TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

DABI'AR ZUCIYA ❤ page: 51 - 52

 51

D/Z



Tana sake matsawa kanta da tambayar tana sake jin maqogoronta yana bushewa,wanda ya sake tabbatar mata da cewa ruwa take da buqatar sha,cusa hoton ta kuma yi qasan filon,ta miqe jikinta na rawa a hankali cikin sanda ta doshi falon.


A hankali ya murda qofar falon ya turata kana ya shigo,jikinsa ko ina yana fidda zufa saboda mafarkin da yayi,babu abinda yake da buqatar sha illa ruwa,sanda ya niyyaci shan ruwan,saiya taras babu komai a fridge din sashen sai drinks,wadanda ba zasu kashe qishirwar da yakeji ba sam.


Idanu ya zuba mata daga nesa cikin mamakin ganinta a dai dai wannan lokacin,duk da cewa babu wadatar haske sosai a falon amma ya ganeta sosai,baqin gashinta daya ware ya sauka a bayanta yanata qyalli,ci gaba yayi da takowa a hankali yana nannade hannayen rigarsa ko zaiji raguwar zufar dake sauka a jikinsa.



Da hanzari take zuba ruwan cikin cup tana daga tsaye a bakin fridge din bayan ta budeshi,alamun takun sawayen da taji ya sanyata firgita sosai,hakan ya sabbaba mata tsoron daya tilasta ruwan da robar faduwa gaba daya a qasa ruwan ya soma malalala a qafafunta,sannan ta waiwayo tana duban bayanta.


Fararen idanunta sun fito tarwai wadanda suka cika da tsoro,tsoron daya bashi mamaki,saiya qarasa gabanta a nutse,ya sunkuya ya dauke ruwan kana ya dago yana duban tsakiyar idanunta,fuskarta tayi wani fayau, fresh babu komai saman fatarta,gab suke da juna har suna iya musayar numfashi,still yana kallonta a tausashe muryarsa can qasa maqoshinsa yace


"Wannan tsoron fa?" Qas tayi da kanta tana son dai daita kanta,tana kuma jin nauyin yadda yake tsaye gab da ita,ta fahimci kuma idanunsa na yawo ne a kanta,har zuwa qirjinta da maballan rigarta guda biyu na sama suke a bude,hakan ya bawa qirjin nata damar fitowa kadan ta saman


Ganin ta kasa cewa komai saiya dauki wani cup din daga saman fridge din,a hankali taji ya kama hannayenta,ya sanya mata cup din a hannu days,daya hannun kuma robar ruwan bayan ya budeta,dora hannayenshi shima yayi saman nata hannayen,ya tayata riqe cup din da robar ruwan,suka fara tsiyaya ruwan a tare,kowannensu idanunshi na ka robar da cup din,saidai kowa da abinda zuciyarsa ke saqa masa.


Sai daya cika shi da ruwan sannan ya tayata daga cup din zuwan bakinta ta hanyar ci gaba da dafe bayan hannunshi cikin tafi hannunta,a hankali take aika ruwan daga bakinta zuwa maqogoranta cikin wani yanayi,sanyin ruwan na kai mata ko ina,jikinta na mutuwa saboda wanzuwarsa a wajen.


Rabi tasha tadan janye shi daga bakinta,ta tsammaci zai sake mata hannu ne amma sai taga ya sake sauke hannun nata tare da sake zuba ruwan ya kuma cika cup din,wannan karon bakinsa yakai ruwan,ya fara sha shima a hankali, Adams apple dinsa na sama da qasa,yayin da idanunsa masu haske da girma ke zube cikin nashi,qas tayi da kanta,tana ji ya gama shan ruwan,ya zare hannunsa cup din da kuma gorar ruwan gaba daya ya ajjiye.



Bata ankara ba taji ya kama tsintsiyar hannunta,haka kawai.mafarkin ya birkita shi,yaji yana da buqatar wani abu da zai daidaira bugun numfashinsa,yana buqatar wanda zaiji yadda zuciyarsa take bugawa,sai ya sake taku sosai ya hade jikinsa da nata,hakan bai masa ba,sai daya dora qafafunta saman nashi,hakan ya qara mata tsaho,sai taji ya zagaya hannayensa zuwa bayanta ya rungumeta gaba daya cikin jikinsa.


Qamshin turarensa laushin fatarsa da dumin dake fita daga jikinsa da kuma ba zatar da yayi mata yaso tafiya da numfashinta gaba daya,bugun zuciyarsu ya cakuda waje daya,kowanne a cikinsu yana iya jin yadda zuciyar dan uwansa ke bugawa da wani irin gudu.


Numfashi mau nauyi ya dunga saukewa ajere,a hankali a hankali har zuwa wani lokaci,cikin jikinta ta karan kanta ta dinga jin wata nutsuwa,kamar yadda shima nutsuwar ta dinga ratsashi ta kowanne sassa na jikinsa,nutsuwar da bai taba jin kamarta ba duk sanda yayi irin wannan mafarkin


"Me ya tsorataki?" Ya kuma jefa mata tambayar cikin wata murya dako a falon kake baka isa kaji abinda ya fada ba,saboda wani feelings dake tsarashi,yana iya jin tudun komai na jikinta a jikinsa


"Mafarki nayi"


"Na umma?,ko na bilal?" Tambayar data sosa mata wani tabkeken miki dake danqare a zuciyarta,wanda dare da rana taketa qoqarin ganin ta sayashi,kiran sunan da yayi ya shiga sosai cikin kunnenta,ya kuma motsa zuciyarta,duk da mafarkinta bashi da alaqa da umman,amma sai taji a take hankalinta ya karkata zuwa gareta,hakan ya bawa hawaye damar taruwa cikin idanunta,cikin qanqanin lokaci kuma suka fara sauka saman fuskarta.


Batasan yadda akayi ya fahimci ta soma kuka ba,saidai hannunsa data ji saman fuskarta yana share mata,batasan cewa yaji sauyin fitar numfashinta da bugun zuciyarta ba,yana sharemata yana runtse idonsa,akwai wani abu daya sanyashi ya zama qwararre wajen gane fitar hawaye ba tare daya kalli fuska ba matuqar a jikin mutum yake,hawayen AMMAnsa,daya daga cikin abinda yasa ya tsani kukan mace,abu guda daya dake sanya rauninsa bayyana.



Yana da burin kaita gida,a yadda aqarta take da yan uwanta da mahaifiyarta yasan cewa tayi namijin qoqarin zama har zuwa wannan lokacin bataga kowa nata ba,bayan an daukota a lokacin da take tsaka da jinyar rashin dan uwanta,to amma a wanne matsayi take?,wacce amsa ce gareshi na matsayinta a wajensa?,MATA KO QANWA?.



**********Tunda drivern ya daukota takejin wani farinciki cikin ranta,kammaluwar jarabawarta cike da alamun sa'a da nasara,nan bada wani jimawa ba zata tsinci kanta a ajin qarshe na secondary,abinda bata taba mafarkin kasancewarsa kaf tsayin rayuwarta,tafi mafarkin gata can gidan nasuru,gatacan a matsayin matar nasurun,sai gata yau cikin wata mota da take hange a baya daga can qololuwar nesa,bata taba sha'awar hawanta bama saboda tasan ba zata hau ba.


Abu daya ne a yazu yake dan motsa mata,daga sanda ta fara karatun litattafan nan ta gane meye aure?,meye ma'ana da manufar aure?,tun daga ranar daya fara rungumeta cikin jikinsa yabar mata wani abu,ya kuma dauki wani abu daga zuciyarta yayi gaba dashi,to amma ta ina zata fara yaqi da qoqarin karbarwa kanta matsayinta?,wannan shine matsalar da takeji lokaci zuwa lokaci tana motsi a zuciyarta.



Yana tsaida motar ta fito zuwa cikin gida,tana da masaniyar gobe zasu wuce azare kamar yadda ya shaida mata cikin wancan daren data yi masa kyakkyawar ajiya a zuciyarta,don haka tana son hada komai nata aka tsari,ta ciri kayan da take da buqata cikin siyayyar da yayi mata wancar ranar.



Ta saba duk sanda zata shiga waje tayi sallama koda babu kowa,yauma sallamar tayi,duk da tasan mawuyacine ta samu masu aikin cikin falon.


Ga mamakinta sai taji an amsa mata,abinda ya daure mata kai kenan,ta maida dubanta ga wajen da taji an amsata din,sai suka hada ido da mubina tana sakar mata murmushi


"Sonshi nake da gaske jawahir,ko zaki taimaka min?" Kalaman mubina a ganinta da ita na qarshe ya dawo mata,hakanan taji yawan farashin fara'ar da takeson maida mata ya ragu,yaqe taji tana mata,amma duk da haka saita dakata suka gaisa kamar yadda suka saba


"Hajiyan suna azare gaba daya" kaltum ta gayawa mubina tana miqewa bayan ta dauki takardunta


"Eh na sani,ai har mama itama tana can,tare suka tafi,kinsan mama aisha kishiyar yayata ce,ni kuma a hannun yayar tawa nake" dan dubanta kaltum tayi ta gyada kai kawai


"Dama ba wajen hajiya nazo ba ai wannan karon....wajen ya saraki nazo,ancemin yana gidan nan ko?,na taras ana masa gyara ta can bangarenshi na gidan daddy professor"


"Eh.....bari na qarasa ciki" kaltum ta amsa mata a gaggauce kawai,wanda sam mubinan bata kula ba,saita miqe


"Tun dazu nake zaune ba abokin hira,tunda kin dawo muje tare,na samu abokiyar hira" bata hanata ba kamar yadda batace mata komai ba,ta bita a baya tana mata surutu,nata eh ko a'ah.


Da suka shiga dakinma bayan ta aje jakarta bandaki ta wuce,sai tayi tsaye gaban mudubi tana kallon smoothy skin dinta cikin dan qaramin hijabin makaranta dake jikinta,fararen idanunta take kalla tana son gano ko akwai wani abu daya bayyana cikin idanunta?,wani abu take ji ya tokare mata wuya tunda taji me mubina ke fadi?,to me kenan hakan?,tana da tabbacin mubina batasan wace ba ita ba,batasan alaqarta dasu hajiya qarama ba,hakanan batasan matsayinta a wajen muhammad samir ba.


Kayanta ta cire kawai gaba daya tayi wanka,ta fito,tana shiryawa mubina na janta da hirarraki,tana da zaton akwai dangantaka tsakanin kaltum ne dasu jawahir,dangantakar da zata iya taimaka mata ta samu waje a zuciyar samir.


Koda ta gama shiryawa ma hada kayanta ta fara yi,har zuwa sannan mubina nata binta da hira,ita kuma tana qoqari qwarai wajen amsa mata ba tare data yarfa ta ba,duk da zuciyarta na mata wani iri babu dadi.


"Wai tare zaku tafi?,ai kuwa inajin dani za'ayi tafiyar nan" mubina ta fada tana dariyar jin dadi,murmushi kawai kaltum tayi mata,saita miqe daga aikin tana dosar qofar fita tayi kitchen.


Ba kowa a kitchen din,da alama sun gama aikinsu ne sunfice,tasan tazarce sukayi abincin,haka suke yawancin lokuta da hajiya qarama bata nan,sai taji sha'awar shirya masa abinci,don tunda yazo gidan bataga ya zauna yaci wani abincin kirki ba,hakan ma zai taimaka mata ta rage lokacinta sosai,ta kuma rage zangon hirarta da mubina.


A nutse ta fiddo komai ta fara aikinta cikin nutsuwa,cikin wani yanayi me burgewa na tsafta da sanin makamar aiki.


,bata jima da farawa mubina ta biyota,ta sanyata a gaba da hirar da sam ita bata jin armashinta.


Har ya gota sassan hajiyan qaraman sai ya dakata saboda jin qamshin favourite food dinsa,da baya ya koma a hankali yake takawa zuwa ciki,fuskarsa na ga fuskar wayarsa sanda jauhar ke kiransa,ya maidata silent ya sanyata a aljihunsa,kwata kwata baya qaunar wannan nacin kiran nata ko yaushe ba tare da wani specific time ba,baisan me take nema haka dashi ba.


Sallamarsa qofar falon tayi dai dai da qaruwar bugun zuciyarta,ta daga kai daga yanka lettuce din da take tana taya mubina da tuni ta saki hirar ta maida hankalinta kanshi amsa sallamar da yayi


"Ya saraki....sannu da zuwa" mubina ta fada taba murmushi gami da miqewa tsaye


"Yauwa,ya kike?" Ya tambayeta a gajarce,idanuwansa nakan kaltum dake kallon qasa,dankwalinta ya zame kadan,kwantaccen gashin gaban kanta ya fito sosai saman chocolate colour skin dinta


"Sannu da zuwa" ta fada tana qoqarin dai daita heart rate dinta ba tare data iya duban idanuwansa ba


"Yauwa,sannu" ya fada yana duban kitchen din,alamu sun nuna masa cewa itace keyi girkin,agogon hannunsa ya kalla


"Ana gama sallar magarib a kawomin abinci" ya fada yana lalubar qwayar idanunta da taqi bari ya gani


"Tohm" ta amsa mishi a tausashe,saiya juya yana niyyar barin kitchen din,da sauri mubina takai hannu xata karbi brief case dinsa


"Ya saraki....kawo na tayaka mana"


Batasan ta daga kai ta dubi sashen da suke ba saida suka kusa hada ido da samir,saita sauke kanta,tana jin wani abu na matsar zuciyarta,kunnuwanta naga amsar da xaya bata


"Nop,na gode" ya amsa mata yana yin gaba,binsa da kallo mubina tayi,saita koma da baya ta zauna jikinta na mata sanyi,kada fa ace sauqin kan da take hanga tattare dashi ba haka bane?.


Tun sanda suka baro kitchen din kowanne a cikinsu kuzarinsa ragagge ne,ga kaltum bata da tabbacin abinda ya sanya yanayin jikinta sauyawa,saidai tana jin zuciyarta da gangar jikinta duka babu dadi,hakanan ta kasa sakewa da mubina.


Mubina kuwa hasashenta daya ne,a yau din ta shirya ta kuma tattara dukkan wani qwarin gwiwarta na fuskantar samir din,a yau ta shirya shaida masa abinda yake cikin zuciyarta,durqusawa wada ba gajiyawa bace,matuqar zata samu samir a matsayin mijin aure zata iya aikata dukkan wani abu da bai taka kara ya karya ba irin wannan,bai kuma kasance kauce hanya mabayyaniya ba.


Tana saman abun salla bayan ta idar amma tayi nisa a tunani,maganganun saliha ke dawo mata tar a kwanya tun daxu,idan itace da miji irin samir kenan sai taga abinda ya turewa buzu nadi?,ita din zata iya itama kamar yadda saliha tace?,wannan tamkar tunkarar wani babban yaqi ne wanda batasan ya tsakiyarsa zata kaya ba,qarshensa dama nasara ce ko akasinta,batasan wanne matsayi take dashi ko ta taka a zuciyarsa ba bare ta dora daga nan,tafi kowa sanin yawan 'yamnatan dake qaunarsa suke kuma farautar soyayyarsa,tun kafin ta soma jin cewa itama ya kamata ta tabbatarwa da kanta matsayinta a wajensa,tana ji da ganin komai daga wajen jawahir,wani lokaci ita kanta jawahir din takan qi daga wayar wasu da dama daga cikinsu,wadanda ke kamun qafa da ita,to amma idan ta saddaqar.....hakan na nufin zai auri wata a gabanta kenan kamar yadda ta soma jin qishin qishin?,haka na nufin warwarewar igiyar aurensu kenan?, Ta koma ta auri wani?,idan kuma qudurinta ya tabbata fa?,ta yayq zai kalli idanun family dinsa ya shaida musu cewa ita din matarsa ce daya aurota a wani qauye waishi dinya ba tare da sanin magabatansa ba?,idan maganar ta fito waye da waye zai amsheta?,waye kuma zai mata mummunan kallo da mummunan fassara?.


Samun kanta tayi da runtse idanunta sanda sunan mommy da najwa ya darsu a ranta


"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" labbanta suka motsa a hankali,kalmar ta kwarara cikin zuciyarta,sannu a hankali kuma hancinta ya cika da qamshin turaren data tabbatar a zahiri take iya jiyoshi,kafin kuma fa bude idanun nata muryar mubina ta cika kunnuwanta.


"Kaltum da magariba fa yace akai masa,nidai a ready,ki debo kayan na tayaki kaiwa,dama inason muyi magana dashi" a nutse ta daga kanta ta sauke ga mubina dake gaban mudubi tana sake fesa turare baya wancan data fesa,wani abu ya matse zuciyar kaltume,amma saita aro jarumta ta miqe tana nannade abun sallarta ba tare data cewa mubina komai ba ta fice izuwa kitchen.


Tana tsaka da harhada kayan abincin mubinan ta shigo,tayi shar cikin wani riga da skert da yadin material na mata me sulbi,sai baza qamshi take kamar tayi barin turare.


Ita tayi uwa tayi makarbiya ta amshe kwandon kayan abincin,kaltum din najin wani abu me kama da haushi yana son sauka a zuciyarta ta sakar mata kwandon,ko banza ita din macace,ya kamata kuma ta mutunta tare da martaba darajarta da mutuncinta na diya mace,bata tanka mata surutanta ba ta dauki flask na tea data hada masa ruwan zafin da bata da tabbacin zaisha tunda batasan zabinsa ba ta bita dashi.


Sanya yake da fara qal din long sleeves shirt,wandon jikinsa ash ne me turuwa,wanda iyakacinsa qauri,sun sameshi zaune da jibgin files a gabansa da alama aikin office ne ya deboshi zuwa gida,waya yake amsawa,amma idanunsa na kan qofar sanda suke shigowa.


Amsa sallamar mubinan yayi yana mamakin shigowarta sashen,saidai kafin ya dauke idanunsa ya hangi kaltum daga bayanta,sanye da madaidaicin hijabi light blue,wanda ya haska zagaggayar fuskarta,ya kuma qara fito da hasken qwayar idanunta.



Duk da amsa waya yake amma yana karantar sanyi cikin yanayinta,daga sanda yaji karatu akan girman amana gaba daya hankalinsa ya sake karkata a kanta,yana jin ashe wani babban nauyi ne akansa daya kamata ya bashi dukkan wata kulawa iyaka qarfinsa.


Ya gama wayar ya katseta yana ajjiyeta gefe,yana daga kai suna hada ido da mubina,saita saki murmushi tana sunkui da kai ita dole taji kunya.


Bai kula da wannan ba,ya fara janye hannun rigarshi zuwa baya tare da lanqwashe qafafunsa sanda take aje masa abincin a gabansa


"Sannu" ya furta can qasa,yanayin da sautin maganar ya fito ya tilasta mata daga kai ta dubeshi,saboda yayi maganar ne tamkar me rada.


Fridge ta nufa da niyyar dauko masa ruwa,sai yace


"Dawo nan ki zauna....jeki cikin gidaki daukomin ruwa mara sanyi" yace da mubina.


Dadi ne sosai ya rufeta,ta miqe da saurinta ta nufi qofar fita,saiya maida dubansa ga kaltum dake laluben wajen zama


"Dawo nan" ya fada yana nuna mata gabanshi,a sanyaye ta dawo ta zauna din inda yace mata,duk da cewa zaman kusa dashi irin haka ya mata nauyi amma ba zata iya kaucewa umarninsa ba


"Mene yake damunki?" Ya jefe mata tambayar yana bin fuskarta data dan cika ta murje da kallo kusan irin na qurilla,dan mitsitsin bakinta yana motsawa kadan kadan, Tambayar ta isketa a bazata,don bata zaci jin haka daga bakinsa ba,saita girgiza kanta


"Babu komai" ta amsa mishi,baice mata komai ba sai yaja abincinsa ya fara ci,ba jimawa mubina ta shigo da ruwan,hakan yasa kaltum miqewa tana neman izinin tafiya,don bata jin zata iya zama mubinan tayi maganar da take da qudurin yin a gabanta.


"Ki jirata ku wuce tare....uhmmm,ina jinki" samir ya fada duka lokaci daya.


Bai fasa cin abincinsa ba sanda take koro bayanta cike da kunya da kuma ɗar ɗar,saidai ya kafeta da manyan idanunsa,zuciyarsa cike fal da mamaki,yana kuma qoqarin danne mamakin da kuma dariyar data bashi har ta kammala bayananta.



Abincin ya aje gefe yana kallonta,ya karanci mata wani bin duka tunaninsu iri daya ne,basa kallon abubuwa a yadda suke,sau tari komai suna kallonsa a baibai a maimakon zahirin yadda yake


"Shekarunki nawa?" Tambayar data jita banbarakwai,saita tsargu,ta saci kallon kaltum,wadda tunda ta sunkui da kanta bata dagashi ba


"Sha....sha,ashirin" yadda ta bashi amsar ya tabbatar masa ta dan qara wani abu akan ainihin shekarunta,murmushin gefan baki ya saki


"Karki bari matata ta san ainihin abinda kike nufi ko fada a kaina,if not kuma.....saita zaneki,ku tashi kuje ku kwanta,gobe akwai tafiya a gabanmu" daga haka ya balle murfin ruwa ya soma sha a nutse.


Tuni kaltum takai qofa,saboda amsar daya bayar tamkar saqo ne zuwa ga mutum biyu kenan,wacece matarsa?,me kuma hake nufi da ita,mema maganarsa gaba daya ke nufi?,wadan nan sune ire iren tambayoyin data kwana tana yiwa kanta.


Tana iya jiyo kukan mubina bayan ta gama gayama kaltum din cewa


"Me yasa ya dauka abinda nake gaya masa bada wani muhimmanci ba?,bayan ni ina gaya masa saqo ne mai muhimmanci?" Ba zata iya cewa da ita komai ba,don itama ta kanta take,har ta gama maganganunta ta barke da kuka,tun tana jin kukan mubina har taji shuru,da alama tayi ta gaji,ko kuma bacci ya dauketa,saita sauka a hankali ta zura qafafunta qasa tayi bandaki.


Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana ture ayyukan dake gabansa,duk yadda yaso ya tilastawa kansa yin aikin abun ya gagareshi,fuskar kaltum din yake hangowa sanda mubinan ke isar mishi da saqon,yana sane ya zaunar da ita,akwai abinda yakeson gani da kuma karanta daga gareta,saidai kuma iya zamanta da tashinta taqi bashi damar komai.


Mirginawa yayi ya koma rub da ciki,yana tallafe fuskarsa da tafukan hannayensa,gami da lumshe idanunsa,yana jin yadda sukayi masa nauyi saboda baccin da ya cikasu,amma zuciya da qwaqwalwarsa sunqi bashi hadin kai.



Saidai shi bacci ba'a ci masa bashi,kamar yadda ba'a qayyade masa lokacin yinsa,a hankali idanunsa suka dinga rufewa har sukayi nauyin da bazai iya budesu ba,ya lula duniyar bacci.



*_DUNIYAR MAFARKI_*


    A firgice ya farka,saidai bakinsa dauke da addu'a,a hankali yake karanto addu'o'in da ma'aiki ya bayar ga duk wanda yayi mafarki mara dadi,saiya miqe ya nufi bandaki,idanuwansa na haska masa fuskar mahaifiyarsa da yake gani tsugune a gefansa,tana kuma masa nuni da mahaifinsa dake tafiya zuwa wani wawakeken rami wanda wuta ce fal keci a cikinsa.


******Babu wani cikakken kuzari a jikinta take qarasa hada jakar kayanta,banda hajiya qarama da jawahir da suka damu da zuwan nata da babu inda zata.


"Ya na ganki a zaune?" Kaltum tayi qarfin halin yiwa mubina magana sanda ta dauki jakarta bayan samir ya aiko a shaida mata ta fito,kaita girgixa qwalla na sauko mata


"Bani da nutsuwar da zan iya binku,saikun dawo" bata iya ce mata komai ba ta soma takawa tana ficewa,mafarkinta na jiya na sake tsaya mata sosai a rai,duk kuwa da cewa kusan maimaici tayi na abinda ya faru a mafarkinta na wancan karon,amma abun sai ya tsaye mata a rai fiye da wancan.


Ga hoton matar har yanzu a wajenta,amma bata da wanda zai gaya mata wacece ita?,ta kasa fassara ma'anar yawan ganinta da takeyi cikin barcinta,saidai a yanzu zuciyarta ta karkata da zuwa gidan masu lalurar tabin hankali taje ta ziyarci matar data gani a gidan,wadda take mata kama da.matar dake zuwa mata a mafarki,duk da cewa waccar ta gida masu lalurar tabin hankalin shekarunta sunfi na wadda take cikin hoton da kuma wadda take gani a mafarkin tsufa........




52

D/Z



Tunda ta tunkaro wajen ya gaza dauke ganinsa daga kanta,karon farko daya soma ganinta cikin shiga irin wannan.


Abaya ce a jikinta baby pink mai sulbi mai kuma hawa biyu,wadda ta wadata da adon baqaqen duwatsu masu wani irin walwali da sheqi,duk da cewa shiya siyo kayan,amma ba tsammaci zasu karbeta har haka ba.


Yayi tayi rolling mayafin ya baiwa gaban gashinta mai santsi damar fitowa,idan ka kalleta zakayi tsammanin irin kyawawan Ethiopians din nan ne,saboda yadda kalar fatarta ya sake fes kamar bata shiga rana.


Igiyar da akayi daga tsakiyar ciki don daure rigar ta zauna daidai jikin me ita,ta taimaka wajen fitar da surar albarkar qirjin da Allah ya bata,wanda sam batasan hakan ya faru ba,saboda ko madubi bata tsaya kalla ba,idanunta sun sake shanyewa saboda rashin wadataccen baccin da bata samu ba a daren jiya,babu koma a fuskarta banda wata powder da jawahir ta siya mata ta masu kalae fatarta, powder din kuwa ba qaramin kyau takewa fatarta ba,sai labbanta daketa qyallin man lebe daya qarawa leban nata taushi da kyau.



Baisan ajiyar zuciya ya saki ba,saida ya tsinci zuciyarsa tana tuhumarsa da yadda ya qure kaltum din da kallo har ta kamashi yana kallon nata,abinda ya sanyata jin kunya,ta saka hannu a hankali ta bude gidan gaba ta zura jikinta kafin qafafunta da suka sha hill shoes su biyo baya,abinda ya qarawa adon nata kyau,budurcinta daya fara bayyana ya sake fitowa fili muraran.


"Ina yini" ta gaidashi a ladabce tana dora purse dinta saman cinyarta


"Lafiya lau" ya amsa mata yana kallon yadda garin ya fara hada hadari,ba kasafai yakeson tuqi da damina ba saboda ruwa,yaso tafiya ne a jirgi,so amma duka yau babu jirgin da zai tashi daga kano zuwa bauchi,don haka ya maida tafiyar kawai a mota,saboda lokaci ya riga ya qure,gobe ne daurin aure,a haka ma yayi missing events masu yawa,ya kuma sha mita da qorafi wajen amiru,amma duka ya shareshi,don dama shi ba kasafai ya fiya shiga irin wadan nan shagulgulan ba sai wadanda suka zama dole.


Yana qoqarin tayar da motar qamshinta nason dagula masa lissafi,sai zai murza key din sai yaji kamar bazai iya ba,kamar wanda aka zarewa dukka lakar jikinsa,har taji shurun yayi yawa,ta daga kanta daga murza yatsun hannunta da take tare da wassafa yadda xasuyi tafiya tare dashi ta awanni masu tsaho daga ita saishi.


Kallon datayi masa akayi katari shima ita yake kalla,a hankali ya motsa labbansa,idanunsa kan dan qaramin bakinta


"Wannan rigar....." Sai kuma yayi shuru ba tare daya qarasa ba,ya cire hannunsa daga kan motar a hankali ya nufo inda take zaune,numfashinta ta dauke gaba daya ganin ya nufo da hannunsa qasan qirjinta.


Yatsa daya ya saka ya kunce igiyar data daure tsakiyar rigar da ita,take rigar ta ware,ta batar da duk wani shape nata daya fito.


Sake qamewa tayi tare da runtse idonta ganin ya matso da jikinsa gaba daya inda take,qwayar idanunsa cikin nata,cikin second biyu qamshin turarensa,da hucin numfashinsa da dumin jikinsa gaba daya suka mamayeta.


Seat belt ya zaro a hankali ya zagayo da ita ta saman cikinta,wanda garin hakan yadan shafi qirjinta da bayan hannunsa,al'amarin daya sanyashi jin wani shock tun daga yatsun qafarsa zuwa kwanyarsa,ya sauke numfashi me nauyi sanda ya gama saka mata ya maida bayansa ya jigina da kujera yana qoqarin maintaining nutsuwarsa.


Har zuwa sanda ya bude nashi idanun,ya murxa key din ya tashi motar yana karanta addu'ar matafiya a fili amma qasa qasa.



Tata addu'ar itama ta fara karantawa sanda suka ficewa daga gidan,wanda basuyi wata doguwar tafiya ba ya sanya karatun daya daga cikin shahararrun malamai kuma bayin Allahn da ubangiji yayi mana kyautarsu wato mlm dr umar sani fage.


Karatun kusan shine ya janye hankalin kowannensu,karatu ne cike da tarin hikima da kuma maganganu na fasaha,tare da tunkuda bawa zuwa kusanta kai da Allah matuqar kusantuwa,tun tana iya jin abinda malamin ke fada tana kokawa da bashin baccin data ci jiya,har yayi nasarar yin awon gaba da ita ta daina jin komai.


Tafiyar awa uku da rabi suka shiga garin azare,kai tsaye suka nufa cikin garin,zuwa lokacin garin azare ya fara duhu saboa hadarin da ya yiwa sama rumfa,saidai mutane da yawa basu kawo zubarshi ba,saboda wannan kusan shine hadarin farko tun bayan sanya ran shigowar damina.


Idanunta biyu a sannan,sabida sun tsaya sunyi salla,ya siya musu take away duk da itadin bata iya ci a gabansa ba.


Ringing wayarsa tayi,yana tuqi a hankali da hannu daya,yasa daya hannun ya daga wayar ya sanyata a kunne idanunsa na bisa titi.


Magana suke da amiru,ya shaida masa akwai dinner din mr and mrs da za'a gabatar takwas na dare,amma saboda ganin hadari yasa an maidota nan da awa biyu


"This is none of my business.....meye amfanin gayamin?,kai kanka ba zaka samu shiga ba tunda tuzurun banza ne,har gwara gwara ni" dariya sosai amiru ya qyalqyale da ita,bazai biye masa suyi abinda suka saba ba,don so yake yallaboshi yazo kodon saboda kada angon ya fassara wani abu daban,saboda yarinyar da zai aura din tadan so samir


"Wai tula ne zaiwa audi gori......gwara kai ame?,tuxurantaka?,meye marabar dambe da fada,ni dakai ai duk d same,amma dai afuwa master,na yadda da kai,yanzu abinda za'ayi,kada ka wuce gida,ka tsaya dai dai Round about din nan da zaka shiga titin gidan ya dikko,kafin ka shiga titin ka tsaya,am on my way" katse wayar kawai yayi ba tare daya amsawa amirun ba,sai ya koma tuqi a hankali yana duban hanya.


Tun kafin su qarasa ya hangi samir din jingine da wata sabuwar baqar mota,dai dai sanda motar take fakawa,daidai lokacin yaga ya cusa kanshi ta window din motar,da alama magana yake da wasu,sai samir din ya kashe motar kawai yaci gaba da xama cikin motar ba tare daya fita ba,ganin haka amirun ya tunakarosu,kanshi tsaya ya tsaya side din kaltum,ya bude murfin motar yana cewa


"Sannu da hanya madam,ga mota can shiga ta ciki" duban samir tayi suka hada idanu kana ta dauki jakarta ta fice daga motar,wanta tashinta ya sanya wani abu fadowa daga jikinta,hannu ya miqa yana qoqarin dauko takardar,saiya kula hotone,ya juya hoton a hankali,take idanunsa sukayi arba da fuskar dake jikin hoton,abinda ya sanyashi bin baya kaltum da amiru dake tafiya zuwa wancan motar da kallo,mamaki na mamayarsa na inda ta samo hoton,saiya bude locker din motar ya saka hoton ya rufe yana juya tambayar inda ta samo din cikin ransa.


Ruqunqumeta jawahir tayi sanda suka shiga cikin motar,kamar xata koka cikin kaltum din,jtakam dariya kawai kaltume din ke mata,har zuwa sanda amiru da yaga basu da niyyar rufe motar ya rufe musu ya koma wajen samir.



*********kayan da amirun ya miqe masa ya kalla


"Am telling you fa,babu inda zanje,ina buqatar na huta malam" kicin kicin amiru ya masa,yasan idan baiyi da gasken ba ba zaya je ba


"Wallahi koda wannan shine last thing da xakayi a azare sai kaje" gira ya dage ma amirun dukka biyun yana dubanshi


"Really?" Harara ya watsa mana,saiya fincika kayan daga hannunsa ya watsa gado ya bisu ya kwanta kawai a kai,qyaleshi amiru yayi,tunda yayi hakan yasan zayaje din koda baiso ba.


      Kanta ta karkatar ta dubi jawahir


"Don Allah ki shiga na jiraki anan mana" kaltum ta fada tana kwabe fuska,tun daga sanda akayi.mata kwalliyar dake fuskarta har zuwa yanzu duk a takure take,sanda taga fuskarta a madubi sai data tsorata,irin kyan da tayi bata taba zata ko tsammatar ganinsa a fuskarta ba,dukka jama'ar dake wajen sai da suka tsaya suna kallonta,saboda yadda kwalliyar tayi masifar bin lafiyayyar chocolate colour din fatarta ta kwanta sosai.


Idanu jawahir ta fitar


"Wa?,ai wallahi saikin shiga,nima setup mukayi da ya amiru a matsayin miji da mata zamu shiga,kema haka zaki haquri kizo mu shiga.....kinga ma yana kirana,hala ya iso" jawahir ta fada tana daga wayarta tana duban me kiran,sai kawai taga ta balle murfin motar ta fita tana duba ta inda suke.



Ta bangaren da take ta leqo ta mata alamar ta fito,a hankali ta janyo jikinta ta zuro qafafunta daga motar.


Yana tsaye ya basu baya kadan,hannayensa zube a aljihun wandonsa yana duban wajen,ranshi baiso zuwa wajen ba,kawai dai yayine saboda ya faranta ran amirun daya dage.


"Oya....muje already ma an fara event din" amiru ya fada,abinda ya sanya samir juyowa kenan.


A hankali idanunsa suka sauka kanta,tana tsaye dab dashi,sai yaji wuta ta dauke masa na wucin gadi,baisan sanda ya bita da kallo tun daga sama zuwa qasa ba,wani kyau na musamman da bai taba tsammatarsa ba tayi masa,komai ya fito perfect,duk wata baiwa tata ta fito,ta zama cikakkiyar budurwar me tashen shekaru da zata iya jan hankalin kowanne namiji da zai dora idanunsa a kanta.


Wani abu da yaji ya tsaya masa a wuya ya hadiye,ya dauke idonsa daga kanta ya maida kan amiru,saiya miqa hannu ya fincikeshi gefe


"How dare you zaka sata tayi irin wannan kwalliyar amiru?" Idanu amiru ya fitar


"Mene aibu to?"


"Ka manta matar aur......." Maganar ta maqale masa ba tare data gama fita gaba daya ba,saboda rashin sanin ma'anar yin maganar.


Dariyar da amirun ke boyewa tadan fito kadan


"Bari na qarasa maka tunda kunyar qarasawa kake,na manta matar samir ce?,ko?,karka damu,ni kadai na sani fa,amma yau kowa a hakan zai kalleta......muje please muna sake makara" amirun ya fada yana yin gaba da sauri,ya jera shida jawahir itama daketa boye dariyarta,duk da batasan alaqar dake tsakani ba amma cewa take


"Wallahi ya Aamir sunyi kyau sosai,sun dace da juna Allah yadda kasan miji da mata,dama zaiso kaltum, she's cute wlh,duk da bayason baqar mace amma kaltum ta dace dashi,yau ka yima ya samir shigar sauri" murmushi shima yayi ya waiwaya yana satar dubansu sanda suke gab da shigewa hall din.


Shuru ya biyo baya a wajen,tana tsaye a inda take kanta aqasa tana wasa da yatsun hannunta,saboda gaba daya jinta take a takure,yayin da yake tsaye,har yanzu hannayensa zube a aljihunsa yana ci gaba da qare mata kallo,a hankali ya tako zuwa inda take,ya zare hannunsa daya dake aljihunsa ya kama nata hannun,gaba dayansu wani abune yabi ta jijiyarsu ya aikama qwaqwalensu saqo,saiya fara takawa a nutse tana biye dashi,wanda kafin sukai ga shigewa ciki yayyafi mai qarfi ya fara sauka.


Suna shigowa wajen idanun jawahir na kansu,baki ta bude tana mamaki,yau yayansu ne da kama hannun wata?,kasa daurewa tayi sai data tabo amiru.


Daga can baya ya zabar musu sit,tunda suka shiga wajen bai motsa ba kamar yadda itama bai barta ta motsa ko nan da can ba,bayaga ango da yaje ya yiwa Allah ya sanya alkhairi,abinda ke bashi haushi da mamaki shine duk wanda zai wuce ta wajen saiya kallesu yakuma juyowa,wayarsa na hannunsa yana amsa saqonnin da baiyi niyyar dubawa bama,lokaci lokaci yakan saki tsaki ya kuma jewa amiru harara.


Sanda aka fara rabon abubuwan motsa baki jawahir ta matso gurin ganin bata taso ba


"Kaltum....bakwa sha'awar komai ne?" Ta fadi tana ajjiye wani paper plate dake hannunta


"Get out malamarsu" samir din yadan fada a kausashe,da alama akwai abinda ya taba rashi,ba zata iya tuna yaushe ne na qarshe daya mata hakan ba,don haka ta dauke plate dinta tana boye fuskarta tabar wajen.


Da kadan da kadan ake raguwa awajen,duk da ruwan saman daya fara sauka bai hana mutane tafiya ba,saboda kusan kowa da motarsa yazo shida iyalinsa,wajen ya qayatar sosai,babu hauka babu baragada,kowa da matarsa yake,masu setup irinsu jawahir kadanne,sai zuwa sannan ya daga kanshi yana maida wayarsa aljihu yana kuma dora kansa a kan kaltum.


Kwalliyarta na nan kamar sannan aka yita,dan qaramin bakinta da yasha jambaki yana motsawa kadan kadan,baisan me take fada ba,daya tsura mata idanu sanda aka yi tsawa sai ya lura addu'ar tsawa take,ta dan rufe idanunta kadan,wanda hakan ya fito da zara zaran gashin idanunta da zaka tsammaci sa mata akayi,saidai mascaran da aka sanya musu ya sake fitar da kyau da tsahonsu,ya fuskanci tsoron tsawa take sosai,saiya miqe a hankali ya miqa mata hannunshi.


Jin tsaiwarsa saman kanta yasa ta bude idanuwanta,suka sauka akan lallausan tafin hannunsa da yake miqa mata,karo na biyu kenan daya taba bata wannan damar,tana jin kunya tana kuma jin nauyi,yana kuma sanyata shiga wani yanayi,amma haka ta dora masa nata hannun a hankali ya rumtse cikin nasa ya kuma jirayi tashinta kana suka nufi hanyar fita.


Dukka akan idanun jawahir,mamaki yana sake kamata,bata taba ganin haka daga yayan nata ba,hannunsa cikin na wata?,me aikin gidansu?,kuma ba muharramarsa ba,shida kullum maganarsa itace su kare mutuncin kansu,kada su yarda koda wasa su hada jiki da wani da namiji?,binsu tayi da idanu har suka fice daga hall din.


Dakatawa yayi da tafiyar yana kallon ruwan,ya soma qarfi sosai,wanda mutane da yawa dake ciki basusan da hakan ba,waiwayawa yayi kadan ya dubeta,sai yaga ruwan ta zubawa idanu itama,da alama tana wasafta ta yadda zata shiga cikinsa.


Yana riqe da hannunta a hankali suka fara taka cikin ruwan suna dosar motarsu,idanuwanta ta runtse sanda sanyin ruwan yake ratsa jikinta,saukarsa ta farko ji tayi kaman numfashinta zaya dauke,tunda can ita me tsoron ruwa ce,shi yasa kaf rayuwarta bata taba shiga rafi wanka ba,saidai tayi rakiya wa su wasila,tana tsaye kuma har suyi su gama.


Qarfin ruwan ya sanya kafin su isa motar ta jiqe,duk da bame yawa ba amma tana jin sayin har cikin qashinta.


Takurewa tayi sosai a sit dinta,tana kallon singalilin hannunsa da ruwa ya jiqa yana kashe ac ya maidata zuwa heater,sumar gargasarsa itama tayi luf,ta rufe idanunta sanda akayi wata walqiya,ta tabbatar tsawa ce zata biyo baya don haka ta sake curewa guri guda.


Binta yayi da kallo,saiya saka hannunsa ga seat din baya,ya dauko hiramin daya siya dazun a store din da sukaje siyayya shida amiru,ya farke ledar ya wareshi ya soma rufa mata,abinda ya sakata bude ido,idanunsu ya shiga cikin na juna,eye lashes dinta sun jiqe sosai sunyi wara wara,sai tayi qas da kanta tana jin dadin rufetan da yayi


"Na gode" ta samu kanta da fada,ya tada motar yana amsa mata da


"You are welcome".


Tun basuyi nisa ba ruwan yayi wani irin qarfi naban mamaki,tituna suka fara cika saboda rashin kyakkyawar magudanar ruwa,tsaki samir din yaja yana kallon yadda titi ya shafe da ruwa,ya rasa aikin me gwamnati keyi?,ruwa a saman titi kamar layukan unguwanni?" Baka bambace titi da kwata?,yana daya daga cikin abinda yasa ya tsani siyasa iyaka kenan,babu komai cikinta sai yaudara da daukan alqawuran dako kusa ko alama basa iya cika koda kaso daya cikin ukunsu.


Ji yayi bazai iya ci gaba da tuqin ba,don baisan yadda zai tadda unguwarsu ya dikkon ba,bugu da qari ma ya tabbatar idan yaje zaiyi horn ne ya taso me gadin da a yanzu yake cikin dakinsa ya samawa kansa mafaka daga dukan ruwan saman,wannan tunanin yasa ya gangara a hankali hannun da yake tuqi qofar wani katafaren guest in,ba tare daya tuna inda zai ajjiye kaltum din ba.


Umarnin fitowa yayi mata bayan ya bude mata murfin motar,ta fito a hankali tana sake hade jikinta waje guda,saiya saka hannunsa saman daya kafadartata ya janyota zuwa jikinsa,abinda ya rage mata dukan ruwan,saidai kuma hakan da yayi mata tamkar ya sake jefa abun fashewa ne cikin zuciyarta,ta dinga sauke qaramar ajiyar zuciya a hankali.


Da tarba ta mutunci receptionist din ya karbeshi,ya buqaci daki biyu


"Saidai kayi haquri yallabai idan babu damuwa kuyi squatting a daki daya,babu dakuna sai wannan da ka karba yanzu guda biyun da suke ba kowa a ciki gyara ake musu,babu damar iya zama a ciki"


"Ba matsala" ya fada a hankali.


Sai daya bude mata dakin ta shiga sannan taga ya sake fita ya dawo bada jimawa ba,hannunsa dauke da wani irin akwati dan qarami me dauke da tambarin wani store,wanda manyan customers dinsu da sukayi siyaya da yawa ko me manyan kudi suke zubawa kaya a ciki.


Tana daga zaunen ya kunna heater din dakin,ya rage haske qwayayen,sannan kuma ya kunna water heater ta bandaki ya shige bayan ya tara ruwa me zafi sosai.


Har sanda ya murda qofar toilet din ya fito tana zaune a wajen jikinta a hade,duk da dumi ya fara ratsata,saidai hankalinta ya rabu biyu,ta yaya zasu kwana a dakin nan daga ita saishi?,me zata cewa jawahir idan ta tambayeta ina sukaje?,zatace mata ne sun kwana tare bayan babu wanda yasan alaqarsu?.


"Ki cire wadan nan kayan kafin sanyi ya kamaki,ki shiga toilet ki dumama jikinki da ruwan zafi" ya fada sanda yake fitowa daga toilet din sanye da sabuwar rigar wanka ta towel har qasa me budadden qirji,abinda ya bayyana tarin sumar dake kwance a qirjinsa baqa sosai mai kuma santsi.


Numfashinta ta dauke gaba daya tana sake qanqame jikinta,ruwan da yayi wanka ya sanya kowacce suma ta jikinsa kwanciya,hatta da qawataccen sajen fuskarsa mai kama da qasumba,saidai baikai qasumba fadi da cika ba.


Wani abu ta hadiye,cikin dakiya tace


"Da zaka qarasa dani gida....saboda su jawahir....." Kasa qarasawa tayi saboda ji da tayi a jikinta ita ya zubawa ido,ilai kuwa haka ne,har baisan sanda murmushi ya subuce masa ba,yana da tabbacin batasan waye samir ba,wannan rayuwar ba irin waddanya fasaltawa kansa ko yake sha'awarta bace,inda tazo masa a matsayin matar aurensa da suka fahimci juna,duniya tasan da aurensu da ba wannan zancan ake ba a yanzu,kwata kwata wannan ba irin rayuwar auren daya tanadarwa kansa bace,saidai akwai wani qwaqqwaran bond da yakejin yana son gilmawa a tsakani,duk da haka aure duka aure ne,zai tunasar da ita abinda takeson mantawa,duk da cewa baison ya wuce gona da iri,saboda yanajin cewa gaba kadan xai bata dukkanin zabi ne.


Batasan ya tsaya a gabanta ba sai da idanunta suka dauka kam xara zaran yatsun qafarsa da gashin ke kan kowanne dan yatsa ke akwance shima,kafin tayi wani motsi ya kama dukka kafadunta ya dagata,sai ya saka hannu ya zare hiraminsa ya aje gefe,jawota yayi jikinsa ya mata sasssuqar runguma,abinda ya kusa sanyata daukewar numfashinta kenan saboda jikinta daya gogi nashi,shi dinma yaji,amma ya dake,yanason ya mata tuni ne kan abinda ta manta,saiya kama zip din rigarta ya saukeshi qasa gaba daya,duk da cewa a iya nata qarfin fa cukuikuye rigar a jikinta amma hakan bai hanashi sabule mata ita ba ya hada harda bra dinta,adalci daya yayi mata tana jikinsa bazai iya kallonta ba saidai duk wata fata ta jikinta da hannunsa ya taba yana jin aiken saqo zuwa kowanne sashe na jikinsa,sai ya dauko hiramin ya rufa mata,ta kamashi kuwa tsam ta riqe tana sake lullube jikinta,ko ina na jikin nata yana rawa,qafafunta kamar ba zasu iya daukarta ba


"Akwai ruwa me zafi kije kiyi wanka kixo ki kwanta,idan sun tambayeki gobe,kina iya gaya musu mijinki kika biyo,naki da zunubi ko dis a wajen Allah" ya fada yana juya mata baya yana takawa zuwa gaban madubin dake fuskantosu,saidai yana iya hangenta ta madubin sanda take takawa da sauri kamar zata fadi ta durfafi bandaki.


Ta dade a tsaye tana haki tare da sauke numfashi,gaba daya ya aza mata wani irin nauyi da tsoro,bata taba kawo haka a tsakaninsu ba,duk da cewa tana jin abubuwa masu yawa dangane dashi cikin zuciyarta.......



*_A WANNAN DAREN_*



      Su biyu ne rak zaune cikin dakin,duk da suna saka ran shigowar mutum na uku wato najwa.


     A hankali hajiya jidda ke qarewa dakin kallo,tana qiyasta yawan dukiyar da aka sake narkawa dakin,kafin maganar hajiya shuwa ta shiga kunnenta


"Idan bakiyi wasa ba hajiya jidda kwabarki tana dab da tayi ruwa,dava tafiyata ace babu wani ci gaba da aka samu?,saima tarin koma baya dani na hango?,me yasa ba zaki kawo qarshen komai kowa ya huta ba kema ki huta?,tun kafin akai lokacin da zaki dora hannunki aka?" Murmushi mummy ta saki tana duban hajiya shuwa


"Akwai abinda nake jira da dako,banason garin sauri naje na aikata kuskuren da kika kusa aikatawa" murmushi hajiya shuwa ta saki


"Iya gidan nan kadai amma ya isheki amsa ko?" Maida mata murmushinta mummy tayi


"Eh qwarai,saidai akwai banbanci,banajin zan iya qarasawa bigiren da kike kai a yanzu" dariya sosai hajiya shuwa ta saki


"Kijimin mata.....da wanda yaci alade,da kuma wanda yaci mushe meye bambancinsu?"kai mummy ta girgiza


"Banbanci me tarin yawa kuwa,tunda ko banza shi mushe ai yankan Allah ne......".



A hankali najwa taja da baya hannunta riqe da cup din tea data hado da niyyar sha,ta taka kuma zuwa dakin da aka sauketa cikin gidan hajiya shuwa tun bayan zuwansu garin azare,wanda sukaqi zama gidan ya dikko.


Katafaren dakin da sai ka zaci dakin wata hamshsqiyar ne,ranta a bace take duban tvn dake aiki a dakin,duk da cewa bata tvn take ba,hirarsu mummy ke dawo mata,ko daya bataji sun tattauna kan matsalarta ba.



shedan ke dake zafafa mata zuciya,ta fuskanci mummy tana slow ne kan abubuwa da dama,to itakam a yanzu tanajin qarfinta ya kawo,zata shiga nata yaqin,zata aiwatar da abubuwan da mummy ta kasa aiwatarwa,bata jin xata yarda ta amince....tasha dukka wata wahalar karatu saboda cikar buri da muradinta,sannan a qarshe daddy yace taje tayi aiki da kamfanin saraki a qarqashin sarakin?ba zata iya ba,kuma da sake.


Miqewa mummyn tayi tana tattaki gaban hajiya shuwa,maganganun da suka sakeyi suna mata yawo akai,hajiya shuwan kuma na binta da kallo.



Tsayin wasu mintuna mummyn ta dawo gabanta ta tsaya


"Na gamsu da dukka bayanai da hujjojinki,kuma a wannan karon ina ji a jikina zan aiwatar da tunaninki,muga kalar naki takun" kalaman da suka sanya fitar murmushi daga fuskarta hajiya shuwa,ta daga hannu tana jinjinawa mummy.


.


"Ya na ganki ke kadai?,Ina kaltum din?" Hajiya qarama ta tambayi jawahir wadda take fidda kayan jikinta da suka jiqe da ruwan sama.


     Tsaiwa tayi da cire kayan,ta ta waiwayo ta dubi hajiya qarama


"Sun rigamu fitowa fa,basu iso ba kenan?"


"Nidai babu wanda na gani a cikinsu"


"Ok,bari na gama na kira ya sarakin" ta fadi tana dauko kayan da zata sauya din masu dan kauri saboda sanyin ruwan da ya ratsata,sai data gama shiryawa sannan ta zauna ta soma kiransa.


   Tana shiga amma ba'a dagawa,already ya sanyata a silent ne,kaltum dake duqunqune cikin bargo tana sheqar lallausan qamshin turarensa daya kama kayansa tana iya hango hasken wayar saboda a saman kanta take a ajjiiye,saidai batason yin magana kwata kwata,tafison ya dauka tayi baccin ne kamar yadda ga zata,tun sanda ya bata rigarsa ta sanya kunya da nauyi suka cikata,saboda barin nata kayan da yayi cikin mota.


Shafa addu'arsa yayi a hankali,sannan yaja bargon daya dora saman dogayen qafafunsa ya dawo zuwa qugunsa,sannan ya zame a hankali ya kwanta a hannunsa na dama.


A hankali ya lumshe idanunsa kana ya budesu,idanunsa suka sauka a bayanta,duk da cewa baya iya hango komai na jikinta sai bargon data duqunquna har kanta da shi.


Wani numfashi mai nauyi ya sauke,yanayi irin wannan yana saukar masa da feelings sosai tun ba yanzu ba,qamshin qasa hade da sassanyar iskar damina ta dare,saiya sanya hannayensa tsakiyar gwiwoyinsa kamar maijin sanyi,haka kawai kasancewarta kusa dashi ke neman dagula lissafinsa,tsahon rayuwarsa wannan shine karo na farko daya taba hada makwanci da diya mace,yaso ya barta ta kwana a qasa kamar yadda ta zaba,saidai kuma yaga hakan bai dace ba,duba da sanyin ruwan dake sauka,ga kuma tiles da ya yiwa dakin qawanya.


Hasken wayar ya hango,wanda ya bayyana bayan walqawar walqiya a sararin samaniya,walqiyar data sanya kaltum runtse ido sosai da kuma curewa waje guda tana addu'a qasan ranta,kan Allah yasa ba tsawa za'a saki ba.


Hannu ya miqa ta saman kanta zai janyo wayar,dai dai sanda qarar tartsatsin walqiya mai qarfi ya baje a fadin duniya ya sauka zuwa kunnen kowanne abu me rai dake sararin subhana.


"Alhamdulillahil lazi yusabbihur ra'adu bi hamdih,wal mala'ikatu min khifatihi" saraki ya fada a hankali yana dan runtse ido saboda qarar tsawar,sannan ya bude idanun nasa a hankali ya sauke a kanta.


   Baiyi tsammanin cewa batayi bacci ba saida aka saki tsawar yaji yanda ta firgita,har kuma bayan shudewr tsawar yana iya jin yadda ta sake tattarewa waje daya,bai fasa dauko wayar ba,ya budeta ya shiga app din karatun qur'ani,qira'ar shaik abdur rahmani assudais,ya kunna suratul baqra,ya sanya volume dinta saisa saisa (indai har zaki iya kwana da waya saman kanki bayan kin gama danne dannenki,to yana da kyau ki koyi sanya karatun qur'ani cikin dakinki sanda zaki kwanta bacci,cikin qaramin volume ba mai yawa ba,hakan yana taimakawa wajen yin bacci me dadi mai kuma cike da nutsuwa,uwa uba ga tsaro da zaya baki daga dukkan sharri,koda bunu chargy indai akwai wuta,jonata a socket,ki kunna qur'anin,yana playing tana chargy,zaki mamakin yadda wayarki zata cika da wuri,ga kuma qur'anin yana yi har safiya,koda chargynki ya kusa qarewa kika kunna,wani hukuncin Allah wayar bata mutuwa,tana kaiwa har safiya yanayi,Allah ya bamu albarkacin qur'ani mai girma,alfarmar shugaba S A W👏🏽👏🏽).


    

      Saman kansu ya sanya wayar,ya raba a hankali zuwa bayanta ya kwantar da jikinsa,idanunta ta lumshe gaba daya zuciyarta ta soma gudu yadda ta saba a duk sanda ya rabota....lokacin data jishi cikin bargon da take,hannunsa saman ruwan cikinta,muryarsa can qasa kamar meyin rada yana cewa


"You are safe..... good night" cikin son yin aiki da maganarsa ta rufe idonta a hankali tana sauke numfashi,dumin kowanne na ratsa dan uwansa yana haifar masa da wani yanayi na daban.........


_to sai ince asuba ta gari kalsam_

Post a Comment

0 Comments