**
Ɗan Jim tayi tana kallon sa , kallon idanun sa tayi yanda yayi maganan kasan iya gaskiyar sa yake faɗi . Ba zan shiga moton ba . Ta furta tana kallon Gyefen ta tare da kame Hannayen ta . Ƙaran ringing din wayar sa ne ya katse masa magana da yake shirin yi mata . Murmushi yayi kana ya ɗaga kiran yana mai gyara zaman Ear phone din dake maƙale a kunnen sa . Mom...”
Ya furta yana Lumshe Lulun idanun sa tare da ware su bisa Kyaƙyƙyawar fuskar Amrah dake gaban sa . Ba tare da Amrah taji mene aka fadi daga Ɗaya bangaren ba sai ji tayi yace " Mom na ganta yau , Yau na Ga Amrah ..” Wani irin Dariya taga yana cikin nuna nishaɗi da jin matsanan cin farin ciki . Ohk Mom” . Ya furta yana Datse kiran nasa . Kallon Amrah yayi a karo na biyu wani kiran yana ƙara shigo masa . Sorry please ”. Ya yi maganan yana Kuma ɗaukar Wani kiran . Cikin gurɓataciyar Hausan shi ya fara Mata magana“ Eh na same ta , na gode Sosai da kika kasance wurin yi mun silar ganin wannan kyaƙyƙyawar Kuma matar Aure na . Wani irin Miƙewa Nana tayi daga Ƙwancen da take a cinyar Mommyn ta . Cikin Rawar murya tace “No ban gane ba , kasan me kake faɗi kuwa Aslaam..? Ina sane mana Nana kike Ko.? Ya ƙare maganan yana haɗe Fuska tamkar ba shi ba . Itako Amrah Saurin kallon sa tayi tana tunanin wacce Nanan ce.? Me kuma ke faruwa ?.
Muryar Aslaam ne ya katse mata tunanin ta yana cewa " bana zo Nigeria bane don na cutar da Amrah nazo nan ne don Na Auri Amrah , daga bisani Mu koma Spain . “Huhmm ...! Nana Ta sauke Ajiyar zuciya mai nauyin gaske ,kamin tace “ Zan baka ko nawa ne tun daga dubu ɗari biyar har zuwa Million 1 ko ma sama da haka . Wani irin murmushi Aslaam yayi kana yace " Baki san Waye Aslaam ba .? Dubu Dari biyar fa kika ce . Ohk lemme told you one thing, Tun ina Secondary school na wuce Karfin Naira dubu Dari biyar . A yanzu kuma sai dai Ni ba baki , Bama Kudin kasar Nigeriya ba , Ni kudin kyauta ne zan baki in Dollars . Just because kece sanadin haduwa ta da Amrah thank you very much, sai kinji Alart . Kamin Nana tayi Wani magana tuni ya Datse kiran yana kallon Amrah Wacce ta saki baki mamaki ne yasa ta zubda Ƙwallah na tausaya ma kanta . Tambayar Kan ta take yi mene tayi ma Nana har take kokarin ganin ta salwantar da Rayuwar ta ?. Gani tayi Aslaaamm ya kai hannun sa yana buɗe mata moton yana yin ƙasa da Kansa tare da dan durƙusar da kan sa kaman bawa a gaban Saurauniya . Cike da Kulawa da nuna soyayya ya furta “ Please Amrah 🙏🏻”.
**
Ihun kiran sunan Zuwai ne yasa matan gidan Saurin miƙewa,sauran matan Auren na fitowa daga Ɗakunan su ciki kam harda Baba Zuwai wacce ta fito tana gyara daurin ƙirjin ta . Wacece Zuwai a cikin gidan nan .? Zaid yayi maganan tamkar Wani Boss . Tun da Baba Zuwai take bata taɓa tsorata irin na yau ba . Ganin shatalelen Namiji tamkar Soja yana wani irin huci akan ta . Larai ne ta kalle sa tana cewa “ Waye kai Bawan ALLAH”. Kallon ƙasa da Sama yayi mata yana watsarwa cike da Wulaƙanci irin na Zaid ya furta “ Kece Zuwai Din kenan”. A'a Wallahi bani bace, Ni sunana Inna Larai. Jin haka yasa Baba Zuwai a dan rikice ta furta “ Ni..n..nic ...nice Zuwai . Ohhh Kece Zuwai , to nazo ne nayi Miki kashedi akan matata . Wallahi na rantse da ALLAH duk ranan da kika kara kuskuren taba mun Amrah sai nazo an tashi gidan nan . A gaban idanun ku sai naga An hake an rushe gidan nan ko tobali ba zan bari ba . Dafe Ƙirji Baba Zuwai da Wasu daga cikin matan Gidan su kayi . Kamin Inna Larai tace " Kawa Girman ALLAH kayi Haƙuri Yaron nan . Juyawa Zaid yayi yana faɗin that's the last Warning. Daga yanzu Na gama magana . Humm Wani irin ajiyar zuciya Zuwai ta sauke mai ƙarfin gaske kana tace " Mun shiga uku mu dai . Tun da yarinyar nan ta taho Gidan nan masifu muke gani iri iri , yanzu kuma har ta kai ga Gidan da muke ciki ne za'a rushe ? Gidan dake Dauke da mutane fiye da 70 saba'in a ciki . Kowa ya kasa motsi daga Inda yake , ita kuwa Lanti Wani murmushi tayi tana cabe baki tare da furta “ Haƙƙi kenan . Haƙƙin ma ta marainiya yanzu kuka fara gani”.
Ohh To pa..! Ikon Allah.” .
Inna Larai ta furta tana kallon Lanti kamin ta cigaba da cewa " Ai ke yau take Miki sallah , zuba ruwa a ƙasa kisha don farin ciki . To Bara kiji Wallahi billahil azeem Amrah ba zata Auri wannan tanbadadden yaron ba. Ji rashin mutunci har cikin gida zai zo ya dage iyayen ta ,wanda suka ci fitsarin ta da kashin ta da wahalar ta baki daya . A'a fa habawa Larai ƙarya bai kamata daga gare ki ba . Kika wahala da ita a yaushe . ALLAH dai ya kula da Amrah har ta kai Iyanxu . Don haka maza kiyi istigfari.
Takaici ne ya kama Baba Zuwai , tun da take ba'a taba ci mata mutunci irin na yau ba a rayuwar ta . Cikin kumburi da cika Wuya ta furta “ Na yanke hukunci Aminu shine zai Auri Amrah a cikin gidan nan. Aminu....? Lanti ta furta tana cabe baki kamin daga bisani ta wani sheƙe da dariya tana tafe hannu tare da cewa " To pah wannan Hukunci haka ? . To bari mu gani ai dai mu namu ido . Tayaya Amrah zata Auri Sauna shashasha bugage mai bin yan farauta kullum yana Aikin buda sigari Shine kamilalliyar yarinya kaman Amrah zata Aura ? , Kai Zuwai kije dai ki ƙara tunani don Malam ba zai taba yarda da Wannan hadin ba .
“Eiye...” yanzu Aminu ne kike kira da Wannan sunan . Salamatu mahaifiyar Aminu ta katse Lanti cike da zafi tana cigaba da cewa " Alhamdulillah, shi yana da Asali da tushe . Ai haɗa Auren su taimako ne aka yi mata . Karuwa kuma yar zina dana na sunnah ya Aura .? Humm Ai wannan rufa mata Asiri yayi , don wannan wanda ya shigo cikin gidan nan ba Auren ta zaiyi ba , yanzu Auren kwarya tabi kwarya ake yi . Sai dai su gama lalube tan da kwakule ta . Kyaunta ne ke ribatar su , sannan Ai kin san Ɗan Zina bai kyau ba . Aikuwa dai”. Zuwai ta katse Salamatu tana kallon Lanti wacce maganan nasu sosai yayi mata zafi . Sai kawai ta Girgiza kai tana cewa ' Dadi abun ko wannen ku akwai ƴammata a gaban sa . Abun da kuma kayi shi za'a yi maka mtswwwww , ta ja dogon Tsaki tana wuce su zuwa Madafi don ta iza itacen murhun nata .
**
Zauren gidan Zaid ya nufa wanda har a lokacin Nurain dukan bakin Zulai yake yi , inda jini yayi kace² fuskar ta yayi hummmm kaman an saka lemo ta ciki . Riƙe sa Zaid yayi yana cewa " It's Okay, mu tafi Amrah fa ta fita , ban san inda taje ba . Dakatawa Nurain yayi da dukan Zulai yana cewa " Gobe don Allah ku kara kula mun matata.!
Matar ka fa kace .? Wannan wani irin magana ce ? , Ban gane ba .? Zaid ya jero masa maganan a lokaci daya . Yass matata ce .”Ƙarya ne wannan malam mind your self . Amrah Tawace Ni kaɗai yaudarar Aminan takan mu zaka yi ne .? Ni yarda da kai nurain, na yarda da kai fiye da Kowa Ni Aboki nawa , but why now ?, So kake kasani a tension.? Da gaske Nurain kake ko wasa .?
Juyawa Nurann yayi yana barin Zauren yayin da Zaid ya biyo bayan sa a fusace . Yana shan gaban Nurain tare da Daga murya a zafafe yake furta “ Nurain magana nake yi , Are You serious or yhu are jocking.? Humm ba wasa nake yi ba , da gaske na ke yi ? . Nurain yayi maganan yana gyara agogon hannun sa , wanda ya Glass din ya fashe sakamakon jibgar Zulai da yayi. Kai a wannan karon ba zan iya sadaukar Maka da Amrah ba , ba iya son ko sha'awar ta nake yi na dan lokaci ba . So nake na riƙe hannun ta ,nasa ta farin ciki na kasance miji a gare ta na har abada . So yhu have to find another Wife , wannan ita tawa ce. Lumshe Sexy eyes din sa Nurain yayi kamin yace “ That is very Good yayi kyau ”. Buhhh bari na faɗa maka Wani Abu da baka sani ba . Amrah tace Wannan Wacce na taso da Soyayyar ta , kai yanzu kasan ta yanzu ka fara son ta ,amma Ni tun tana karamar yarinya nake son ta . Don haka ka bar mun Amrah ba taka Bace , Amrah ta wace . Mtswww . kai malam ka dawo hankalin ka , zan iya yi maka komai Wallahi a yanzu . Ohk . Nurain yace yana nufar moton sa tare da shigewa yana mata key .
Wani irin zafin zuciya ne ya ciyo Zaid shima nan take ya nufi moton sa ,kan sa ya dau zafi Ainun , A Zuciyar shi furtawa yake "Amanata zai ci kenan .? That's the Great mistake da Zaka tafka a Rayuwar Nurain... Amrah tawa ce , bana kowa bane Nine mijin ta . Saurin yin burki yayi ganin Amrah da Wani saurayi a bakin layin , sai Nurain dake fitowa daga moton shi cikin sauri Zaid ya budo Murfin Moton yana nufar inda suke . Kallon kallo suke yi tsakanin su duka . Kamin Zaid Da Nurain su hada baki wurin cewa “ Waye kai ..? Kallon Su Aslaaamm yayi yana kafe su da tsayayyun idanun sa , kana yace " Aslaam..” . Ba sunan ka muke son sani ba , me kake yi anan , waya baka izinin kula matata.? Cewan Nurain yana wani irin huci . Murmushi Aslaaamm yayi kana yace “ No..! Kace duka muna layin jarangiyar masoyan ta , Ohk Ai ba Abin damuwa bane , Kowa sai ya fafata iya rabon sa . Wanda yayi nasara shikenan . Wanda ya zama failure sai ya dau hakuri , Amma Amrah tawace ”.
Wani irin kallo Zaid yayi ma Aslaam kana yace “ Daga Wani ƙasar mahaukatan kake ? Oya faɗa mun , London, America Japan Ina sauraren ka . Daga Spain . Ohhhh yayi kyau to is better for you ka hakura ka cire Amrah a zuciyar ka Cox she's mine.
Hayaniyar ce ya fara tashi A wurin , Ko ina na jikin Amrah rawa yake , musamman yanda Taga Nurain na mata Wani irin kallo wanda ta kasa Fahimtar Saƙon hakan .motsa bakin ta tayi cikin Muryar kuka ta furta “ Don Allah kuyi hakuri... ”. Amrah wuce gida yanzu ....Nurain ya furta yana kafe ta da idanun sa . Ba tare da ta jira jin me zai kuma cewa ba , da sauri ta juya tana barin wurin tare da nufar Hanyar layin su . tafiya take yi tana Wani irin kuka mai ban tausayi , gaba ɗaya ta gama ficewa cikin hayyacin ta .
1:00pm .
Zaune Suke a tsakiyar Falon Daddy Kasantuwar week end ne , Daddy bai fiye zuwa ko ina a wannan rana ba . Lemo Nusaiba take sha a hankali da ganin ta kasan bata da karsashi don ba'a jima ba suka yi waya da Nana taji zallar madaran butulcin da Aslam yayi masu ,shine yanzu sam bata da sukuni . Shigowar Alart da taji ne yasa ta duba Wayan nata dake kusa Da ita , 2.million ta ga Alart din su , Wanda cikin sauri ta juya tana kallon Daddy tare da Saka Ihun farin ciki tana furta " Ohhhh Thank yhu so much Dad . Murmushi Daddy yayi yana cewa “ Zai ishe ki dai ko .” Saurin gyaɗa masa kai tayi tana furta “ Sosai Daddy . Mom Sa'adah ce wacce take zaune hannun ta dauke da Magazine tana duba news na Wannan satin , ta kalli Nusaiba tana cewa “ Duk Sanyayyar da zaki yanzu ba Zakiyi shi a nan Gida Nigeria ba sai kin haura kin tafi Dubai .? Bikin fa Saura kwana ki biyar ne yau . Humm . Nusaiba ta numfasa kana tace “ Daddy Nifa tsoro nake ji wallahi...Ya Nurain he totally change , Ina ganin Kaman ba zai yarda Da Wannan Auren ba indai yarinyar nan tana na . Kallon Nusaiba suka yi duka , suna nazarin maganan nata , kamin Daddy yayi Murmushi yana cewa “ Zan saka A kawar da yarinyar na yan kwana ki , har ayi Auren sannan .” . Wow Dad Hakan ma is better . Kasa motsi Mommy tayi sam wannan maganan bai mata daɗi ba , amma kuma babu yanda zata yi dole tayi shiru ta hakura ta zuba ma sarautar ALLAH ido .
Kan Nurain ne ya kulle gamm . Kasa murɗa Handle Door ɗin yayi yana sauke hannun sa a hankali don wannan maganan Daddy da yayi na karshe a kunnen sa ya Sauka . A sarari ne ya furta “ Dole a yau Na yi nisa da Amrah , a yau zan Yi nisa da Matata nisar da babu wanda zai sam inda take . Nima kuma ba za'a ganni bare har a ɗaura Auren , Dad , mom bye . Ya furta yana saurin juyawa tare da nufar Part ɗin shi don ya tarkata duk wani Abu mai muhimmanci nasa ......!
0 Comments