwa saboda motsawar mahaifa,zata fitar da jinin dake cikinta ne,zan tura maka pain reliever tasha,zata samu sassauci,sai kuma hot or cold water therapy,amma fa,zata iya samun kamar bleeding haka,so she needs somebody else close to her"


"Okay dr, thank you for your help"


"Ba komai" suka kashe wayar,ya maida dubansa ga kaltum wadda batasan ma bayanin da akeyi ba,saiya tada motar yasa kafin su isa bakin pharmacy din ya turo da maganin.


A gaggauce ya karbo magungunan ya dawo ya sake tada motar suka wuce gida,kokaci lokaci yana juyawa yayi mata sannu.


Da kansa ya zagaya ya bude mata murfin motar,yadan matsa gefe don ya bata damar fitowa.


Kasa motsawa tayi,sabida a jikinta take jin danshi,wanda batasan na meye ba,data duba kadan sai taga kamar jini,don haka ta sauke idanunta qasa,ta kuma kasa motsawa.


"Taso" taji ya fada,sai taga hannunshi yake bata,rau rau tayi kamar zata saki kuka,sai kuma ta hadiye ta miqa masa hannun nata a hankali ya dagota,qin motsawa tayi,don tana ji a jikinta ta bata masa seat,tana kuma kunyar ya gani,amma ba yadda zatayi haka ta motsa.


Karon farko ya hangi inda ta bacin,saiya sake mata hannu,ya zagaya ya bude booth din ya zaro ledar siyayyar ya sake dawowa inda take tsaye.


Tafin hannunta ya sanya cikin nashi ya hade yatsunsu waje guda,abinda yasa wani shock a jikin kowannensu kamar haduwar wutan nefa da ruwa,sai yaci gaba da takawa zuwa cikin gidan sannu a hankali tana biye dashi.


*BAYAN AWANNI*



A hankali ta bude idanunta daga nannauyan baccin da yayi awon gaba da ita,wanda batasan yaushe ya dauketa ba.


Ci gaba tayi da bude idanuwan,har sukayi tarwai,saita dan dakata tana duban dakin,take abinda ya faru awanni uku da suka shude suka dawo mata,ashe komai a gaske ne ya faru ba mafarki ba yadda ta tsammata


A hankali ta juyar da fuskarta muhallin daya zauna a dazun kafin bacci yayi awon gaba da ita,wayam yake wajen babu kowa,da alama ya fice ne daga dakin,saita dora hannunta saman shafaffen cikinta zuwa mararta,tana iya jin yadda hannunsa ke yawo har yanzu a wajen,tsigar jikinta ta zuba,saita runtse ido tana girgiza kai,abinda bata taba kawowar faruwarsa ba,wai wani namijin da taba jikinta ba tare data iya hasala komai ba.


A hankali idanunta suka doru kan agogon dake dakin,qarfe shida na safe saura minti daya,da sauri ta miqe,saboda yau din suna da jarabawa,kuma qarfe takwas invigilator din zaizo,sai kuma ta tsaya cak tana wara idanu,saboda canjin da taji a jikinta,sai a sannan ta tuna cewa itama yanzu ta fara period kenan kamar yadda sauran mata keyi,hakan yasa ta fara takawa a hankali ta nufi bandaki.


Tana gab da qarasawa taji an tura qofar dakin,batakai ga waiwayawa ba,hakanan baikai ga magana ba ta gane cewa shine ta hanyar sassanyan qamshinsa,baice komai ba ya koma da baya,a hankali ya mayar mata da qofar ya rufe mata.


Ajiyar zuciya ta saki da taji ya koma din,don nauyinsa ma bazai bari ta iya hada ido dashi ba


"Yanzu bakan kalar pant dina da brazier din da nake boye masa duka ya gani,innalillahi" ta fada tana dafe qirji,bayan tayi tsaye a gaban mudubi,saita kauda tunanin,ta fara cire kayan jikinta.


Wanka tayo gaba daya,sosai taji dadin jikinta,tana shiryawa tana tuna yadda ya dinga treating nata jiya with care,saidai kuma ya haifar mata da feelings da wasu abubuwa masu wuyar mantawa cikin zuciya,saboda wannan shine karon farko da suka taba zama kusa da juna very close irin haka,wannamn shine karo na farko data taba kallon fuskarsa sosai,fuskar da take cike da kwantaccen saje mai duhu sosai,wanda ya qawata ta ya kuma qawara labbansa masu tudu da suka yiwa fuskarsa kyau.



Tsaf ta gama shirinta kamar ba ita tayii fama da ciwo jiya ba,tayi cas cikin uniform din da akullum suke mata kyau kamar kayan gida,tsai tayi gaban madubi tana kallon fuskarta,sai ta sanya hannu tana shafar gefan fuskarta tana jiya yadda yayi.mata jiya,idanunta ta lumshe murmushi yana qwace mata,sai kuma ta bude idanun da hanzari sanda taji alarm na agogon ya buga qarfe bakwai.


A kitchen ta samu su baba,suka gaisa a gurguje,ta karbi wani daga cikin breakfast din daya zama ready ta soma karyawa dashi,baban na tambayarta ya jiki tace mata aita samu sauqi,don babu wanda yasan ma ciwon da tayin a jiyam cikin gidan daga ita saishi.


Tea din data kurba ya tsaya mata a wuya sanda taji tattausan muryarsa na magana cikin kitchen din,cikin girmamawa baba ke bashi haqurin rashin kammaluwar abincin da wuri


"No,no need to worry.....zanyi break a waje" ya furta maganar yana sauke idanuwansa akanta,duk da baya ganin fuskarta yasan cewa itace.


Ajjiye cup din tayi,ta juyo a hankali,kallo daya tayi masa tayi qas da idanunta,yau shigar ta fari ce,suit ce wadda ta amsa sunanta three in one,saidai komai nata fari ne kamar yadda shima duk abinda ya saka a jikinsa yake fari,wataqa hakan yana da nasaba da kasancewar ranar juma'a ce,ba qaramin zama shigar tayi a jikinsa ba,itakam ba zata iya cewa ga wasu kaya da ya saka basuyi masa kyau ba,ba tare data bari sun hada ido ba tace


"Ina kwana"cikin rusunawa


"Lafiya lau" ya amsa mata yana juyawa tare da fadin


"Muje na saukeki,ya kirani ya gayamin bazai samu zuwa yau ba" da sauri ta bi bayansa bayan ya fice tana yiwa baba sallama.


Cikin motar saukar numfashinsu gami da qamshin turarukan jikinsu,jinta take gaba daya a takure,wani kwarjini yake mata matuqa


"Ya jikin naki?" Sai data dan qwato numfashinta sannan ta amsa


"Na samu sauqi" shuru na second biyu ya sake cewa


"Ma sha Allah,but idan kikaji ko kikaga wani abun daban kiyi magana,yace a gaya masa zai duba" 


"In sha Allah,na gode" ta furta qasa qasa,kansa kawai ya gyada yana ci gaba da tuqin,amma kuma wani abu yana dawo masa a kansa shima,wanda daga jiya zuwa yau mutuwar jikin da yakeji bata sakeshi ba,har i yanzu babu wani qwaqwwaran kuxari tattare da shi,har ya sauketa makarantar,ta jawo jakarta ta rataya,sai kuma tace dashi


"Don Allah inason inje gidan mummy....." Dubanta yayi 


"Kiyi me?,suma daxu sun tafi azare,su biba kawai suka rage" 


"Abubuwana na manta nakeso na dauko" kamar ya tambayeta wanne abu sai kuma ya fasa,ya gyada kai yana cewa


"Is okay" hannu ya zura aljihun gaban motar ya ciro kudi ya miqa mata,kudin ta kalla ta kalleshi,ta girgiza kai alamun a'ah,yadan matse fuska kadan yana dubanta


"Jawahir ta gaya min bakya karbar wani abu cikin kudinki na wajenta....me yasa?" Kai ta kada,tana jin zuciyata na karyewa,duk sanda tatuna da cewa ummanta nacan cikin tsananin buqatarsu,sai taji tamkar taci amanarta idan ta karba tayi amfani dasu taji dadi alhali umman nata nacan a wani hali da batasan wanne iri bane


"Ohhhh....na manta fa,bakyason sababbin kudi kudi ko?,to amma fa.....wannan mijinki ne ya baki su ko?" Furucin nasa ya sanyata daga kai da hanzari zuwa gareshi,cikin sa'a suka hada idanu,kunya ta sanyata sadda kai tare da kubucewar murmushin da bata shirya masa ba,sai yaji dadi a ransa,yayi hakanne don yaga murmushinta kuma haqansa ya cimma ruwa,a taqaice yace


"Take it" hannu biyu ta saka ta karba


"Na gode,Allah ya biya" tayi maganar sanda ya sake kunna motar yana gyada mata kai,ta juya ta nufi ajujuwansu.


"Mijinki" kalmar data dinga yi mata amsa kuwwa kenan cikin kunnuwanta,da qyar ta samu ta kori sautin muryar sanda aka gama raba musu question paper ta fara amsa tata.


Tana daga dalibai na farko da suka gama amsa tambayoyinsu suka kuma yi submitting,saita zauna daga bishiyar dake gefan ajinsu tana jiran fitowar saliha.



"Anya ba umara ko hajji aka biya miki ba?" Ta tsinci muryar saliha daga saman kanta,saita daga kai


"Me kika gani?" Kaltum ta tambayeta tana matsa mata wajen xama


"Tunda kika shigo aji kike murmushi,yanzun kuma tunda na fito nake daga miki hannu amma baki ganni ba" husna dake tsaye tana maida question paper Jakarta tace


"Indai ko hakane wannan sign ne na falling in love wallahi,irin farin shigar nan,kin manta alamunsu ne?,yawan tunanin da yawan murmushi kai kadai?" Dubanta sosa kaltum tayi,maganar husna kusan tafi jan hankalinta,me husna takeso tace?,indai ko ta fahimta wani abu,lallai husna dince tafi cancanta tayi mata tambayar da take damun ranta.





50

DZ


Wani littafin ta sake karba wajen salaha,tanaji suna mata tsiya amma batabi ta kansu ba,ita kadai tasan yadda take qaruwa da karatun da takeyi din,wanda ya haska mata abubuwa da dama


"Husna muje tare mu taru napep,nima yau mai daukan nawa baya kusa" kaltum tace da husna,saida husnan ta tsaya ta siya agwaluma daga bakin makarantar sannan suka soma takawa zuwa bakin titin


"Nikam husna.....wata tambaya nakeson yi miki"


"Duk yadda kike ja kaltum?,kece fa kike daukan 1st position a ajinmu duk term" kafadarta kaltum ta daka tana murmushi me kama da dariya


"Ke dalla,ba akan karatu bane,wannan karatun kun fini ilimi ta fanninsa" murmushi tayi mata itama tana gyara saqalen jakarta


"To ina jinki,ai wai don karki qureni ne" sukayi dariya gaba daya,sannan shuru ya biyo baya,kaltum din cikin ranta tana juya yadda zata gabatar mata da tambayar,tsahon wasu mintuna sannan tace


"Asa misali kece kika tashi cikin rayuwar rashin wadata,baki da ilimi kyau ko arziqi,kwatsam sai Allah ya kawo wani kyakkyawan matashi,wanda ya fiki kyau kudi ilimi dama wayewa nesa ba kusa ba,irin nesan nan can can can,kawai tausayinki yasa ya aureki,yazo ya ajjiyeki a gida,ba abinda ke hadaku,kuna zaune kamar yaya da qanwa......"


"Wai,wanann shi ake kira da tsintar dami a kala" husna ta katse kaltum na tare data bari kaltum din takai qarshen maganar ba,tana ta murmushi tare da sake bawa kaltum hankalinta.


,ganin yadda husnan ta bawa zancan muhimmanci hakan ya bata nutsuwar ci gaba da magana


"A hankali kuna zaune kika fahimci yadda mata ke rububin sonshi,da kika lura da kyau,sai kika gane bayan dukka wadancan siffofi.....yana da kyawawan dabi'u kuma"


Hannayenta sama husna ta daga


"Wallahi ta fadi gasassa.....wannan mata idan nice sai inda qarfina ya qare wajen janyo hankalinsa ta dukkan wata hanya data dace,duk namijin da ya hada wadan nan siffofin tabbas babu shakka ya isa,ya kuma cancanci a soshi,rasashi kuma babbar hasara ce" maganganun da suka sanya kaltum nazari kenan,tayi shuru tana sauraren yadda husna keta wassafa kanta cikin lamarin har suka qaraso titi.



Tsaki yaja a hankali yana rufe file din gaban nasa,tare da dora bironsa akai,ya maida bayansa ya jingina da kujerar yana relaxing a jikinta,kana ga furzar da iska me dumi daga bakinsa,a hankali kuma ya soma juya kujerar daga hagu zuwa dama,daga dama zuwa hagu.


Tun daga lokacin har kawo yanzu ya kasa jin qwarin jikinsa kwata kwata,yanajin kowacce jijiya ta jikinsa ta zama weak,ya dunqule hannunsa waje daya kamar wanda ya boye wani abun yana kallon hannun,jijiyoyin dake tsintsiyar hannun sun tashi rada rada,har yanzu yana iya tuno laushi da dumin fatar cikinta,tun a lokacin jikinsa ke shaida masa da matsala,amma burinsa na ta samu relief na pain din yasa yaci gaba da abinda yakeyi.


Idanunsa ya lumshe,saiya dinga gano fuskarta wadda bayan ta gama jigata bacci ya dauketa har sai da kanta ya karkace,shi ya gyara mata kwanciya amma har ya gama yabar dakin batasan anyi ba.


A hankali aka tura qofar, secretary dinsa ya bayyana yana shaida masa neman izinin shigowa da fawwaza keyi,shuru ya danyi,sam baison hayaniya yau din,a niyyarsa yace ya shaida mata yana da ayyukan da yake dubawa,kuma suna da muhimmanci da kuma buqatar nutsuwarsa,saidai kafin yakai ga furtawa har ya hangi fawwazan tsaye daga bayan secretary din,da alama a shirye take ta shigo koda bai bata dama ba,don haka yace


"Ok, let her" ya fada yana tura kujerarsa baya,sannan ya miqe tsaye yana zuba hannayensa a aljihun wandonsa kafin daga bisani ya fara takawa cikin nutsuwa zuwa sashen da fridge dinsa yake.


Tunda ta shigo ta kasa zama,ya bata baya amma kallo take qare masa,tako ina samir din yakai namiji,tana jin sonsa yakai mata ko ina cikin rai da rayuwarta,amma ta fuskanci har yau ya kasa gane hakan.


A duk sanda zata dauko maganar saiya sako wani abun da zai kauda gaskiya da kuma qarfin maganar a ranta,ta rasa me zata masa ya tabbatar masa da dukkan abinda take fada da nunawa a kansa gaskiya ne?,tun tana ja masa aji da kuma shan qamshi,har ta daina ta sauko,da a tunaninta baiwar kyan da Allah yayi mata da iya gayunta kawai sun isa suja mata ra'ayin saraki,saidai kuma a hankali ta gane cewa tayi bahagon tunani ta kuma canki kuskure.


"Have a set" ya furta bayan ya juyo dauke da kwalin lemo da kuma cup yana nuna mata empty kujerar dake gaban table dinsa,saita dauke kanta a hankali ta qarasa ta zauna.


Gaban kujerarsa ya tsaya ba tare daya zauna ba yace


"Allah yasa lafiya" yana dan kurbar lemon kamar wanda aka yiwa dole,fuskarta fal da damuwa ta girgiza kai


"Ba lafiya ba samir,kuma babu lafiyar sam a tattare dani?" Dukka girarsa ya dage bayan ya dakata da shan lemon,abinda yayi masa kyau sosai


"Me ya faru kuma?" Kai take kadawa tana hadiye wani abu


"Hakafa....haka kullum kake pretending kan cewa bakasan komai ba,baka gane komai ba,bayan na maka bayani basau daya ba basau biyu ba,to yau zan gaya maka baro baro, Muhammad samir sonka nake,ni fawwaza ina sonka" a hankali ya sauke cup din hannunsa saman table din,tabbas yana daga cikin tsarinsa mace tace tana sonshi,irin hakan idan ta faru yasan cewa zai samu dukkan wata kulawa fiye da yadda yake da buqata,gidansa kuma zai sarrafu fiye da yadda yake tunani ko hange,saidai kuma bata wannan sigar da fawwaza tazo da ita ba,abu na farko totally fawwaza batayi masa ba tako ina,sannan yasan waye mahaifinta sarai,bashi da sha'awar hada zuri'a dashi.


"Da farko dai nan wajen aiki ne,ba muhalli bane na irin wadan nan maganganun,amma inaso na fara da gode miki kan qaunata da kikeyi,naji dadi na kuma yaba miki,amma ina me baki haquri.....am sorry to say.....na fitar da matar aure,yanzu haka kwanaki kadan suka rage a saka ranar aurenmu,ina mai baki haquri akan hakan,tare da miki addu'ar samun miji na gari" sam batasan sadda ta barke masa da kuka ba


"Ya salam.....mene haka?" Samir din ya fada,iyakar qoqarinsa don tayi shuru amma taqi,kuka take sosai tare da fadin dukka abinda yake zuciyarta,har sai daya zauna saman kujerarsa,ya tsiyaya sassanyar lemo ya tura gabanta 


"Sha wannan sai muyi magana" tana goge qwallarta ta dauka tasha kadan ta ajjiye



Cikin siga ta lallashi ya soma magana

"Banga abinda zaisa hankalinki ya tashi ba,bayan a cikin maza nidin ba kowa bane,akwai dubban maza da suka fini komai da komai,don na gaya miki hakan ba yana nufin yankewar rayuwarki ba,idan kikayi haquri kikabi komai a hankali sai Allah ya kawo miki wansa ya fini komai da komai....."


"Ba ruwana da kowa,ni kai nakeso" ta fada zuciyarta na sake yin zafi .



Sake birkicewa tayi gaba daya,daga qarshe ma tana kukan ta zari muqullin motarta ta ficw daga office din,kiranta yake amma taqi saurararsa gaba daya.


Ya tabbatar tuqi zata je tayi a hakan,kuma idan tayin a yadda take din komai na iya faruwa,don haka ya koma da sauri,ya dauki wayarsa ya kira umar,ya bashi umarnin ya tabbatar yayi qoqarin settling komai,sannan ya kife wayar ya koma ya zauna yana fidda iska daga bakinsa,hannunsa saman kansa yana shafashi kadan kadan.



Ya jima zaune a hakan,kafin yaja qaramin tsaki ya miqe a hankali,yana jin jina qaramar qwaqwalwa da kuma wauta irin ta wasu matan.


Dukka abinda yake da buqatar wucewa dasu gida ya tattare ya fice daga office din.


Duk da cewa hankalinsa a rabe yake,amma hakan bai hanashi ganin alamun wahalar abu hawa ba,saboda yawaitar jama'a tsaye a bakin tituna,baisan ya akayi ba,saiya tsinci kansa da sauya akalar motarsa zuwa hanyar makarantarsu kaltum,bayan ya duba lokaci.



Tsaiwarsu basu rufa minti biyu ba ta hangi bullowar motar,da fari harta dauke kai saboda bata taba kawowa kanta shine din ba,amma sai taji zuciyarta nason tabbatarwa,hakan yasa tadan bi motar da kallo.



Sai daya tsaya gabansu ya rage tsayin glass din sannan ta tabbatarwa kanta shine.


Da idanunsa ya mata nunin ta shigo,kamo hannun husna tayi,tana sarrafa wanne suna zata bashi wajen husnan,har tayi ta maza duk da batason tafiya tabar husnan kada taga rashin kyautawarta,hakanan batason azarbabin cewa tazo suje tare


"Husna,yaya na ne yazo"


"Ayyah to sai ranar final kenan?" Kai ta gyada bayan ta mata sallama,ta bude gida gaba ta shiga.


Yana zaune sosai kam seat dinsa,ya cire 'yar saman suit dinsa ta farkon da takalmin qafarsa,saidai har yanzu mayen qamshin nan nasa na manne da motar kamar wanda ya fesa turaren yanzu bawai tunda safe ba


Taja murfin motar a hankali ta rufe,sannan ta fara gyara rigarta tana dan janta kadan don ta rufe mata cinyoyinta sosai yadda zataji dadin zaman.


Dubanta yayi suka hada ido,kowa ya dauke kanshi,ya tayar da motar suka soma tafiya.



Ya a faka motar ta fita zuwa cikin gidan,saidai kamar yadda yace dinne babu kowa cikin gidan sai ma'aikata,don haka tana ajjiye jakarta ta soma neman biban cikin gidan,bata ganta ba,saboda haka ta nufi dakinta.


Kadan ta tura qofar,sai taji kamar ana kuka,don haka ta leqa da kanta ta yadda zata iya hango cikin dakin.


Biba ce,zaune saman carfet,hannunta riqe da hoto,data duba sosai sai taga hoton nan ne dai data saba ganinta riqe dashi,hoton da har yau bata taba katarin ganin fuskar waye ba.


A hankali taga ta ajjiye hoton,ta miqe ta nufi bandaki,ta tura qofar bandakin ta shige.


Qarasa tura qofar dakin tayi,ta shiga a hankali har ta isa inda biban ta tashi,idanunta suka sauka kan hoton,ta miqa hannu a hankali ta dauka.


Kyakkyawar macace wadda a qalla zatayi shekara talatin da takwas zuwa arba'in,wankan tarwada mai dogon hanci da manyan idanuwa,kanta babu dankwali sai qananun kitso da aka yiwa sassalkan gashinta,tana sanye da atamfa dinkin riga da zani,rigar mai kwala ce,irin dinkin mutanen da,fuskarta a wadace da murmushi,har wushiryarta tana fitowa,kana kallonta kasan macace 'yar kwalliya da son ado.


Sosai ta zubawa hoton idanu,fuskar na mata yawo a qwaqwalwa,tana jin kamar tasan fuskar,kamar ta taba haduwa da me irin kamannin,amma ta gaza gano a ina?.


Motsin fitowar biba ya sanyata saurin tura hoton aljihun rigarta cikin firgici da tsoron kada ta ganta,da murmushi tambayar kaltum din yaushe tazo,tace yanzun nan,tana takawa zuwa inda ta ajjiye hoton gaban kaltum na faduwa,cikin ikon Allah daya daga cikin ma'aikatan ta turo qofar,tace tazo maza mummy ta kira wayar gida tana nemanta,saita dubi kaltum


"Muje ki tayani rubutawa,wasu abubuwa takeson a siya mata a baku ku tafi mata dashi"


Da to ta amsawa biba,ta kuma bi bayanta gabanta nata faduwa.



Sam ta mance da cewa ta taho da hoton,sai bayan ta koma gida,tana hada uniform din xata sanya cikin laundry basket ta zaro shi,komawa tayi ta zauna tana sake nazarin hoton


"Tabbas tasan fuskar,ta taba ganinta,amma ba zata iya tunawa a ina ba,to amma ya meye alaqarta da matar da har zatasan fuskarta?,bayan idan bata manta ba,biban ta gaya mata cewa 'yar uwarta ce data rasu,wadan nan abubuwa biyu yasa ta saddaqar bata santa din ba,saita cusa hoton qasan pillow dinta,ta gama dukka shirin kwanciyarta,saita janyo ledar da saraki ya bata a dazu bayan ya sake dakkota daga gidan mummy sun dawo gida.


Murmushi ta saki bayan ta gama kallon kazar,saita tuna sanda hannayensu suka hadu waje daya sanda yake miqa mata kazar,ita ta fara zare hannunta saboda wani yarrr dataji,saiya aje mata ledar daga gefanta.


Gasashshiyar kaza ce da chips a ciki,kadan taci ta rufe,ta kwanta,tun tunani kala kala na bijiro mata har bacci ya saceta.



_DUNIYAR MAFARKI_


     Sannu a hankali take takawa cikin sanda tsakiyar hanyar dake dauke da dakuna hagu da dama,hanyace mai duhu sosai,sai wani dan siririn haske data hangowa daga can gabanta kadan.


A hankali take dosar hasken,harta cimmasa,qofa ce yar siririya sosai,sai taga kamar jikinta bazai iya shiga ta qofar ba,don haka ta koma ta window,tayi dage ta leqa cikin dakin,fetal hake dauke da gado guda daya,sai wata mace dake zaune kanta a qasa,kamar matar tasan ta tsaiwarta a wajen ta daga kanta a hankali tana yaye rufin mayafin data lullube fuskarta dashi,sai suka hada ido.



Tarwai taga fuskar matar,kamar matar rannan ce,ta sake duban dakin,kamar dakin rannan ne shima,saita maida kallonta ga matar,sai taga ta zuba mata idanuwa qurrrr,wanda daga bisani kuma hawaye ya fara fita daga idanuwan matar shar shar babu qaqqautawa,a hankali kuma sai hawayen suka fara canza kala kamar kalar jini,ta miqe a hankali matar ta tako zuwa inda take tsaye hawayen naci gaba da fita daga idanunta.



A bakin window din ta tsaya,ta daga hannunta ta dorashi saman nata hannun,take kaltum taji wani irin sanyi yana shiga jikinta ta kowacce gaba dake jikinsa.


Ci gaba da kallon juna sukayi ita da matar,ta bude baki tana magana amma kaltum din bata iya jin abinda take fada,gashi dai a haka bakinta yana motsawa sosai,magana takeyi amma bata iya jin koda harafi guda


"Kaltum!!!" Taji an qwala kiran sunanta daga bayanta,sai tayi maza ra waiwaya,mummy ta gani tana nufota da sassarfa,sai taji ta zame daga dagen da takeyi,data daga kai kuma sai taga babu wannan matar daga gabanta,babu komai a gabanta sai wani mutum dake tsaye,shi kuma bata iya ganin fuskarsa sai bayansa



"Samir!" Taji bakinta ya kira da mugun qarfi,wanda sautin kiran ya shiga kunnenta ya kuma farkar da ita daga nannauyan baccin da ya dauketa.


A mugun firgice ta tashi,zuciyarta na bugawa da sauri kamar wadda tayi tsere,haki ra fara yi tana maida numfashi,qirjinta yana dagawa,ta fara bin dakin da kallo,babu abinda ya canza,yadda ta kwanta haka komai yake,hatta qwan fitilar da bata kashe ba yana nan a hakansa a kunne


"La'ilaha illal lah,wahdahu la sharika lah,lahul mulku wa lahul hamd,yuhyi wa yumitu wa huwa ala kulli shai'in qadir" ta dinga maimaitawa qasa qasa a hankali.



Sannu sannu taji nutsuwarta na dan dawowa,tasa hannunta a hankali ta zame dankwalin kanta saboda gumin da takeji,maqogoronta ya bushe sosai,don haka ta zame daga gadon da niyyar sauka,hakan yasa pillow din data tada kanta dashi ya biyota saboda santsin zanin gadon.


Duqawa tayi ta daukw pillow din,idanuwanta suka fada kan hoton data cusa anan kafin ta kwanta,idanu ta zuba masa sosai,kamar yanzu ta fara ganinsa,take jikinta yayi sanyi ta koma dirshan ta zauna,saboda sak kamannin matar da tayi mafarkinta a yanzu su take ganin a wannan fuskar dake jikin hoton


"WACECE ITA?" Tambayar data yiwa kanta kenan,wadda bata da amsarta,batasan ma inda zata samu amsar ba,tabbas!,akwai wata a qasa,wannan hoton shike saka biba kuka,kukan da biban tace matuqar ta gayawa wani tana yinsa to rayuwarsu na cikin barazana,barazana a wajen wa?,wa zata tambaya ya gaya mata wacece wannan matar?,meye hadin mommy da ita har da zata bayyana cikin mafarkinta?,me yasa suna sa siffar samir suka fito cikin mafarkin?,kukan me matar takeyi bayan biba tace mata ta mutu?.


Miqewa tsaye tayi wani abu na dawo mata,dakin dataga matar shine dakin dataga wannan matar randa ta raka mommy gidan masu tabin hankali,saita sake kallon hoton da kyau,da matar data gani a asibitin mahaukata,da matar data gani a mafarki,da matar dake jikin wannan hoton kamarsu daya,tabbas kamarsu daya,saidai banbancin shekaru,amma suna tsananin kama,to me kenan?,meye wannan?,su wadan nan matan su waye su?.


Post a Comment

0 Comments