TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 22-23

 09032345899[3/31, 10:57 PM] Zafafa: *_MQ 22_*


*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*


*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*


*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆🏾‍♀️🙎🏽‍♀️


*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaɗa ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯🏽‍♀️👯🏽‍♀️


*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*

*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*


*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*


*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾🤞🏾



************

Cikin kulawa yake tambayarta ya jikin nata itama cikin kulawar take amsawa tanason fada Masa komai na Abinda yafaru tun zuwansu asibiti tanajin nauyin anty zarah 

Ganin hakan yasa anty zarah miqewa tayi toilet Dan taimakawa ta hada Mata ruwan wanka tana hamdalar cikin dayake lafiya kalau Babu Abinda ya samesa.


Tun tanayin wayar a zaune harta Dan jingina da Kan gadon tana rufe idanuwanta tana sauraran abubuwan da Dr ke fada Mata tana murmushi sbd sbd girmqn mahimmancinta a rayuwarsa yake fada Mata Yana Mata fadan ta rage ciye ciyen kayan shiririta.


Ganin ba gamawa zasuyiba yasa anty zarah karbe wayar tareda kashewa Tana cewa''


Tashi kije kiyo wanka yanda jikinki zai qara warwarewa,


Miqewa tayi tana murmushi har lokacin ta cire kayanta tareda daura towel ta fada toilet din.


Ahankali take wanka tana tunanin Rabin ran Anty zarah ta yanda zai iya wanke jinin daba na matarsa ba,

A yanda yakeda tsafta da Shan qamshin Nan Bata tunanin zai iya taba rigar bare ya wanke da kansa,

Duk yanda za'ayi ita zata karbo rigar ta wanke da kanta tunda jinin natane koba komai abin kunya ne gareta wani ya taba jinin al'adarta Wanda ba mijintaba.


Kodata fito wanka anty zarah na dakin tana sauke abincin da hafsatu tashigo dashi Wanda akayi domin Amatun kawai.


Tasamu qarfin jiki matuqa sosai datayi wankan shiyasa cikin walwala ta shirya bayan tafara shafa Mai kadan ta sanya doguwar riga me Fadi sbd ganin anty zarah nata kallon cikinta cikin kulawa itadai lafiyar cikin ce a gabanta.


Zama tayi suka hau breakfast tareda anty zarah din suna 'dan taba firar Dr daya damu da haryana cewa zai dawo yau daqyar ta hanasa.


Suna gamawa ta hau gadonta ta mimmiqe Anty zarah takira hafsatu tana Mata tausa ahankali ahankali har bacci ya dauketa sai alokacin Anty zarah tasaki ajiyar zuciya tareda miqewa tabar dakin.


Dakinta tafara zuwa ta sauya kayan jikinta tareda qara shafawa jikinta body mist ta fito tana gyara zaman qaramin qyalen dake daure akanta Wanda yaqarawa kyakkyawar fuskarta kyau ta nufi dakin mijinta.


So daya tayi knocking tareda bude qofar bedroom dinsa tashiga bakinta daukeda sallama Mai sanyi.


Tsaye yake gaban mirror daureda brown towel iya qugunsa Yana shafawa jikinsa spray din Hugo boss fuskarsa a fuske kamar dai koyaushe.


Kallon budadden bayansa tayi dayake fari tas Babu tambon sai qyalli yakeyi kamar na mace har zuwa wuyansa da faffadan qirjinsa datake gani ta jikin mudubi Wanda tuni yaji ajikinsa shi take kallo saiya juyo ahankali yayi Mata kallo daya yaga yanda take kallonsa cikeda so da qaunarsa saiyaji zuciyarsa ta danyi sanyi sbd yasan zarah mace ce me tsananin hakuri da juriya Wanda yasa yake matuqar respecting dinta akan hakan,.


Gabanta ya qaraso ahankali ya tsaya Yana kallon fuskarta itama shi take kallo tana jin sabuwar soyayyarsa na shigarta ahankali ta matsa ta shige jikinsa tareda zura hannuwanta bayansa ta rungumesa ahankali tana kwantarda kanta akan qirjinsa tareda lumshe ido tana sauke boyayyar ajiya zuciya.


Sai daya jima shiru Yana sauraran bugun zuciyarta dake dukan qirjinsa kafin ya daga hannuwansa ya rungumeta ahankali tareda lumshe ido ya sauke numfashi,

Sun dauki kusan mintuna biyar ahaka  shiru Babu me motsi kafin ahankali ya dagota daga jikinsa ya dauketa gaba dayanta ya nufi gadonsa da ita Yana kallon fuskarta data soke cikin qirjinsa,

Yana kwantar da ita Kan gadon yayi Mata rumfa da fadadden qirjinsa Yana Kai hannu Kan zib din gaban jallabiyarta.



Bayan wasu lokuta haryayi sabon wanka ya fito ita alokacin take qoqarin saukowa daga gadon tayi saurin daukar fadawa toilet din nasa duk da shi mutum ne dabai cikason wani na amfani da toilet dinsaba Amma kasancewar yanzu Basu kadai bane Dole bazata iya fita ahakaba kamar da wani zai iya ganinta.


Wanka tayo tafito lokacin harya shirya cikin farin filtex transparent da hular qube coffee brown Yana fesawa jikinsa turarensa na IMPERIAL MAJESTY.


Kayanta ta maida bayan tagama goge jikinta ta shafa oil kadan tareda turarensa.


Sai alokacin ta tunoda Abinda yakawota ta kallesa Yana qoqarin daukar wayarsa dake Kan bedside cikin taushin murya tace"


Am...amm dama rigar dazu ta jikinka nace ko zaka kawo na bayar a wanke sbd Naga ta samu lalacewa....


Cak ya tsaya daga Abinda yayi niyar Yi hakanan yaji maganar Tata kamar ta ciza ransa,

Idan tunaninsa na aiki daidai yasan me wankin zarah din namiji ne Wanda kusan duka familyn shike yiwa wasu da yawa daga ciki wanki,

Tana nufin shi gardin zata bawa jinin dayake sirrin Amatune ga wani gardin ya wanke???


sake 'dan tamke fuska yayi tareda juyowa ahankali kamar zai kalleta saiya fasa ya juya ya dauka wayarsa batareda yabata amsaba yafara qoqarin barin dakin.


Saurin biyosa tayi tana cewa''


Nace bakajiba rigarka ta yau da safe nakeso kabani zanbawa wa....


Kallon daya dago yayi Mata yasata matsawa baya kadan tana sauke Kai zuciyarta na bugawa da sauri.


Kamar zai wuce baiyi Magana ba saikuma ya tsaya batareda ya juyo ya kalletaba cikin sautinsa me daukan hankali yace"


Karki sake kawo maganan riga da Abinda yasamu riga agabana ok????


Kallonsa tayi tana son sake maganar Amma ganin yanayinsa na Babu Wasa ko sakin fuskarsa yasa ta 'daga Masa Kai tana cewa''


Adawo lfy.


Can qasan maqoshinsa yace"


Thank you"tareda wucewa ya sauko qasa tareda ficewa zuwa office. 

##Mamuh#


Gashinan please yauma kuyi manage gobe Inshallah zamu koma pages dinmu masu tsawo yauma uzurine ya riqeni kuyi hkr da wannan din🙏🙏🙏




ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[4/1, 10:47 AM] Zafafa: *_MQ 23_*


*_INA KUKE MATA MASU AJI,MATAN DA SUKE DA BUQAYAT GYARAN JIKINSU DA INGANTATTUN MAGUNGUNA WADANDA BASA CUTAR DA JIKI KO LAFIYA_*


*KINA DA LABARIN ZEE HERBALS APHORODISIAC?*


*wadda ta tanadar muku ingantattun supplenmt masu maida tsohuwa yarinya*


*magungunan da suke gyaran jikin diya mace su maisheki wata ta daban cikin mata*💆🏾‍♀️🙎🏽‍♀️


*magungunan da xasu sanyaki qyalli da sheqi,su ciko miki gami da tada duk wata komaɗa ta jikinki ki ganki dai dai da zamani*👯🏽‍♀️👯🏽‍♀️


*karki xama 'yar kallo,kuma karki bari ayi babu ke*

*garzaya maza ki nemesu a shafinsu na INSTAGRAM http://www.instagram.com/zeeherbalsaphrodisiac*


*ko kai tsaye ta WATSAPP https://Zeeherbalsaphrodisiac.whats.bz*


*_KO KI KIRASU KAI TSAYE BABU WANI JIRA TA WANNAN LAMBAR WAYAR 08169380189_*


*_ZEE HERBALS APHRODISIAC A INGANCI BASU DANA BIYU_*🤞🏾🤞🏾🤞🏾🤞🏾



**********

Yinin ranar cikin farin ciki dukkaninsu sukayisa sbd musamman Andi da Modibbo suka aiko akaje da Amatu gurinsu suka duba lafiyarta qarima Dr Fatima Dr khalil yaturo ita taduba musu lafiyarta taqara Basu tabbacin komai lafiya daga ita har cikin,

Musamman Andi yayowa Amatu kyauta ta musamman Wanda tasake qara Mata baqin jini da qiyayya gurinsu umme da Haj maryam wadda taga Salman dinta na wani rawar Kai akan Amatun tun agabansu Modibbo ta buga tsalle tace"


Wlh Salman karka kuskura kace zakamin kwashe kwashen bacin Rai Dan ni ba dauka zanyi ba.


Ganin basusan akan me take Magana ba yasa kowa tayi watsi da ita saishi uban gayyar datake Magana akansa yafahimci Abinda take nufi sai anty zarah da Amatun dake aika musu da kallon hadarin kaji sbd yanxu daidai takeda kowa kaf cikin zabeera sbd Andi daya tsaya Mata.


Koda suka fito a hanyarsu ta komawa suka hadu da Nuratu tana ganinsu tahau yada maganganu in marasa Dadi Har Amatu zata tankata anty zarah tayi saurin riqo hannunta tajata  sukabar gurin sunaji tana cewa zarah din munafuka Amma Basu kulataba suka wucewarsu.


Da yamma Salman da kansa yazo ya maidata asibiti tasake ganin Dr Fatima suna baro asibitin kamar a mafarki sai kawai tagansu qofar gidansu yayi parking mota


Da sauri ta juyo ta kallesa bakinta da fuskarta daukeda tsananin mamaki da farin cikin dayasa takasa mgn sai kawai ta bude motar ta fito da gudu tayi ciki.


Da iyami tafara cin karo a tsaye tana kwashe shanya cikin tsananin farin cikin ganinta ta rungumeta tana cewa''


Iyami wlh bansan haka nayi kewarkuba sai yau Dana ganni a qofar gida Ina kawu da usi???


Kawu dake fitowa daga daki Yana jinta dama ya fito Yana ganin yanda Amatunsa ta koma take ya washe baki Yana cewa''


Maza kuzo mu shige daki kada Ido da baki suyi Miki yawa kinsan gidan harda qarin 'yan bani na iya aka samu.


Dariya tayi tana sakin iyami tace"


Yanzu nasan Ina gaban kawuna.


Kallonta iyami takeyi itama cikin Jin Dadi da farin cikin ganin yanda ta sauya tayi kyau kamar 'yar masu kudi har wani qyallin haske fatarta keyi ga suturar alfarma ajikinta sai annushuwa takeyi.


Dakin suka nufa suka zazzauna Nan aka nude sabuwar fira saiga shima usi dake shirye shiryen tafiya jibi yashigo Nan aka Dora firar ga fankasu da iyami tayi aranar dayaji miyar Naman rago da Ganda Nan aka kawo musu suka hau ci suna Santi musamman Salman dan shima yamasa Dadi matuqa.

Suna Nan saiga Kiran Dr khalil yashigo wayar kawu dauka yayi suka gaisa ckin sakewa kamar 'dansa na cikinsa yakejin khalil sbd shiga ransu da yayi iyami ce madai takejin nauyinsa na sirikantaka sbd tuntuni sunsan Amatu yakeso Dan Yama fada musu Kuma sunyi na'am da hakan jira kawai suke tadawo asa ranar aure,

Sabuwar Hira suka Dora da Dr din a waya su Amatu na fada Masa Abinda suke ci Yana cewa''


Umma iyami idan nadawo Nima shi zakibani wandama yafi nasu Dadi.


Murmushi iyamin tayi cikin Jin nauyinsa tace"


Khalilu duk Abinda kakeso idan kadawo Inshallah duk sainamaka su.


Yawwa nagode umma.


Kawu ke tambayarsa ya aikin dayaje yi dafatar akwai nasara??


Eh yace Masa Yana qarawa da alhmdlh Inshallah muna gamawa zan juyoma.


To Allah yakawo ku lfy.

Amin


Basu bar gidanba sai kusan yamma sosai Wanda anty zarah tayi musu Kira yafi a qirga 

Itama Saida iyami ta hado Mata fankasu suka je Mata dashi.


Kamar kada su tafi hakanan ta fito suka tafi tana sake dagawa Yan gidan hannu kowa nasakejin kamar kadata koma.


Saida suka biya sahad yayi Mata soyayya sosai har abin na Bata mamaki Amma ganin yanda ya dauketa kamar 'yar uwarsa ya nuna bayason godiyarta da mamakinta itama saita daukesa kamar usi Nan suka sake shiriricewa sai magriba suka kamo hanyar gida.


Suna tafe suna fira harda qyaqyata dariyarsu sukeyi Yana tuqi da gudu gudunsa aikuwa Basu ankaraba wata mota tayo Aron hannu a guje itama me motar yake tahowa,


Cikin wani razanannen firgici yaso kaucewa Amma ganin akwai express dayan gefen sai kawai yayi dayan gefen sukai Kan wata bishiya suka daketa Amatu da tuni ta saki ihun sadaqarwa kanta ya daki qofar motar tsananin tsoro da firgici yasata somewa agurin.



Cikin sauri ya juyo Yana qoqarin dagota Yana Kiran sunanta da qarfi cikin damuwa sbd yasan suman tsoroce kawai tayi gashi Babu wani abindama yafaru din sbd bai daki bishiyarba sosai.


Ruwan dayasha ya rage kafin alamarin ya dauka ya shafa Mata saigata tasaki nannauyan ajiyar zuciya a rude tana cewa''


Wlh banason na mutu yanzu saina cikawa Dr khalil burinsa na aurena.


Dariya maganarta ta basa duk da ta daki zuciyarsa Kuma.


Cikin kulawa yace"


Nima banason ki mutu sainaga rabon wace ke a qarshe.


Kallonsa ta juyo tayi cikin rashin fahimta tana qoqarin sake dawowa nutsuwarta.


Murmushi yayi tareda tayarda motar yayi ribas sukabar gurin Yana cewa''


AMATULLAH ki dinga tuna sauran bayin Allah yayin yiwa mijinki na baa dauraba addua.


Sake rudata yayi tasake juyowa gabaki daya tana kallonsa saidai ganin kamar reaction dinta nasake basa damar yadda da hasashensa koma dai yardarsa sai kawai ta basar da zancen tana dariyar tsoron dataji da sumanta tana cewa''


Dan Allah Dr Salman kada anty zarah tasani 

Tana sani zata Fara daga hankali ta fadawa Dr banaso ta daga Masa hankali.


Sai alokacin ya Dan juyo ya kalleta zuciyarsa na wani sarawa Yana maida hankalinsa Kan titi cikin sautin nutsuwa yace"


Idan zuciyarki na tsananin kulawa da qaunar Khalil haka

Meyesa zata so MD ZABEERA???


Cak ta tsaya gabanta yayi mummunan faduwa Amma sbd Bata fahimci zancen nasaba saita saki wani yaqen dolen Dole tana kasa juyowa ta kallesa tace"


Meye hadina da Rabin ran Anty zarah kuma?

Ko gaisuwa Bata hadani dashi bama ya cikin mutanen danake qauna gaba daya sbd halayensa na wulaqanta antyna.....


Baya cikin wainda kike qauna sbd shi sonsa kikeyi Amatu.,

Amatu bansan meyasa shedan yake yawo atsakaninmu ba dayake haifar Mana da wani tunanin dabai kamataba bayan sanin cewa ke amatsayin matar khalil kike,

Amatu nafada Miki hakane Dan kije kiyi tunani kada ki auri Wanda farin ciki ya cancanta a rayuwarsa ba dakon son maso wani ba,


Dr Khalil zabeera shine duk duniya cikin maza ayanzu yafi cancanta daya asameki gaba dayanki daga zuciya har ruhi da ganganr jiki

Dan haka kada ki azabtar da rayauwarsa ta basa gangar jiki da qauna kawai

Yana buqatar dukkanki gaba daya har soyayyarki da zuciyarki sbd koba komai shi din Asthmatic patient Wanda yakeda alaqa da zuciya 

Dan haka AMATULLAH kije ki zauna ki nutsu kiyi tunani ki Fara koyawa zuciyarki soyayyar khalil ba qaunarsa ba soyayyarki yake buqata.


Kallonsa takeyi sosai kanta na neman bugawa da maganganunsa ta girgiza Kai Yana rintse ido cikin rudewa take cewa''


Mezaisa naso Rabin ran Anty zarah ni Dr nakeso, shikadai nake qauna, shikadai nake tunani shikadai nake gani, shikadai nake.......


Mafarki fa???


Tsit tayi tareda kasa qwaqqwaran motsi sbd Jin tambayarsa,

Idan har ba qarya zatayi Masa ba to tabbas 'daidaikun ranakune Bata kwantawa batayi mafarkin Rabin ran antynta ba.


Cikin firgici ta dago idanuwanta na cikowa da hawaye zatayi Magana yayi parking Yana cewa''


Mun iso gida.


Da sauri ta juya ta kalla waje tagansu qofar part dinsu anty zarah din 

Ta sake juyowa gurinsa zatayi Magana cikin rawar murya da sarkewar tunani

Ya katseta da sakar Mata murmushi me sanyi sbd jikinsa da zuciyarsa dasukai sanyi idanuwansa na Dan sauyawa sbd yanayinta ya Gama tabbatar Masa da hasashensa katseta yayi cikin sanyi da cewa''


Kije ki zauna kiyi tunanin Abinda yakamata.


Shiru tayi tana kallonsa kamar bazata fito motarba saigashi kuwa motar MD ZABEERA ta iso gurin yayi parking Dan da kansa yayo tuqin yadawo gida.


Motarsa ta qurawa ido zuciyarta na bugawa da sauri da sauri kamar zata bullo qirjinta ta fito,

Saida yadauki mintuna biyu zuwa uku kafin yafito motar Yana amsa waya fuskarsa a 'dan sake Wanda yasata kusan suman zaune da sauri ta rintse idanuwanta tanaji kamar yanzu ne da Salman yayi maganar ya zuba Mata son MD din me tsanani cikin ranta ta girgiza Kai da qarfi Yana cewa''


Bazan taba son Rabin ran Anty zarah ba.


Bude motar tayi da sauri ta fito batareda ta sake waiwayo Salman ba Wanda tunda motar MD tashigo fuskarta ya tsurawa ido 

Jan motarsa yayi yabar gurin Yana sauke numfashi me zafi ya nufi gurin mum dinsa da tun rana take kiransa duk tabi ta hargitse ta daga hankalinta akan alaqarsa da Amatu Wanda yakejin da akwai matsala Dan kuwa kome zatayi bazai iya rabuwa dasu Amatu da familyntaba.


A sukwane tashigo ba cikin hayyacintaba tayi nisa cikin tunani da fargaba tareda tsoro taji andafa ta tayi saurin dagowa sukai Ido biyu da anty zarah tana sakar Mata murmushi tace"


Amatu Yaya dai?

Sai yanzu kuke dawowa tundazu nakira Usman yace kunbaro.


Qaqalo murmushi tayi tana qarasa shigowa palon tace"


Wani guri mukaje Salman yayi min siyayyar kayan babies da kayan dadi" ta qarasa fada tana qaqalo dariya sbd kawar da banzan tunanin dayake yawo cikin kanta.



Siyayyar ta miqawa anty zarah tareda fankasu din dasuka Zo Mata dashi 

Cikin farin ciki ta karba tabawa hafsatu tace ta zubo Mata a plate 

Ita Kuma dakinta ta nufa Dan yin wanka ta gyara jikinta Amma cewa anty zaran tayi zatayi sallah ne.


Wankanta tayo tareda shiryowa cikin riga da wandon bacci masu Dan kauri ta sanyo qatuwar rigar sanyi akai sbd ana Dan sanyi gashi gidan Sam komai sanyi sunsaba da rayuwar AC ta sanyo hula tareda slippers ta fito tana waya da Dr khalil Wanda yanzu take tsananin Jin kunya da tausayinsa.


Cikin annashuwarta ta fito suna wayar harda 'yar dariyarta sosai sbd labarin abincin dasuka ce na 'yan Chinese yake Bata kamar zaiyi kuka da amai

Ganin yanda labarin ke sakata nishadi yasa yaketa Jan labarin Yana sake fada Mata yanda kalar abincin yake da yanda ake cinsa sbd walwalarta na basa farin ciki da nutsuwa.



Dining ta nufa tana sake qyaqyata dariyarta datasashi tsayawa cak daga cin abincin dayakeyi akan dining din tareda zarah wadda yau duk farin cikinta a bayyane yake sbd gata ga Rabin ranta suna cin abinci tare.


Qoqarin zamata takeyi a dining din idanuwanta suka sauka cikin nasa daidai dagowarsa ya kalleta da idanuwansa dasuka narketa gaba dayanta saita samu kanta da kasa dauke idonta daga kansa zuciyarta na harbawa ahankali.


Sarqewa yayi sbd wani dalili daya kasa sani yafara tari ahankali Yana Kare bakinsa da tissue 

Anty zarah dake Shirin Magana tayi saurin daukar ruwan sanyi zata miqa Masa daidain Amatun ita Kuma ta miqa Masa juice cikin cup.


Kallon juna sukayi itada anty zarah din tayi saurin dire cup din tana barin gurin da sauri ya 'dan bi bayanta da kallo qasa qasa ahankali kafin ya karbi ruwan hannun zarah din yakai bakinsa ya kurba kadan ya ajiye yakai hannunsa ya dauki cup din juice din yakai bakinsa yasha kadan sai kawai ya miqe Yana cewa''


Alhmdlh I'm full.


Binsa anty zarah tayi da kallo harya haye stairs din zuwa samansa tana karantar yanayinsa 

Idan nazarinta yabata daidai MD na wasu abubuwan dabata ganewa kwanakin Nan duk da dai dama can Bata ganewa MD Amma dai yanzu kamar tana nazartan wasu abubuwan nasa.


Bin bayan Amatu tayi tana kawar da tunanin komai tana zuwa dakinta ta sameta Dr khalil na qoqarin cigaba da sata nishadi itama tana qoqarin nuna Masa nishadantuwarta sbd kada ta sace Masa gwiwa.


Palo suka dawo da anty zarah tasata gaba akan saitaci abinci ga cake din datakeso koyaushe Wanda ake Mata duk Bayan kwana biyu Amma ta kasaci komai ko ruwa ta kasa Sha sbd kanta dake daure tamau har wani sarawa yake Mata takasa cire tunanin komai cikin ranta saima wani irin tunanin MD din dayake neman zauta kanta bangare daya ga tunanin Dr da koma me zaije yadawo shi tayiwa alqawarin kanta matuqar suna raye saidai tunanin MD dakuma yake sake rikitata.


Miqewa tayi ahankali tace"


Anty kaina Yana ciwo sosai zanje na kwanta kozai rage.


Kallonta anty zarah din tayi tace"


Dakin daure kinci abinci ko kadan ne Kinga pasta ce aka dafa Kuma me ruwa ruwa ce zuwa anjima kadan lalacewa zatayi kada yunwar dare ta tayar dake ki rasa abincin ci yau ko fruits Babu a gidan Nan baa siyoba gashi rabonki da abinci tun rana da Kika ciyo a can gidanku.


Girgiza Kai tayi tana Dan dafesa tace"


Wlh banajin cin abinci saidai zuwa da safe idan ya warware zanci harda biyan bashin na yanzun din.


Miqewa anty Zaran tayi itama tareda wucewa gaba tana cewa''

Shikenan Allah ya tashemu lafiya Kisha magani kafin ki kwanta Dan Allah.


Hanyar dakin MD ta nufa tana gyara zaman rigarta a jikinta Wanda yasa Amatun binta da kallo idanuwanta na qoqarin cikowa da hawayenda suka sata saurin dawowa hayyacinta tayi dakinta da sauri tareda fadawa Kan gadonta tana rintse ido.



Tunda ta kwanta takasa bacci tana kwance ta qurawa Dan qaramin hoton Dr khalil dinta Ido dake cikin qaramin frame gefen gadonta Wanda anty zarah ce ta kawo Mata.


Dr Dan Allah kayi gaggawar dawowa sbd Ina buqatar kayi saurin aureni na zamo mallakinka 

Bazan iya jira cikin Nan yakai wata taraba kadawo kasan yanda zakayi dashi nidai aurenka kawai nakeso yanzu fiyeda komai tun kafin zuciyata tafi qarfina.


Har qarfe goma sha biyu da arbain batayi bacci ba gashi zuwa lokacin yunwa tafara hanata sukuni sbd jikinta harya Fara 'yar makarkata 

Ta tashi zaune tana kallon agogo.


Saukowa Kan gadon tayi tareda mayarda qatuwar rigar sanyinta me kaiwa har gwiwa ta zura hula tareda sanyo slippers ta fito tana adduar Allah yasa abincin bai buga ba Dan wlh bazata iya kwana haka ba.


Tana fitowa ta nufi dining Kai tsaye daidai shima yafito daga dining din sbd abincin daya sauko ci Dan duk yinin ranar baici abinci ba sai Daren Kuma spoon biyu kawai yaci yatashi sbd Abinda yafaru gashi yanzu yasauko abincin ya buga.


Kallonsa tayi bayan itama ta bude abincin batasan lokacin datace wlh yunwa nakeji ni bazan iya kwana ahaka ba.


Palo yadawo Yana tunanin zancenta koba komai tunda tanada juna biyu ayanda sukace Dole tana buqatan abinci akai akai.


Shima Dole Yana buqatan abinci bazai iya kwana a hakan ba ya juya zuwa dakinsa ita Kuma tayi kicin ta hau dube dube Babu Abincin ci ta dauko ruwa Tasha taji cikinta na neman qullewa ta fito tana riqe cikin daidai ya sauko sanyeda riga da wando masu Dan kauri kamar na sanyi hannuwansa daukeda mukullan mota da wayarsa batareda ya kalli fuskartaba kamar bada ita yake maganarba yace"


Muje.


Tsayawa tayi binsa da kallo harya fice kafin tabi bayansa da sauri.

##mamuh#



ZAFAFA BIYAR👇👇👇


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


SARAN BOYE

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

Post a Comment

0 Comments