TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 11-13

 15, 10:51 AM] Zafafa: _*MIN QALB 11*_

_mamuhgee_




Babban palone na alafarma irin tsarin sarautar zamani daya dauke setin royal kushins hudu golden and red sbd girmansa ga kalar dasuka qara qawata palon,

Shine palon da dukkanin familyn ZABEERA ke meeting acikinsa qarshen kowane wata to wannan watan ma hakan ce tafaru dukkanin daukacin zabeeras dake jahar suna cikin palon kusan su sama da arbain kowanne yasamu guri ya zauna ana tsimayin fitowar me kankat wato Modibbo Wanda fitowarsa tayi daidai da tsit da gurin ya dauka sai gaisuwa kawai dake tashi Yana amsawa ta hanyar 'daga Kai batareda ya bude baki ba.


Zama yayi Yana bin kowa da kallon jinjinawa na riqe wannan al'adar dasukayi har idanuwansa suka sauka akan MD ZABEERA wanda ke zaune can bayani iyayensu dukkanin hankalinsa gabaki daya Yana Kan waya dayake karanta email din saqo daya shigosa,


Kallon zamansa Modibbo yayi har zuwa fuskarsa dake daukeda wani irin kwarjini da haiba ya jinjina Kai Yana cewa'


Tabbas Babu wani zabi daya wuce akan mulkin zabeera ayau taron naka ne.


ZARAH kuwa duk da ta shige cikin 'yan uwa da qawayenta 'yan uwanta Amma hankalinta na kansa akai akai take satar kallon gefen dayake sbd ganin yauma dai kamar ko yaushe arayuwarsa ya kebe ne daban duk da yanzu duk Wanda yashigo cikin qanne da tsaransa ma harma da wainda suka girmesa zuwa sukeyi suna gaidashi Wanda Shima yawanci daga Kai ne kawai bai cika bude bakinba Yana amsawa musamman sbd rashin sabo da Yan uwan duk wasu da dama baisansuba.


Khalil ne abokin zamansa akowane meeting tun quruciya Amma yau Khalil din baishigo da wuri ba Abinda baitabayiba ranar meeting wato latti.


Khalil kuwa yanacan ne hanyar gidansu amatu data Hana rayuwarsa da zuciyarsa sukuni,

Tsawon kwanakin Nan bayan haduwarsu da ita bincike yayi me kyau akanta sbd shigo da ita a rayuwarsa Dan sauya musu ingantacciyar rayuwa dakuma tunaninta daya kasa fita ransa da kansa,

Tabbas yasan babban laifine a zabeera neman aure a waje wanda bama ataba yiba asai yanzu dazai Fara shigo da tsarin karya dokar manya sbd bayajin zai iya hkr da maganar amatun a shirye yake daya tallefi yarinyarda zuciyarsa ta riqe a gani na farko Koda hakan na nufin barin zabeera ne barema yasan zai shawo kansu da taimakon MD.


Babban rashin sa'ar dayaci shine bayan isarsa kawu yayi Masa bayanin aiki tasamu ta tafi training Amma dai yabasa numbernta Dana usi din duk da shi Usin Rakata kawai yayi dawowa zaiyi.


Koda ya karba lambar agogo ya duba yaga yayi lattin meeting ga umme Bata gansa ba sai kiransa takeyi 

sai bai tsaya Kiran numbrn ba yayi saving tareda dawowa zabeera cikin sauri sbd yasan zuwa yanzu anfara meeting din.


Yana qoqarin shiga gate din zabeera yaga motar 'yan jarida na tsayawa ta gate suna qoqarin gyara cameras dinsu ya Dan tsaya Yana kallonsu cikin mamakin meya kawosu musamman ma da zabeera basa muamala da duk Abinda zai hadasu da 'yan jarida sbd tsira da mutuncinsu da sunans ahalin,

Ganin yayi latti sauri yakeyi yasa bai tsayaba yashigowarsa,

Yanayin parking harabar gidan Kiran nuratu nashigowa wayarsa ya saki siririn tasaki Yana dafe kansa dake Masa ciwo sbd rashin bacci kwana biyun yayi rejecting kiran ko Ina bai tsayaba Kai tsaye ya nufi palonsu na meeting dasuke Kira da zabeera hall.


Yana shiga yaga har anyi nisa yayi saurin yin gefenda ya hango md zaune Ya lumshe fararen idanuwansa ya kwantarda kansa ta baya jikin kujerar dayake Yana sauraron Abinda ake fada cikin nutsuwa.


Qoqarin miqewa alhaji qarami yakeyi zaiyi mgn suka Fara jiyo hayaniya me 'dan qarfi tana tashi daga wajen qofa,

Sharewa sukayi alhaji qaramin yafara bayani Amma sai gaba hayaniyar keyi

Alhaji qarami ya kalli yakub babban 'dan alhaji qaramin yace"


Yakub dubo meke faruwa ne.


Miqewa yayi ya fita Dan dubowar sukuma suka cigaba da meeting din.


Mintuna biyu da fitar yakub sai gashi yadawo da sauri yazo gefen babansa yayi qasa da murya yafada Masa abin dake faruwa da sauri ya kallesa Yana cewa'"


Mene?


Kowa najin haka yayi tsit suna jiran jin abindake faruwa.


Je kashigo dasu""alhaji qarami yace Yana qoqarin cigaba da bayanin dayakeyi.



Sallama sukayi wadda tasa kowa juyawa hadda Shima dazaiyi maganar duk suka kalli qofar wadda ke seti tana kallon center inda Modibbo yake zaune Shima sbd ba'a taba barin wani shigowa ba idan suna taron yasashi dakowa ya kalli qofar.


Baba Jamila ce agaba amatu na bayanta fuskarta rufe da doguwar hijab dinda tasaka fuskarta da idanuwanta a kumbure sosai sunyi jajir tsabar aboniki dasuka Sha kamar wadda tayi wata biyu tana kuka.


Tsit sukayi kowa palon na aika musu da kallon mamaki da jiran bayani Amma sai qif qif baba Jamila keyi da idanuwanta tana sunkuyar da Kai.


Alhaji qarami ne ya kalleta tareda kallon amatun dake bayanta kafin ya kalli qafafunsu har zuwa zamansu ya gyara murya yace"


Malama Yaya dai??

Lafiya??

Daga Ina??


Saurin zubewa qasa tayi tareda sauke kanta qasa cikin rawar murya tanason fashewa da kuka tace"


Ranka ya Dade adalci nazo nemarwa 'yata...,


Kowa kallonta yayi wasu Kam Kai tsaye kallon mahaukaciya suke Mata mamakinsuma yanda akayi tashigo zabeera harta iso Nan din.


Cikin mamaki alhaji qarami ya miqe ya qaraso gurinta ya tsaya Yana cewa'"


Malama adalci kike nema ai banan ake zuwaba,

Mu Nan Kinga Muna wani taro ne me mahimmanci kinyi batan hanyane kije security zasu nuna Miki qofar fita......


Girgiza Kai tayi wannan karon tana fashewa da kuka Mai shiga zuciya tana bubbuga kanta.


Yanxu Kam mamakinsu yafara cirewa sai fargaba

Kamar daga sama taji saukar muryar dattijo me ran qarfe,

Muryar data saka 'yan hanjinta kadawa Dan tsoro da firgita da wani irin amo yace"


Idan da kanki a hayyacinki kikazo Nan kifadi Abinda yakawoki kokuma ki hadu da hukuncin kutse da datse mahimmin Abu acikin zabeera.


Jan hanci tayi tana shage hawayenta dasukaqi tsayawa murya na rawa tace"


Ranka ya dade 'yatace gatanan cikine a jikinta......


Cikin tsawa me qarfi alhaji qarami ya e"


To Nan asibitine ko gidan aurenta dazaki......


Uban cikin Yana Nan"""ta katsesa cikin rawar murya tana sake bulbulo da ruwan hawaye.


Atake gurin yayi tsit kamar ruwa ya cinyesu musamman Modibbo daya gyara zama Yana kallon matar da kyau kafin ya dago ya kalli amatu dake tsaye har lokacin tana matso hawaye cikin hijab.


Kallon amatu yayi cikin wani irin amo yace"


Ke yarinya bude fuskarki kiyi bayaninda mahaifiyarki keson fada saidai duk Abinda zaki fada kifara tunanin a inda kike.


Qarar wayar Dr khalil ce ta katse maganar Modibbo wadda tasa kowa juyowa ya kallesa da sauri ya Danna wayar tareda miqewa ya fita da sauri Yana magana qasa qasa sbd daga asibitinsane ake Kiran wasu takardune da ake buqata emergency yace suzo su karba Nan gida.


Harabar gidan ya nufa gurin motarsa yana tareda budewa ya dauko takardun cikin Burnet din motar ya nufi bakin gate ya fita Dan miqawa Dr ashir.


Sama sama yayi Masa bayanin takardun sbd hankalinsa dake Kan 'yan jaridar da har lokacin suna gurin take yaji yakasa samun nutsuwa da hakan,


Meke Shirin faruwane?

'yan jarida a qofar zabeera,

Ga Kuma wasu baqi aciki suna maganar anyiwa 'yarta ciki.....


Da matsala yafada Yana sallamar Dr ashir ya juya ciki da sauri Yana tunanin Dole da akwai inda matsala take,

Me zaisa wannan matar su gayyato 'yan jarida??anshirya hakan ne Dan idan baa karbi cikin bane kokuma me??

Something is definitely fishy mezaisa tazo da masu jarida ita Bata damu da mutuncin 'yarta bane idan Yan jaridar suka watsa to kodai tanada wani manufa be??? Oh no.." yafada da sauri tareda yin ciki da sauri haryana hadawa da gudu gudu...


Karo yayi da mutum Wanda yasashi yin baya zai Fadi USI yayi saurin rikosa Yana cewa'"


Dr.


Da sauri Dr khalil din ya dago Ya kalli Usin mamakinsa a bayyane Dan komai nasa ya nuna mamakin cikin sauri yace"


Usman?

Kaine anan?

Me kakeyi anan??


Kallonsa Usman yayi Yace"


Aiki amatu tasamu anan......


Saurin gintse bakinsa yayi sbd shaf ya manta Abinda ya kawosun.,


Ya shafo kansa Yana waskewa yace"


Dr kaima me kakeyi anan din???


Kafa Masa Ido Dr khalil yayi ba Wasa a fuskarsa yace"


Wane aiki ne amatu tasamu anan din??

Ina amatun take????


Shiru yayi Yana shafa Kai Yana qoqarin hado qarya Dr khalil ya katsesa da cewa"


Ina amatun?


Rasa yanda zaiyi yayi yace"


Tana ciki tashiga da wata Mata.....


Wattt???

Yafada da qarfi cikin firgici da tashin hankali yace"


Meke faruwa?

Me sukaje yi?

Infact meya kawoku Nan din nakeson ji""zuwa lokacin yafara hasala yace"


Kuma wlh karka kuskura kamin qarya.


Kame kame usi yafara Yana neman yanda zaiyi saidai gskia zai fadawa Dr khalil idan yaso qila shi zai taimakesa ya shawo Masa Kan amatun kar tayi Abinda zatayin

Kallonsa yayi tareda jansa gefe yace"


Dr Dan Allah kayi alqawarin zaka taimaki amatu bazakayi Abinda zai jefata hadariba Dan Allah kayi wannan alqawarin.


Cikin zaquwa Dr khalil din yace"


Koba Dan alqawarinka ba bazan taba Bari amatu tashiga hadariba zan tsaya Mata ako Inane just tell me.


Cikin fargaba Usin yafada Masa yanda amatun tayi da hajiya aisha saidai ya boye Masa da yardar amatun nuna masa yayi kamar tursasata hajiyar tayi sbd amatun ta daukar Mata kudi.


Tsit yayi kamar ruwa ya cinyesa 

Har wani duhu duhu idanuwansa ke gani sbd tsananin tsoro da firgicin zancen,

Ita umme ko tunanin hadarinda zata jefa 'yar mutane batayi da kantama tunda komai jimawa dai wataran gaskia zata fito,

Idan ita amatu hankalinta bai Kai ba ita meyasa zatayi hakan??

Qarin tashin hankalinsa MAHMOUD za'ayiwa wannan mummunar 6ata sunan

Haqqinsa bazai bar umme ba hattasu yayanta sai haqqin MAHMOUD ya shafesu Dan haka bazai Bari tadau wannan alhakinba dazai ja Mata azaba gaban Allah hakama bazai Bari rayuwar 'dan uwansa ta lalace ba hakama amatu rayuwarta nacikin mugun hadari.....


Da sauri ya kalli usi yace"


Usman Yi sauri kabar Nan katafi gida namaka alqawarin dawo da amatu Babu Abinda zai sameta maza katafi karka fadawa kawu komai..


Da gudu ya nufi ciki yayi hanyar palon Yana adduar Allah yasa amatun Bata bude fuskartaba Yana Isa ya fada palon da qarfi daidai lokacinda amatun tariga ta bayyana fuskarta akace ta fada cikin waye ajikinta,meye alaqarsu dame cikin?¿


Bude baki tayi hannuwanta da qafafunta na rawa zuciyarta na harbawa da qarfi zatayi magana tana kallon inda MAHMOUD ke zaune har lokacin idanuwansa lumshe Kuma duk yana jin abindake faruwa kawai dai ba huruminsa bane shiyasa ko hankali bai badaba,

 cikin wani irin sauri Dr khalil ya dako tsalle ya fado tsakiyar palon tareda cewa"


Allah ya taimaki Modibbo nine.


Wattttt????umme tafada da sauri tareda miqewa tsaye tareda haj Maryam

Nuratu ma da antynsa juwairiyya duk miqewa sukayi cikin tsananin firgici

Take palon yadauki hayaniya cikin rasa abin fada alhaji qarami yace kowa yatafi antashi meeting.


Hayaniya aka Fara saidai yanayin Modibbo yasa kowa yin tsit suka Fara sulalewa suna ficewa.


Kaf kowa ya fice Banda uwayensu maza da 'yannansu maza sai iyaye mata hatta MAHMOUD na gurin bai fitaba lokacinda yaji muryar khalil amatsayin me cikin yasashi bude Ido ahankali ya sauke Kan amatu dake gefen Khalil din tana kallonsa cikeda mamakin daga Inda ya fado.


Kallonsa takeyi tanason Kiran sunansa Amma ganin yanayinsa ta tana hango tsananin 6acin Rai da takaicinda yake ciki,


Idan har da khalil da MAHMOUD yayan hajiya mama ne kamar yanda tafada mata to acikinsu duk Wanda tace shine me cikin ta cecesa daga hawa mulkinda zaa salwantar da rayuwarsa to kenan duk dayane koba komai zatafi farin cikin kubutarda Dr khalil sbd kurkinsa akansu.


Da hanzari umme ta qaraso gabansa ta kalli cikin idanuwansa cikin 6acin Rai tace"


Me kake fada?

Maza maza fice wannan ba Abinda ya shafeka bane...ba magana nake maka ba""ta fada cikin tsawa da firgici.


Gyaran murya Modibbo yayi akaron farko bayan shock din daya samu na daqiqu ya kalli khalil tareda kallon amatu dake kallon Khalil din cikin rashin Jin Dadi qunci da bacin ran datake hangowa cikin idonsa.


Khalilu ta Yaya kazama uban cikin jikin yarinyar na???


Hadiye wani yawu me mugun daci yayi sbd dai gskia bazata faduba Dan idan yafada gski umminsa da amatu duk suna cikin hadari Dan umminsa har zamanta cikin zabeera saiya ware.


Rintse ido yayi ya budesu suna kadawa jajir take jijiyoyin kansa suka firfito sbd qarya ba halinsa bane bare wannan qaryar datafi kowace muni.


Muna sauraronka Khalil kafin fushinmu ya sauka akanka kayi bayani"cewar alhaji qarami.



Sauke Kai yayi daga kallonda Modibbo ya tsaresa dashi me girgiza jarumtarsa yace"


Mun jima muna qaunar juna tsawon shekaru uku 

Nasan bazaa Bari na aurotaba shine mukaje wani guri aka daura Mana aure.....tassssssss


Umme tasakar Masa wani gigitaccen Marinda Saida ya zube Kan gwiwoyinsa tareda sauke Kai.


Cakumo amatu tayi cikin tsananin 6acin Rai tace"


Modibbo ba gskia yake fadaba Khalil bazai taba aikata wannan qazamin aikinba wannan ita zata fada ubanda ya Mata ciki Amma badai Khalil ba....hannu ta daga zata kaiwa amatun Modibbo ya daka Mata tsawa da cewa"


Aishatu ki dawo hankalinki ciki ne ajikinta kada hannunki ya sauka jikinta..


Ke matso fili ki fada Mana Abinda yafada gskia ne kokuwa??


Fitowa tayi daga bayan Khalil din tana kallon idanuwan umme dake fitowa da ruwa tace"

Eh gskia ya fada.


A Ina kuka hadu??


A asibitinsa.


Shekara nawa yanxu da auren??


Rawar murya tafara tana neman dufewa tace"


Daya.


Aikuwa take kowa yaqarin tsit cikin tashin hankali.

##mamuh#




______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899[3/16, 1:57 PM] Zafafa: *_MIN QALB 12_*

_Mamuhgee_




Kasa riqe hawayenta umme tayi suka gangaro Kan fuskarta ta shafa cikin firgici ta dago hannunta ta kalla taga tabbas hawayene,


Yau ni Aisha mezan gani ne??

Wace masiface wannan yarinyar na gayyatowa kaina ranar farko data sako kafarta gidana hawayenda na manta ya akeyinsu tun quruciya yau sune a fuskata,

Wlh shirina bazai lalace ba Koda kowama zai rasa saidai kowa ya rasa...


Juyawa tayi Kan khalil cikin tashin hankali da rudewa tace"


Khalil karkayiwa kanka haka ka 6ata rayuwarka kafada gaskia wannan yarinyar bakada alaqar komai da ita,


Rintse ido yayi Yana danne tsananin 'dacin da zuciyarsa ke Masa 

Ummin ta girgizasa da qarfi tana sake Marin fuskarsa tace"


Kafada gaskia Khalil wlh bazan yadda a maqala maka cikin qaryaba wannan yarinyar 6arauni.....


Katseta Modibbo yayi da cewa"


Aishatu ki nutsu kisan a inda kike,


Shiru yayi Yana nazari cikin tsananin baqin cikin da takaicin Abinda ke faruwa ya dago ya kalli khalil 

Khalil din yayi saurin sauke kansa

Yace"


Khalilu Abinda kayi a tunaninka meye shi??


Modibbo a musulunce shi aure idan har an daurashi Akan yanda sharuddan aure sukace to banyi laifi ba,

A tsakanina daku iyayena Kuma laifi ne sbd na boye Muku nayi bada izininku ba saidai nayine sbd girmamaku Dan inajin tsoron kawo muku zancen sbd tsoron bazaku Bari,

Dan haka na aikata laifi babba Kuma Ina neman yafiyarku dakuma amincewarku da amatun kodan Abindake cikinta baida laifin komai kada a hukuntasa ko mahaifiyarsa nine me laifin Kuma na dauka a shirye nake da dukkanin wani hukunci saidai Allah ya huci ran Modibbo ina fatan itama amatu abata adalcin datazo nema duk yanda akayi hukuncin zamu dauka.


Tsit sukayi suna kallon bakin Khalil din cikin girgizuwa da kalamansa,

Dukkanin Abinda yafada jin sukayi kalmomin na son tabasu,

Shi cikin babu ruwansa to meye mafita ga wannan alamarin?


Kallon mahaifiyar amatun Modibbo yayi yace"


Ina mahaifin yarinyar??


Ya rasu tun tana yarinya qarama.


Ina danginsa?


Daga maiduguri mukayo Nan munrasa kowa bamuda kowa nanma amatsayin 'yan gudun hijira muke har mahaifinta yasamu aikin sanaar Saida kayan Miya harya rasu daga Nan ne muka hadu da......sai tayi shiru tana satar kallon hajiya aisha sbd Abinda zata fada itama ba yanda ta iya Dole tabi tsarin yanda al'amarin ya juya kodan fita da ranta tace"


Daga Nan ne muka haduda likita shine yake taimaka Mana harya sanyata makaranta shine yakawo maganar son aurenta nikuma na amince saidai bai fada Mana cewar iyayensa Basu aminceba yakawo Mana wani amatsayin mahaifinsa aka daura auren yanzu shekara daya kenan,

Mu Kuma kusan wata biyu kenan bamu sake ganinsa ba munyita zuwa asibiti bama samun ganinsa saigashi ciki ya bayyana atareda ita

 mutane harsun Fara binmu da gori da maganganu marasa Dadi shiyasa mukazo...


Faduwa ummi tayi Kan kujera tayi zaman 'yan bori tana kallon baba Jamila tayi wani kukan kura tayi kanta tana cewa''


Qarya takeyi Modibbo wlh taron maqaryata ne....


Saurin riqeta hajiya Maryam tayi cikin tashin hankali take itama tace"


Modibbo Sam wannan matar qarya takeyi wlh daga gani sharri ne zuke qullawa sbd kudi......kallonda Modibbo yayi Mata yasata yin shiru baqin cikin future din 'yarta dake Shirin lalacewa na cinta kamar ta rufe amatu da bugun mutuwa.


Khalilu duk Abinda tafada gskia ne kokuwa? 


Gyada Kai yayi kansa na qasa Dan duk duniya bai ta6a Jin tsanar wani lokaci 'daya ba kamar baba Jamila.


Bsyan dogon nazari da tunanin irin rashin 'da'a da wulaqanta zabeera da Khalil din yayi take yafita ran Modibbo da kusan kowama a gurin kai tsaye cikin nuna qyamarsa ga khalil din da halayyarsa Modibbo yace"


Ban karbi wannan auren naka ba likita haka Kuma kaima na cireka daga iyalina ka dauki matarka kuje kibar Nan karka sake Kiran kanka da zabeera har abada,

Kuma kuje ga adalcin dakuke nema Nan anbaku,

Anbarwa 'yarki mijinta har abada duk ranarda qafarku ta tako zabeera aranar ne zakusan asalin hukunci da zafin Zabeera.........


Kuka ne qarfi umme ta fashe dashi tareda riqe Khalil din da idanuwansa suka qarasa rinewa jajir Yana Mata kallon kece Kika jawo..


Girgizasa tahauyi tana kuka Mai qarfi tace"


Dan Allah Khalil kafada musu gskia bakai bane

Wlh bazan yardaba nizan fada gskia..


Girgiza Mata Kai yayi tareda zamewa daga hannuwanta yayi qasa da murya cikin qunci Yana cewa'"


Ummi kema kisani idan har kina Sona da 'dan sauran farin cikin daya ragemin bazaki taba fadar gskia ba sbd zata saki keda amatu cikin hadari Wanda bazan iya daukaba,

Umme kece rayuwata gabaki 'daya amatu kuwa itace zuciyata

Meyasa zakiyi haka ummi....??


Mutuwar tsaye tayi tana kallonsa cikin tsananin tsoro da tashin hankalin Abinda yafada,

Me Khalil ke nufi?

Amatu zuciyarsa,

Dama sunsan juna da gske kokuwa ita yakeson rainawa hankali,

Amatu dama tasan 'danta shine ta karbi aikinta kenan ita take rainawa hankali tabbas zatasan tayi Wasa da wuta.


Gangarowa wasu sabbin hawayenta sukayi ta girgiza Kai tana cewa'"


Khalil wlh bazan iya gani na rabu dakaiba,

Ka saketa saki uku,

Cikin ma a zubar kabawa Modibbo hkr Amma Dan Allah Khalil kada katafi yaqarasa cikin kuka tana sake riqesa.....


Cikin tsawa wannan karon Modibbo yakira sunanta Yana kallon Khalil yace"


Ko bayan kabar Nan duk ranardaka saketa daga ranar zakasan ainihin fushin mahifinka,

Haka cikin dake jikinta.


Zubewa qasa umme tayi da sauri Yana cewa'"


Na roki Modibbo daya taimaka ya sassautawa Khalil wannan hukuncin.


Miqewa Modibbon yayi Yana cewa'"


Taro yaqare kowa ya tafi.


Kamar daga sama sukaji security din bakin qofar shigowa na bada sanarwar isowar Andi Wanda yasa kowa miqewa cikin tsananin firgici sbd Abinda andin yafi shekaru ashirin beyiba wato zuwa meeting palon.


Hajiya Maryam data yiwa amatu text din takira andin tafada Masa halinda ake ciki ta saki ajiyar zuciya tana riqo umme data miqe da sauri itama ganin Andi yau da kansa take ta shiga taitayinta tana shanye kukanta saidai hawayenta dasukaqi tsayawa ta kalli hajiya Maryam tace"


Kin kyautamin Maryam sbd Andi ne kawai zai iya ceton Khalil Dina yanxu.


Modibbo da kansa ya miqe yabawa mahaifinsa dake tattareda wata irin izzar mulki da cika Ido tareda razanarda mutane da kallo 'daya idan yayi maka Wanda kaf cikin zuriar zabeera mutum biyu ne suka 'daukosa sak alqasim zabeera mijin haj Maryam daya rasu sai MAHMOUD ZABEERA wanda beyi mulki ba Amma Yama wucesa a mugun miskilancin da kwarjini me ban tsoro.


Shigowar Andi tasake saka kowa cikin tsoro da firgici Saida yayi zaman minti biyar tsit bayan gama amsa gaisuwar kowa kafin ya bude muryarsa me amsa amo yace"


Khalilu da kanka zakayi bayanin abindake faruwa daga farko.


Ba inda inda Khalil yasake koro Masa bayanin komai tareda hukuncinda Modibbo ya yanke Masa ya 'dora da fadin"


Na aikata babban kuskure Kuma na amsa laifina nakuma karbi hukuncina Andi,

Zanyi nesa da Nan Kuma bazan taba Bari maganar ta fitaba bare sunan zabeera ya baci,

Nayi alqawarin daga lokacinda zan fita Nan zan aje sunan zabeera Dan kada gaba nayi Abinda zan kawo batanci gareku ba da......


Cikin firgici ummi tayi saurin zubewa qasa tana cewa'"


Allah ya taimaki Andi Dan Allah Andi ya tausaya a sauqaqawa Khalil tsaurin hukuncinsa kada arabasa da sunansa da zuriarsa indai akan laifin wannan yarinyar ne Andi abasa dama yayi Mata saki uku bayan ancire cikin.......


Maganar ummin yasa Andi dagowa ya kalli Modibbo 

Modibbon yayi saurin qasa da Kai Yana cewa'"


Ayi Mata afuwa Andi uwa ce dake cikin firgicin rabuwa da 'danta.


Kallonsa andin yasake hakan yasashi yin shiru Yana cewa"


Allah ya huci zuciyar Andi da Abinda aishatu tafada.


Kallonta Andi yayi tareda kallon baba Jamila yace"


Aishatu matsayinki na mahaifiya kikeson a cutatarda 'yar wata sbd naki 'dan wannan ba adalcin Andi bane.


Kallon baba Jamila yayi cikin sautin dayasata rudewa qafafunta suka hau rawa yace"


Kinxo neman adalci anbaki adalci

Kin aminta da auren 'yarki Dan haka 'yarki zatayi zaman sure bayan munyi bincike akan auren,


Zaki bar 'yarki anan Kuma zata zauna cikin gata da aminci

Zata raini cikinta a hannun matar 'dan uwansa MAHMOUD ZABEERA bayan haihuwarta anbawa mahaifiyarsa halak malak saimu sake daura musu aure,


Aishatu kinason kashe abindake cikin tun baizo duniyaba to kece zaki rainesa har girmansa bayan zuwansa duniya an mallaka Miki shi halak malak.


MUHAMMAD""fada sunan Yana 'daga sautinsa.


Sai alokacin MAHMOUD ya dauke idanuwansa daga Kan Khalil da amatu sbd jin a hannunsa yarinyar zatayi rainon cikinda bai gama yadda da akwaisaba sbd aduniya shine yafi kowa sanin wannan ba halin Khalil din bane ya kalli inda Andi yakira sunansa ya taso cikin nutsuwarsa dake qarawa Andi ganin kwarjininsa ya qaraso ya tsaya gaban andin tareda sauke kansa cikin girmamawa yace"


Allah yaqarawa Andi tsawon Rai.


Matar 'dan uwanka zata zauna a hannun matarka har tsawon lokacinda zata haihu,

Cinta da Shanta duk na hannunka,

Ciwonta da maganinta na damqasu hannunka Dana matarka,

Na damqa maka tsaron lafiyarta Dana Abindake cikinta sbd aishatu ta tabbatar Mana da AMATULLAH da abundake cikinta na cikin hadari a hannunsu Dan haka Kaine kawai Wanda na yarda dashi nabaka amanarsu a hannunka.


Shiru yayi bai motsaba sbd Abinda andin yafada yaxo da wani al'amarine da kansa yake kasa dauka,

6arauniya a gidansa?ta Yaya zai iya Bari wannan yarinyar ta zauna acikin inda yake rayuwa 

Khalil dinma haryanxu yakasa yarda da shidin ne uban cikin wannan yarinyar

 ahankali yadan dago ya kalli gefen datake tsaye riqeda rigar Khalil sbd zuwa lokacin tafara firgita da abindake faruwa Jin hukuncin da aka yankewa Khalil daga farko taji bazata iya Bari tazama sanadin batawarsa da rabuwa da iyayensaba saiga zuwan wannan Andin Wanda ganinsa kawai yasa taji tsoro da firgici ya kamata gashi ana maganar riqeta ta haihu

Ta Ina dakuma ta Yaya zata haihu

Kasa riqeta qafafunta sukayi tsabar rawa shiyasa ta boye bayan Khalil din.


Taro ya tashi kowa ya watse nagama magana abubukar a aika mahaifiyarsa gida tareda kayan abinci da jarin sana'a me kyau sbd itace kakar Zabeera na shida Inshallah.


Modibbo a qarqashinka zaa kula sosai matuqa da AMATULLAH Ina fatar Nanda watanni kadan za'a bani zabeera na shida a hannuna.


Kallon amatu yayi akaro na farko data saki fuska dukkaninsu Saida suka bude Ido sbd ganin murmushi akan fuskar tasa yace"


AMATULLAH ni Andi nine gatanki keda Abinda yake cikinki acikin zabeera nayi Miki alqawarin baki kyakkyawar rayuwa keda Abindake cikinki sbd zalincin da khalil yayi miki da Wanda mahaifiyarsa ke shirin Yi na cutatar dake da Abinda ke cikinki Dan haka na Miki alqawarin idan har Ina Raye Kika haihu indai namiji sai yayi mulkin zabeera wannan shine babban adalcin dazan baki,

Kece mace ta farko Kuma mutum ta farko data shigo zuriar zabeera a tarihi ki riqe wannan a ranki Dan haka karki Bari har abada Nasameki da illa ko laifin dazai sakani takaicin hukuncina sbd cin Amana,yaudara da qarya ba abubuwan da Andi ke yagewa bane.


Kai Kuma Khalil hukuncinka na ranardazan daura maka aure da ita.


Kowa yatafi nagama mgn.


Hannu umme take Shirin dorawa akai tasaki kukan baqin cikin wannan alamarin Modibbo ya aiko Mata da mugun kallo Haj maryam ma dake Shirin fasa ihu Andi ya nuna musu qofa sunaji suna gani suka hadiye cikinsu bame iya Jan wani suka fito Babu me ganin gabanta tsabar tashin hankali.


MAHMOUD ma ficewa yayi batareda yaqara ko second dayaba.

Baba Jamila da Sha Taranta ta arziki aka kaita gidanta inda suka tsara komai Koda anxo bincike.


ZARAH aka kirawo ita tazo aka damqa amatu hannunta wadda atake alokacin amatun tashiga ranta ta kalli amatun dake qara damqe rigar Khalil sbd hankalinta daya tashi gaba daya da alamarin sbd ita yanzu Tama rasa Ina aikin data zoyi yaje Sam sun rikita 'yar qaramar qwaqwalwarta.


Kallon Khalil tayi tana sake matsesa tana girgiza Kai tace"


Dr gida zani nafasa bana......


Hannu ya Dora a bakinta tareda girgiza Mata Kai Ya bude bakinsa daya gama nauyi muryarsa na nauyi a karye yace"


Kije kibi ZARAH komai zai daidaita bazan Bari komai ya sameki ba na Miki alqawari,

Kuma zansamu kawu nayi mgn dashi zan Masa bayani yanda zai fahimta Inshallah.


Qura Masa Ido sosai take kallonsa sbd yadda dashi datayi dari bisa dari kafin ta daga Masa Kai tasakesa ahankali tareda kallon zarah dake Mata murmushi suka wuce.


Bayan fitarsu Kai tsaye motar zarah din suka nufa suka shiga ta jazu sukabi ta bayan gefens Modibbo zuwa part dinsu dakeda nisa cikin zabeera din sbd kusan sune na qarshe.



Umme nashiga palonta ta zube qasa tareda Dora hannu akai zata saki ihu juwairiyya tayi saurin rungumeta tana Kiran sunanta itama muryarta na karyewa dason yin kuka.


Haj maryam ma kuka takeyi wiwiwi itada nuratu dake wani irin kuka tana kwantawa jikin momyn Tata sukam yau wace irin baqar ranace agaresu.

##mamuh#




______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09

Post a Comment

0 Comments