TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 9-10

 09032345899[3/14, 12:09 PM] Zafafa: *_MIN QALB 9_*

_mamuhgee_



Gabaki 'daya hankalinsa nakan fuskar amatu da ita Kuma hankalinta nakan usi da akewa dressing raunikansa bayan an wanke Masa hadda 'dinki Saida akai Masa a inda kwalba ta fasashi.


Sakin murmushi ganin yanda takeyi kamar ciwon ne ajikinta tanata yamutsa fuska tana cewa"


Usi daga yanxu ko sunan Luna nasake ji abakinka nice zanmaka dukanda ko kawu bazai iya ganekaba bare iyami,

Yanxu duba kaga yanda kakejin azaba

Shima wancan kabirun nasa Amin maganinsu Dan na aika buge katangar bayinsu ta bayan gidansu ta yanda duk kudin dasuka karba zai qare a gyara kaikuma....


Cikin 'yar qaramar dariya ya katseta Yana kallonta cikin burgewa yace"


AMATULLAH antyn Usman ki kwantarda hankalinki Usman is perfectly fine,ba gashinan angama dressing ba shikenan kawai magani zai ringa Sha yanzu daganan raunikan zasu warke Suma.


Kallonsa tayi tareda kallon Usi dake cewa'"


Likita bafa antyna bace qanwatace.


Duka takai Masa da Jakarta tana cewa"


Kaine zakaita zama qani ako yaushe Dan haka kayi Mana shiru agurin 

Ina sake ganinka da kabiru nice zan dawo maka da duka raunikan nan sababbi.


Dafe dinkinsa yayi da sauri Yana cewa'"


Wayyo amah jini na fita dinkin ya warwa.....


Da sauri ta durqusa cikin firgici tana qoqarin Kai hannu tana cewa"


Dagaske?

Mun shiga uku,


Likita Zo ka duba Mana...


Dariya Dr Khalil zabeera yayi Yana kallon firgicinta dayasa takasa tsayawa ta lura usi din tsokanarta yakeyi ya kalli usi Yana cewa'"


Usman ka daina 'dagawa AMATULLAH hankali ko na saka a warware dinkin Nan ayi maka sabo yanzu.


Dariya usi din kewa amatun Yana qoqarin miqewa sbd dukan datake Masa da Jakarta sbd sosai ya fifgitata Dan sanin Babu Abinda take tsananin tsoro kamar wani abu ya samu Usin.


Takardar maganin daya rubuta musu ya miqawa amatun Yana cewa'"


Ga maganin dazai ringa Sha Nan bayan sati daya saiku dawo mu warware dinkin ko?¿


Karba tayi tareda kallon fuskarsa dake yalwace da murmushin dake qayatar da ita tace"


Mungode likita.


Girgiza Mata Kai yayi Yana cewa'"


Ki kula da kanki ba USI kawai ba AMATULLAH.


Qoqarin fitowa sukeyi nurse dinda yayiwa usi dinki na shigowa ya miqa musu takarda yana cewa"


Yawwa ga wannan zakuje ku biya kafin ku wuce.


Karba amatu tayi suna kallon juna da USI ta duba ita batama gane Abinda ke rubuce ba ta miqawa Usin tana cewa"


Duba kaga Abinda sukace aje abiya din.


 Karba yayi yana duba takardar Yana qoqarin hada kalmomin turancin Amma sunqi jaduwa ya duba gurin da akasa kudin yaga anyi 9 da zero hudu ya zato Ido da sauri Yana rawar murya yace"


Dubu casa'innn....


Mene?????ta fada da qarfi tana fizge takardar da sauri ta duba gurin kudin taga 9000 ta hadiye mugun yawu tana cewa"


Basuda hankaline??

Kuskure dai sukayi muje yayi Mana bayani

Dubu casa'in saikace fatarka suka sauya maka gaba daya tsabar gyara raunika.


Dr Khalil dake jinsu tun ayanda ya lura basuda wani ilimin bokon yasan ansamu rashin fahimta gurin duba kudin yaji sun sake burgesa ya taso yabi bayansu zuwa gurin biyan kudin.


Suna Isa amatu ta ajiyewa cashier takardar tana cewa"


Oga wannan dubu casa'in din da aka rubuto ta waye??

An Mana musayar takarda duba kagani.


Yanda tayi maganar yasa saurayin dagowa ya kalleta a wulaqance yace"


Malama takarda indai Kai aka bawa to Babu maganar kuskure idan biya zakuyi ku biya,idan kuna mamakin Abinda aka rubutane to wayace kuzo Nan da saiku tafi asibitin gwamnati.


Yanda yayi Masu maganar yasasu quluwa dama amatun a qule take da kudin cikin takardar kallon walaqanci tamasa tana cewa'


Kai Karen asibiti karkace zaka gaya Mana magana anan gurin 

Da kake maganar asibitin gwamnati idan har irinku zasuzo Nan suyi Karen asibiti mezaisa muma bazamu zoba???


Miqewa yayi tareda fitowa ya zagayo gabansu Yana nunata da yatsa Yana cewa'"


Kisan Abinda zaki fada Nan bama tolerating 'yan iska irink.....


Saukar mari yaji daga sama kafin yakai qarshen maganarsa

A gigice ya dago usi ya cakumosa Yana cewa"


Bayan wannan Marin har kamanni zan sauya maka duk bakinka yasake furtawa 'yar uwata wannan kalmar.


Da sauri mutane dasuka Ankara sukayo kansu ana qoqarin rabasu Koda Dr Khalil ya iso gurin harya 'dan cika abin ya girmama da sauri ya qaraso gurin Yana zuwa ya kalli usi cikin tausasa murya yace"


Usman sakeshi.


Dakinda USI yayi Yana cewa'"


Ka iya bakinka wannan tafi qarfin ko uwarka.


A harzuqe saurayin ya taso Dr Khalil yayi Masa wani mugun kallon dayasashi dakatawa Yana huci yace"


Dr wainnan 'yan iskan.....


Shut up""Dr khalil yace da Dan fada Yana cewa'"


Jafar koma gurin aikin and everyone should leave from here please.


Da sauri kowa ya watse Yana mamakin Dr Khalil daya marawa wainnan baya maimakon staff dinsa.


Bayan kowa ya watse ya kalle Usman da har lokacin ransa zafi yake da kalmar 'yar iskar da aka Kira amatu da ita yace"


Usman this is not how to behave with people musamman wainda kasama gurin aikinsu,

Meye abin fada anan infact meyema matsalar??


Kallon Usi amatu tayi tareda sakin murmushi danta saka ya sauko tace"


Kai usi meye na wani fada tun bamu biya wannan kudin da ake fada akai ba zakayi wani fadan kaji rauni kasa kawu ya cinyeni 'danyata.


Kallonta yayi a raunane zaiyi magana tasaki murmushi tana ce Masa"


Karka damu ka manta bama saka maganar kowa aranmu sbd bamuda abin damuwa,

Duk sunanda zai kirani dashi tunda dai banida Wanda hakan zai zubar Masa da mutunci to meyene aciki?

Kawu ne Kuma Shima zagi da maganar kowa Bata tabasa Dan haka barsu su kirani da kowane suna baya damuna,

Usi Kaine damuwata Dan Allah ka daina shiga rigimarda zata saka a hadari,

Ka manta munada burin cikawa na zama alhazai" ta qarasa fada tana dariya sbd Shima ya sake.


Sakin fuska yayi Yana cewa'


Muje nidai.


Tunda suka Fara magana yake kallonsu cikin wani irin yanayi yanason fahimtar zancensu dakeson nuni da su din marayune.


Gyaran murya yayi tareda gyara tsayuwarsa Yana miqa Mata hannu yace'"


Bani takardar kudin mugani.


Miqa Masa tayi tana shafawa idonta toka tace"


Dr mudai wannan kudin da aka rubuta mu biya bazamu iya biyansu ba sunyi yawa ni banma taba Kai qirqen casa'in ba a lissafin kudi

Ni ko inadasu bazan bayarba wlh ba kawuba koni bazan iya barciba duk ranarda nabayar dasu.


Murmushi yasaki sbd dama yasan za'a Rina ya kalleta yana cewa"


Basaikin kasa bacci ba AMATULLAH dubu Tara ne a rubuce ba dubu casa'in ba.


Kallonsa tayi da sauri tana karban takardan da sauri tana sake dubawa tana bin numbobin dakyau tace"


Eh hakane kuwa..


Dagowa tayi tana kallon Usi cikin masifa zata Fara magana yayi saurin cewa'"


Yi yi hakuri da masifar Inaga banduba daidai bane kokuma ban fahimta bane.


Hadiye masifar tayi tana cewa'"


Usi rashin karatun Nan saiyasa an dauremu wata Rana.


Dariya sukayi atare kafin ta kalli Dr khalil tace"


Dr ai maganar gskia ko dubu Taran Nan bazan iya biyaba zandai biya dubu biyu idan zaa karba.


Kallonta ya shagala da yi tana sake burgesa yace"


Usman kanada 'yar uwa anan,

Kawun Nan Shima yanada 'ya anan.


Murmushi tayi tana dauke ido daga wallet dinsa daya 'dan fito da aljihunsa daga gani Kuma tasan bazai rasa kudiba aciki Amma sbd kirkin Dr din tanata dauke ido akai sbd hakurinta yakusa qarewa takaiwa wallet din Hari.


Zaro wallet din yayi ya bude yaciro ATM dinsa ya miqawa cashier ta window tareda takardarsu yace acire.


Bayan ancire aka miqo Masa receipt ya miqawa amatu receipt din Yana cewa'"


Shikenan har dubu biyunki anbar Miki AMATULLAH.


Karba tayi ba wata kunya a idonta tace"


Aikuwa ka kyauta Mana Dan akan dubu Taran Nan nafison na kwana 'daya a station da safe na fito nayi gida da dubu Tara ta.


Girgiza Kai yayi Yana murmushi harsuka wuce Yana binta da kallo zuciyarsa na karban baqon yanayin dake shigarta akaro na farko da mace ta sauya bugun zuciyarsa a ganin farko.


Suna fita ya koma office dinsa yasa Akira Masa daya daga cikin nurses dinsu dayaji Yana fadin yasansu amatun lokacinda ake fadan dazu

Yana buqatar sanin inda suke.

##mamuh#



_________________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

[3/14, 12:09 PM] Zafafa: *_MIN QALB 10_*

_mamuhgee_




Suna fitowa daga asibitin gurin aikinta suka nufa ya ajiyeta da adaidaita kafin shi yawuce gida,

Babban Abinda yasa yau tazo aikin shine Jin ko hajiyar Nan tazo nemanta sbd yanzu dai Kam tana buqatar ganinta kodan Abinda yafaru yau na rashin ilimin dasukedashi sosai yasa taqarajin buqatar karatun nasu Amma dai yanzu na usi ne agaba.


Da manager tafara haduwa a reception din blue fox din tana ganin ya washe Mata baki ta tsuke fuska tana cewa"


Wannan Dan wahalar zai Fara damuna yanzu da surutansa wainda basuda amfani aguna,.


Yana qarasowa itama ta washe Masa baki da gayya tana cewa'"


Manager sannu da yawo.


Washe baki yasake yi Yana shaga dogon kansa yace"


Amah 'yan amata ya aikin?¿ Sai yanzu Kika shigo?


Eh sai yanzu nashigo na yagi robana daya wuceni kwana biyu.


Me Kika??


Aa cewa nayi nayi latti Bari naje kafin a nemeni.


Tana fadar haka ta wuce tana cewa''


Kuje kuga gayu da wayewa gurin Dr

Amma kunzo kaida insfector Garba bansan Waye haqoransa sukafi na wani dafewa ba.


Tana shiga saloon madam bell ta kalleta cikeda mamaki tana cewa"


Amah sai yau kikaga Daman zuwa aikin???


Ta gefen ido ta watsawa madam din mugun kallo kafin tace"


Madam lalurace ta hanani zuwa ba ganin dama ba.


Bude Ido madam tayi tana cewa"


Ni kike wa magana haka?


Dauke Kai tayi tai qasa qasa da murya tace"


Ke din uwatace?


Me kike cewa amahhh?


'dan washe baki tayi cikin gatse tace"


Cewa nayi sorry madam.


Qwafa tayi sbd taji Abinda amatun tafada da farko tace"


To ki tafiyarki kawai Dan anyi replacing dinki da wata.


Kallon baibai tayi Mata tana cewa"


Madam korata kikayi ne?


Eh" madam din tafada Kai tsaye tana cigabada da aikin datakeyi.


To Ina tayaki murna madam bansan an maidake manager ba da bana nan.


Aje Abinda takeyi tayi tana yiwa amatun kallon mamaki sbd tasan baqar Magana ce ta jeho Mata wato tunda ba itace manager ba bazata iya korarta ba.


Amatu na ganin ta kunnata ta gyara tsayuwarta zata sake wata maganar aka bude qofar shigowa ana cewa" welcome ma.


Madam ce tayi saurin aje towel din hannunta tana nufar qofar bakinta a washe tana cewa'

Welcome ma.


Gyara tsayuwa amatu tayi batareda ta juyaba Kuma batada alamar juyawar 

Taji ankira sunanta 

Da sauri ta juyo sbd ta 'dau muryar 

Aikuwa ita din ce ta qarasa gabanta tana kallon madam bell tasaki yaqen tura haushi tace"


Madam dama bankwana nazo Miki tareda tayaki murnar samun matsayin manager Dan haka Allah ya sanya alkairi.


Kallon hajiya aisha tayi tana qaqalo murmushi tace"


Haj Mama Ina kwana???


Murmushin mamakinta umme tasaki tareda kallon madam bell tace"


Dama ita nazo nema sai dai next time idan nadawo,amah muje ko???


Gaba amah tayi tana murmushin farin cikin daga yau rayuwarsu zata canja idan har hajiya mama tabata sabon aikin datake cewa.



Motar haj Aisha din suka shiga wani sanyin AC da qamshin ya ratsata ta lumshe ido tareda shafa kujerar motar datajita da wani irin laushi da santsi,

Yaune karo na farko a rayuwarta data taba shiga motar Dana taxi ba ko taxi din tafi shekara goma rabonta datashiga.


Kallon motar takeyi tako Ina tana tabawa ta kasa 6oye farin cikin datake ciki a fili tace"


Hajiya mama ko ahaka Kika barni kincikamin qaramin burina....


Dauke Kai haj Aisha tayi cikin gundura da amatun tun yanzu tace"


Motarma gaba daya zata iya zama mallakinki ko 'dan uwanki usi da Wanda ma ya tsinceku idan har zakiyi Abinda nakeso Wanda a wata biyar kingama aikinki Kuma kin mallaki Abinda zakiyi hannun riga da talauci.



Parking motar tayi daidai kwanar gidansu amatun Wanda yasata juyowa ta kalleta ta yanda tasan gidansu zatayi magana hajiya aishan ta katseta Kai tsaye da cewa"


Zan baki naira miliyan uku tareda makaranta me tsada wa 'dan uwanki harya gama sai gidan zama me kyau ga kawunki da jarin sana'a me kyau ga matar kawunki idan har zakimin Abinda nakeso.


Suman zaune amatu tayi tareda sakin baki gaba daya ta daga hannu tana lissafa abubuwan da hajiyar tace har lissafinta ya 6ata tayi saurin girgiza Kai tana 'dan dukan kanta tace"


Amatu amatu amatu dawo kanki... Dawo kanki.....

Hajiya mama duka abubuwan Nan dakika fada saidai naji kokuwa kunnuwanane????


Qaramin tsoki umme tasaki tareda bude wata 'yar jaka dake daukeda kudi dubu 'dari uku ta miqa Mata tana cewa"


Kije kibawa su kawunki wannan idan kingama aikin zanbaki dukannin Abinda nace

Qaninki kuwa zanbaki takardun makarantarsa ki riqe a hannunki.


Da sauri ta karba kudin ta shafa cikin zaquwa take cewa"


Wannan yanxu duk nawane halak malak??

Hajiya mama na amince zanmiki aikinki koma wane iri ne na shekara biyarma zanmiki bana wata biyar ba.


Kallon takaici umme tai Mata tana mamakinta saidai duba da 'yar tashace Kuma 'yar bola hakan ba wane abin mamaki bane Dan duka tarihinsu tasamu agurin binciken datasa akai Mata akansu Wanda alhaji mande ne yabada bayajin

Shiyasa tasan tsaf amatun zatayi wannan aikin ba gashi indai akan kudi ne.



Zanje dake gidana zaki gabatarda kanki a matsayin wadda akayiwa fyade harda ciki ajikinki,

Ba shaidu,

Duk wasu manyan shaidu na tanadar Miki su tun daga Kan likitoci harzuwa Abinda zai biyo baya,

Aikinki na kammala na tanadar muku gida da sanaar yi a wani guri can nesa da Nan bazaku sake dawowa Nan ba shikenan kunyi bankwana da talauci da damuwa zaku samu damar Fara sabuwar rayuwa.



Duk iya yanda ta rude da Jin abubuwan dazata samu Bata taba kawo hajiyar batada isashiyar lafiya ba sai yanxu datai wannan maganar Amma Kuma bataga alamar hauka atareda ita ba,

Itadai yanxu matsalar dayace ko haj nada lafiya ko batada bazata mayar Mata da kudin nanba.


Yanda amatun ke kallonta yasa ta fahimci tunaninta ta 'dan qaqalo sakin fuska tace"


'dana ne nice na haifesa

Nasa kimin hakan ne sbd banason abawa 'yayana mulkinda zasu cutu Kuma Allah ya tambayesu ranar qiyama,

Mulkin zabeera akwai hadari,

Za'a iya hallakarmin da 'yaya sbd kwadayin mulki shiyasa nakeson kije amatsayin hakan Dan kada abawa 'yayana mulkin da zarar an nada wanda yakamata a nada zan kaiku inda zakuyi rayuwa cikin farin ciki da walwala.


Shiru amatu tayi tareda gyada Kai sbd soyayyarta da kudi yasa Kai tsaye tayi na'am da hakan Kai tsaye tunda daima ceton Rai ne zatayi koba komai Babu ruwansu da wani abin kunya tunda dai bayi tayiba tasan dai kawu ne bazai yadda da wannan tsarin ba bare iyami.



Kallon kudin tayi ta kalla hajiya aishan tace"


Kinada tsarin fadawa kawuna ya amince???

Dan nidai nariga na amince.


Murmushi umme tasaki tareda tayarda mota suka qarasa shiga layin gidansu amatun tace"


Kawunki bazaisan gskia ba sbd gudun samun matsala agaba,

Kidai saka aranki aikin kudine zakiyi domin samun ingantacciyar rayuwarsu kawai zan aiko a sanar dashi kinsamu aiki a zabeera tareda albashi me kyau zaki ringa zuwa duk sati kina ganinsu har tsawon wata biyar.


Kawu bazai yadda ba"tafada tana tunanin mafita.


Karki damu zai yadda idan wadda zanturo tazo saiki qara da dubarunki ta yadda zai yarda.


Kallonta amatu tayi kafin ta kalli kudin tsawon daqiqu tana nazari zuciyarta na son yin rawa a alamarin Amma burinta na hana hakan.


Rintse idanuwa tayi tareda sauke ajiyar zuciya me qarfi ta furta na amince saitazo nikuma Ina fatan wannan alqawarin yacika.


Gyada Kai kawai hajiya aishan tayi tareda nuna Mata qofa.


Fita tayi tareda kudin tabi motar hajiya aishan da kallo harta bace mata ta sauke ajiyar zuciya tana cewa'


Amatu wannan sa'a ce ko rashin sa'a???


Tana shiga gida Kai tsaye gurinsu kawu taje Allah yasa duk suna dakinsu kawun harda USI dayashigo yanashan magani kawu Kuma na gefe yanashan waqar 'dan indo,ta qaraso ciki tana sallama tareda qarasawa ta zauna gefen iyami dake ballowa usi magani ta ajiye Daurin kudaden tareda sauke boyayyan numfashin zancen dazata qirqiro.


Idon kawu na sauka kan kudin yatashi zaune da sauri daga kishingiden dayake Yana qarar radionsa Dan kada aji Abinda zai fada yace""kudi" Yana sake bude idonsa akansu.


Iyami ma dakatawa tayi daga bude maganin ta kalli amatu da sauri,


USI ma kallon amatun yakeyi zaiyi magana ta rigasu da cewa"


Duk nasan tunani kukeyi dabam dabam 

Iyami wlh tallahi ba kudin wasu bane na dauko,

Kawu aiki aka koreni sbd nayi kwanaki banje ba to, to ,to shine dama inawa wata babbar hajiya mama aiki a saloon dinmu shine tace ita zata daukeni aiki zata budemin gurin aiki irin fire fox me sassa dabam dabam wanda nice zanzama managan gurin Amma....


Amma me????iyami ta tambaya da sauri zuciyarta naqin gasgatuwa da zancen..


Amma Wai sai nashiga training dinda zaayiwa manyan ma'aikatansu a can inda aka kebe na tsawon wata biyar zuwa shida.


Tsit sukayi a dakin duka kowa na qoqarin fahimtar zancen saidai ta Yaya??


Kallonta USI yayi dakyau yaga itama shi take kallo yace"


Amah idan har cigabanki ne me kikeso yanxu to.


Kallon kawu da iyami tayi Shima kawun kallonta yake yace"


To wannan kudin fa???


Kai tsaye tace kudin albashinane aka bani na watannin Dan daukar nauyin Kai kafin mu fito training din.


Iyami ta kalla tace"


Wlh iyami aiki zanje Yi ba qarya nakeyiba na rantse Miki...


Duk shiru sukayi kafin kawu yace"


Naji kuje zanyi tunani akai.


Miqewa tayi ta fito usi ya biyo bayanta suna fitowa yafara watso Mata tambayoyi tajasa zuwa dakinta da sauri Dan kar kawu yajisu suka zauna tafara yimasa bayani komai Kai tsaye yace wlh bai amince ba.


Hayaniya suka Fara tayi saurin rufe qofa tana cewa"


Idan baka gaji da yawon cell ba ana maka dukan wulaqanci to ni nagaji da ganin hakan,

Rayuwa me kyau nakeson muyi kamar kowa Usman,

Idan har kanason farin cikina danasu kawu wannan maganar mungamata,

Banyi Dan Jin dadinaba sai Dan wainnan bayin Allan dasuka sadaukar da komai saboda mu,

Babu uqubar dabasu shigaba amma suka riqemu da Amana,

Kaima inason ganin kasamu ingantacciyar rayuwar sbd ka tallafesu a gaba Dan ni nasan rayuwata acikiku taqaitacciyace kobanaso nasan Dole wata Rana kawu saiyamin aure..


Usman mubar maganar Nan kawai qwarin gwiwarka nake nema.


Kallonta yayi idanuwansa na cikowa da hawaye yanajin inama ya mutu ya rage Mata 'dawaimiyar datake ganin itace akai,

Maimakon yazama jagora Amma yazama wani irin koma baya itace jagorar.


Ficewa yayi Yana share hawayen fuskarsa dasuka saka jikinta yayi sanyi matuqa Amma batajin zata fasa sbd tariga takai qarshe zasu bar Nan din sbd karatun Usman din.



Kwana biyu ana rigima sosai a tsakaninsu kafin iyami da Usin suka amince akan aikin nata bayan dattijuwar da aka aiko tayi zuwa kusan hudu tukuna.,


Kwana uku masu zuwa zata tafi Amma duk sai jikinsu su hudun hakanan ya mutu sosai suka shiga damuwar tafiyarta duk da dai Basu fadaba sai hakan yataba 'yan gidan Suma sbd su kawun dadu amah sune hayaniyar gidan dake qara Raya gidan shiyasa Suma duk sai sukaji ba Dadi,


Amatun ma hakanan takejin kamar zata rabu dasu kawun ne rabuwar har abada Wanda usi ne ma tadawo Yana qoqarin cire Mata damuwa,


Iyami da kantace ta hada mata duk wani abin buqata a 'yar Jakarta ta goyawa ranarda akazo tafiya da ita iyami duk hakurinta saidatayi hawayen rabuwa da amatun sbd zuciyarta takasa samun nutsuwa da tafiyar,

Kawuma kasa rakiyarta waje yayi saidai Usman ne aka tafi dashi Dan yaje yaga inda take.


Su maman junior hadda rungumeta sukayi sunajin kewarta tun Bata tafiba.





****

Wayarta data gamayi ta kalla tareda kallon haj Maryam dasuke zaune a palon tace"


Su amah ne gasunan a hanya isowa zasukai mintuna ashirin kafin su iso zuwa lokacin an halarta gurin meeting din familyn ZABEERA daza'ayi yau

Yau komai zai qarewa MD ZABEERA.


Murmushi haj Maryam tasaki tana miqewa tsaye tace"


'yan jaridar Dana gayyatoma suna daga baya suna jiran kirana suzo ya sakarwa duniya wannan labarin da dumi duminsa.


Dariyar farin ciki suka saki atare daidai lokacinda nuratu tashiga cikin kyakkyawar adonta na wata Kuwait jallabiya datayiwa fatarta kyau sai qamshi takeyi tace"


Momy kusan kowa fa ya halarto dan gasu anty bahijja nacan sun iso taredasu anty juwairiyya dasu baba qarami.


MD ZABEERA ma Naga shigowarsa yanxu tareda ZARAH.


Kallon juna sukayi tareda cewa"


Shikenan muje.




***

_40 min later_


A bakin babban qaton gate din ZABEERA motarsu ta Parker Wanda akayi juyensu da ita zuwa wata matacciyar golf baqa.,


Akaro na farko ta 'dago hoton MAHMOUD ZABEERA da aka Bata bayan anmusu bayani wasu abubuwa akansa ta kalli hoton zuciyarta tayi wata irin bugawa akaro na farko...


Rintse ido tayi zuciyarta na wani irin tsalle tayi saurin rufe hoton tana dafe zuciyarta dake bugawa da qarfi tace"


Ya Salam..


Meyasa zuciyarta ke bugawa da ganinsa a hoto???


Kallon Babar dasuka Zo tare tayi tana qoqarin Hana zuciyarta bugawa Amma sai qara bugawa tayi tayi saurin miqa Mata hoton tana cewa'"


Ki riqe a hannunki nariga Naga hotonsa zan ganesa da kaina.


Kallonta baba Jamila tayi tana cewa'"


Ki nutsu fa.


Gyada Kai tayi tana yiwa qatoton gate din zabeeran kallon kwadayi da qauyanci.


Shima usi kalle kallen yakeyi baki abude sbd tsananin girma da kyan gate din kafin suka nufo gate din Babu dogon musu sbd babban security in charge yasan da zuwansu yasa aka Bari suka shigo suna kalle kallen baki asake 

Amatu tace"


Usi kana ganin Abinda nake gani kuwa????


Kasa magana yayi yafarabin manyan motacindake harabar gidan da kallo Yana cewa'"


Wlh amatu wannan gidan aljannar duniya ce muka shigo.


Itama motacin tahau shafawa tana cewa'"

Aikuwa sa'a takawoni Nan ni amatu.

##mamuh##



______________

KUNA BUƘATAR A TALLATA MUKU KAYAN SANA'ARKU A PAGES ƊIN BOOKS ƊIN ZAFAFA BIYAR 2021?.


To kuzo ga dama ta samu💃🏻💃🏻.


        Ina ma'abota son a tallata musu hajojinsu a kafafen yanar gizo suke?.


Tofa kuzo dama ta samu, dan jerin gwanon haziƙan marubanku ƴan biyar sun fiddo muku da hanyar da kuma kasuwancinku zai zagaya lungu da saƙo ta dalilin shafukan littatafai.


Ga duk mai buƙatar a saka masa tallan kayan sana'arsa a shafin littatafan mu na zafafa biyar zai iya tuntuɓar waɗan nan Numbers 0903 234 5899 or 09033181070 ta vWhatsApp, idan har agama buks ɗin kana buƙata a sakamaka talla zamu saka maka akan farashi mai sauqi. Idan kuma wasu adadin pages kake buƙata koda ɗaya ne duk zamu saka maka akan farashi mai sauƙin gaske🤓.


Kuyi maza ku kawo, mai haja shike talla, mai saya kuwa shike neman sauƙi😻😻😄🤗.


______________________


#MIN QALB❤️

Mamuhgee


ZAFAFA BIAYAR


SIRADIN RAYUWA

safiyya huguma


MIN QALB

mamuhgee


YANKAN BAYA

billyn Abdul


KIBIYAR AJALI

Miss xoxo 


ABINDAKE CIKIN ZUCIYATA

hafsat rano


Pay @09033181070

Or 09032345899

Post a Comment

0 Comments