TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB PAGE 1-2

 Bismillahir-rahamanir Raheem.



Qoqarin durqusawa takeyi ta dauki busashen biredin dataga wani yaro yazo ya zubar a babbar bolar bakin anguwar wadda za'a Kira da qaramar kasuwa sbd hargitsi da cunkushewar anguwar da manya da qananan kwatocinda suke cike taf da ruwa da ledoji tareda qananan abinci na wanke wanke dasuke biyowa,


Daukar biredin tayi tana kakkabewa tareda kaiwa bakinta daya gama bushewa yayi fari fat harya Fara yayyankewa alamar ko yawun bakinta sun gama bushewa ta gutsura kadan ta Dan tauna taji zai shiga 

Da sauri ta qarasa turasa cikin bakin tana taunawa da sauri jikinta na rawa tareda hanjinta dasuke qugin jin wani abu ya saukar musu bayan kwanaki dasuka Dan dauka a na'de.


Ganin wani almajiri yayo gurin Yana kallon biredin a yunwace Shima Dan ko gabansa baya kallo idonsa nakan biredin ko kyaftawa bayayi yasa tayi saurin miqewa tana qara tura biredin cikin bakinta da sauri sauri tana kallon almajirin karya iso gurinta Bata cinyeba ya kwace sbd wannan shine Abinda yake faruwa a bolar qwacewa daga marasa qarfi Wanda a duniyarma hakane duk me qarfi shike qwace Abinda yakeso gurin masashi,


Batada uwa batada uba,

Batasan kowa aduniyaba Wanda zata ce nata ne,

Ita aduniyarma gaba daya batasan komaiba face yawon bola da tsince tsince.


Almajirin na isowa gurinta yayi wuf da qarfi ya qwace biredin hannuwansa na rawa Shima yakai bakinsa yanaci da sauri sauri Yana hadiyewa ko taunawa bayayi sbd sauri yakai bakinsa.


Kallonsa takeyi tana hawaye tana lashe sauran Dan gari garin biredin dake hannunta tareda uwar dau'dar dake tafin hannuwan nata dasuka sauya kala sbd dau'da.


Tana kallo ya cinye biredin ya dago Yana kallon hannuwanta ko zaiga wani abin naci sbd yunwar dakeci hanjinsa yakai ko numfashi baya iyayi ko mushe yagani zai iya ci sbd qarfinsa daya gama qarewa gurin yawon bara.


Ganin yanawa hannuwanta kallon yunwa yasa ta juya ta tafiyarta zuwa tsakiyar bolar tana bincikawa ko zata Kuma samun wani abin.


Yarinyace qarama sosai Yar kimanin shekaru bakwai saidai yunwa da wahala Sunsa ta matse sosai kamar Yar shekaru shida,


Dau'da tasa fatarta takoma baqiqirin ko tantance asalin kalar fatarta ba'ayi 

Ga gashin kanta daya gama tsinkewa sbd dau'da da zamansa a bude.


Gangarawa tayi yafito cikin bolar tana qoqarin bude gwangwanin data samu cikin bolar fuskarta na nuna 'dokin son ganin me tasamo.


Bakin shagon alhajiyat me abincin bakin titin ta zauna daga can gefe inda ake Mata wanke wanke ta faki idanuwansu ta dauki wata matacciyar butar tsarkinsu ta Dora baki tafara kwankwadar ruwan da sauri sauri wani sanyin rahama na sauka cikin hanjinta ita batamasan wani abu qazantar ruwanba burinta dai su sauka a cikinta.


Fizge butar akayi da qarfi tareda jefarwa cikin masifa matar tasaka qafa ta tureta gefe tana cewa'"


Wannan yarinya wlh anyi muguwar mayya,

Yarinya saikace kafira ayita korarki Amma kullum saikin zo.


Kallon matar takeyi tanason yin kuka Amma Sam takasa sbd tunda ta taso batasan wani abu waishi so,qauna,kulawa ba ko gata bare tasan zafin rashinsu hartayi kuka.


Tunda tafara wayo daga ita sai kakarta kurma suke rayuwa a wani mataccen kangon shaguna wadda ita a wayonta batasan shin kakartace kokuma mahaifiyarta

Itadai tasan itace komanta gashi kurma ce bataji Bata iya mgn ga tsufa ahaka suke rayuwar Bara da yawon bola neman rubabben abincinda zasuci idan dare yayi sukoma shagunan dasuke kwana su kwanta duk da Basu kadai bane shagunan duk mabaratane da nakasashshi,


Koda iya tsohuwa tayi kwanaki kusan ashirin a kwance batada lfy tana gani tana kalla 'yarinyar ke fita yawon bola da bara tana ciyo abinci dame kyau da Mara kyau,

Wani lokacin ma idan ta ciyo Mara lafiya tana gani zatazo tayita amai da zawo Amma ahaka take sake fitarta tasake samowa Koda a bolar ne taci abinta,

Ciwo da yunwa da tausayin ganinsu ahaka yasa jikinta yin tsanani matuqa ahaka ta rasu batareda jamaa suna ankaraba ita Kuma batada wayon dazatasan meke faruwaba ahaka gawar tayi kwana biyu da yini take layin yafara daukar wani mugun wari wanda yasa sukasan akwai gawa.


ahaka kullum da daddare itakam take zuwa ta kwanta gefen gawar tayi kwanciyarta tayi bacci gari ya waye ta fita.


Koda aka gano gawar take suka Kira Yan sanda akazo aka bincika gawar suka tabbatarda rasuwa tayi ba wani alamar kasheta akayi suka kwashi gawar akai daji da ita acan aka binne a wata qaramar baqabarta.


Tundaga lokacin rayuwarta tasake gararewa sbd ankorosu daga waincan shagunan yanxu duk inda dare yamata acan take kwana saidai kasancewar shagon abincin alhajiyat na sabuwar anguwar data fado masu dafa Mata abinci anan suke kwana shago yasa itama ta fake anan bayan shagon take kwanciyarta tayi baccinta. 


Bayan qawace butarda matar tayi komawa tayi gefen shagon daga inda suke watso ruwa ta zauna tafara qoqarin bude gwangwanin Amma Bata iyaba takasa.


Kokuwa takeyi da gwangwanin tana saka farcenta tana budewa da qarfi Amma takasa sai jin tayi ankwace ta dago da sauri taga almajirin daya qwace Mata biredi ne da sauri ta miqe tana kallon gwangwanin hawaye na cikowa idonta tace"


Abuna ne kabani inaso"ta qarasa tana Kai hannu zata karba ya tureta ya juya da gudu Yana qoqarin budewa Shima.


Zaunawa tayi agurin tana hawaye daganan bacci yayi gaba da ita dama gashi yamma tafarayi.


Cikin bacci tasaki fitsafinta Wanda tsumman kayan jikinta suka shanyesa ko gangarowa beyiba.


Mangariba bayi ta farka tazo ta zauna gefen qofar shagon tana rarraba idanun samun Abinda zaa jeho waje.


Ahaka har akayi ishai qarfe Tara tayi Bata samu komaiba ta miqe tana Sosa kanta dake danqare da dau'da Takoma bayan shagon tayi kwanciyarta.


Gari ba wayewa ta miqe ta kama hanya neman Abinda zataci.



Yauma duk Abinda tasamu almajirin jiyane ya qwace Mata ya cinye Kuma duk inda tayi kusan Yana biyeda ita sbd ga dukkan alamu shi sabon zuwa ne kamar baisan ko inaba kamarma baisan ya ake hakurin yunwaba sbd shi komaima yasamu ci yakeyi gashidai Shima zasuzo sa'a daya danshima bazai wuce shekaru bakwai dinba.


Abun mamaki almajirin Nan saigashi gurinda take kwana Shima anan yake kwana idan gari ya waye tatafi duk inda tayi Yana biyeda ita.


Ganin haka yasa yanxu tana samun Abu take rabawa biyu tabasa Rabin tun bai qwaceba ya cinye.


Ahaka harsuka Saba sosai lokaci yaza sosai duk inda zasu tare suke zuwa harsuka samu wata roba a wata babbar bola da ita suke zuwa bara.


Yau Kam ranar babu wata sa'a acikinta sbd ko ruwan dazasu sakawa cikinsu Basu samuba duk inda sukace korarsu da hantararsu akeyi sbd bayan wari da zarnin fitsarin tareda tsamin dau'da babu Abinda sukeyi.


Kwanciya sukayi cikin bacci tafara jiyo sheshekar kukansa tayi saurin tashi zaune cikin tsoro ta kallesa tagansa zaune riqeda cikinsa.


USMAN?????? takira sunansa cikin sanyin maryar dake bayyanarda itama a galabaice take sbd yunwa.


Dagowa yayi ya kalleta da ido sharkaf da hawaye yace"


Amah cikina ciwo sosai.


Tashi tayi tareda kallonsa kafin ta juya tana cewa'"


Zansamo ruwa saimu sha.


Tana juyawa wasu manyan samari su biyu dake boye suka fito tareda toshe Masa baki suka dagasa cak suka wuce dashi suna zuwa motarsu suka bude da sauri suka jefasa da gudu suka bar gurin.



Cikin sanda ta Isa qofarsu alhajiyat ta dauko butarsu dake cikeda ruwa ta sidado ta dawo da sauri saidai tana zuwa taga babu usaman din cikin sauri ta ajiye butar tafara duddubasa koina tana Kiran sunansa.


Har kusan asuba Bata gansaba tadawo ta zauna shiru tareda qurawa robarsu ido,

Akaro na farko arayuwarta bayan iya tsohuwarta data samu wani arayuwarta Wanda taji ayau tanason karya tafi koina ya tsaya gurinta suyita yawon neman abinci atare,

Tasaba da usman sosai sbd a yanzu Koda Basu samu Abinda zasuciba sunada junansu damuwarsu kadance tunda suna debewa juna kewa.


Har gari ya waye Rana ta fito Bata gansaba tayi yawon duk inda suke zuwa bara tare Amma Bata gansaba ga yunwa ga gajiya ga qishirwa ga Rana haka ta dawo agajiye da daddare ta kwanta bayan Tasha ruwan butarsu alhajiyat.


Cikin bacci gaji motsin mutane tana bude ido taga wasu su biyu sunzo gefenta sun anjiye Usman din sun jiya da sauri sun tafiyarsu.


Da sauri ta tashi tana cewa''

Usman Ina kaje??


Bai motsaba sbd ko numfashi baya fitarwa

Ta juyoda fuskarsa tadan bubbuga tana sake Kiran sunansa har lokacin bai motsaba.


Ganin kamar bacci yakeyi yasa ta gyara Masa kwanciya tareda juyawa ta kwanta tanajin Dadi akaroro na farko a rayuwarta sbd usaman yadawo.


Koda gari yayi haske ta tashi har lokacin usman be tashiba ta dawo gabansa tana Kiran sunansa ya bude ido ya kalleta idanuwansa jawur jikinsa nata wani irin rawa atake taji tsoron ganinsa cikin yanayi da sauri tace' 

Usman menene? Kanajin yunwane haryanxu? Cikinka na ciwone haryanxu ma??


Ahankali ya nuna Mata duwawunsa Yana hawaye da dasasshiyar murya yace"


Sunmin wani abu anan zafi yakemin sosai''sai kawai ya fashe da wani irin kuka Yana dafe gurin sbd tsananin azabar dayasha agurin dasuka dannesa sukai amfani dashi.


Ganin irin kukan azabar daya keyi yasa itama tafashe da kukan ahankali musamman dataga jini a wandonsa tasan ciwone suka jimasa duk da basanma menene Abinda sukayiba.


Wasa wasa sai zazzabi ya rufe usaman sosai har jikinsa na wani irin mazari duk saita rude takamasa suka kutsa cikin kasuwa neman bara.


Suna shiga kasuwar taji wani me magani da lasifika Yana cewa'


Idan duwawunka ba ciwo baka iya miqewa bayan bahaya to kazo Muna mafaninka,

Idan kanajin fitsari baya fita sosai Shima kazo munada maganinka.


Da sauri taja hannun Usman dake tafiya a duduqe sbd ciwo da zazzabi sukazo gaban mutumin ta kalli maganinsa tana nunawa tace'"


Wannan zaka bawa Usman yaji ciwo a duwawu.


Kallonta me maganin yayi kafin ya kalli Usman da kyau Yana tauna goro da jajayen haqoransa ya washe baki tace'"


Ku kawo kudi' yana miqa musu hannu.


Kallon hannunsa sukayi kafin ta dago ta kallesa ta girgiza Kai alamar ita batamasan meyene ba.



Dari diyar ya fidda tareda nera dubu daya ya budesu ya nuna musu Yana cewa"


Kuje ku samo wannan ko wannan ku kawo nabaku magani yanasha zai warke.


Kallonsa tayi tana sake kallon kudin hannunsa kafin suka juya jikinsu a sanyaye sukabar kasuwar.


Kwana biyu jikin Usman babu wani sauqi gashi itama qarfinta yafara qarewa dole ta fakaici idon mutane da daddare tashiga shagon alhajiyat ta sato irin kudinda me magani ya nuna musu har guda uku.


Tana fitowa suka boye tunda safe suka shiga kasuwar neman me magani cikin saa suka Ganshi tabashi kudin duka tsabar zalinci saiya karbe duka dubu ukun yabasu canjin dari biyu tareda maganin Dan kanoma yafada musu su siya Koko susha dashi.


Kokon duka Darin biyu tasiya musu Usman yasha maganin ta shanye sauran kokon jikinta na rawa.


Dayake Shima Usman din harda yunwa dake cinsa yasa jikin tsananin 

Saigashi sun samu qarfin jiki bayan sun shanye kokon take suka kutsa kasuwa bara.


Da daddare yauma batada zabi bayan sake sato kudin 

Tunda safe suka sake siyan Koko yau harda qosai.


Sannu ahankali sata tashiga jikinsu 

Tun alhajiyat Bata ganewa ana Mata sata harta gane tafara saka ido sosai akan son kama barawon.


Cikin saa takamasu aikuwa tasa akayi musu mugun dukanda Saida suka fita hayyacinsu Kuma tasa aka koresu daga anguwar gaba dayama.


Wata sabuwar anguwa suka fada wadda tafi wadda suka baro hargitsi saidai wannan din 'yan ta'addane sukafi yawa acikinta sbd gasunan koina suna shaye shaye.


Cikin saa nanma suka samu wata tsohuwar makaranta suna kwana aciki sauqinsu daya makarantar nada megadi shiyasa sukejin saukin kwana.


Ranarda suka cika kwana shida a sabon gurin cikin dare suna dawowa wasu maza biyu suka taresu.


Saurin riqe hannun juna sukayi suna ja da baya sbd yanzu sunfara wayo sosai.


Damqo amatu dayan yayi da qarfi Yana cewa'"


Kai saketa ka ware daga Nan gun.


Dayan hannunsa yasa yaqara riqeta Yana girgiza Kai alamar aa.


Wani wawan Mari dayan ya sakar Masa Wanda yasashi ihu. 


Suka toshe masa baki tareda matsesa 

Shikuma dayan ya fizge amatu tareda kwantarda ita qasa da qarfi.


Kuka tasaki tana miqawa Usman hannu tana Kiran sunansa itama da sauri dayan ya rufe Mata baki Yana qoqarin cire wandonsa.



Kuka sukeyi duk su duka musamman Usman dayaga irin Abinda akai masane zaayiwa amatu Kuma ya dandani tsananin azabar hakan bazai Bari amatu ta dandana ba.

#mamuh.



#Zafafa biyar#


Saran boye

Billyn Abdul


Abin dake zuciyata

Hafsat rano


Kibiyar AJALI

Miss xoxo


Siradin rayuwa

Safiyya huguma


Min qalb

mamuhgee


Pay@

09033181070

Or 

09032345899

[3/2, 2:25 PM] Zafafa: _*MIN QALB*_

_Mamuhgee_


2


Bazai iya ganiba 

sunaji suna gani qaton saurayin yake kokarin keta rayuwarta dabata gama sanin ciwon kantaba,

Ita kukan datakeyi dannewar dayayi Mata akan duwatsu suna cin jikinta

Shikuma Usman kukan zabar dayasha yake tunowa itace zaayiwa amatu Wanda sanadin hakan sunzama 6arayi dole da qarfi da yaji.


Qoqrin bude qafafuwanta qaton keyi 

Usman yayi wani yunkuri tareda kama hannun Wanda ke maqure dashi ya sakar Masa mugun cizo Mai qarfi da haqoransa dasuka gama bushewa da dau'da.


A gigice yasakesa Yana yarfe hannu sbd azabar cizon.


Wani qaton dustsi Usman din yadauka baiyi wata wata ba ya buga akan qaton dake kan amatu 

Take ya sulale gefe kansa na tartsin jini sosai ko ihu daya beyiba ya zube agurin Yana wani irin Shure Shure.


Suna ganin hakan wani irin tsoro yashigesu da gudu ya kamo hannun amatu Yana cewa'"


Zo mu gudu amatu.


A firgice dayan ya riqesu Yana cewa'"


Kun kasheshi....a kidime yake fadar hakan cikin tsananin tsoron ganin abokinsa na Shure shuren mutuwa.


Qoqarin jansu yakeyi Yana cewa'"


Wlh police zan kaiku Kun kashesa,

Bazaki guduba ku barni cikin masifa akamani.


Jansu yakeyi da qarfi cikin firgici da tashin hankali suna kuka sosai suna rokonsa ya sakesu Amma Shima a rude yake kansa zai wanke kota halin Yaya.


Irin kukan dasukeyi Basu taba yinsaba arayuwarsu sbd jin wani ya mutu sbd su Kuma Suma kashesu dayan sukaji yanacewa zaayi.


Sosai suke kuka suna rokonsa ya sakesu Amma ko jinsu bayayi Dan Shima kusan kukan yakeyi na tsoro da firgici.


Wata qatuwar gora daga bayansu aka kwadawa qaton a tsakiyar Kai 

Ya tsaya cak tareda sakin hannuwansu Yana qoqarin juyawa yaga ko waye ya yanke jiki yafadi jini nafita a qeyar kansa.


Jikinsu na rawa cikin tsananin tsoro da firgici suka juyo suna qanqame hannuwan junansu tareda ja baya suna kallon qaton dashima yake Shure Shure.


Cikin sauri megadin makarantar ya matso gabansu tareda riqo hannuwansu yasaka musu kudi Yana waige waige Yace"


Kuyi gudu sosai kuje can qasan layin gaban kasuwar baya akwai makarantar almajirai ku shige cikinsu ku kwanta ku boye zanzo idan ankwana biyu

Kuyi sauri karku taba dawowa tanan 

Kuyi sauri kuje..


Kallonsa sukeyi suna sake sakin sabon kuka sbd sunqara firgicewa da Abinda yake fada,


Yaturasu Yana cewa'"


Kuje kuje kuyi sauri karku dawo.


Gudu suka Fara suna waiwayensa sbd akaro na farko da wani ya taimakesu arayuwarsu.


Tun suna waiwayensa harsuka bace suna gudu cikin Daren gashi yace karsu hau titi subi kwana kwana.


Koda suka Kai makarantar almajiran dare yayi sosai gashi karnika sai haushi suke musu duk inda sukabi.


Suna kaiwa bakin makarantar suka tsaya suna rarraba idon Ina zasu boye sbd almajiran gasunan kwance birjik a fili kowa da matacciyar tabarmarsa wasu Kuma da kwalaye wasuma hakanan suke kwance a qasa ga cinnakai da qwari da komai Amma ba ruwansu kwance suke abinsu suna bacci.


Hanunta usman yakama suka qarasa can qarshe yacire matacciyar rigar jikinsa data gama yagewa ta mutu ya shimfida musu suka kwanta kowannensu jikinsa na rawa numfashinsu na fita da sauri sbd tsananin tsoron dasuke ciki.


Asubar fari dukkanin almajiran aka tadasu suyi sallah 

Wanda wannan shine karo na farko dasuka tabayin sallah Shima Suma dai sunyi yanda sukaga kowa nayi gurin bin Abinda malam yayi.


Ana gama sallah kowa yadauko allonsa Yana bita.


Gari yafara haske sai sukaga almajiran na kallon amatu cikin mamaki suna kallon kanta Wanda gashinta ke butu butu da dau'da da qazanta Wanda yake son nuna ita mace ce.


Daga dama sukaji wani almajiri yace"


Kai wallahi idan malam yazo yaga mace dukanku zaiyi wayace mace tana zuwa Nan?hmm

Korarki ma malam zaiyi yanzu Yana fitowa.


Usman najin kora ya kama hannunta suka miqe anabinsu da kallo suka fice  a sanyaye.


Harsunyi nisa kadan yatuno da maganar kawu megadi na cewa karsu koma yayi saurin juyawa da ita Yana kalle kallen inda zasu fake Kuma.


Ganin har yamma tayi suna gararin gurin zuwa yasa ya lalubo kudinda kawun yabasu yaje shagon dake kallon inda suke yasiyo Rezar nera ashirin yadawo yajata suka zagaya bayan wani gida Yana cewa'"


Amatu zo muyi aski irin nasu almajiran malam saimu koma cikinsu tunda bamuda wani gurin.


Haka ta zauna yahau yimata aski

Saida ya aske kan tas Wanda duk kusan Rabin kan ya yayyakenta sai jini ke fita kadan kadan Amma Sam Basu damuba Shima sama sama yayi nasa askin rabi yayi rabi beyiba suka dunkule Rezar sbd gaba suka koma makarantar dama kayan jikinsu duk riga da wandone dasuka gama yayyagewa suka sauya kamanni.


Dayake makarantar ba qa'ida sukebi ba take malam ya kaebesu yaga sabbin alamjirai aka Basu tsoffin allon karatu take suka shiga sahun almajirai batareda kowa yasan cewa amatun mace ceba Koda malam ya tambayi sunayensu sukace Usman da amadu.


Ahankali suka Saba da rayuwar almajiranci duk da akwai wuya Amma tafi musu rayuwarsu ta baya dansu yanzu ganin sukeyi sunyi gata.


Akai akai Usman kemata aski sbd kar gashinta yafito musamman sbd tanada saurin tsirowar gashin,


Sunsaba idan sungama ayyukan gidan malam akayi karatu aka gama su fita yawon bara sai yamma sudawo karatun yamma sannan sufita barar dare daga Nan Kuma dare nayi zuzo su kwanta.


Yanzu suna samun yin wanka a sati ko so dayane shiyasa suka Dan Fara canzawa.


Tun suna qirgen kwanakin zuwan kawu megadi harsuka daina suka koma qirgen kwanakin zuwansu har lissafi ya batar musu.


Ko ayanxu dasuke cikin inuwar almajiranci abun dai 'dayane shine idan baka tsayawa kankaba Kaine a qasa ko yaushe,


Sunsha gwagwarmaya zamansu makarantar malam din,


Idan anyi sata su ake maqalawa,

Barna sune,

Laifi sune,

Hatta laifin cikin gidan malam su ake maqalawa shiyasa sunfi kowa azabtuwa sbd irin dukan da malam da ya manyan yaransa suke musu,


Shatin buloli ajikinsu yazama tamkar zanen fatarda aka haliccesu da itane,


Tun suna kuka a almari harsun qame sun daina sbd ganin rayuwar ahaka take koina na sama ya danne na qasan.


Duk hutunda akeyi sukam basa zuwa koina sbd basuda gurin zuwa shiyasa rashin tausayinsu yafi yawa sbd ansan ko an zalincesu basuda me tsaya musu.


Ahaka dai rayuwa taja tsananin rayuwa Yana qara musu yawa musamman yanxu da amatu take Fara nonuwa kullum cikin boye boye suke gashi yanxu abubuwan naqara tsanantar musu ne gashi amatu ko mgn batayi sosai da qarfi da yaji suke boyon mganarta kar agano mace ce.


Yanxu dasukayj wayo Usman shine me wahalar Abinda zasu ci duk da tare suke zuwa duk inda zasu gashi baqin jini tamkar a jininsu yake sbd duk inda sukaje tsanarsu da kyararsu akeyi shiyasa suka riqe aransu duniya kowa kansa kawai yasani basuda Abinda yafi musu junansu.


Wani hutu da akayi kamar daga sama saiga kawu megadi Wanda tuni suka Fara mantawa da kamanninsa,


Farin ciki da murnar dasukayi kamar shine danginsu da basuda musamman dasukaga yazo musu da gari kusan kwano buyi jikinsu har rawa yakeyi gurin yimasa godiya.


Amatu ya qurawa ido musamman kanta dake aske tas Yana qyalli ga wasu qananun quraje a jikinsu zuciyarsa na susa yaji dukkanin kuzarinsa ya karye sbd tabbas duk da baitaba haihuwaba ita 'ya mace ce bazaa jima ana boyeta ba amatsayin namiji.


Dazai tafi yasiya musu gwanjo kowannensu riga da wando masu Dan dama dama.


Tun daga lokacin yake Dan zuwa akai akai Yana dubasu sai rayuwar tadan Fara yimusu sauqi.


Awani zuwa da yayi

Baizo da niyar tafiya dasuba Amma atake tunaninsa ya sauya akan amatu sbd girma daya Fara zuwar Mata gadan gadan Yana tsoron amatsayinta na mace ta abalage acikin maza.


kallonsu yayi bayan sun zagayo bayan makarantar cikin karyewar zuciya Yana jinjina rabasun dazaiyi yace"


Usman kaga amatu tafara girma akwai hadari abarta cikinku anan..


Kallonsa sukayi atare cikin rashin fahimta.


Gyara tsayuwa yayi yace zantafi da ita zan kaita gurin me 'dakina idan yaso Kai saika riqa zuwa Mana hutu.


Atare suka girgiza Kai itada Usman din suna kallon juna idanuwansu na cikowa da hawaye.


Nasan zaa rina yafada cikin ransa Yana kallonsu zuciya a karye.


Kamo hanun Usman yayi yajasa gefe ya fahimtar dashi sosai ta yanda zai gane Abinda yake nufi 

Harya gane Yakuma amince sbd har abada bazaiso Abinda zai samu amatu ba.


Daga haka suka hakura sunaji suna gani suka rabu da juna kawu yatafi da su kafin daga baya Usman yadawo makarantar malam.


Tunda amatu tadawo gidan kawu Bata taba haduwa da tsangwama ba saidai Kuma babuwa wani janta ajiki da iyami tayi.


Basuda qarfi sai rufin asiri da haka malam yasakata primary school dinda yake gadi wadda tuni aka maidata 'yar maigadi.


Usman shekara daya yayi batareda itaba ya tattara karatun yadawo gidan kawu Yana kwana a soro komai tsananin sanyi da zafi kuwa.


A haka kawu yasamar Masa aikin tsaron gidan wanka da bahaya a Tasha har Shima yashiga primary 2 

Yana shiga primary 5 ya tattara karatun ya ajiye sbd gwagwarmayar rayuwa.


Kawu da iyami sune gatansu na farko,

Kawu da iyami sune wainda suka cirosu daga bola suka basu sunanda ake kallonsu da daraja ayanzu.


Shekakarda tashiga js 2 a shekarar suka shiga wata sabuwar masifar da akayiwa kawu sharrin satar cire winduna da qofofin makaranta ya siyar.


Duk inda ake zuwa roqo da Kai kuka sunkai akan alamarin Amma Abu ya agagara qarshe dpo nunawa yayi sai idan ita amatu kokuma matar kawun zasu kwana dashi tukuna zai taimakesu.


Akaro na farko da amatu ta tsani maza da taimakonsu.


Ranar dukkaninsu kwana sukayi kukan baqin ciki sunaji suna gani akayi gidan yari da kawu hukuncin shekara biyu dama Kuma abin hadda gayya sbd Shima alqali yaso amatun tabasa hadin Kai sbd irin wankewa da jikinta yayi gashi fatarta Ashe me irin hasken Nan ce ga jikinta daya gama fitowa ana mace tsaf yanzu iyakaci qarasa balagewa ne dabatayiba a cikakkiyar mace.


Tunda akayi gidan yari da kawu alamarin duniya yasakosu gaba ko abincinda zasuci ya gagaresu dole Usman ne yanaji Yana gani yake fita gwagwarmaya Amma sai ahankali.


Wata bakwai da zuwan kawu gidan yari aka koresu daga gidan dasuke suka rasa gurin zuwa ga iyami Dan cikinsa take dauke dashi wahala tasaka ya bare ko kudin asibiti basuda.


Akaro na farko da Usman yakoma sata kenan arayuwarsa ya kama musu daki buyi a wani gidan haya me dakuna goma reras a jere kamar shaguna,

Gidanda ya hada mutane dabam dabam masu halaye dabam dabam.

#mamuh#


MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

Post a Comment

0 Comments