TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 30-31

 _MQ 30_*





Wani irin sanyin farin cikine ya Shiga zuciyarsa Wanda ya manta rabonsa dashi ya kalli kawun cikin girmamawa yace"


Nagode sosai kawu 

Allah yaqara girma da Nisan kwana.


Amin Amin" yace Yana cigaba da yimasa nasiha akan hakuri da rayuwa komai lokacine dashi wata Rana komai zai wuce.


Bai jira sake ganin Amatunba yanayin sallar ishai a masallaci taredasu kawu yayi Masa Saida safe ya wuce.



Ahanya ya tsaya ya siya cardigan me kauri da sabon bargo me laushi kafin ya wuce gida.


Sbd sanyi hatta qafaguwansa da hannuwansa Saida ya sakawa socks bayan yasaka rigar sanyin ya dunqule cikin bargo Amma har lokacin yanajin sanyi na shigarsa hakanan ya daure har wahalallen barci ya daukesa.



Washe gari da safe ba laifi da kuzarinta ta tashi saidai kawai sauyi sosai data gani daga iyami har kawu Wanda ya tabbatar Mata da fushi sukeyi sosai da ita sai taji hankalinta ya tashi duk yanda taso Basu hakuri ko fuska taqi samu Saida Dr khalil yashigo ne taga sakewar fuskarsu ta kallesa da Ido ta nuna Masa fushi sukeyi da ita yasakar Mata kyakkyawan murmushi Yana nuna Mata Babu ruwansa

Suna Nan zaune saiga salman zabeera yazo Yana ganin Amatu cikin tsananin farin ciki yaqaraso Nan aka hau sabuwar fira inda anan ne takejin dukkanin Abinda yafaru hadda komai da Khalil din ya rasa bayan aikinsa da asibitinsa baida komai yanxu.


Jitayi sabuwar soyayyarsa tasake shigarta hartanajin ko bayada komai zata auresa ta zauna dashi Kuma alqawarine ta dauka saita shiryasa da familynsa ta maidasa cikinsu.



Koda maganar aurensu sati me zuwa ta bayyana tuni kowa yahau murna Nan aka Fara shirye shirye musamman iyami data bada himma gurin gyaran Amatun ga umminsa ma kusan kullum saitazo gurin duba Amatun taso taimakawa sosai Amma Khalil ya nuna kada tayi Masa komai zai iya iya qarfinsa shiyasa Dole tabari sai itama ta maida hankali gurin gyaran Amatun sbd 'danta yaji Dadi.



Sauran kudaden dasuka rage Masa yaso Kama wani gidan hayar dasu Amma duk gidajen babu Wanda zasu iya zama saiya aje kudin da niyar bayan daura auren Koda da sati biyune zaiyi qoqarin hada kudaden dazasu Samar musu gida me Dan kyau.


A bangare daya sanyi yayiwa jijiyoyinsa da qashinsa muguwar shiga a 'yan kwanakin sbd yanxu takai kowane dare Baya iya bacci daurewa kawai yakeyi cikin mutane baya nunawa Amma ciwonsa yatashi matuqa yanajin yanda lungs dinsa sukai mugun laushi baya iya Jan numfashi yanda ya kamata duk iya qiqarinsa yanayi Dan ganin ba'a fahimci halinda yake cikiba.




_GERMANY_


Kallon hoton katin Daurin auren da Khalil yaturo masa yakumayi da fararen idanuwansa dasukai wani irin laushi lokaci daya ya lumshe ido Yana sake kallon hoton katin ya ajiye ahankali tareda miqewa ya nufi gaban qaton window din dakinsa dake kallon swimming pool din gidan ya zuba hannuwansa cikin aljihun three quarter din dake jikinsa Yana qurawa waje Ido zuciyarsa na sanyi.


Tunani zuciyarsa keyi Amma ya yakuce hakan Yana lumshe ido 

Tabbas zai halarta sbd ranar farin cikin Dan uwansa ce.


Juyowa yayi ahankali tareda dawowa yadauki wayarsa daya kashe sbd rashin son damuwa ya dannawa PA dinsa Kira Yana dauka Kai tsaye cikin muryarsa me sautin girma yace"


Ka shirya Mana komawa gida jibi akwai Daurin auren dazan halarta.


Done sir.


Kashe wayar yayi ya ajiye Yana sake karanta sunan dake rubuce 6aro 6aro akan hoton katin KHALIL DAHEER ZABEERA da AMATULLAH K SALEH.


sake dauke Kai yayi yana lumshe ido tareda sauke ajiyar zuciya ya juya yabar gaban labtop din.




_NIGERIA_


da kanta ta shirya tsaf Babu Wanda yasani ta fito suka fita da salman zuwa zabeera mansion.


A sashen Andi sukai parking tafito ahankali tana kallon koina komai na dawo Mata sabo tana tuno yanda tabar anty zarah dinta cikin kuka da damuwa take taji idanuwanta sun ciko da hawaye Bata damu da tsaidaduba Saida suka gangaro tasaka hannu ta gogesu ta nufi qofar shiga palon Andi din ta tura tashiga da sallama dama Salman ya tabbatar Mata da a irin wannan lokacin Modibbo na gurin Andi.


Modibbo ne yafara gabeta ya zuba Mata idanuwansa masu kwarjini da Khalil da MD suka dauko ta qaraso ahankali ta zube qasa gabansu sai alokacin Andi ya dago ya lura da waye.


Cikin tsananin biyayya da nuna damuwarta a fili tace"


Ina miqo gaisuwata ga Andi da Modibbo tareda neman afuwar babban kuskuren Dana aikata Wanda ya shafi 'da mafi biyayya da gujewa zuciyarku.


Kallon mamakin rashin tsoronta da gwarin gwiwarta suke Mata su duka din ta sauke Kai cikin nutsuwa da girmamawa tace"


Wallahi tallahi Dr khalil zabeera baitaba aikata laifin da kuke tunanin ya aikataba koma wane irine,


Taimako ya hadani da Dr khalil Kuma shine yasa yayita ajiyata acikin zabeera,


Ni marainiya ce kuma Yar bola kamar yanda kowa ke fada Amma Kuma banice nakai kaina bolarba harnayi rayuwa acikinta na tashi acikin

Rayuwa da jarabawar rayuwace takaini wadda itace tabaku girma da matsayi tareda sunan dakuke ganin yafi Dan Adam daraja,


Nayi rayuwar maraici da tozarci irinku masu arziki Baku dubemu ba kuka taimaka Mana saidai maigadin makarantane Wanda yake karban dubu bakwai a wata ya taimakemu,

Nayi rayuwar almajiranci Ina matsayin mace sbd kawai na rayu,

Nayi rayuwar wahala da qasqanci duk Dan sbd na rayu,

Munkwana da yunwa muntashi acikinta,

Lokacinda yaranku da jikokinku suke karatu mu bara mukeyi alokacin sbd muci,

Da kaina na koyi yanda zanyi yaqi da maza na qwaci kaina daga sharrinsu tun inada qananun shekaru

Shin nayi dukkanin wannan ne sbd nazama karuwa a rayuwa????


Nice na zabarwa kaina yin sata amaimakon karuwanci Dan kawai na rayu sbd sata Zan iya rokon me Abu ya yafemun wata Rana Amma Zina fa???


Dr khalil zabeera shine mutum me arziki na farko daya shigo rayuwarmu,

Yakawo Mana walwala da farin ciki a zukatanmu,

Talakawan bangarenmu wainda Dr khalil zabeera yakawo farin ciki akan fuskokinmu da rayuwarmu basa qirguwa,

Meyasa mutum me zuciya irinta Khalil maimakon ayi alfahari dashi za'ayi fushi dashi?

Shin Kuna tunanin ladar aikin Khalil kawai Bata Isa takawo qarin haske da walwala acikin zabeera ba??


'yayan da Allah yabaku dukkaninsu amanace agurinku Allah zaitambayeku alaqarku dasu idan da akwai cutatarwa,

'yayanku ne Amma Kuna gudanar da rayuwarsu kamarta dabbobinku kokuma bayinku,

Wasunsu da dama a tauye suke basa rayuwar farin ciki,

Zaman auren Dole da qunci sukeyi duk sbd bin umarni da qaidojinku,

Shin haramun ne neman farin ciki a wani gurin kokuwa musulunci ne ya hana?


Shi mutunci da girma Allah ne yake badawa Kuma shiya Baku 

Idan Allah yabaku suna duk Abinda wani Dan Adam zaiyi bazai Bata hakanba Koda kuwa me zaiyi.,


Nazo zabeera ne sbd son kudina dakuma rashin sanin ciwon kaina Amma sbd tseratar da mutuncinku yasa ya karbi laifi da bacin sunan da baisan lokacinda aka hadosaba,


Wallahi niba karuwa bace,

Bantaba aikata zinaba,

Bansan ta Yaya ake aikataba,

Aikin gidajen abinci danayi nayine Dan neman halak Dina Wanda haryanxu Ina alfahari da hakan sbd Allah bai bani matacciyar zuciya ba.


Dagowa tayi da idanuwanta dasukai jajir ta ajiye katin Daurin aurensu cikin sanyin jiki tace"


Babban burinsa shine aurena yakawoni gabanku Dan neman yafiyarku da gafararku nikuma babban burin danakeson cika masa shine bashi kaina amatsayin mata dakuma sasantawarsa daku iyayensa,


Hawaye masu tsananin zafi suka gangaro Mata cikin daci da damuwa tace"


Dan Allah Ina roqan gafarar ku yafe Masa kodan kasancewarsa 'da me biyayya da gudun zuciyarku a baya,

Ku basa farin cikin dabai taba samu daga garekuba tun haihuwarsa....


Umme dake bayanta tuntuni a tsaye batasan lokacinda tafashe da kukaba tana sake Jin qaunar Amatu ta qaraso gabansu Modibbon ta zube itama cikin kuka tace"


Andi Dan Allah ku yafewa khalil kubarsa ya aureta wlh dukkaninsu ba laifinsu bane nice me laifin sbd nice na kawo Amatu zabeera da wata manufarda rashin wadataccen ilimina yabani.


Zayyane musu komai tayi sukai tsit Babu me motsi musamman Andi dashi maganganunsa Amatu ne sukafi shigarsa,

Shin dukkanin yawancin 'yayansu rayuwar kunci sukeyi sbd gudun zuciyarsu???



Tabbas tunda yake tsawon rayuwarsa Babu Wanda yataba kallonsa yafada Masa haqiqanin gaskia sai yau yaringa qanqanuwa daya Isa haihuwar ubanta koma kakanta ta kallesa tafada Masa quncin dayake saka 'yaya da jikokinsa shekaru wa shekaru.


Modibbo Kam dama tuni Amatu ta Dade dashiga ransa bazai iya nunawa bane sbd bacin ran Andi Amma tuni yajima da sanin yarinyace me fadar gskia batareda tsoro ko shakkaba.


Miqewa tayi ahankali ta juya ta fice tana share hawayenta daketa fita da gudu ta fada mota suka bar zabeera.




Kwance yake yau kwana biyu kenan ciwonsa nacinsa harya Fara cin qarfinsa ko fita daqyar yakeyi sai dare cikin duhu yake zuwa gidansu kawu sbd kada agano halinda yake ciki magungunsa yasiyo dasu inhaler Amma Sam kamar basa Masa aiki sbd kullum sanyi sake shigarsa yakeyi a gidan.


Yau laraba saura kwana daya Daurin aurensu Amma abin yaci qarfinsa tuni aka gano baida lafiya sosai sbd Koda Ibrahim yaje gidan tuni ya Dade da fita hayyacinsa hankali tashe ya kwashesa sai asibiti.


A asibiti Koda aka karbesa numfashinsa yayi nisa sosai cikin gaggawa akai emergency dashi ana qoqarin saka Masa oxygen.


Su kawu Ibrahim din yafara fadawa kafin yakira salman yafada Masa cikin qanqanin lokaci duk suka halarto asibitin hankalinsu duk atashe.



Kallo daya Amatu tayi Masa hankalinta yayi mummunan tashi sbd lokaci daya sanyi ya kumburasa 

Numfashinsa Sam kwata kwata Babu saidai oxygen dinne ke janyo Masa ahankali idanuwansa a rufe fuskarsa tayi haske hakama bakinsa yayi haske sosai ya bushe.


Hawaye ne suka kufce Mata ta saki siririn kuka ahankali tana cewa''


Meyasa zaka boye bakada lafiya harsaida abin yayi tsanani haka?


Zaman rashin hankalin kurame sukeyi a asibitin daga ita har kawu da iyami duk suna asibitin da salman sai ummensa dasu Nuratu dasuka iso kowa cikin tashin hankali bama kamar umme datasha kuka idanuwanta sukai jajir.


Sunanan zaune har magriba saiga anty zarah da MD ZABEERA sun iso tana ganin anty zarah suka tsaya kallon juna cikin tsananin kewa da qaunar juna tazo da gudu tafada jikinta tana fashewa da sabon kukan datake ta riqewa tuntuni na ganin har lokacin sai Abinda yayi gaba ajikin nasa.



MD ne dakansa yaje yayi mgn da likitocin suka sake yimasa bayanin sanyine yayi mugun shigarsa Wanda yasa gaba daya jijiyoyin huhun Jan numfashinsa sun daskare ya tayarda ciwonsa gaba daya harya basa attack Sam numfashinsa yaqi dawowa ta oxygen dinma alamarin sai ahankali.


Tsorone yashigesa akaro na farko rayuwarsa 

Dawowa yayi dakinda Khalil din yake ya tsaya akansa Yana kallonsa yaji zuciyarsa na neman karyewa da sauri ya juya fice.


Anan ta kwana asibitin itada ummensa da iyami har gari ya waye be farkaba zuwa lokacin Kam ko mgn basa iyayi da junansu sbd damuwa zazzaune kawai suke suna rarraba idanuwansu dasuka kode sukai zuru zuru.


Da yamma tayo alwalar magriba tazo gefensa ta tayarda sallah tayi tagama tana cikin addua taga kamar ya motsa hannunsa kadan ko shafa adduar batayiba ta zabura ta miqe sai taga idanuwansa a bude sunyi fari tas dasu cikin tsananin farin ciki ta fada kansa ta rungumesa tana sakin hawayen farin ciki.


Umme data fito toilet din dakin tana ganin haka tayo kansu da gudu har sanyin ruwan qafarta na zameta itama fadawa tayi kansa ta rungumesa 


Ya lumshe ido ganinsu su biyun ba qaramin farin ciki yasashi ba yasake lumshe ido cikin azabar ciwo yanason motsawa Amma sun dannesa 


MD daya shigo yayi gyaran murya itace tafara juyowa sukai Ido biyu tayi saurin dauke Kai tana maido da kallonta Kan Khalil cikin tsananin farin ciki tace"


Dr Dan Allah karka sake rufe idonka.


Qarasowa yayi ahankali Yana kallon fuskar Khalil din yau farin cikinsa dai Kam ya bayyana 

Shima Khalil din shi yake kallo fuskarsa nason bayyana farin cikin ganinsa Amma azabar ciwo ya hana.



Cikin sautin murya me taushi yace"


Kun sakar Masa nauyi da yawa inaga.


Da sauri dukkaninsu suka dagasa kafin suyi wata Magana saiga Andi da Modibbo tareda alhaji qarami sun shigo salman yakawosu take umme da amatun suka saki hawayen farin ciki suna kallon fuskar Khalil din da idanuwansa suka nuna zallar farin ciki ganinsa hawaye masu dumi suka gangaro ta gefen idonsa

Andi da kansa ya matso gefen gadon ya dafa kansa yasaka tissue ya share Masa Yana jinjina Masa Kai.



Salman da MD ne suka tayar dashi zaune amatu ta hado ruwan zafi da towel suka gyara Masa jikinsa tareda Sanya masa shirt Mara nauyi aka basa tea yasha kadan har lokacin da oxygen a hancinsa Kuma har lokacin bai iya mgn sbd bai iya jan dogon numfashi.


Kafin dare yadan warware ba laifi sbd Yana Dan magana ahankali tareda zuwa toilet idan ankamasa.


Da kawu yaso daga Daurin auren a gobe Amma Andi yace abarshi kada a daga tunda anriga anyi sanarwa.


Da daddaren ranar duk yanda ta nace hanata kwana asibitin akayi akace Takoma gida Salman zai kwana dashi tunda washe garine Daurin auren Dole ta koma bayan tayi Masa bankwana yabiya da Ido cikin kewarta tun Bata wuce dinba.



A gida duk wani hidimar al'ada sunyi abinsu hatta lalle anyi Mata a blue fox anty zarah takaita akayo Mata tareda gyaran Kai dana jiki Daurin auren kawai suke jira a goben akaita zabeera.


Tunda ta kwanta mafarkin Dr kawai takeyi sai kawai ta tashi tayo alwala tazo ta tayarda sallar nafila.


Tunda gari ya waye takejinta batada qarfin jiki sbd barin gida dazatayi.,


Qarfe daya da rabi dubban JAMA'A suka shaida Daurin auren KHALIL ZABEERA da AMATULLAH SALEH Wanda ya bayarda tarihi me girma sbd itace mace ta farko da aka auro daga waje.


A asibiti dagashi sai MD ZABEERA ne Wanda yace zai zauna dashi tunda kowa na gurin Daurin auren.

Bacci yakeyi sbd alluran da akai Masa bada jimawaba sbd jikin daya dawo Masa sosai.,


Bayan Daurin auren JAMA'A duk asibiti sukaita zuwa dubasa sai yamma lilis ya farka cikin ikon Allah saiya tashi da qarfin jiki haryana iya Magana tana Kuma fita sosai.


Wanka MD ya taimaka Masa yayi ya sanya farar jallabiyar datai Masa kyau matuqa yayi sallolin da ake binsa yazauna kenan saigasu umme da Nuratu wadda idanuwanta sukai luhu luhu sbd kukan data kwana tanayi.


Abinci ta zuba Masa ta zauna gefensa ta miqa Masa kanta a sunkuye batareda ta kallesaba.


Karba yayi tareda sauke numfashi cikin sanyin muryarsa dake fita ahankali yace"


Nuratu inshallah zaki samu Wanda zai wadata rayuwarki da farin cikin Dana kasa baki.


Kallonsa tayi idanuwanta na cikowa da hawaye murya na rawa tace"


Meyasa kakeson Amatu???


Lumshe idanuwansa dasuke a 'dan galabaice ahankali yace"


Allah ne yasamin sonta fiyeda komai

Kuma Ina fatar zaki qaunaceta kodan sbd ni.


Murmushi me ciwo tasaki hawayenta na sake gudu tace"


Zangwada.


Murmushi shima ya sakar Mata tareda juyowa ya kalli MD dake amfani da wayarsa yace"


Kaifa MAHMOUD???

Zaka gwada qaunar matata ko Dan sbd ni?


Juyowa yayi ya zuba Masa idanuwansa batareda yace qala ba.


Abinci umme ta matsa Masa ahankali yaci kadan Tasha tea me zafi har zufa yadan karyo Masa aka kunna Masa AC kadan.


Ganin yanayin jikin nasa dakuma shi kansa daya nema sallama yasa suka sallamesa bayan sallar magriba zuwa ishai Koda suka Isa zabeera daidai isowar motacin dasuka je dauko amarya Amatu.


A gurin Andi aka kaisu duk su duka yayi musu nasiha sosai kafin aka wuce da ita gurin zamanta wato sashen Khalil din Wanda aka sauyawa komai sabo.


Iyami da kanta taredasu maman junior suka kawota har cikin dakinta suna jinjina arzikin duniya irin na familyn ZABEERA kafin aka maidasu gida.




Ahankali yashigo dakin datake zaune zugum bakin gado tana tunanin da batamasan tanayiba...


Ji tayi anzauna kusada ita ahankali ta juyo sukai Ido biyu dashi gabanta taji yafafi ahankali ta dauke Kai zata sunkuyar ya riqo fuskarta ahankali tareda girgiza Mata Kai ya rungumeta cikin jikinsa ahankali tareda sauke ajiyar zuciya batareda yace komaiba.


Sunjima ahaka kafin ya saketa tareda cewa ta tashi suyi nafila.


Tashi tayi Babu musu sukaje toilet din tare sukayo alwala suka fito yakama hannunta suka nufi dakinsa.


Bayan sungama sallar hannunta ya riqo cikin nasa ahankali yace"


Zakici abinci ko wani Abu?

Akwai abinci da umme da antynki suka kawo gashi can a dining.


Dagowa tayi ta kallesa ahankali kafin ta girgiza kai.


Murmushi yasake ganin yau itama tazama kurma kamarsa tunda yafara ciwon baya iya doguwar Magana.


Miqewa yayi tareda tayarda ita tsaye Yana zame Mata mayafinta kyakkyawar fuskarta ta bayyana da kyau cikin qarfin hali yace"


Alhamdulillah.


Sunkuyar dakai tayi tana qaqalo murmushi ya janyota ya sanya cikin jikinsa ya rungumeta Yana lalubar zib din goguwar rigar Julius Holland din dake jikinta me laushi ya bude rigar ta Fadi qasa tabarta daga ita sai farar bra din dake jikinta da farin under.


Saurin rintse ido tayi zata durqushe ya tareda tareda rungumeta cikin jikinsa baida qarfin jiki sbd ciwo Amma hakanan ya cirata tana qanqamesa ya kwantar da ita Kan lafiyayyan gadonsa tareda rage hasken wutar dakin ya zare jallabiyarsa ya hau gadon ahankali tareda jawota jikinsa Yana kallon fuskarta ya Dora bakinsa akan nata tareda 6alle hook din bra dinta Yana cillowa qasa.




Qarfe ukun dare taringa Jin wani irin Nishi sama sama cikin kunnuwanta ta bude idanuwanta ahankali tana kallon inda take saita tashi zaune da sauri tana kallon gefenta a firgice tagansa numfashinsa na qoqarin daukewa cikin tsananin firgici ta diro gadon ta zagayo gabansa tana Kiran sunansa cikin tashin hankali Amma Sam tayi nisa a kidime ta janyo jallabiyarsa ta zura sbd itakadaice zata shigeta alokacin sbd firgici 

Sam Bata damu da tsakiyar darene ba ta fito da gudu tayi hanyar sashensu anty zarah dake kusa da nasu a kidime tahau buga musu kofa tana Kiran sunan anty zarah da qarfi.


MAHMOUD dake zaune daram acikin Daren yakasa ko rintsawa sbd tsananin ciwon Kai yafara jiyo bugun qofar ya sauko daidai itama zarah tafito daga dakinta Dan taji bugun qofar itama.


Shine yafara cewa"


Waye??? ta jikin qofar


Cikin sauri da tashin hankali tace"


Nice Amatu Dan Allah kuzo Dr ne......


Tun kafin ta qarasa ya bude qofar yanayin datake ciki yasashi Kama hanyar sashen nasu batareda tagama fadar Abinda zata fada din ba.



Koda suka iso tuni Dr khalil zabeera yayi nisa shima yau gigitar yashiga ya janyo wata jallabiyar da sauri ya sanya Masa ya daukesa da dukkanin qarfinsa yafito dashi suka biyosa 

Zuwa lokacin Amatu kukanma takasa Yi suka fada mota Banda zarah dayace taje hafsatu ta Rakata ta fadawasu umme.



Koda suka Isa asibiti cikin gaggawa aka karbesa akai ciki dashi zuwa lokacin Amatu idanuwanta neman qanqancewa sukeyi kamar wainda ke bayansu saiga umme da Modibbo harma da Salman sun qaraso asibitin Babu me nutsuwa Hakanan yau ciwon nasa yasasu cikin wata irin rashin nutsuwa da firgici.


Dr ashir ne da Dr Fatima suka fito daga dakin emergency din idanuwansu kowanne jajir Dr Fatima tuni idanuwanta suka kawo hawaye rauninta na bayyana Dr ashir ya sauke Kai gaban Modibbo yace"


Saidai hakuri Allah ya karbi Dr khalil zabeera.


Wuta kowannensu ya dauke musamman Amatu da umme 

Amatu qyafta idanuwa tayi kusan so biyu kamar zata makance sbd duhu dake mamaye idanuwanta suka yanke jiki a some kusan atare itada umme wadda Modibbo ya tare ita kuwa MD ne ya tareta ta zube jikinsa dukkanin jikinta ba saki.

##Mamuh#*_MQ 31_*



MAHMOUD ZABEERA ma yau dukkanin jarumta da qarfin ransa ji yayi Yana kakkaryewa daga zuciya har gangar jikinsa, tarota kawai yayi Amma shima Jin yake kamar faduwar zaiyi,

Dr Fatima tayo gurinsa da sauri tana hawaye ta tattaro Amatun jikinta tana Kiran nurses da duk asibitin jikin kowa da zuciyarsa tayi sanyi da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda ya zamto cikakken mutum sbd kyawawan halayensa dasukeda wuyar samu acikin mutanen yanzu.


Dr ashir kuwa ganin dukkaninsu kowa neman zauce musu sbd tsananin tashin hankali da sauri ya dauko kujera yakawo wa Modibbo daya tare ummen data Suma,

Kiran wasu nurses yayi aka Kama umme itama akai ciki da ita aka kwantar gadan dake gefen Wanda aka kwantarda Amatu cikin sauri aka Fara Basu taimakon gaggawa dansu farfado tinda suma.


Su Modibbo kuwa zaunar dashi MAHMOUD yayi dukkanin jikinsa na rawa idanuwansa sunyi jajir ko mahaifin nasu yakasa kalla 

Jin yanda jikinsa ke rawa sosai yasa Modibbo dagowa da jajayen idanuwansa ya kallesa tareda dange hannunsa Yana rintse ido tareda jinjina Masa Kai alamar sai hkr.


Dr salman zabeera kuwa kuka yakeyi sosai kamar mace sbd rasuwar Khalil din tamkar saukar tsawa sukajita kwatsam Babu Wanda yakawo tunani ko zancen mutuwa yanzu ba'a kansaba kosu Andi dasuke tsofi Basu kawo tunanin mutuwa akansuba.


MAHMOUD ne yayi qarfin hali da jarumtar karban wayar Modibbo yakira Andi dake zaune cikin tsakiyar Daren Yana salati sbd baccin dayaji haka kawai ya dauke daga idanuwansa Kiran farko na asuba dayaji anyi yasashi miqewa zaiyo alwala yafara ko nafilfili wayarsa tadauki haske alamar Kira.


Juyowa yayi ya kalli wayar yana mamakin Wanda ke iya kiransa a wannan lokacin saiyaga sunan Modibbo

 ya sake shiga mamaki ya dauki wayar tareda dauka cikin nutsuwa yayi sallama.


Daga can asibiti Saida MAHMOUD ya tattaro qarfin halin iya bude bakinsa cikin rawar muryar dabai taba ba arayuwarsa yace"


Muna asibine taredasu Modibbo da umme Allah yakarbi Khalil cikin Daren Nan.


Tsit Andi yayi tsawon mintuna Yana qoqarin kakkamo zancen dazai fada yafara da Kiran"

Innalillahi-wainna ilaihirrajiun.


Kashe wayar yayi tareda ajiyewa yakoma bakin gadonsa ya zauna Yana sake maimata taslima Yana jinjinawa al'amarin ubangiji dayakeyin yanda yaso alokacin da yaso,

Ya dauke Khalil bayan cika masa burinsa na kwana daya tal,

Wannan shine cikakkiyar ikon ubangiji da Babu Wanda ya Isa ya sauya sbd yau da ace dukiya da mulkinsu nada iko meya hada Khalil da mutuwa a ranar yau da ko awa ashirin da hudu aurensa baiyiba.


Astaghfirllah" yafara maimaita tawa Yana rintse idanuwansa ya sunkuyar dakai cikin tsananin jimamin rasa yaro me tsaftatacciyar zuciya da tausayi tareda tawakkali irin Khalil.


Allah yayi maka rahama yabaka hasken kabari da sakamakon gidan aljanna KHALIL.



Koda asuba tayi akai sallar asuba tuni rasuwar Khalil ta yada zabeera da familynta nako Ina da ko Ina tuni kuku ya sauka a zabeera sbd mutuwar ta girgiza kowa sbd Babu Wanda yayi tunanin mutuwa Kuma tasa adaren,


Koda gari yayi waye sosai tuni family suka Fara halarta zabeera tafara cika tun kafin akawo gawar tasa gida dama wainda sukazo biki Kuma dama Basu tafiba tunda a Daren jiyan aka kawo amarya Ashe basasu koma daga bikinsa ba saisunyi zaman makokinsa,

Duk Wanda ya iso saiyayi kukan wannan babban rashin na khalil zabeera sbd kowa Yana shaida kyawawan halayensa da nutsuwarsa wadda tasa yakeda jamaa ciki da wajen zabeera.




Ahankali tabude idanuwanta ta rufe tasake budewa tana qyaftasu 

Da fuskar usi dake rungume da kanta tafaracin karo ta rufe idon ta bude taga shi din daine ta zabura da sauri ta tashi zaune har tana zamewa saura kadan ta fado qasan gadon iyami da maman junior da idanuwansu sukai jajir musamman iyami da har lokacin hawaye Basu dauke daga idanuwanta ba sukayi saurin tarota ta kallesu da manyan idanuwanta dasuka firfito sun bushe sai wani irin ja dasukayi tafara qoqarin miqewa qafafunta da hannunwanta tareda muryarta dasuke wata irin rawa tana cewa''


Ina...ina..Ina khalillll????


Sunkuyar dakai sukayi Banda iyami datayo kanta tana neman rungumeta tayi saurin qwacewa tana nufar qofar dakin asibitin USI dake kuka sosai yayi saurin tarota Yana kuka yace"


Amatu Ina zakije antafi dashi gida muke jira ki farko muma muke gidan.......


Zamewa tayi ta zube qasa tareda sakin wani irin gigitaccen kuka me qarfi dayasa asibitin suka qara daukar shiru kowa na sake rafka tagumin rashin Khalil din dakuma kuka da tashin hankali dazata shiga idan ta farka Wanda suka shirywa Sha dama.



Tsayawa sukayi kowannensu na nasa kukan me tsananin cikin tausayinta da Kuma zafin rashinsa Suma daya bugesu Babu Wanda yayi yunqurin hanata sbd kuka Kam yariga ya sameta abarta tayisa ko zataji sassucin radadin ZUCIYA.


Irin kukan datakeyi ne yasaka hankalin duk Wanda ke asibitin tashi sbd kukan nata taba zuciyoyinsu yakeyi Yana sake tuno musu da Dr khalil sbd rashinsa ne kawai yasa take wannan kukan Dan kuwa da Yana Raye Amatunsa bazatayi irin wannan kukan ba matuqar ba al'amari yafi qarfinsa bane.


MAHMOUD ne da kansa Modibbo yasashi yadawo asibiti yadaukosu Amatun tunda yashigo asibitin yaji tsit Yana Kama hanyar dakin datake yafara jiyo kukanta dayasashi tsayawa cak qafafunsa da zuciyarsa na qara daukar nauyin rashin Dan uwa mafi soyuwa garesa.


Jin kukan na kakkaryasa yasa yayi jarumtar qarasawa dakin ya tura ahankali yaci karo da ita zube bakin qofar tana kukan idanuwanta kamar zasu zazzago qasa.


Saurin juyawa yayi yacewa su iyami su kamota sutafi gida.


Daqyar suka tattarota suka saka mota suka nufi zabeera inda take cike tundaga farkon layin anguwar talakawane tako Ina bulbulowa sukeyi dukkaninsu yawanci mutanensa ne da taimako ya hadasu.


Ko a anguwarsu kawu jama'ar dasuka halarto dan jana'izarsa basa qirguwa 

Hakama ko anguwar gidan Ibrahim daya zauna Saida yayi mutane sbd ko acikin rashin Saida ya taimaki mutane da dama.


Sashen Modibbo akayi da ita inda gawarsa take shimfide an lullubeta su Modibbo da Andi taredasu alhaji qarami da kawu dake gefe zaune Yana tsiayayar hawayen dasuka kasa tsaya masa,wallahi ayau ki yakeyi tamkar 'dan daya fito daga tsotsonsa ne ya rasa sbd Khalil yarone daya shiga ransa Wanda yakejin inama ace haddashi ya tsinta lokacinda ya tsinto su Amatu da Usman.


Kukan umme ne dake zaune gaban gawar ta daga qafafunsa tana addua tana kukan da bayama fita sbd disashewa da muryarta tayi hakama ko gani batayi sosai ayanzu sbd kumburin da idanuwanta da fuskarta sukayi.


Tun kafin ta iso gaban gawar tasa qafafunta suka kasa daukarta ta zube tana sake sabon kukan dake taba dukkanin mutanen dake palon tafara rarrafowa tanajan jikinta ta matso gaban gawar tana kallon fuskarsa dake bude tayi fari fes Yana sheqi kamar zaiyi murmushi.


Qoqarin daukewa numfashinta yafarayi Salman da USI sukayi kanta suna Kiran sunanta anty juwairiyya dake palon itama tayi saurin tarota tana shafa Mata fuskarta zuwa bayanta numfashin na Dan daidaituwa.


Cewa akayi su fita za'a yiwa Khalil din wanka sbd lokacin jana'izar yayi sabon kuka Amatu tafashe dashi tana kallonsa tana Kiran sunansa ganin zata karya musu zuciya yasa Andi yace juwairiyya tayi cikin gida dasu itada umme wadda sai anriqeta sbd sosai Bata gani komai sai dishi dishi.


MAHMOUD ne yabiyo bayansu bayan sun fito Yana rintse idon damuwar tambayar dasu Andi suka turosa yayiwa Amatun ya tsaya bayansu kadan yayi Dan gyaran murya kadan yakira juwairiyya ta tsaya tareda juyowa tana kallonsa da jajayen idanuwanta

Ya Dan kalli Amatu da umme dake hawaye Babu me lakkar qwaqqwaran motsi acikinsu a taqaicema baya tunanin zasu fahimci Abinda zai fada ya Dan dauke Kai cikin qaqalo nutsuwa yace"


Zaki tambayetane ko da akwai janaba atare dashi.


Dummm taji itama juwairiyyar tareda sauke Kai ta gyada Kai tareda matsawa gurin Amatun dake tafiya tanajan qafa jiki a sake ta riqota tana kallon fuskarta datai ja ahankali tace"


Amatu wanka za'a yi Masa anason sanin idan da akwai janaba ataredashi¿


Cak Amatu ta tsaya tareda juyowa ta kalli anty juwairiyya da jajayen idanuwanta dasuka Fara bushewa taji sabon kuka na zuwar Mata sbd tun yanzu taqara tabbatarda mutuwa tonon asiri ce, Amma tunda tariga ta rasashi meya rage Mata tun yanzu tafara ganin tonon asiri ahankali ta juyar dakai tana qoqarin wucewa ta 'dagawa anty juwairiyya din Kai Wanda yasa MAHMOUD ZABEERA dayaga amsar data bayar juyawa ya koma Yana qoqarin Hana mutuwar jikinsa bayyana, cikin sanyin jiki ya sanardasu Andi Nan aka Fara yimasa wanka,

Suna gamawa aka shiryasa cikin farin likafaninsa aka shimfidesa tsaf aka sake aikawa matarsa da mahaifiyarsa sukazo sukai masa adduar data Kuma Kai Amatu ga Suma akai ciki da ita aka dauki gawarsa aka fito da ita inda dubban mutane ke jira Wanda yasa iyayensa da Yan uwansa mamakin lokacinda yayi wainnan jama'ar a waje wanda yawancinsu talakawane da marasa lafiyarsa Wanda yasa Andi Jin kunyar kansa alokacin dasuke zaune suna zuba mulki da oda alokacin 'yayansu nacan suna taimakawa talakawa da marasa qarfi,

Ya tabbata koshi ya mutu yanzu bazaiyi jama'ar Khalil ba Wanda sukewa fatan ya dace tun anan.



Anyi jana'izar Dr khalil zabeera ankaisa kwancinsa na qarshe andawo anci gaba da karban gaisuwar da aketa ganin mutane kala kala a zabeera Wanda yaketa saka iyayensa da Yan uwansa alfahari da Jin sasssaucin zafin rashinsa sbd ganin Inshallah ya dace tunda kowa yazo da alkhairin dayake fada akansa.



Acan cikin gida kuwa a sashen umme ake karban gaisuwar 

Umme ko Magana Bata iyawa idan anmata gaisuwa saidai daga Kai kawai Dan ko mutanen Bata ganewa sosai,

Amatu kuwa zazzabine me qarfi ya rufeta bayan anty juwairiyya da anty zarah sun taimaka Mata tayi wanka ta gyara jikinta tareda sallar asuba aka kwantar da ita a quryar bedroom din umme anty zarah ta zauna tareda ita tana shafa kanta sbd irin ajiyar zuciyar datakeyi Babu qaqqautawa kuka tuni idanuwanta suka bushe ko zuwa bayayi sai ajiyar zuciya da idanuwan datake zarewa.


Nuratu kuwa hajiya Maryam tafi kowa shiga tashin hankali bayan iyayen Khalil din da matarsa sbd Nuratu da abin ya buga sosai sai zabura takeyi tana somewa qarshe dai ankira likita yace saisun tafi da ita asibiti fatarsu alamarin bai taba qwaqwalwartaba.



Da daddare Amatu sashenta aka maidata tareda iyami da da anty salamatun gidansu da zasu zauna da ita kafin agama zaman gaisuwar asan abin yi.


Bedroom dinsa tashiga ahankali ta kunna wutar dakin tana juyowa ahankali da jikinta da Babu qarfi ko kadan idanuwanta suka tsaya akan shimfidar dasuka kwana a Daren jiyan ta qurawa jinin dayake Kan shimfidar ido tafara takawa ahankali ta Isa bakin gadon ta zube qasa tareda jawo zanin gadon ta qanqame tana sake kuka ahankali tana tuno Daren na jiya wanda yayisa a cikin yanayi na ciwo da rashin qarfin jiki sosai kamar Wanda rabo ke cizo Kuma kaman yasan rabuwa zasuyi, gwara da Bata hanasa kantaba Ashe datafi kukan datakeyi ayanzun.


Cukuikuye zanin gadon tayi cikin jikinta tana shaqar qamshin jikinsa dake jikin zanin cikin kuka tace"


Jiya kana taredani Dr meyasa zaka tafi??????


Kuka take fitarwa me qaramin sauti a bakin gadon har wahalallen bacci ya dauketa zaune a qasan.


Sai asuba ta bude idanuwanta dasukai nauyi sbd kumburi ta tashi tana gyara zamanta kafin ta miqe ahankali tana kallon zanin gadon dake jikinta ta sake kallonsa kafin ta nannadesa ta nufi cikin wardrobe din dakin tayi Masa kyakkyawan boyo ta fito dakin takoma dakinta inda su iyami suke sanyin AC yasa wani irin dogon bacci ya daukesu,

 ta shiga toilet tayo alwala tana fitowa iyami na farkawa ganin alamar alwala atareda ita dakuma Jin ana sallah a masallacin cikin zabeera yasa tasan asuba ce ta tashi zaune tana qoqarin saukowa gadon ta nufi bayin itama.


Sallah Amatun ta tayar kanta na tsananin ciwo kamar zai tsage qarshe dai a zaune tayi sallar.


Guraren qarfe Tara na safiya aka kawo abincin safe aka jere musu a dining tareda sabuwar me aikin da aka iko ma Amatun.


Anty zarah ma tunda safe ta iso sashen ta gaidasu iyami dake zaune Palo jigum sbd Amatun ta rufe kanta a dakin Khalil din tanata kuka ita kadai taqi fitowa.


Duk yanda anty zarah tayi qin fitowa Amatun tayi salman da USI ma sunxo sunyi sunyi taqi bude dakin Saida akaje aka sanarwa umme.


Ummen na zuwa qofar bedroom din nasa kasa Magana tayi itama sai kawai ta fashe da sabon kukan daya daga musu hankali 

Amatu dataji kukan ummen hankalinta yaqara tashi ta rarrafo ta bude qofar tareda fadawa jikin ummen tanajin kukan ummen har cikin ranta kamar yanda idan Dr na Nan tasan zaiji kukan ummensa.


Daqyar juwairiyya dasu anty zarah suka sallashesu aka fadowa su Modibbo saiga Andi dakansa ya zauna yayi musu nasihu masu karya zuciya da saka tawakkali Nan suka dauki qaddara suka dangana.


Anty zarah ce da iyami suka Bata abinci Dan Dole Tasha tea kawai sai guntun slicebread anty zarah takaita ta watsa ruwa ta sanya doguwar riga da hijab suka dawo Palo ta zauna cikin mutane.


Dukkanin kulawa da cinta da yanayinta anty zarah ce takeyi sai su iyami dasuke kwana yimata addua suna tofa Mata sbd yanda take firgita cikin bacci idan ya dauketa.


Anyi adduar uku anyi ta bakwai an watse kowa yakoma inda yafito sai anty salamatu da sabuwar me aikinta da aka bar Mata tayi zaman takaba Wanda taso takoma gidansu tayi umme ta ringa roqonta kada ta tafi tabarta Dole akace ta zauna anan tayi takaba tukuna.




****

Rayuwa me sauyawa kamar yanda mutuwa take Dole hakama dangana daci gaba da rayuwa yake Dole.,

Kusan sati hudu kenan yanzu da rasuwar Dr khalil zabeera Wanda tuni wasu suka manta suka koma harkokinsu Banda Amatu da mahaifiyarsa da har abada mutuwarsa bazata taba sakinsuba,


USI yakoma makaranta daqyar sbd kasa tafiya yayi yabar Yar uwarsa alokacin datafi buqatarsa Amma itace da kanta ta tuna Masa cewa burin Dr khalil ne yayi karatu me zurfi Dan ya tsayu da kansa ya tsaya musu wataran kamar irin yanzu da basuda Khalil din tabbas sunyi Rashi Dan yanzu zasu koma Matsin rayuwarsu ne na dah.


Sosai anty zarah da anty salamatu ke kula da ita hakama kullum umme saitazo da kanta ta dubata musamman saka mutuwar arai datayi arai sosai sai lafiya take neman gagararta sbd kullum cikin zafin jiki da zazzabin dare take,


Modibbo da kansa kullum yake Kira yaji lafiyarta da kansa ba saqo ba shikuwa Andi kullum saiyayi musu aikin idan da Abinda Amatun ke buqata saidai Kuma MD ZABEERA baibar ko wace irin qofa dazasu buqaci wani abinba koyaushe buqatarsu cikakkiyace daga garesa duk da baitaba zuwa inda takeba rabon daya kalli ko inda sashen yake tun ranarda ta dawo.


Rasuwar 'dan uwansa ta dakesa sosai harsaida hakan ya taba himmarsa da jajircewarsa a aiki shiyasa take dukkanin iya qoqarinsa gurin cire tunanin wanzuwarta a zabeera yariga ya damqawa zarah komai na buqatar Amatun harta fita takaba Dan haka yagama komai baida sauran tunani akanta saima busy daya qara saka kansa zama Dan yanzu tafiye tafiyensa sundawo dama sbd Khalil ne dake takura Masa yasa yarage tafiye tafiyensa Amma yanzu Kam sai ya qarawa kansa yawan tafiye tafiyen.

##Mamuh#



*_'yan uwa inaga anan zamu tsaya sbd duba da azumi daya riga yazo inshallah saimu Bari idan Allah yabamu yawancin ran kaiwa bayan sallah saimu qarasa Inshallah._*

Post a Comment

0 Comments