TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 48-49

Mamuh#*_MQ 48_*


*_THE FLAVORLAND BY ACEEY_*

Ina ma’abotan son ingataccen yaji, Different Flavors that complements each other, Yajin da ke daidaituwa da duk sinadaran abinci na al’adance da zamanance, Muna muka albishir da sanardaku cewa nesa tazo kusa domin @the_flavorland by Aceey yakawomuku duk nau’ukan yajinda kuke iya buqata Saboda yajin ya hada da:

Daddawa Yaji, Waton yajin daudawa

Garlic Yaji, waton yajin tafarnuwa da kuma

Beef Yaji, wato yajin Nama kuma me hade da nama

Domin ayukkanku da yau da kullum wanda ya hada da:

Dahuwar abinci/nau’uka na miyoyi DA

Gashe gashe da soye soye kamar su

Kaza

Kifi

Nama

Doya

Dankalin turawa/hausa

Awara

Danwake

Gurasa

Kwado da dai sauransu....

Ba Mu tsaya anan ba——

The_flavorland ya hada da kayan tande tande da lashe lashe da suka hada da

Hoppers wato Fara

Milky candies wato alawar madara da kuma

Milky balls wato Gullisuwa da de sauran abunda rai ke buqata...

Zaku iya tuntubar mu a kafofin sada zumunta kamar haka

IG: @the_flavorland

Whatsapp:08104673847

Sending Some treats your way.... l


Let us satisfy your cravings:

We Deliver anywhere and everywhere.

*******



*********

Suna Isa zabeera Kai tsaye motar data daukota sashen Andi aka nufa dasu sbd har Modibbo da umme na can dashi kansa MAHMOUD din Wanda ranar yakoma MD ZABEERA dinsa sak miskilanci da izzarsa sun motsa ko wayoyinsa duk akashe ma suke Abu daya kawai yakeji atare dashi shine nutsuwar zuciya data ruhi harma data gangar jikinsa Wanda yagama tabbarwa da kansa cewa tabbas Amatu tarigada tazama wani babban bangare an zuciya,jiki da rayuwarsa tunda haryakejin wannan nutsuwar me sanyin Dadi tattare da dawowarta garesa.


Suna shigowa akansa idonta yafara sauka ta dauke Kai Yana sunkuyarwa ta zauna daga qasa gefen umme dake kallonta fuskarta na bayyanarda farin ciki da murmushi.


Da MAHMOUD din Andi yafara nasiha akan haqqoqan Mata dake Kan mijinta dakuma ire iren halayen .ata da Dole namiji saiyayi hkr dasu sbd rauninta dakuma rashin zurfin tunani  da Rashi haquri irin na wasu matan kafin yadawo Kan Amatu da nasihar zama da miji da girman haqqoqinsa akanta da girmansa dayafi na kowa akanta yanzu yaqara da nasihar adalci tsakanin mataye biyu dakuma haqurin zama da abokin zama Dana rayuwa kafin daganan Andi yayiwa Amatun kyautar aure ta sabuwar mota fil sak irinta zarah datake hawa banbancin kalane kawai dayace Tata Ash ce ta zarah farace.


Godiya sosai sukayi suka fito umme na riqeda hannun ta saka Mata wani acikin hannun dayake rufe cikin qaramar kwalbar roba suna shiga mota tace"


Shanye kiban roba.


Kallon ummen tayi tana sake kallon abun ta Dan 6ata fuska zatai mgn tace"


Bansan Jin komai hanzarta kishanye kiban.


Marairaice fuska tayi tana kallon abun.

Anty salamatu dake sit din gaba ta juyo ta kwace kwalbar ta bude tareda Dora Mata abaki tana cewa''


Dallah shanye da abin dadine da yanzu kinfara maganar qari to wannan dadinsa saikin fi kowa.....


Rufe Mata baki Amatun tayi da sauri tana zaro Ido kunyar umme kamar ta nitse ta saci kallonta tace"


Haba anty salamatu nidai karki fara zancenki Dan Allah.


Itama anty salamatu kunya taji sbd mantawa tayi da umme da iyami dasuke taredasu sbd sun Saba zantukansu na banza dasu maman junior shiyasa.


Shanyewa tayi ta miqawa umme kwalbar daidai isowarsu qofar part dinta motar har qofar palonta ta faka suka fito umme na riqeda hannunta tana fada maganganu qasa qasa na rikita miji wainda sukafi qarfin duk rawar Kan Amatun kunya kamar ta qwace hannunta ta zura da gudu Amma ummen ba ruwanta fada Mata takeyi har suka shiga suka zauna palon tana sake zayyano Mata zantuka masu qarfi wainda wasune suka samu damar shiga kanta wasu kuwa nauyinsu yasa suna kasa shigewa Kan nata.


Turaruka ummen ta fitar cikin jakar hannunta ta fesawa Amatun ko Ina jikin masu wani irin sanyin qamshi dagaji tasan bazasu wuce ouds ba masu tsananin tsada take qamshinta ya qaru tana fitarda wani qamshi me ni'imtaccen sanyin dadi suka Fara qoqarin tafiya anty salamatu tace"


Zarah ko lafiya Naga banganta ba na dauka ma zamu sameta anan gashi har zamu tafi.

Umme tace'


Eh Kam gashi dai Nima duk yau banganta ba Nima nai zatan zamu sameta anan din tana jiran isowarmu.


Iyami data miqe tsaye tana gyara zaman mayafinta yace"


Mezaisa zarah tazo ta zauna anan tana jiranmu karku manta bafa kamar da bane yanzu ana Magana akan Amatu tazama matar mijintane Dole wani abun zata Kama kanta ba kamar da ba da Amatun take matsayin qanwarta yanzu kishiyarta ce Dole akwai radadi ko yayane aranta.


Tsit Amatu tayi tana saurarensu sbd duk lokacinda akai Mata tunin kishiya saitaji kamar hankalinta nason tashi saidai girma da nauyin anty zarah da haryanxu take gani da ji atareda ita yana danne kishin datakeji shiyasa take sauke zafin kishinta agun MAHMOUD sbd bazata iya kallon fuskar anty zarah tayi fitinar kishi da ita ba duk zafin kishinsa kuwa sbd Abu daya data fahimta takuma lurarwa kanta MAHMOUD da kansa zai iya kiranta butulu akan zarah idan bata nutsu ta iya zama acikinsu ba yanzu Kam akwai aiki agabansu su dukan na iya zama da juna.


Bayan tafiyarsu iyami kasa tashi tayi daga Inda take zaune tashiga tunani daban daban akan rayuwarta da Kuma ranar farko da aka Fara kawota cikin part dinnan amatsayin matar KHALIL DAHEER ZABEERA yanzu Kuma gashi ankuma kawota amatsayin matar Dan uwansa MAHMOUD DAHEER ZABEERA,

Duk da ansauya sashen gabaki daya Babu inda zaka iya gane shine wancan din Amma dai memories diinsa suna cikin zuciyarta.

Hawayene suka ciko idanuwanta suna qoqarin gangarowa taji bude qofa 

Bata dagoba Amma qamshin daya shiga cikin hancinta da motsinsa da baya qarfi yasa ta fahimci waye yashigo ta rufe idanuwanta ta bude ahankali batareda ta dago ta kallesa ba saima sake lumshe idanuwanta datai.


Qarasowa yayi cikin nutsuwarsa da kamalarsa ya zauna kusada ita sosai qamshinta ya Shiga hancinsa yanl dago fararen idanuwansa dasuka Gama gabalaituwa a sonta ya zuba Mata tareda riqo hannuwanta ya sarqe da nasa ya sauke ajiyar zuciya wadda itama ta sauke tata a boye cikin cikinta.

Kasa Magana yayi sbd bayajin yin maganar ya kwantarda kansa Kan kafadarta Yana sake sarqe hannuwansu ya lumshe idanuwansa sukai shiru ahakan sai numfashi da qamshin juna dasuke shaqa nutsuwa na shigarsu duk da Babu Wanda yafito yagfada Amma numfashinsu dake fita ya bayyanarda hakan.

Sun jima ahakan Babu wani motsi Saida yagama samun dukkanin nutsuwar daya rasa kafin ya sauke numfashi tareda dagowa ya kalli fuskarta suka hada idanu ta sauke nata tana qoqarin rufesu ya Kai hannu ya juyo da fuskar tata Yana kallon halittar da ita kadai ke iya rikita MD ZABEERA baisan lokacinda ya saki wani irin murmushi ba yana kallon bakinta daya iya fidda Magana ta arziki data tsiya.

Fuskarsa yakai dab da tata Yana kallon cikin idonta yabawa bakinta light kiss Yana sake sakin murmushi cikin taushin muryar data sanyata dago idanuwanta cikin rashin yadda ta zuba Masa yace"


I can't live without you Mrs MD ZABEERA so kada ki sake tunanin barina sbd komai zakiyi bazaki iya barin rayuwa Dani ba.


Miqewa yayi tsaye hannunta cikin nasa har lokacin ya miqar da ita Yana cewa''


Let's have dinner zarah is waiting.


Ba musu tabiyosa suka fito hannunsa na riqe da nata itama saiyi takeyi tana kallonsa duk da tasan so yake azauna lfy Amma dai mamakinsa bai daina kamata ba sbd ganin yanda ya sauya din dama ita batada niyar zama da miji Babu shaquwa Babu Wasa da dariya Babu hayaniya Babu muguwan wasan gudu gudu idan ma takama to Ina dadin rayuwar auren take tanason morewa sauran kuruciyarta a tareda mijin aurenta Dan haka Babu wani daga mulki sai oda a Shirin zamanta dashi.


Suna shiga anty zarah na fitowa daga bedroom dinta cikin adon riga da skirt na lace maroon tayi Yar simple makeup ga qaramin cikinta daya Dan fito tayi kyau itama sai qamshi take saidai suna qarasa shigowa qamshin dake fita cikin Amatun saita ji ta daina Jin natan ta qurawa Amatun idanuwanta dake son raunana da irin dacewa da kyan dasukai tareda juna ta kalli hannuwansu dake sarqe tafara Kiran sunayen Allah tana kore shedan daga zuciyarta ta saki murmushi tana kallonsu tace"


Sannu da zuwa Amatu.


Murmushi Amatun ta saki tana kallonsa da shima ita yake kallo tace"


Thank you anty.


Kallon MD din zarah tayi tana dauke idonta daga Kan hannunsa dake riqe Dana Amatu tace"


Dinner is ready fa.


Dining suka nufa su dukkansu suka zauna zarah ce ke zaune kusada MAHMOUD din sukaci abinci itadai Amatu drink kawai Tasha sai spoon biyu datai ta miqe tace ta qoshi.


Shima ba wata yunwa yakeji ba Amma ya zauna yaci abincin sosai tareda zarah haryana yaba abincin sosai sbd Fara sanin halin Mata dayayi ya fahimci sunfi son ko yaushe ka nuna musu yabawa da kulawa.

Aikuwa hakan ya faranta ran zarah musamman daya nuna Jin dadin abincin a fili saitaji damuwarta ta ragu sosai suka baro dining din itama Yana riqeda hannunta suka iso ya zaunar da ita Kan kujera ya zauna gefenta Yana kallon Amatu data matsu tawuce yafara musu bayani da nasiha tareda roqon Dan Allah a zauna lfy plus respecting juna duk da yasan suna ganin qimar junansu sosai kafin ya sanar dasu 2days ne kwanan daga haka aka tashi Amatu tafara wucewarta shikuma zarah yabi Dan sake lallasarta Abinda Baya faruwa a zamansu mamakinsa da Jin dadin hakan ya sanyaya zuciyarta sosai harta cemasa yatafi gurin Amatu tana jiransa.

Bedroom dinsa ya nufa yashiga wanka Yana fitowa Saida ya tsaya wata waya kafin ya fice.


Bedroom 'dinda ta tabbatarda shine nata tashiga data dawo daga sashen na zarah ta ajiye wayarta ka bedside drawer ta warware lafayarta ta nade takai wardrobe

tana budewa ta tsaya kallo cikin mamakin ganin Kaya a shaqe maqil da hadda wainda aka dinka da wainda ba'a dinkq ba ga qananun Kaya da jallabiyas ire iren wainda yasan tana sanyawa.

Murmushi ne yaso subuce Mata data Kai hannunta Kan tarin qananun kayan dake jere Wanda taga bumshorts ne sukafi yawa abin data lura yafiso kenen wato shigarta zata fiddo cinyoyinta duka a waje.


Rungumeta taji anyi tayi saurin juyowa sbd bataji motsin shigowarsa ba,

Kallon fuskarsatayi cikin basarwa ta zame daga jikin nasa ta jefa lafayar ta rufe wardrobe din ta bar gurin ta nufi toilet ta jima ciki Babu Abinda zatayi tana saqa da warwara kafin dai ta wanke hannuwanta tayi alwala kawai ta fito tana goge fuskarta da qaramin towel sai ganin lafayarta tayi ya miqo mata Yana cewa''


Ki mayar inason nizan cire miki inason sake ganinki cikinta you look innocent acikinta.

Batareda ta kallesaba ta karba ta nufi gaban mirror tana nadawa ya zauna Kan sofa Yana kallonta hannuwansa nade da qirjinsa.


Tana gamawa ta juyo ta kallesata ta gefen Ido ya taso Yana murmushi ya Kama hannunta suka nufi bedroom dinsa suna shiga wani sanyin qamshi ya doki hancinta sbd kalar turarukansa ba Arabians bane nasa designers Eglh perfumes yake amfani dasu,

As she expected komai na dakin fari ne da milk sbd sune colours dinsa.

Daddumar sallah ya Ciro itama milk color ce ya shimfada Yana kallonta yace"


Kinyi alwala right?


Saida ta dauke Kai kafin tabude Baki daqyar tace"

Yes.


Yanda taketa daure Masa din Yana sake burgesane Bata saniba sbd shi fushin ma nata Yana Masa kallon wani sabon feeling.

Sallah sukayi ta nafila rakaa biyu kafin ya juyo ya riqo hannuwanta duka biyun Yana kallon fuskarta ahankali ya furta"


Sorry.


Qin juyowa tayi ta kallesa ta zame hannuwanta zata miqe ya matse hannun Kai tsaye yace"


I love you..


Cak ta tsaya daga qwace hannun dazatayi zuciyarta ta Fara tsananta bugu takasa motsawa hakama takasa juyowa ta kallesa.


Ya lumshe idanuwansa yasake budewa ya Dora akan hannuwanta dayake riqe dasu cikin murya me taushi yasake cewa''


I love you AMATULLAH K SALEH and I am saying sorry so please wannan fushin yakamata ya sauka please.


Juyowa tayi tana kallon fuskarsa zuciyarta na qarasa bugawa da qarfi ta kasa yadda da Abinda taji idan MAHMOUD ZABEERA dinda tasani ne yake furtasu saidai zumudin zuciya dakeson kamata gudun bada kanta yasa ta miqe ahankali tana zare hannuwanta ya dawo da ita jikinsa ta hanyar fixgota ta Fado qirjinsa ya Bata kyakkyawar runguma Yana fada Mata Magana cikin kunnenta data sanyata saurin zaro Ido waje tana kallonsa takaici da muguwar kunya suka dabaibayeta batasan lokacinda ta Fara mintsinansa ba ta bude baki Dole tana cewa''


Wlh ni sharri ne wannan kakemin, Allah bazan yaddaba....


Dariya yakeyi Mara sauti da hayaniya wadda yaune karonta ba farko ganin dariyarsa ba murmushi ba.

Ganin ta kunnu sosai da Abinda ya fada din yasashi miqewa Yana Sosa inda ta mintsinesa Yana cewa''


Zaki fasamin fatane da wannan mintsinin naki..

Biyosa tayi tana sake kunnuwa har lokacin kunyar zancen bai saketa ba ta nufesa tana cewa''


Saika janye wannan sharrin dakamin bazan yadda ba..

Tana isowa gurinsa ya riqe hannuwan tareda shigar da ita jikinsa ya Kai fuskarsa Kai tsaye ya hade da Tata ya hade bakinsa da nata yana Bata wani ni'imtaccen kiss daya kashe jikinta harya warware Mata lifayar jikinta Bata saniba Saida ya cirata gabaki daya zuwa Kan qaton gadonsa Yana rage musu hasken dakin ta makunnin gefen gadonsa.

##Mamuh#*_MQ 49_*




*_THE FLAVORLAND BY ACEEY_*

Ina ma’abotan son ingataccen yaji, Different Flavors that complements each other, Yajin da ke daidaituwa da duk sinadaran abinci na al’adance da zamanance, Muna muka albishir da sanardaku cewa nesa tazo kusa domin @the_flavorland by Aceey yakawomuku duk nau’ukan yajinda kuke iya buqata Saboda yajin ya hada da:

Daddawa Yaji, Waton yajin daudawa

Garlic Yaji, waton yajin tafarnuwa da kuma

Beef Yaji, wato yajin Nama kuma me hade da nama

Domin ayukkanku da yau da kullum wanda ya hada da:

Dahuwar abinci/nau’uka na miyoyi DA

Gashe gashe da soye soye kamar su

Kaza

Kifi

Nama

Doya

Dankalin turawa/hausa

Awara

Danwake

Gurasa

Kwado da dai sauransu....

Ba Mu tsaya anan ba——

The_flavorland ya hada da kayan tande tande da lashe lashe da suka hada da

Hoppers wato Fara

Milky candies wato alawar madara da kuma

Milky balls wato Gullisuwa da de sauran abunda rai ke buqata...

Zaku iya tuntubar mu a kafofin sada zumunta kamar haka

IG: @the_flavorland

Whatsapp:08104673847

Sending Some treats your way.... l


Let us satisfy your cravings:

We Deliver anywhere and everywhere.




************

Ahankali ta bude idanuwanta dake cikeda nauyin baccin dabai Gama isarta ba sbd sai Bayan sallar asuba ne tasamesa tana Gama budesu da kyakkyawar fuskarsa tafara cin karo daf da tata numfashinsu na sarquwa cikin na juna,ta kalli idanuwansa dake lumshe ta gangaro da idanuwanta Kan lips dinsa wani gajeran murmushin samun nutsuwa ya subuto Mata ta motsa hannuwanta dake sarqe cikin nasa taji yasake matsesu ta maida kallonta Kan fuskarsa da mamakin da alama idanuwansa biyu kenan?

Hancinsa taji akan nata ya hade fuskarsu ya Dora mata ta Kai idanuwanta Kan idonsa daidai Yana budesu cikin kasalar baccin dabai Gama sakinsa ba ta dauke idanuwanta ahankali daga nasa zata sake zamewa yasake qin Bata damar motsawa.


Ahankali ta bude bakinta dake daidai kunnensa cikin qaramin sautin daya qarasa kashe jikinsa da saukar Masa da kasalar tace"


Yunwa.


Daqyar ya iya bude idanuwansa dasukai laushi da yanayin yanda dumin numfashin bakinta ke shiga cikin kunnensa ta maganar datai Masa.

A kasalance ya saketa ta tashi zaune ta sauka daga Kan gadon ta nufi toilet ta Shiga.

Wanka tayo tana fitowa daureda towel brown ta nufi closet dinsa ta dauko wani sabon towel din qarami Tana sake goge kanta ta nufi gaban mirror Yana duba dryer Amma Babu a dakin ta waiwaya ta kallesa taga idanuwansa qyam akanta Yana binta dasu kamar wani mayen qarfe saita fasa tambayarsa sbd ganin hadda miskilancinsa daya hanasa tashi bare Magana sai binta yake da idanuwa ta nufi qofa ta fice zuwa bedroom dinta sbd akwai acan taganta jiya gaban mirror.


Tana Isa dakin ta zauna gaban madubin ta jonata ta kunna ta hau busarda gashin tana kallon fuskarta dake wani irin blushing da qyalli ta cikin madubi,

Tana gamawa ta gyara Kan ta daure ta shafa Neutrogena oil sai bodymist dasu spray ta qara da humra me sanyin qamshi ta miqe takoma jikin wardrobe ta bude Bata wani tsaya zabe ba ta dauko wani plain drylace peach ta saka riga da skirt ne saita fito Palo tana qoqarin nufar kicin akai Knocking ta nufi qofar ta bude,

Cikin sa'a kuwa abinci ne anty zarah ta aiko musu Dan haka saita fasa aikin ta ajiye a dining ta Kama hanyar zuwa tadoshi aka Kuma knocking taje ta bude wani abincin ne daga umme itama ta karba duk ta hada ta ajiye a dining tana juyowa da nufin zuwa tadosa saigashi yafito shirye tsaf cikin wani milk yadi me tsananin taushin daya bayyanarda tsadarsa fili ya nufota Yana kallon kwalliyarta tareda nuna yabawarsa a fili Yana Mata kallon qasa qasa daya sanyata Jin kunya me tsanani sbd kallon ya qunshi yagama da saninta cikinta da wajenta ga sauke Kai daga kallonsa tana juyawa ya riqota ya dawo da ita gefensa suka nufi dining din Yana kallonta qasa qasa da wani irin murmushi harsai data gaji cikin muryar shagwaba tace"


Dady Allah zantashi na tafi.


Qaramar Daria Mara sauti ko kadan yadan saki Yana sauya kallonsa daga kanta yace"


Ok sorry sorry na daina Zo Nan lemme feed you.


Akan cinyarsa taci abincin tana bashi Yana Bata sai sake kashe Masa jiki takeyi da rashin zamanta guri daya ajikinsa daqyar dai aka gama cin abincin ya dauketa suka koma daki tana wani zille zillen daya qarasa juyar dashi daga MD ZABEERA.



Qarfe goma sha daya harda kusan rabi suka fito tana riqeda hannunsa ta sauya wasu kayan sbd wani wankan datayi tayi simple makeup da wani irin hot red lipstick daya zauna daram Kan lips dinta dayaketa saukar hankalinsa Amma Dole ya dauke Kai suna shiga palon zarah ya saki hannunta ya nufi sama inda hafsatu tace musu tana can yatafi yabarta tana kallon hannunta daya saki domin zuwa ga wata wani rashin Jin Dadi ya taso ya rufe zuciyarta ta zauna Kan kujerun dake palon Ahankali tana Kiran sunayen Allah tareda kore shedan daga cikin Kai da tunaninta taji motsin saukowarsu ta daga Kai tana kallonsu hannuwansa duka biyun riqeda zarah din suna saukowa yanajin kamar ya daukota gaba dayanta ya sauko da ita sbd ganin yanda take tafiyar sbd tace Masa da ciwon qafafu ta kwana.


Har Kan kujerar yakaita ta zauna Rana kallonsa cikin farin cikin kulawarsa gareta tace"


Thank you MD.


Murmushi me sanyi ya sakar Mata Yana zama kusada ita yace"


Akwai godiya tsakanin miji da Mata ne?


Dariya tayi tana kallon Amatu dake qaqalo murmushi tace"


Amatu Yana tambaya tayani bashi amsa sbd zaifi ganewama idan Kika fada Masa Dan Naga yafi gane yarenki.


Maganar ta daki zuciyarsu daga Amatun har shi Musamman shi ya tsura Mata idanuwansa yanajin wani irin yanayi me nauyi na rashin Jin Dadi wato tariga da ta amincewa kanta yafi son Amatu kokuwa yafi daukar Amatun da mahimmanci akanta ko me?


Amatu ma Jin tayi nauyi da rashin Jin Dadi ya dabaibayeta take sbd maganar antyn Magana ce data fito dauke da raunin da zuciyarta ke ciki batareda tasani saitakejin sabon mutuncin antyn na sake shigarta koba komai haryanxu anty mutum ce me tsananin mutunci da ganin qimar Dan Adam duk wannan auren na bazata da akaiwa mijinta da qanwar data ke yiwa kallon uwa daya uba daya bai canzata zuwa wata daban hakama vai sauya kyawawan halayenta ba.


Kallonta tayi taga cikin Yar dariya tai maganar bakin gskiyarta batasan tayi mgnar da wata manufa Abinda yake gskia ta fada Dan haka sai itama ta qirqiro murmushi cikin batar da zancen tace"


Anty baya buqatan amsa yasan akwai godiya tsakani ma'aurata musamam ma keda kikeji da Rabin ranki godiya bakomai bace.

Dariya anty zarah tayi tareda kallon Amatun tana jinjina sunan Wanda rabonta dataji tun zamansu asibiti jinyar Muhammad.


Yanason fita Amma sbd yakira Dr Fatima yasa ya jira harsaida tazo ta duba zarah din ta tabbar Masa da bakomai bane duk cikin laulayin cikine sai nauyi da cikin zai Fara shiyasa Dan haka bayan fitar Dr Fatima fita yayi shima ita Kuma Amatun ta Dan jima kafin ta tafi sbd qafafun anty zarah din ciwo sukai Mata sosai Sai data Dan tattausa Mata su tasamu tayi bacci kafin ta fito Takoma tayi sallah ta kwanta tanajin bacci.


Da daddare Takoma tasake dubo anty zarah din duk da ba wani Abu dake Mata ciwo kawai qafafun ne acan tabarosa tadawo Saida antyn tayi bacci yadawo sukai wanka suka kwanta.

Washe gari zai bar sashenta yakoma na anty zarah Dan haka tun safen bai fita ko Ina ba suna Palo suna shiririta ita ala Dole saiya lallasheta yasata bacci kafin yatafi haka dai suka shiririce har sallar magriba tayi ya tafi.


Zarah duk yanda tayi tunani da Shirin dauriyar abubuwan dazataita gani tareda daukarwa kanta alqawarin dangana tayi Shirin zaman hkr sai abin yazo Mata a baibai yabarta da mamaki sbd MD sauya Mata yayi daga MD ZABEERA zuwa asalin miji,

Ya sauya ta bangarori dabam dabam,

Babban mamakinta ayanxu shine zaman gida daya koya sosai yake zama agida wani lokacin Yana yini guda cikin zabeera bai fita ba Yana tareda iyalinsa ga yawan fara'a daya samu kansa aciki Abu daya datake maimaitawa shine Bata taba Tunanin ummanta datace Mata wata kishiryar kamar alheri ce sbd tana gyara maka mijin daka jima Yana wahalarda rayuwar aurenku hakama wasu yancin naki wata kishiyar itake kwato muku keda yayanki gurin miji ta hanyar sauyasa,

Tabbas ta yadda da hakan,

Akwai Abinda bazaka iyaba arayuwar zamantakewarka da mijinka sbd ka kashe zuciyarka Dan haka kodai duk wadda za'a auro kingama cutarta sbd kin sabawa mijin da yin shiru akan haqqinki Dan haka itama bawani dadinsa zataji ba kokuma kisamu wadda zata sauya mijin kisamu rayuwar dabaki samuba abaya,

Kishiya ko wace iri kasamu ta gari ko akasinta tasan da akwai ciwo Amma dai duk da hakan tana jinjinawa Amatu sbd ta taimaketa tanan Dan ita dai daza'a barta saidai suyi rayuwarsu sugama ayadda suka Fara bazata iya yiwa MD hayaniya ko yunqurin sauyashiba sbd yafison rayuwar kadaicinsa kamar tafi Masa nutsuwa takega shiyasa batason shige Masa sosai.

 Abu dayane data lura dashi shine wen ever Amatu is around idanuwansa akanta suke sbd bazai iya Hana zuciyarsa Abinda takeso ba saidai Bata damuba sbd itama aduk lokacinda take kusa to hannuwansa bazasu iya zamaba sai acikin nata Koda Amatun na kusa Wanda hakan ya tabbatar Mata da tanada nata bangaren me mahimmanci a rayuwarsa.


Anasa bangaren kuwa yasamu kwanciyar hankalinda baitaba samuba a rayuwarsa tun bayan rasuwar mahaifiyarsa tabarsa,

Yasamu nutsuwar zuciya da rayuwa,

Yasamu kwanciyar hankali data ruhi,

Rayuwa cikin iyalin dakake matuqar so suke sonka tareda baka nutsuwa shine asalin Abinda baisaniba sai yanzu,

Amatu ce takawo sauyi arayuwarsa da zuciyarsa Amma Kuma zarah ce abar jinjinawa kwanciyar hankali da nutsuwar rayuwar dasuke sbd itace ta dauki komai da salama da dangana tareda sawa kanta nutsuwa batareda damuwa ko tashin hankali ba azaman Wanda yasa ake zaune kalau,

Da Bata bada wannan gudunmawarba da duk yanda suka Kai ga tsananin son juna shida Amatu bazasu samu wannan kwanciyar hankalinba da nutsuwar zaman lafiya.

Nuratu tazama tamkar aminiyarta yanzu sbd kusan kullum gurinta ma take yini hardai ranarda anty salamatu tazo gidan yini sukeyi fira USI ma da tintini yarinyar ta fice Masa arai sbd kusan itace silar komai tun Yana shareta har suka Fara sabawa sbd Amatu dakuma yaganta Dr salman dayake babban abokin shawarar USI dabaida amintaccen Dan uwa irinsa da hakan dai suka Fara sabo da ita sosai.



Satinta hudu da tarewa tafara Shirin komawa sbd school karatunsu yadauki zafi Dole zata koma Dan haka duk sukabi suka wani sukukuce musamman ita dazata Koma ita kadai ko Muhammad gurin umme zaiyi zamansa daqyar ma dadynsa yabari Dan acan yaso sanyashi school Amma ummen ta toqa hakama shima Muhammad din yafison gurin ummen yanzu sbd tana sakaltashi da yawa gashi Kuma yaga Yana ganin dadynsa anan.


Ita kanta anty zarah zatai kewar Amatun sbd sunyi sabon sabo duk da har abada zasu taba komawa yanda suke Ada ba Amma ko yanzu sunyi sabon shaquwarsu suna tsananin mutunta juna da gujewa Shiga haqqin juna.


A gidansu ta yini Daren ranarda zata koma canma Saida tayiwa su iyami kukan barin gida kafin yazo da daddare ya dauketa suka koma gida.

Washe gari Saida tayiwa kusan kowa dake cikin zabeera bankwana kafin suka wuce USI ne dakansa yakaisu airport suka wuce yadawo.


Sbd son cire Mata damuwar data sanyawa ranta yasa Basu koma Greece ba direct suka nufa US.

Wata irin rayuwar Jin Dadi da sakewa sukai a US tamkar turawan qasar Dan sai alokacin tasake sanin asalin waye MAHMOUD ZABEERA sbd wani bangarensa data gani na dabam wato Dan rayuwa.

Duk yanda zatai rayuwa bazata manta wainnan kwanakin dasukai a US ba sbd ya shayar da ita soyayyarda har abada bazata barta ba,

Ya sanyawa zuciyarta wani sabon maganadisun sonsa da qaunarsa.


Kwanansu takwas suka tattara suka nufi gida saidai Kuma kamar karsu dawo tunda suka dawo tafara zuwa school kwana biyu shikenan ciwon zazzabin dare ya sanyota gaba sunyi yawon asibitin hardai aka tabbatar musu da ciki ne Dan haka ba wani magani haka suketa fama duk wani aikinsa ya ajiyesu jinyar matarsa yake cikeda kulawa da tsananin qauna.


Ganin harya share kusan wata daya da rabi yasa ta daure ta bawa kanta qwarin ta nuna Masa ta warke sarai kafin yafara maganar komawa sbd tarin ayyuka da Kiran dayaketa faman Sha dazai tafi ita dakanta takaisa airport suka fito motar ya kamo hannunta ya matso da ita cikinsa Yana kallonta da fararen idanuwansa dake bayyana newarta tun kafin ya tafi ya bude baki ahankali Yana shafo cikinta cikin laushin murya yace"


I will miss you wife.


Dan dago qafarta tayi sbd yafita tsayi takai bakinta Kan nasa ta Dora ahankali ta zura Harshenta tabashi wani irin kiss tana kallon cikin idanuwansa tace"


I will miss you More.


Rungumeta yayi tareda sauke ajiyar zuciya Yana shafa Bayanta yace"


I love you.


Qanqamesa tayi kalmarsa na sake kashe jikinta.

Sun jima ahakan kafin lokacin tafiyarsu yayi yabata kiss a goshi ya wuce tana kallonsa harya shige ta juya jiki amace ta shiga mota tabar airport din tana Jin kewarsa kamar tabisa. 

##Mamuh#*_MQ 50_*



https://youtu.be/1VyZ6f1GTWg

Please subscribe to our YouTube channel 👆👆👆




Tana komawa gida kwantawa tayi tun anan Palo tana waya da anty salamatu akan maganar zuwan datakeson tayi suna gamawa anan palon bacci ya dauketa.

Bacci me nauyi tayi sai kusan yamma ta farka ta tashi zaune tana Dan dafe kanta dayayi Mata nauyi sbd baccin datai dakuma Dan ciwon dayake Mata.

Miqewa tayi ta nufi daki Kai tsaye toilet ta wuce tayo wanka dan jikinta yasaki tayo alwala tafito ta sanya riga da wando me Fadi ta sanya dogon hijab tahau dadduma ta tayarda sallah.

Bayan tagama sallar kicin taje ta hado tea da biscuits tazo ta zauna Tasha tana kallon agogo tasan zuwa yanzu ya Isa sauka Amma bazata kiraba zata Bari idan yahuta yasamu lokaci zai kirata.



Washe gari da wuri ta wuce school sbd akwai asibitin dazasuje daga school din,

Tunda safe shine ya tayarda ita daga bacci suketa waya Saida zata Shiga wanka suka aje tana Shirin fitowa yasake kiranta harta Isa school suna waya har Anty zarah yabata suka gaisa tayi Mata ya jiki daga Nan daqyar tasamu yayi hanging wayar ta maida hankali Kan Abinda yakawota,


Sai yamma likis ta dawo gida amatuqar gajiye Dan haka ko abinci Bata tsaya Ci ba wanka tayi ta kwanta baccin gajiya da daddare data tashi bayan tayi komai tasake komawa ta kwanta suna waya ta rikice Masa akan sai anturo Mata anty salamatu wlh bazata iya rayuwa ita kadaiba.

Dole ya amince wa buqatarta yaje yasamu kawu da kansa yayi Masa roqon zuwan anty salamatun wannan karon hadda iyami ya roqa taje tadubota tunda batada lafiya zataji dadin ganinta sosai.


Kawun bedai cemasa ya amince da zuwan iyaminba tukuna Amma dai ita salamatun zataje itama bazata jimaba sbd maganar neman aurenta da Andi ya nemawa alhaji qarami Wanda yake autansu Modibbo basason doguwar bidia kamar a taqaice suke son ayi auren.


Da kansa yasa akawa anty salamatun shirye shiryen tafiya sbd kusan shima a matse yake dataje din yasamu me kula Masa da Amatun Dan gabaki daya hankalinsa ba'a natse yakeba Jin yake kamar yaje da kansa yayi jinyar abarsa Amma Kuma ayanzu zarah dake kusan haihuwa tafi buqatarsa shiyasa ma duk wasu tafiye tafiyensa ya rage saita haihu sbd Bata kulawar datake buqata.


Duk yanda yaso anty salamatu ta Isa cikin kwanaki qalilan bai yiyuba sai bayan sati biyu da maganar ta tafi tareda USI dazaiyi 6month program acan aikuwa Nan suka dasa sabuwar rayuwa a Greece hakan kuwa ba qaramin nutsuwa yabawa MD din ba Dan dama shineya tsayawa USI akan zuwa Greece din yin program dinsa acan infact ma shine yadauki nauyin komai sbd kawai Amatun tasamu Yan uwanta atareda ita hakan ne kawai zai bashi cikakkiyar nutsuwa sbd yanayin datake ciki.


Zaman USI agarin tareda zuwan anty salamatu ya kawarda duk wata damuwarta da rage Mata kewarsa sosai Dan haka saita kwantarda hankalinta take karatunta cikin kwanciyar hankali da bada himma musamman yanzu da cikinta yafara girma Dan kusan wata hudu cikin na biyar kenan ita Kuma zarah ayanzu tana gab da shiga cikin watan haihuwarta shiyasa Koda yazo gurinsu bai wani dadeba yakoma yasake barinta cikin sabuwar kewarsa Dan har wata qaramar tafiya sukai dayazo din.


Zaune suke apalo tana duba wasu textbook na school anty salamatu Kuma tana yanka Mata gwaibar data siyo daga wani superstore ahanayarta ta dawowa school suna Dan fira sama sama sbd Rabin hankalinta nakan books din wayarta tayi ringing tun daga Kan kalar ringtone din tasan waye me Kiran ta Kai hannu ta dauki wayar tana sake wata qaramar ajiyar zuciyar son mijin nata ta daga cikin kasalalliyar murya tace"


AMATULLAH's husband..


Duk da Yana cikin wani yanayi na damuwa Saida yadan murmusa hartaji sautin murmushin ta cikin wayar ahankali tace"


Barka da yamma.


Barka wife,

Hw are you and my baby?

Ya anty salamatu hope duk Kuna lafiya?


Yes lafiyanmu kalau it's just that we're missing you badly.


Numfashi ya sauke Wanda yasata Dan gyara zama tana ajiye books din jikinta cikin sauti me nutsuwa tace"


Lafiya kuwa? You sound worried.


Dafe goshinsa yayi cikin yanayi na damuwa yace"


Zarah na asibiti tun safe she can't deliver by her self itama aiki za'a yi Mata.


Faduwa gabanta yayi cikin tsoro da damuwar itama zatazo wajen ga tausayin anty zarah din sai jikinta yayi sanyi da rawar murya tace"


Yanxu tun cikin dare anty zarah take cikin wannan halin Amma baka fadaminba dady sai yanxu?

Wlh na tausaya Mata yanxu kenan suna ZABEERA specialist?


Yes yau sukeson ayi aikin sbd qarfinta harya qare nagaji da ganinta cikin wannan halin.


Kwantar da murya tayi cikin tausayawa anty zarah din da tausayinsa shi kansa sbd tana iya Jin irin damuwar dayake ciki a muryarsa tafara qoqarin kwantar Masa da hankali tana sake bashi qwarin gwiwa akan Allah yasa ayi aikin lafiya akuma dace.


Bayan sungama waya tana fadawa anty salamatu tana lalubo numbern umman zarah din ta Danna kiranta,

Tana dauka ta gaidata cikin ladabi ta Dora da cewa''


Umma Ashe anty zarah haihuwar tazo wlh bansaniba sai yanzu dady yake fadamin tun safe Kuna asibiti.


Amatu antynki Kam tanajin jiki kitayata da addua Allah yarabasu da bbyn lafiya.


Inshallah Allah lafiya kalau zasu rabu 

Allah yasa ayi aikin cikin sa'a 

Nasan bazata iya mgn yanzu ba Ina Mata sannu zuwa anjima zansake Kira naji Inshallah.


Shikenan Amatu angode Allah yayi albarka.


Amin umma ngd sai anjima.


Aje wayar tayi tana kasa cigaba da karatun ta shiga damuwa da tunani tasake Kiran MD din takuma kwantar Masa da hankali.


Haka Takoma sukuku tunda sukai Magana takasa sukuni sbd hadda tsoro tsoron zuwan tata haihuwar yake sake shigarta takasa zama sai kiransu takeyi akai akai tana tambaya har lokacinda aka shiga aikin da zarah Amatun kiransa takeyi tana Kiran umman zarah din harsaida umman tace Mata"


Amatu ki kwantarda hankalinki tunda kema bake kadaiceba kada ki daga hankalinki wata matsalar ta taso Kuma ku rabawa mijinku hankali Kashi biyu.


Ana fitowa sallar magriba aka fito da lafiyayyan jaririn zarah cikin qoshin lfy sai kuka yakeyi cikin qoshin lfy aka wuce dashi sukai duk aune unen dasuke buqata kafin aka shiryasa cikin fararen overall masu kauri nurse ta fito dashi fuskarta daukeda murmushi ta nufo inda MAHMOUD yake tareda mahaifinsa Modibbo daya iso asibitin alokacin tareda umme da Haj maryam.


Modibbo aka miqawashi ya karbesa cikin farin cikin ganin jikinsa 'da na farko ga MAHMOUD dinsa.

Addua yayiwa jaririn kafin ya miqawa MAHMOUD da idanuwansa suke Kan fuskar yaron Wanda tunda nurse tafito dashi kafin yashigo hannunsa zuciyarsa tagama cika da soyayyar 'dansa.

Zarah tabasa farin cikin rayuwarsa,

Ada baidamu da samun 'dan kansaba Amma tun Bayan haihuwar Muhammad zuciyarsa ta cika dason Tara zuriar me yawa kodan ya Gina tashi zuriar sbd fita rayuwar kadaici.


Addua yayiwa yaron tareda Masa huduba yakirasa da sunan Muhammad DAHEER Modibbo.

Godiya Modibbon yayi cikin Jin dadin takwaran da akai Masa.

Nan kowa yafara karban yaron ana Yaba kyawunsa da kamannin babansa daya Dan dauko.


Saida aka gama murnan samun Modibbo aka koma murnar samun nasarar aikin da akayi umman zarah kuwa farin cikinta a bayyane yake ganin yanda kowa ke murnar haihuwar 'yarta.


Babban tashin hankalin dasuka shiga na samun mugun labari daga bakin likitoci shine ba lallai zarah din tasake haihuwa ba sbd rashin qwarin mahaifarta data fashe kafin Cs din.

Hankalin ummanta yatashi sosai hakama da duk Wanda yake gurin Saida jikinsu yayi sanyi Amma ganin MAHMOUD dakansa ya dauki qaddarar ya dauki juriya yasa kowa ya hkr suka buge da tarairayar zarah wadda tayi kukan wannan mugun labarin MAHMOUD na aikin lallashinta cikin nuna Mata tsananin damuwarsa Dole qarshe ta dangana tabarwa Allah akan hakan shine qila mafi alkhairi.


Amatu data sake Kira kusan karo na biyar kenan bayan haihuwar sai yanzu tasamu damar Magana da anty zarah din Tai Mata barka tana sake Mata sannu daga Nan suka Dan gaggaisa da jamaar dake asibitin ta kashe wayarta.


Kallon babynta takeyi idanuwanta na cikowa da hawayen farin ciki Dana damuwa taji an zauna gefenta tareda zagayeta da hannunsa har ita har Modibbon Yana kallon Modibbo dake baccinsa cikin nutsuwa ya shafa fuskarsa tareda maido kallonsa Kan fuskarta Yana riqo hannunta cikin kulawa da nutsuwa yace"


Zarah ki daina damuwa akan Abinda ba Allah ne yafadaba,

Banson Baki empty hopes Amma Dan ance bazaki sake haihuwa ba ba lallai bazaki sake haihuwar ba sbd ba fadan Allah bane ki dauki qaddara ki rungumeta Allah nason bayinsa masu yadda da qaddara.


Dago jajayen idanuwanta dake tsiyayar ruwan hawaye tayi ta kallesa cikin tunani daban daban Wanda ya kunshi irin hope din data hangowa kanta na samun soyayyarsa ta hanyar Tara zuria me albarka dashi sbd gano burinsa da qaunarsa tason Tara Yara.


Kamar yasan Abinda take Tunani ta ganin irin kallon datake Masa ya rungumeta ahankali tareda shafa Bayanta cikin murya me taushi yace"


Zarah yanzu ke ba matata ce kawaiba ke uwar 'yayana ce,

Ayanzu kin riga kinzama wani sashe na rayuwata da zuciyata,

Samun haihuwa a tsakani wani alamarine me girma Dan kuwa kinriga kinzama tamkar jagoran zuriar dazan Tara a gaba ko ba naki yayanba,

A da ke zarah ce matar MAHMOUD yanzu Kuma ke zarah ce matar MAHMOUD uwargidansa Kuma uwar Dan haka ki cire kowane irin tsoro ne kikasa acikin ranki sbd mi MAHMOUD DAHEER ZABEERA Ina baki tabbacin mutuwace kawai zata cireki daga rayuwata.


Wani irin kuka tasaki tana sake qanqamesa zuciyarta na cika da farin ciki da nutsuwar zancensa....


Ahaka ummanta tashigo tagansu Dadi yasake kamata ta karba Modibbon ta fita dashi sbd su iyami dasu maman junior dasukazo ganinsa.



Kwanansu shida a asibitin aka sallamesu suka dawo gida inda kowa keta zuwa barka da farko gida taso komawa MAHMOUD din yace tazauna a gidanta bayason zuwanta ko Ina.


Amatu kullum tana kiransu Jin takeyi kamar tazo Amma Babu dama Dole saidai take ganinsu ta hotuna shikansa MAHMOUD din bataga alamar zai barta tabiyo hanyar zuwaba sbd ko school yanzu ya hanata tuqi da kanta anty salamatu ke kaita wani lokacin Kuma USI idan yanada time kenan sbd akusa da street dinsu yakama apartment yake zaune.

Ranar data Fara Masa maganar tanason zuwa Kai tsaye yace"


No,Babu inda Zan iya Bari kije until you deliver.


Dama tasan haka zai fada Dan haka Bata wani damuba ta bar zancen ta maida hankali Kan rainon cikinta da karatunta ta bangare daya ga MAHMOUD din dayanzu wani soyayya yakeji kodan itama lokacin haihuwarta ya matso ne Amma sam yanzu ko barinta bayayi ta sarara akan Kiran wayarsa.


Bayan sunan Modibbo da sati uku yayi daidai da Gama exams dinsu tana gida kwana biyu Babu inda take fita ga nauyin cikinta ya dameta ma gabaki daya.


Zaune take ita kadaice agidan anty salamatu sunfita da USI siyayyar wasu daga cikin kayansa na lefe dayake siya tun anan sbd Shi da Nuratu sungama daidaicewa tsakaninsu yana dawowa yakeson ayi idan son samunsanema to ahade aurensu danasu anty salamatu sbd dagashi har nuratun kamar zasu cinye juna sbd soyayya shiyasa itama yanzu nuratun kamar ta hadiye Amatu sbd qauna Dan sai yanzu take qara sanin mahimmanci Amatu agurin USI da irin tsananin qaunar junansu dake tsakaninsu.


Kallon wani tv program na likitoci takeyi a CWTv hankalinta rabi nakan waya sbd tun safe take kiran wayarsa Bata shiga Kuma shima tun Daren jiyan raban daya kirata.


Sake Danna kiransa tayi akaro ba adadi still Bata shiga tana qoqarin sake Kira taji ana qoqarin bude qofarsu ta shigowa ta juyo tana kallon qofar da waya a hannunta sukai Ido biyu itada shi ta Dan zaro Ido tana kallonsa tareda miqewa tsaye komai nata na bayyanarda mamakin ganinsa shikuwa kallonta yakeyi cikin kewa da soyayyarta ya tsaida kallonsa Kan cikinta dayayi girma cikin wata free doguwar rigar masu ciki data saka wadda batakai qasa ba sbd kada ta takurata ya ware Mata hannu Yana kallon fuskarta daukeda boyayyan murmushi da gudun dabatasan zata iyaba tayo kansa ta fada jikinsa ya rungumeta Yana Dan dagata sama cikin farin ciki da murna tace"


I love this surprise of urs Husband.


Sauketa yayi tareda Kama hannunta suka qarasa shigowa taso karban luggage dinsa ya hanata suka nufi dakinsa tafara gyarawa Yana tayata suka gyara dakin duk da Babu Abinda yayi 'yar qurace kawai.

Wanka yashiga ta fita zuwa kicin hada Masa abincin dazaici.

Cikin farin ciki tafara dafa Masa pasta da carrots sai beef meat ta hado Masa Kan tray takawo Masa har bedroom dinsa yaci tana zaune tanata tambayarsu Modibbo Wanda kamar ubansu daya da Muhammad sbd suna dibar kamanni.

Yana gamawa ta kwashe kayan ta maida ta dawo ta zauna Kan cinyarsa tana sake tambayarsa meyasa be fada Mata zaizoba.


Fuskarsa ya Dora kan tata Yana sauke ajiyar zuciya a boye yana kallon cikin idanuwanta da itama shi take kallo ya Dora hannuwansa Kan cinyoyinta Yana shafawa cikin malalacin sauti yace"


Sbd inason ganin farin cikin bazata a kyakkyawan fuskan matana.


Murmushin Jin Dadi tasaki tana sake shigewa jikinsa ahankali tana qara cukuikuyesa qasa qasa da murya tace"


Ko acikin barci MAHMOUD ZABEERA yazomin farin cikina bayyananne ne bare ganinka a zahiri so lovely husband zuwan bazatanka ya tafi da zuciyan AMATULLAH K.


sake matsota yayi cikin jikinsa Yana shaqar qamshin jikinta ya shaqi numfashinta dake sauka Kan fuskarsa sbd matsuwar dasukai da juna ya Dora bakinsa Kan nata Yafara kissing dinta Yana zame hannuwansa zuwa wuyan rigarta.


Koda anty salamatu suka dawo da daddare guraren 9 Bata tareda wata gajiya sosai sbd sun Dan bibbiya guraren hutawa sun shaqata bataga Amatun ba a apalo ta shige da kayan zuwa dakin Amatun inda sauran kayan lefen suke Nan na Bata ganta ba sai tayi tunanin toilet Dan haka dakinta Takoma ta fada toilet itama tayo alwala tazo ta tayarda sallah.


Jin shiru shiru ba motsin Amatu yasata fitowa tana zuwa kicin ta duba ko tana can,

Ganin anyi sabon girki a kicin din yasata bubbudewa tana dubawa tafito Palo ta nufa dining tana ganin plates da kayan da akai amfani dasu ta fahimci oga kwata kwata ya taho kenan ta fito kicin tana kallon hanyar zuwa dakinsa tasake tabbatarda shi dinne yazo ta wucewa daki tana cewa''

Naji dadin zuwanka nasamu yanzu nabi usi next week idan zaije gida.



Washe gari tana kwance cikin jikinsa tana bacci cikin nutsuwa sbd irin kyakkyawar rungumar da yayi Mata suna bacci cikin baccin tafara Jin kamar ciwo ciwon Mara na damunta Wanda yasata bude idanuwanta tana sake saurarawa Abinda takejin saitaji da gaske ciwon yake ta yunqura zata tashi zaune yabude idanuwansa Yana kallonta ta yunqura ta tashi zaune ya tashi shima Yana riqota yace"


Lafiya kuwa?


Kallonsa tayi da sauri tana dafe qasan cikinta a Dan tsorace tace''


Ina ganin labour ne..... kasa qarasawa tayi cikin tsananin azaba da firgici tace"


Hospital hospital hospital take me" duk arude take maganar a jujjuye batareda tasaniba 

Ganin hakan ya sauko gadon ya nufi wardrobe ya dauko shirt da wando yasaka cikin sauri tareda dawowa ya dauko Mata riga kamata ya sanya Mata suka fito tana sake dafe cikinta cikin azaba tana Kiran sunan Allah Dana MAHMOUD din cikin ciwo.


Jin dogon salati da qarfi yasa anty salamatu fitowa daidai qarasowarsu tsakiyar palon a Dan rude ta kallesu tana maida kallonta Kan Amatun daketa faman salati ba qaqqautawa cikin mamaki tace"


Subhanallah haihuwar ce ko me?

Lafiya kuwa?


Muje asibiti"kawai ya iya furtawa anty salamatun Yana nufar qofa da matarsa.

A gigice suka Isa asibiti musamman da ciwon ya taso Mata gabaki daya suna Isa ruwan haihuwa na fashewa akai labor room da ita.


Zama yayi Kan kujerun jira Yana kashe wayarsa sbd baya buqatan ko hayaniyar ringing waya.

Suna zaune saiga USI shima ya iso Nan suka Fara zaman jigum jigum cikin zullumi da fargaba,

Wannan zaman jiran dayakeyi yau yana daya daga cikin ranakun tsananinsa na rayuwa sbd gabaki daya Jin yake kamar nutsuwarsa zata bar jikinsa Amma haka dai yake zaune shiru kamar ba Wanda ke cikin tension ba.


USI da anty salamatu ne ke samun damar waya da Yan gida sunajin yaya kota haihune?

Zaman awa uku sukayi cikin ta hudu kafin Allah yabata ikon haihuwar baby girl lafiyayya da ita saidai ba qatuwa bace sosai sai kuka takeyi aka shiryata aka miqowa familynta ita ya karbeta Yana kallonta cikin wata irin nutsatsiyar sonta da qaunarta ya shafa Dan qaramin kumatunta Yana Mata adduoi da murmushi akan fuskarsa yace"


De symbol of my love FADIMATU ZARAH MAHMOUD ZABEERA.


Aikuwa cikin farin ciki anty salamatu itama ta karbi babyn tana kallon fuskarta cikeda murna tace"


MAHMOUD wannan 'ya da yayunta take Kama.

Murmushi kawai yasaki zuciyarsa na sake wanzuwa da farin ciki sai alokacin ya bude wayarsa da atake Kira suka Fara shigowa ya fice Yana amsawa.


Yana dawowa ya tararda anfito da Amatun ankaita dakin hutawa ya shigo Yana aika Mata da wani irin kallon samun nutsuwa ya qarasa bakin gadonta ya zauna tareda Dan rungumota yabata kiss agoshi yace"


Thank you.


Murmushi tasaki tana Dan harararsa tace"


Bazan qaraba daga wannan.


Dariya maganar tabawa anty salamatu takuwa ringa qyaqyata dariyarta shikuma wani guntun murmushi ya sake Yana sake kissing hannunta dake cikin nasa batareda yace komaiba.


Acan Nigeria kuwa cikin both families din haihuwar ta Isa kunnen kowa akaita Sanya alkhairi da yiwa FADIMATU ZARAH adduar Allah ya raya Akan sunna,

Zarah da akaiwa takwara kuwa rasa abin cewa tayi sbd farin ciki shiyasa ma tace zatazo taga takwara da kanta.


Kwananta daya a asibitin suka sallamota suka dawo gida Nan anty salamatu tayita hidima dasu ganin suna hutu Kuma gashi umme da zarah hadda Nuratu since zasuzo yasa ya yanke shawarar su dawo gida bayan ko 30days ne saita dawo.


Kwana biyar da haihuwar suka dawo Nigeria Nan aka kacame da sabuwar murnar zuwansu 'yan barka suka Fara sintiti musamman aminanta su maman junior da kullum saisun Zo iyami ma kwana biyu ta jera tana zuwa Saida akai suna tukuna suka samu sauqin baqi sai alokacin tafara samun kanta.


Yau satinsu uku da zuwa tuni tafara Shirin komawa musamman ganin yanda ogan yafara shishige Mata tanason Takoma tasamu matakin dauka kafin wani abun yasake Shiga sbd taga alamar son dawowa bakin aiki yake.


Ana gobe zata koma tafito palonta zuwa sashen anty zarah saigasu taci karo dasu sunfito itada MAHMOUD din Yana daukeda Modibbo hannunsa daya Kuma Yana riqedana ZARAn sunci ado cikin traditional attire sai murmushi suke ta qaraso suka hade tana murmushi ta gaida anty zarah tana cewa''


Fita zakuyi?


Eh Amma ba dadewa zanyi ba gurin umma zai ajeni.


Ok to adawo lfy Ina gaida umman bansamu nazo nayi Mata bankwana ba.


Kallonsa tayi shima tana sauya kalar murmushinta zuwa na neman mgn tace"


Take care.


Fuskar fadimah ya shafa Yana gyada Kai.

Suna wucewa Takoma ciki taqarasa sauran parking din da bataiba.


Washe gari anty zarah ce takaisu airport suka wuce dagacan ta wuce gidansu gurin ummah.


Bayan dawowarsu Greece da sati biyu yakoma bayan sun dauki me aiki da Nanny hakan saiya taimaka Mata sosai sbd samun damar maida hankali ga karatunta.


Rayuwa ahankali tafara sauri fadimah tayi wayo sosai tana cikin final exams dinta ta fahimci tanada wani cikin hankalinta yatashi sbd fadimah Bata Isa yayeba Dan haka taso cire cikin saigashi kamar Wanda aka fadawa yayi Mata zuwan bazata cikin sa'a kuwa kafin yatafi Saida yasanda zaman cikin Wanda yasama ya daga komawarsa yaqara kwanaki Saida tagama exams dinta akai duk wata hidimar daza'a yi ta karbi takardunta suka dawo Nigeria sbd shagulgulan bikinsu USI da aka Fara Wanda aka hade danasu anty salamatu Dan haka biki sosai akeyi a zabeera Koda ta iso ta fada cikin hidimar gadan gadan sbd dama amatse ake ta iso sbd wasu abubuwan da akeson gudanarwa Wanda suke buqatar kasantuwarta bikin USInta guda dakuma antynta anty salamatu.


Ranar asabar aka gama bikin amare kowacce ta tare gidanta

Anty salamatu zabeera ita Kuma Nuratu cikin sabon qaton sabon gidanta da USI ya Gina musu Wanda zasu zauna tareda iyayensa.


Ana kammala bikin ta yaye fadimah wadda anty zarah ce ta hadasu ya yaye tareda Modibbo takwashesu suka koma gurin umma tace sunyi yayen acan.


Ganin zarah batanan dazaiyi tafiya saitace zata bisa takuwa shirya tabisa suka tafi sudan.


Satinsu biyu suka dawo anty zarah ta karba miji daganan zaman ya Dore ahaka cikin kwanciyar hankali ba hayaniya sbd kowacce ta shafawa kanta lafiya sbd fitinar wani lokacin Hana komaima takeyi a tsaya guri daya akasa gaba akasa baya.


Lokacin haihuwarta nayi ta haifi baby boy aka saka Masa sunan kawu suna kiransa ABBA bayan haihuwarta da wata shida anty salamatu ta haihu a hannunta a asibitinsu wadda MAHMOUD yasake sauya Mata tsari da girma tafara aiki tun bayan haihuwar ABBA shiyasa itacema ta karba haihuwar antu salamatun data samu BBY girl itama bayan sunan anty salamatu da sati biyu Nuratu ta haihu itama a hannunta tasamu Me sunan kawu DR USMAN K SALEH yasawa babyn.


Fadimah a hannun anty zarah take Dan haka ita ABBA ne kawai agabanta Muhammad ma tuni yafara zama saurayi Yana gurin Rabin ransa umme wadda takejinsa fiyeda sauran 'yayanta Dan haka Babu me tabasa.

Shima ABBA Yana Isa yaye iyami ce tayi yayensa Nan MD yasata gaba akan sabon baby yakeso tanajin yafara fadar haka taso daga hankalinta Saida anty zarah Tai Mata waazin damace Allah yabata tayi haihuwar ta huta tunda gashi ita tanaso Allah be Bata ba.



Kallonsa tayi lokacinda tafito daga toilet daureda qaramin towel da ko Gama rufeta baiyiba ta qaraso inda yake zaune Yana aiki da laptop ta zauna Kan cinyarsa tana tanayi kamar zata saki towel din ta marairaice murya tace"


Positive.


Dagowa yayi Yana kallonta da fararen idanuwansa Yana Mata kallon are you serious?


Daga Masa Kai tayi yayi saurin rungumeta Yana zura hannu cikin towel dinta Yana cewa'' 


Thank you love.

##Mamuh#



ALHAMDULILLAH.


Da yardar Allah anan mukazo qarshen wanann littafin namu me suna MIN QALB wato DAGA ZUCIYA,


IDAN NAYI MANTUWAR WANI ABUN DABAN QARASA FADABA A LABARIN KUMIN UZURI KU DAUKESA AMATSAYIN AJIZANZI IRIN NA DAN ADAM.


INA ROQON ALLAH YABAMU IKON AMFANI DA ABIN ALKHAIRIN DAYAKE CIKI SABANINSA KUMA ALLAH YA MANTAR DAMU YAKUMA YAFE MANA,


AKWAI WAINDA TUN BAAZO QARSHE BA SUNA MAGANAR DANGINSU AMATU DA USI,

ANSAN KOWA BA DAGA SAMA YAFADO DUNIYA BA AMMA KADA KU MANTA AKWAI MARAYUNDA ADUNIYA HARSU BARTA BASUSAN ASALINSUBA BARE DANGINSU,

AKWAI WAINDA SUKE RAYUWA BATAREDA SUNSAN ASALINSUBA KO INDA SUKA FITO AMMA SAI ALLAH YABASU IKON GINA TASU RAYUWAR SU GINA ZURIAR KANSU DAN HAKA KU SANYA SU AMATU AKAN MASU IRIN WANNAN QADDARAR SBD A DUNIYA BAKOMAI KAKE SAMUBA.


ALLAH YA GAFARTAMANA

AMIN.







ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰

KIBIYAR AJALI......!

      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

   

          Mamu gee🥰

MIN ƘALB!!😋🤗


        Hafsat rano🥰

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


         Bilyn Abdull🥰

SARAN ƁOYE🤗😋


    Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍



ZAFAFA BIYAR 2021


Hafsat miss xoxo🥰

KIBIYAR AJALI......!

      (Sulke baya tareta saita gitta).😋🤗

   

          Mamu gee🥰

MIN ƘALB!!😋🤗


        Hafsat rano🥰

ABINDA KE CIKIN ZUCIYA...!!😋🤗


        Safiyya huguma🥰 SIRAƊIN RAYUWA😋🤗


         Bilyn Abdull🥰

SARAN ƁOYE🤗😋


    Duka akan farashi mai rahusar gaske.


Kamar haka👇🏻💃🏻


Ɗaya___300

Biyu____400

Uku_____450

Huɗu____500

Biyar_____700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO 0812652655

ACCOUNT NAME- HAFSAT LAWAN GAMBO

BANK NAME: ACCESS BANK.


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


0903 234 5899


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


  09033181070


💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻💃🏻

TEAM----ZAFAFA BIYAR🔥😘🥰😍


ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻.


*_Thank you 4 d prayers_*🥰🙏



ZAFAFA BIYAR

NA KUDI NE::: 


Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,


Guda hudu 4 Kuma 500,


Guda uku 3 Kuma 450,


Guda biyu 2 Kuma 400,


Guda daya akan 300.


Ma'ana

Each one is 300

2 is 400

3 is 450

4 is 500

5 is 700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO- *0812652655*

ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*

BANK NAME: *ACCESS BANK*


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*+234 903 234 5899*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


*09033181070*


Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne

SABUWAR SHEKARA 

SABON SALO


TEAM#ZAFAFABIYAR🔥




_INA MASU SHA'AWA DA QAUNAR KARANTA LITTAFIN DAZAI SANYASU CIKIN NISHADI DA DAWWAMÀMMIYAR NISHADI TO GA DAMA TA SAMU KU NEMI LITTAFIN_ _*WASA DA ZUCIYA*_ _NA ZINNEE SMART  DAN SAMUN WANNAN QAYATACCEN LABARIN NATA ME SANYAYA ZUCIYAR ME KARATU

TA WANNAN NUMBERN_

👇👇👇

08080840567

##Mamuh#_ASSALAMU ALAIKUM BEAUTIFUL PEOPLE.. INA KUKE YAN UWA NA MATA? TO KU MATSO KUSA DOMIN GA DAMA TA SAMU.. KAI BAMA MATA KADAI BA, HAR IYAYEN MU MAZA, ZAKU IYA KAWO SISTERS DINKU, DAUGHTERS DA MA WIVES DINKU. KAI HARDA BAE DA KE SHIRIN ZAMA MRS🤩😉...!_


_UMMU AYMAAN’S KITCHEN, UMMU AYMAANS’S KITCHEN, UMMU AYMAAN’S KITCHEN..._


_INA YAN UWANA MASU SON SU KOYI BAKING DA DECORATIONS? TO NESA TAZO KUSA.. UMMU AYMAAN’S KITCHEN ZATA KOYAR DA MATA MASU SON SU KUYI BAKING DA DECORATIONS NA KWANAKI BIYU. AKAN FARASHI ME RAHUSA, NAIRA DUBU 6 KACAL, (6k)._

 

_ZATA KOYAR NE A UNGUWA UKU LAYIN MAIFATA, ZARIA ROAD KANO.. PRACTICAL CLASS NE, SANNAN AKWAI GARABASA DA NA NESA DAKE SON SU KOYA SUMA ZASU IYA KOYA TA ONLINE DUK AKAN NERA DUBU SHIDA KACAL, DUK ABUNDA YA KUNSHI BAKING ZATA KOYAR KAI HAR MADA BONUS NA DECORATIONS._


  _*CLASSES DIN KWANA BIYU NE, AKWAI PRACTICAL DA ONLINE, CLASSES DIN ZA’A YISU NE RANAR 5 DA 6 GA WATAN YUNI WATO 5&6 OF JUNE (NEXT MONTH)RANAR WEEKENDS ASABAR DA LAHADI*_


_* 2 DAYS DEMO CLASS ON BIRTHDAY CAKE.. (BAKING AND DECORATIONS)* YAR UWA HANZARTA KI BIYA KI KOYA KEMA KIN HUTA DA BIYAN BAKERS, DA KANKI ZAKI IYA YIN NAKI, DA DUBU 6 ZAKI IYA BIRTHDAY CAKES KALA KALA, WANDA BA KARAMAR SANA’A BACE, IDAN YARAN KI KO KANNENKI ZASUYI BIRTHDAY KIN HUTA SIYA SE KEYI DA KANKI, KIYI KI BIRGE MAI GIDA AS SUPRISED GIFT.. INA YAMMATA? IRIN CAKE DINNAN ME HEART KI KOYA KIYI KI BAWA BABYN BABY🥰 LOVE IS LIFE, CAKE IS LOVE🙃._


_BA ANAN KADAI TA TSAYA BA, TANAYIN DUK WASU MOUTHWATERING SNACKS AND CONTINENTAL DISHES😋, AKWAI NA YAN GAYU IRIN SU CAKE PARFAIT, CUPCAKES, SAMOSA, SPRING ROLLS, MEAT-PIE, DOUGHNUTs, DUKA WADANNAN TANAYIN SU NE NA BUKUKUWA, SUNA, SHAGULGULAN TARO, KAI DAMA NA CI HAKA KAWAI😋_


_BA ANAN KADAI TA TSAYA BA, TANA CLASSES NA GIRKIN ZAMANI DANA GARGAJIYA, MOUTHWATERING DISHES NA YAN GAYU, MESA KISHIYA KWAFA, WANDA FACCALA ZATA DINGA CIZON YATSA, IRIN HADADDEN GIRKUNA MAI SA KUNNUWAN MAIGIDA SU MOTSA. KAI HARDA NA BUKUKUWA KUNA IYA ORDER TA MUKU SHI_


_INSTAGRAM HANDLE DINMU:_ Ummu_aymaan_kitchen


_DOMIN KIRAN NAMBAR TARHON MU DAN KARIN BAYANI DA BIYAN KUDIN SHIGA SAI A TUNTUBEMU TA: 08032964266_


_MUNA TURA KAYAN SNACKS DINMU A KOINA A FADIN NIGERIA, 100% TESTED AND TRUSTED.._


_UMMU AYMAAN’S KITCHEN IS YOUR NO 1 STOP KITCHEN FOR MOUTHWATERING DISHES, BAKES AND SNACKS_


____


_*KIBIYAR AJALI....🧚🏻‍♂️🥰*_

_(SULKE BAYA TARE TA, SAI TA WUCE..)_


_BOOK 2_

_PG:6 & 7_


_LITTAFAN ZAFAFA NA KUDI NE, MALLAKI NAKI A NAMBOBIN MU DAKE KASAN SHAFUKAN MU, KI GUJI KARANTA NA WANDA BA’A BAKI NA DON GUDUN SHIGA HAKKIN WANDA SUKA SIYA DAMA MASU RUBUTAWA_


....

Cikin tsananin tashin hankali sai ga Ammi ta aiko a kirawo ni, Kila wani ne ya sanar mata halin da ake ciki. Tafiya nayi, Sashen nata Ina zuwa ta kamo hannu na muka shiga cikin dakin ta . Bata saki hannu na ba har sai da muka karasa kujerun dake harabar dakin. Cikin tsananin tashin hankali ta shiga ban hakuri,


 “Kiyi hak’uri Khadija.. Dan Allah s..”


“Dan Allah kiyi hak’uri Ammi Kiyi shiru, Nasan komai, Kuma wallahi nagane ba a hankalin sa yake ba. Insha Allah nan gaba kadan komai zai daidaita da yardar Allah..” Na karasa fada ina mai rik’o hannun ta na zaunar da ita a kujera, Na koma na dakko ruwan sanyi na zuba a cup na mika mata. 


“Sha Ammi.. Ki kwanta dare yayi.”


Murmushi tayi da alamun taji dadin maganganu na. Daga kasa na nemi waje na zauna, Tv na kunna na kai tashar karatun AlQur’an, A hankali sautin kira’ar sudeis ya dinga tashi. Haka muka kusan raba dare da Ammi, Sannan tace naje dakin gefen nata na kwana aciki. Ba musu na mike don wallahi bacci nakeji, Sai da nayi sallar nafila sannan na kwanta, Bacci mai nauyi ya dauke ni...


Wasa wasa, Sai da na kusa shafe sati biyu a sashen Ammi, Kemadagas Abdullah ya kafe kan wallahi ba zai bani sashen sa na zauna ba aciki ai nasa ne. Ban wani damu ba, Saboda dama wajen Ammin yafimun dadin bacci cikin kwanciyar hankali. Bansan wanda ya gayawa Sarki Salmaan bana kwana a sashe na ba, Ranar wata sanyayyar asabar da asubah naje turara magani kawai ya same ni da maganar...


Kasa kasa ya shiga kallo na ina hankalce dashi,


 “Ancemin bakya kwana a sashen ki, why? Aina kike kwana.”


“Sashen Abdullah kasa aka kaini... So yanzu ya dawo yana bukatar wajen sa. Awajen Ammi nake kwana, Da magana ne?”


Na bashi amsa a gatsine haushi yake bani, Sanyin sa yayi yawa kamar ba sarki ba. Shiru yai yana danna ipad dinsa can ya dago yace,


 “Ki shirya komai naki... Duplex (ginin bene) din dake kusa da wannan an gama gina shi, Ki kwaso kayan ki ki dawo..”


Na gwalalo idanu ina girgiza kai,


 “Akan wane dalili? Gaskia gaskia banason nan, Kayi hak’uri.”


Wani kallo ya watsamin ya ajiye ipad din hannun sa, Mikewa nai daga gefen da nake nai hanyar fita ina mai ajiye burner din dake hannu na. 


 “Ke zo nan..”


Ya fada cikeda kasaita, Wai ke! Seka ce yar aikin sa, Na tab’e baki na tsaya inda nake ban jiyo ba. Takowa yai har wajen kofar da nake, Na matsa can karshen k’ofa na takure, Kasa jure kallon idanun sa nai dake saqale ta cikin gilashi. Yasa hannu biyu ya tokare ni a tsakiya yana taune k’asan leben sa,


 “Kikace me? Maimata abunda kikace.”


Na hadiye kakkauran abu a wuyana, K’amshin turaren jikin sa da nawa suka hadu suka bada wani kamshi na daban. Nadan kauda kai na gefe kirji na sai dukan uku uku yake. Bakin sa ya kawo daidai kofar kunne na:


 “Scaredy cat.. Me kike cewa?..” 


Shiru nai kaman an jika dan tsako a ruwa, Sai raba idanu nake. Banda iskanci meye namin haka? Numfashin mu sai had’uwa yake yi. Na takure hannuwa na a kirji don na lura kamar yafi kallon sama na. Yadda glass dinsa yake kallon saitin wajen.


 “Kwalelanka dai wallahi..”

Bansan nayi sub’utar baki na fada ba..


Murmushi yai kawai yana nuna ni,


 “Mekika ce?”


Na shiga girgiza kai ina kara matsawa jikin kofa Sosai,


 “Ki hada komai naki... Ki dawo sabon ginin da akeyi.. Kafin ma..”


Bai karasa ba aka turo kofar da sauri ya koma baya yana sosa k’eyar sa. Shaheeda ce ranta a matuk’ar bace,


 “Honey... Me naji kana cewa? Kunnuwana ne suka jiyemin ba dai dai ba ko kuwa? Bangane ba..? Wane gida zata dawo? Nace wani gida zata dawo?”


Ta karasa fada a dan tsawace, Na tsaya ina binta da kallon mamaki, Toshe kunnen sa d’aya yai da yatsan sa karami,


 “Haba.. Banason tsawa please.. Shaheedah! Meye haka?”


 “Meye wani meye haka? Hakan ce ta kawo haka Salman, Bangane cin amanar da kakemin ya wuce tunani na ba sai yau.. Ta dawo sabon gidan fa kace, Lalle ka taro babban balai. Kana nufin kace dama mallakinta ne ko kuwa.”


Bai amsa taba ya koma kujera ya zauna yana sauke ajiyar zuciya, Na lura mutum ne shi marar son hayaniya. Gashi ita kuma tanada kwakwazo da mita.


Kallo na tayi ta zabga min harara, Zan rama kenan naga ya dago glasses dinsa yana kallon mu, Na fashe da kuka ina mai komawa jikin kofa, Nasa hannuna na dora kai na akai ina kuka.. Ya mike da sauri ya yo waje na yana dafa kafadata,


 “Menene... Uhm? Meta miki? Eh..!?”


 “Kutmar kan babban balain can, Ke ni zakiwa sharri? Uban me nayi miki! Kai kuma sannu sharukhan baban soyayya, Daga ta fara kuka ka mike jiki na rawa kana tambayarta, To koma ka zauna bamu gama magana ba...” 


Zai koma kenan, Nayi sauri na rik’o hannun sa, Ni zata nunawa isa? Lalle zan nuna mata na ninkata a kissa.. Kasa juyowa yai kuma ya kasa tafiya, Na rintse idanu na fada kan faffadan k’irjin sa, Duk da yanda gabana yake faduwa abunda bantaba yi ba, Haka na cije don karta gane ba abunda ya taba shiga tsakanin mu. Shi kansa Salman yayi mamaki, Na zagayo da hannu na ta kugunsa na rike shi sosai, Ahankali na kwantar da kai na akan kirjin sa, Na barwa banza ajiyar ta.. 


Wani shegen marayan kukan shagwaba na saki da har sai da Shaheeda taja dogon tsaki tana cizon yatsa, 


 “Ke ni zaki nunawa bariki.. Kai kuma ka tsaya sakatoto mace na maka makirci. Salman magana nake..”


B’angaren Salman kuma kasa cewa koma yayi, Ga kyakkyawar rungumar da Khadija ta bashi mai ratsa magudanar jini da tsoka dan dadi, Gashi k’amshin turarukan jikin ta sai kara saka masa kasala suke, Bugun zuciar sa sai kara yi yake yi... Da sauri da sauri, Zuciar sa bata taba bugawa wani dan adam haka ba fyace Khadija.. Dama ita kadai ransa da zuciar sa kai harda jikin sa suke begen samu. Wani lokaci kalilan yake jira ya bayyana mata komai, Amman yanzu ba zata taba ganewa yana kaunar taba. 


Shaheeda tasa hannu ta janyo shi cikin izza da bacin rai,


 “A gabana? A gabana zakuyi bariki, Ba’a haife ki ba wallahi. Ke ba ki isa ki shigo ki raba ni da miji na ba.”


Ahankali ya hanya hannaye na ya koma kan kujera ya zauna, Daman nasan ai badan na ri’ke shi ba saki na zaiyi, Nan gaba kadan zaka zayyanemin abunda yasa ka auroni, Sannan kaban hak’uri da doriyar takardar saki na. Bazan iya auren wulak’anci ba. Yanzu ma inayin hakane sahada Shaheedah, Idan ban muna ba wata kofa a tsakanin mu ba to zatai saurin shiga tsakani. 


Gefen inda yake zaune ta zauna tana shafa fuskar sa da hannun ta na dama,


 “I’m sorry please, Kasan idanuwana da zucia ta bazasu juri ganin ka da wata ya mace fyace ni ba. Uwa uba waccen low class din. Da har take ganin zatai takara dani.. jokes apart maganar ginin can. Karka sake yinta. Ni acikin week dinnan zan dawo ita ta koma sashe na, Karka manta nice matar ka tafarko my love..”


Daria abin yaso bani, Yadda yake kallon agogon hannun sa yana cije lebe da alama ko sauraranta ba yayi. Nima agogon dake saqale ajikin bango na kalla ganin karfe 7 Saura kwata na safe yasa na matsa kusa dasu, Caraf na zauna akan cinyar sa, Dai dai saitin kunnen sa na shiga fada ahankali yadda zata iya jiyowa,


 “My whole world....”


Dak’yar na karasa shi kansa Salman Sai da ya kware na bubbuga bayansa saboda tsantsar mamaki, Shaheeda kuwa tacika tayi fam zata fashe..


 “Uhm.. Ashe dagaske kake agaban matar ka ba zaka iya kira na da sugarplum ba.. Anyways! Ni zan koma sashe na, Nagaji sosai kasan jiya bamuyi baccin kirki ba anata abu d’aya.. Zan dawo later mu karasa daga inda muka tsaya.. Oh yes maganar sashe na... Zan dawo ayau ba sai next-week ba. Bye. Ka kulamin da Kan ka..”


Light kiss na sakar masa a gefen kumatun sa na fice da sauri ina kambama kokari na, Ina jiyo kwakwazon Shaheedah tana surfa zagi da masifa, Na gimtse daria ta na koma sashen Ammi.. Ni kai na nayi mamakin acting dina.. Dole na bawa Addah Maryamah labarin abunda ya faru, Don duk koyarwarta ce. Sai karin rashin tsoro na na dije Oganniya.. ‘kaya nake bansan na gida ba. Oganniya yar baffanta.. Ta gajiyalle mai yar hakiya...! 


      Tamkar sabuwar mota haka shaheeda tafice daga sashen Salman zuwa nasu gimbiya Huwaila, Tana tafe tana share hawayen takaici. Lalle Khadija ta taro World Cup, Zatayi dana sanin shiga ragarta. Shi kuwa Salman bawan Allah shiru yayi yana nazarin kalaman Khadija, Yasan duk dan saboda takonawa Shaheedah rai ne tayi haka.. Amma meyasa nayi haka? Ya taambayi kansa.. Saboda kana kaunar ta. Zuciar sa tabashi amsa. Kishingida yayi akan kujerar sa yana shafa inda ta sumbace shi, Daya shafa sai yai murmushi kamar zararre. Dak’yar ya iya mikewa ya hau sama.. Aka shirya shi ya shiga fada.. 


       *FADAR SARKI SALMAAN ALIYU SALMANU*

..


ZAFAFA BIYAR

NA KUDI NE::: 


Duka BIYAR 5 zaku samesu akan garabasar naira 700 kacal,


Guda hudu 4 Kuma 500,


Guda uku 3 Kuma 450,


Guda biyu 2 Kuma 400,


Guda daya akan 300.


Ma'ana

Each one is 300

2 is 400

3 is 450

4 is 500

5 is 700


Zaku biya kudinku acikin wannan asusun namu na banki👇👇


ACCOUNT NO- *0812652655*

ACCOUNT NAME- *HAFSAT LAWAN GAMBO*

BANK NAME: *ACCESS BANK*


saiku turawa wannnan numban shedan biyanku(evidence of payment)👇👇


*+234 903 234 5899*


IDAN KUMA KATIN WAYANE KO VTU/TRANSFER ZAKU TURA TA WANNAN NUMBER TAREDA SHEDARKU👇👇


*09033181070*


Karku Bari ayi Babu ku domin wannnan salon na daban ne

SABUWAR SHEKARA 

SABON SALO


TEAM#ZAFAFABIYAR🔥

Post a Comment

0 Comments