TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 26-27

 hutun weekend naje dakuma mura dake damuna🤦🤦🙏🙏[4/6, 9:36 PM] Zafafa: *_MQ 26_*




Zaune suke a Palo itada anty zarah anty zarah na Mata fira Dan sakata nishadi ganin duk tazama so serious Wanda Sam kowa yasan ba halinta bane tafi sabawa da hayaniya shiyasa duk inda take to hayaniya na gurin.,


Ana bude qofar palon atare dukkaninsu suka kalla qofar shigowar kowacce fuskarta daukeda murmushin yiwa Dr khalil din maraba Musamman Amatun da murmushinta na yau ya banbanta Dana kullum sbd yau sauran zuciyar Khalil takeson qarasa sacewa sbd ta zamo Tata ita kadai shiyasa yau komai nasa na musamman ne agareta saidai sabanin ganin fuskar Dr khalil zabeera a cikin idanuwan MAHMOUD ZABEERA idanuwanta suka sauka murmushinta me sanyi da tsada akan fuskarsa yafara sauka gabanta yayi mummunan faduwa ta hadiye sauran murmushinta fuskarta na sauya cikeda mamaki da fargaba da sanyin jiki..


Tsayawa yayi kallonsu fuskar na bayyanarda mamakinsa daba'a cika ganewaba ganin yanda dukkansu suka waiwayo suka zuba Masa Ido kowacce fuskarta daukeda murmushin daya mugun daukar hankalinsa da sakashi wasi wasin mamakinsu musamman Amatu datafi bayyanarda murmushinta da dukkanin farin cikinta dabai taba ganiba,

Ganin Ahankali Amatu ta dauke idanuwanta dake cikin nasa tana kallon bayansa murmushinta da farin cikinta fiyeda na farko Yana dawowa yasashi dawowa MD dinsa ya sauke boyayyan numfashinda Babu Wanda yaji ya Fara takowa ahankali idanuwansa na sauyawa cikin wani boyayyan yanayin dayake ciki sbd sai alokacin ya fahimci Khalil ne keda wannan murmushi da farin cikin,


Zama yayi Kan couch din dakinsa Yana rintse idanuwansa tareda yamutsa kansa yanajin wani irin zafi na ratsa dukkanin jikinsa 

Take kuwa zufa ya kakkaryo Masa Tako ina bayan ga kukan AC Nan yanaji yasan a kunne yake....


Zarah ya tuno da itama taketa washe baki tana murmushi to idan ita waccar tayi Dan Yana sunan mijinta to itafa???


Jin kansa ya dauki zafi Yana neman saukewa zarah laifin sai kawai ya miqe ya fada toilet yayo wanka yayi clearing mind dinsa ya shirya cikin kayan bacci ya dauki laptop yafara wani aiki Yana basar da tunanin komai da kowama.




Dr khalil kuwa duk yanda yake tunanin Amatu takai cikin ransa sai yanzu yake gane ta wuce Nan sbd wannan murmushin datake jifarsa dashi yagama hargitsa Masa Kai da tunani.,


Zama yayi bayan sungama gaisawa da zarah ta wuce tabasu guri ya juyo suna fuskantar juna Yana kallonta cikin kulawa yace"


Hw are you AMATULLAH???


Zuba Masa idanuwanta tayi har lokacin murmushinta bai daina fitaba tace"


Nayi fushi ka koma na barwa Nuratu.


Wani irin Dadi yaji ya kamasa me sanyi cikin nutsuwarsa yace"


Kishi kikeyi ita tafara tarbona???


Harara ta sakar Masa tana cewa''


Zanyi maka kuka idan kasakemin maganarta.


Kallonta yayi Yana cewa''


Ok tom yanzu duk wannan adon sbd zandawo akayisa?

To Meyesa baki shafamin Dan lipstick dinnan naku danaga ana sakawaba Nuratu tasaka ita......


Miqewa tayi a fusace tayi dakinta Yana kiranta ko waiwayosa batayiba tana shiga gaban mudubi ta wuce Kai tsaye

Ta dauki janbaki hot red tashafa a bakinta tana kallon madubin saikuma taga tayi kyau saita dauki turare taqara fesawa tadawo palon tana kallon yanayin dayake kallonta fuskarsa na bayyanarda farin ciki sosai sai taji farin ciki yakamata sbd ganin ta kyautata Masa shiyasama take nuna kishin Nuratu sbd ganin hakan na sanyasa farin ciki.


Cake din datayi da fruit drink dominsa taje ta dauko takawo Masa Nan suka Fara fira cikin nutsuwarsa yake cin cake din duk da a qoshe yake Amma sbd itace tayi da kanta yakeci cikin alfahari.


Sai guraren qarfe goma yabar part din ta rakosa har waje kafin tadawo ciki ta wuce dakinta tanajin farin ciki kamar bazata iya bacci ba yau din.



Washe gari ataredasu Dr khalil din yayi breakfast kafin suka fita tare harda Dr Salman daya Fara aiki asibitin Dr khalil kafin ya kammala shirye shiryen sa danshi ba anan qasar yakeson aikiba.


Gidansu kawu suka Fara zuwa tunda ta Isa gidan kowa ke Mata wani irin kallon burgewa suna tayata murna Wanda yasata sakin baki tana kallonsu cikin mamaki.


bakin dakin iyami tagan akwatina a jere tsaf su maman junior sai washe baki sukeyi suna budewa iyami ma yau bakin Nan har kunne sai annashuwarta takeyi tana sake bubbudewa su maman junior kayan suna gani suna shewa.


tsayawa tayi tana kallonsu cikeda mamaki kafin ta juyo ta kalli su Dr khalil dasuka tsaya qofar shigowa suna Magana da kawu Wanda shima yau harda saka babbar rigar farar shadda wadda itama Dr khalil ne ya dinko mishi su kusan kala bakwai.


Sake juyowa tayi gurinsu iyami da suke Mata barka da zuwa Maman junior kuwa rawa tahau Yi tana janyota tana waqarsu ta yarbawa tana cewa''


Amatunmu tasamu mijinda zai Bata farin ciki da suna me girma na mutunci.


Kallon rashin fahimta tayi Mata gabanta na mummunan faduwa ta qwace da sauri zatayi Magana iyami datasan Abinda zata iya fada tayi saurin cewa''


Kayan Dr khalil ne jiya da daddare aka kawo.


Kallon iyamin tayi da sauri tareda juyawa ta kalli inda suke Magana da kawu Yana Dan sato kallon inda suke Dan yaga reaction dinta..

Wani irin farin ciki Mara misaltuwa ya shigeta da sauri ta rungume maman junior tana cewa''


Alhamdulillah ya Allah.


Dariyar farin ciki iyami ta sake tana sake sakawa Khalil din albarka sbd duk iya bincike kawu yayi akansa Kuma sun Dade da yaba nutsuwarsa da halayensa sbd a wannan zamanin basu taba haduwa da yaro me nutsuwa ba kamar Khalil din,

Shiyasa Babu wani dogon janye janye na al'adu kawu yabasa auren Amatun kawai waliyan Khalil din yake jira idan sun daidaice da khalil din sbd Khalil ya sanar dashi akwai Yar hayaniya a zuriar tasu idan ta lafa zasu zo idan Kuma akasin hakan ne ya amince asamu waliyai a daura musu aure.


Zama tayi gefen iyami ta bude kayan tsaf taga abinta tana sake Jin inama gobene ranar auren ayi kowama ya huta.


Ciki su Dr khalil din suka qaraso suka gaida iyami tareda gaisawa da sauran mutanen gidan suka koma waje suna jiran Amatun tagama ganin kayan su fito.



Kusan awa biyu ta Bata kafin ta fito suka wuce asibiti inda ya ajiyeta a office dinsa suka Shiga meeting tayi zamanta tareda miqewa a kujerarsa tana game a wayarsa daya barmata wadda kyakkyawan hotonta yake shimfide lock screen dinsa na ummensa Kuma a main screen dinsa sai hakan yasaka jikinta yin sanyi sbd a rayuwar Khalil yanzu duk Wanda yasansa yasan itada ummensa sune sanyin zuciyarsa da idaniyarsa Amma Kuma gashi Sam ko inuwa daya basa zama a taqaicema ummen Babu Wanda ta tsana a rayuwa kamarta ita Kuma Babu wadda take ganin ta rainawa wayo kamarta 

sai kawai taji Bata girmama soyayyar Dr khalil dinba.


Sai qarfe uku suka baro asibiti sai kawai suka wuce gurin cin abinci a 5star daganan ma gurin shopping suka wuce sai gab da magrib suka shigo zabeera 

Kai tsaye sashen ummensa ya nufa tana ganin sunyi parking bakin flat din tayi saurin kallonsa shima ita ya kalla Yana cewa''


Inason ganin Mata biyu masu mahimmanci gareni sun zama daya wannan shine babban fatana,

Amatu please kiyi hkr da duk Abinda umme ke Miki ki Bata dama kigani tanada zuciya me kyau,

Abinda nasani shine duk Abinda nakeso ummina na sonshi bare ke datasan Ina Miki tsaftatacciyar so Wanda bazan iya dainawaba

Dan haka nasan zata soki wata Rana ko Ina Raye ko bana Raye nasan wata Rana saita soki kamar yanda takesona,so please AMATULLAH ki qaunaceta ki kulamin da ita I promise you wata Rana zata daina tsangwamanki zata qaunaceki kamar yanda take qaunata.


Wani irin sanyi jikinta yayi sosai saitaji kunyarsa ta kamata ta dago a sanyaye ta kallesa ya da yayi saitaji kamar Bata girmama soyayyarsa ba tunda takasa girmama mahaifiyarsa.,

Ajiyar zuciya ta sauke ahankali cikin sanyi tace"


Inshallah Zan kiyaye zancenka daga yanxu zanyi iya qoqarina gurin kyautata Mata.


Numfashi ya sauke ahankali yace"

Thank you AMATULLAH.


Fitowa sukayi suka nufi ciki Yana gaba tana gefensa jiki a sanyaye take tafiyar sbd yanayinsa duk ya Gama sanyayata ga wani irin damuwa daya shigeta ga faduwar gaban yanda zasuyi da ummen Amma koma menene tayi alqawarin jurewa sbd shi.


A palon farko dasuka shigo take qoqarin zama ya tsaya tareda juyowa ya kalleta yana girgiza Mata Kai tareda cewa''


Follow me.


Falonta na qurya suka nufa Wanda dagashi sai bedroom dinta Yana gaba tana bayansa.


Zaune take tana kallon wani Shirin girke girken larabawa da akeyi a mazzika taji shigowarsa tareda sallamarsa ta juyo fuskarta daukeda murmushin dake bayyanarda girman son datakewa Dan nata sai idanuwanta suka sauka akan wadda ke bayansa ta hadiye sauran murmushinta fuskarta na sauyawa zuwa bacin Rai da fushin ganinta ta tsuke fuska sosai tana dauke Kai daga bakin qofar.


Tsayawa Amatu tayi daga Inda take tana sauke Kai ganin irin kallon qyama da tsanar da ummen ke Yi Mata,


Qarasowa yayi gefen ummen ya zauna Yana kallon fuskarta data canza yaji ransa yaqara jagulewa ya sauke wani irin numfashi Mara Dadi Yana dafa hannun ummen cikin kulawa da sanyin jiki tareda sautin daya sakasu kallonsa duk su duka biyun yace"


Umme Meyesa Zaki dauki halayyar daba naki ba¿

Shin Amatu tanada wani banbanci ne da sauran mutane da Kika zabi qyamarta ita kadai?

Umme Amatu matar dazan aurace sbd Ina sonta da dukkanin zuciyata

Shin umme kodan son datakewa dan naki bazaki qaunacetaba kodan hakan?


Girgiza Kai tayi tana danne 6acin ranta ta kallesa tace"


Khalil kadaina cewa tana sonka wannan bayan kudi duk duniya Babu yaren datake ganewa,

Wannan Babu wani buri a rayuwarsu Bayan samun kudi ta ko wane halin Yaya,

Kudine kawai agabanta ta yanda zata iya yin komai akan kudi ciki ina fada maka harda mutuncinta zata iya siyarwa akan kudi,

Wlh khalil kaima sbd kudinka take sonka da bakada kudi bazata taba sonkaba

Irin wannan matar kakeson nabari ka aura Khalil???


Dagowa yayi ya kalli Inda Amatun ke tsaye cikin wani irin yanayi na damuwa ya sauke ajiyar zuciya tareda cewa''


Zo AMATULLAH,

Zo Nan kusada umme.


Kallon ummen tayi taga ko kallon inda take Bata qaunar Yi sbd qiyayya ta tako ahankali tazo gefensa ta zauna ahankali Kan carpet din dake gurin tana sauke kai maganganun ummen na sake jujjuyawa cikin kanta.


Numfashi ya Kuma saukewa cikin wani irin yanayi na damuwarsa dake bayyane wadda tasa dukansu su biyun kallonsa yasake riqo hannun ummen cikin sanyin murya yace"


Ummen banfara son AMATULLAH ba Sai danasan asalin wacece ita,

Nafara sonta ne bayan nasan batada kowa aduniya,

Banfara sonta ba saidanasan a bola ta tashi acan tayi wayo ta koyi gwagwarmayar rayuwa,

Banfara tsananin sonta ba saidanasan irin wahalalliyar rayuwar datayi amatsayin almajiri Mara yanci Wanda ta rayu cikinsu amatsayin namiji bayan tana matsayin mace,

Amatu bakowa mace face yarinyarda wasu bayin Allah suka taimaka suka daukesu Bayan sungama wahalalliyar rayuwa acikin bola da mataccin gidaje da shagunan daba'a gamaba,

Babu Wanda yataba kallonsu da idon Rahama,

Babu Wanda yataba duba yanayin shekaru da jinsinta amatsayin mace ya taimakesu,

Sun kwana da yunwa suntashi da ita,

Sunyi sata dan suci suyi rayuwa,

Maza da yawa sunyi yunqurin lalata rayuwarsu da sunan taimakawa shin umme Wanda yake ciki irin wannan qaddarar Dan yayi sata dan yaci ya Hana kansa Zina illa ne dahar za'a gujesa??????


Umme wallahi tallahi ina tsananin son AMATULLAH da dukkanin zuciyata bansan ta Yaya zanyi Miki bayani ki qaunaci Amatu ba,

Na shirya auren AMATULLAH na zamo gatanta itada zuriarta Wanda Babu wani Abu dazai sauya niyata akan hakan,


Shin umme kintaba zaunawa kinyi tunanin irin tarin Lada da farin cikin dazaki samu aduk lokacinda Kika kawo murmushi da farin ciki a rayuwar marayu?

Umme tarin ladace me yawa wadda zata iya gyara Miki ko wanke kurakurenki Kuma yabaki nutsuwar zuciya da ruhi....


Zuwa lokacin Amatu kuka takeyi sosai sbd Bata taba sanin khalil yasan asalinta ba daduk halinda suka Shiga arayuwa Kuma ahakan yake sonta tabbas yagama bawa rayuwarta girgizar data sauya zuciyarta akansa gabaki daya.


Umme ma hawaye takeyi sosai tsananin so da qaunar danta na ratsata...


Ahankali ya zamo qasa ya durqusa gabanta tareda riqo hannuwanta idanuwansa dasukai laushi na kallonta a karye yace"


Umme ayau gani na durqusa a gabanki Ina roqonki daki ajiye dukkanin wani burin rayuwa ko komawa Allah kodan samun nustuwar zuciya,

Umme Ina roqonki da ki qaunaci Amatu ki da zuciya daya sbd bazan iya ganinku acikin halinda kuke cikiba,

Umme......


Bata Bari ya qarasa ba tayi saurin dagosa tana rungumesa hawayenta na qara tsiyayowa tace"


Nayi maka alqawari Khalil wlh Babu wani al'amarin duniya dazan sake Bari na 6ata akansa,

Idan dai Amatu ce Kuma wlh na amince maka bazan qara qintaba idan har na tabbatarda har zuciyarta itama take sonka....


Rungumeta yayi da sauri Yana cewa''


Thank you ya umme.


Share Mata hawayenta yafarayi tareda juyowa ya kalli Amatu dake kuka sosai ahankali tanajin Sam Bata cancanci soyayyar khalil ba,

Zuciyarta batayi Mata adalci ba son wani 'da namiji a zuciyarta Wanda ba khalil ba...


Ahankali yakamo hannunta ya dawo da ita gefen umme dake kallonta cikin wani irin sabon yanayi ya zaunar da ita ahankali yace"


Amatu ga amanar ummi na ki kular min da ita amatsayinki na matar 'danta.


Dago jajayen idanuwanta tayi ta kallesa kafin ta kalli ummen ta daga Kai ahankali takasa cewa komai sai binsa takeyi da Ido zuciyarta na karban zazzafan baqon yanayi akansa Wanda ta tabbatarda sone me zafi.


Murmushi umme tasaki ahankali tareda kallon Amatun tana nuna Mata gefenta tace"


Kimin alqawarin zaki so shi fiyeda yanda yake sonki??


Murmushinsa me nutsuwa ya saki Yana kawar da zancen da cewa"


Umme wannan son Kaine zakice ta Soni fiyeda yanda nake sonta sbd bazata iya Sona yanda nake sontaba nawa me girma ne.


Murmushi sukayi Banda Amatu dake Jin wani babban al'amari me girma atareda ita hakanan taji gabaki daya nutsuwarta na barinta.



Haj maryam da Nuratu dasuka jima Bakin qofar palon suna jin dukkanin Abinda yafaru baqin ciki me girma yarufe zukatansu da idanuwansu musamman nuratu data gama zaucewa a fusace ta juya tana qoqarin sakin ihun baqin ciki da zuciyarta dake neman tarwatsewa da gudu Haj maryam tabi bayanta tana cewa''


Yau tunda Kika juyamin baya Aisha akan danki kowa ya shirya tashin hankalin dazai biyo daren Nan Dan wlh yau sai takardun asalin Amatu sun kwana a hannun Modibbo da Andi.

##mamuh#

[4/7, 2:51 PM] Zafafa: *_MQ 27_*





Ko gabanta Bata gani ta qarasa sashensu tana qoqarin dafe qirjinta dake mugun zafi da radadi kamar zai tarwatse 

Tana shiga palonsu ta zube qasa Kan gwiwowinta tareda fashewa da wani irin kuka me tsanani da zafin Rai,


Da sauri momynta ta qaraso ciki tana rikota tana Kiran sunanta cikin nata ciwon ran me tsanani da tausayin 'yarta tana sake kamota tace"


Nuratu please kada kiyi irin wannan kukan wlh karyamin zuciya zakiyi bazan iya ganinki cikin irin wannan halin ba Dan Allah kidaina kuka zamu samu mafita,

Bazan taba Bari Khalil ya auri wadda bake ba musamman wannan barauniyar karuwar yarinyar Dana Gama alwashin bazata taba aurensaba kodan yanda ya fifita sonta akanki.


Tsananta kukanta yayi tana girgiza Kai tana cewa''


Momy wlh inoson Khalil fiyeda yanda 'dan Adam zai iya lissafawa,

Zuciyata zafi takeyi sosai bazan iya kallonsa ya auri wata ba,

Gwara na mutu danaga wannan ranar.....


Da sauri momyn ta rufe Mata baki tana girgiza Mata Kai cikin tashin hankali tace"


Dan Allah Nuratu kidawo hayyacinki ki daina wainnan maganganun

Zan zamo Mana mafitarda zamu Kori Amatun daga rayuwarmu gaba daya da duk ahalin zabeera ma bama Khalil kadai ba.....


Dagowa nuratu tayi da idanuwanta dasukai jajir suna tsiyayo hawaye tana qoqarin fahimtar zancen momyn ta zabura da sauri tana tunowa da takardun data karbo hannun manager na kaf asalin Amatun harma da qarin rayuwar karuwanci datasa aka qara Mata akai,


Dakinta ta nufa kamar mahaukaciya ta nufi inda handbags dinta suke tahau wargazasu tana neman jakar da tasaka envelope cikin hauka,

Ganin yanda take wargaza Kaya yasa momyn saurin qarasowa tana sake riqota saigashi ta zaqulo jakar 

Jikinta har rawa yakeyi ta bude ta dauko envelope din gaba cewa''


Momy yau Babu Abinda zai Hanani wulaqanta wulaqantacciyar rayuwarta,

Saina sakata kuka ninkin Wanda ta sakani tun zuwanta zabeera,

Ayau zata San asalin irin girman soyayyar Dana kewa Khalil.


Juyawa tayi ta fice tana share hawayenta dasuke sake bulbulowa cikin tsananin zafi da baqin cikin da zuciyarta ke ciki


Da gudu momy tabi bayanta tana Kiran sunanta sbd ayanda take yanzu ba acikin hayyacintaba komai lalacewa zaiyi Bata haka zasu tona asirin Amatun ba so takeyi harda umme ta fito cikin zancen....


A firgice ta biyo bayan Nuratun tana Kiran sunanta Amma tuni nuratun ta hada da gudu gudu tana sake sakin sabon kuka ta nufi sashen Andi inda tasan Modibbo nacan taredashi a daidai lokacin.


Ganin takasa cimma Nuratun data nufi hanyar sashen Andi yasa hankalinta mummunan tashi tuni ta firgice sbd wlh tasan Kwana zasuyi aciki Suma sbd zancen ba qaramin tashin hankali da masifu zai janyo ba,,,

Salman dake qoqarin parking yaga wucewar Nuratu da gudu gudu kamar tana kuka Yana qoqarin kashe motar ya fito saiga momynsu cikin sauri itama tanabin bayan Nuratun hankalinta amatuqar tashe daga ganinsu yasan ba lafiya ba bare ganin sunkama hanyar sashen Andi koma meyene to ya girmama dan duk Abinda yasa aka wuce Modibbo aka nufi Andi to da matsala babba.


Kashe motar yayi da sauri ya fito yana qoqarin bin bayansu saiga Dr khalil ya fito daga sashen ummen tareda Amatu da ummen zasu mayarda Amatu

Da sauri Khalil ya taresa ganin Yana Shirin gudu yace"


Lafiya likitan qashi???


Kallon hanyar Sashen Andin yayi cikin sauri sauri yace"


Inaga akwai matsala ne Naga Nuratu da momy sun nufi sashen Andi kowannensu Babu nutsuwa atare dashi Nuratu ma kamar kuka takeyi...


Juyowa yayi ya kalli khalil din cikin fargaba yace"


Ina Jin tsoron Abinda zaisa suje gurin anty musamman Nuratu nasan halinta da tsananin fushi da rashin tunani Wanda kowa yasan yawancin fushinta akan Abinda ya shafeka ne 

Akwai Abinda yafaru yanzu a tsakaninku ne????



Dukkaninsu su ukun da sauri suka kallesa cikin wasi wasi da shakku 


Da sauri umme ta kalli me aikinta dake fitowa dan kawo Mata wayarta dake ringin cikin sauri tace"


Shafa'atu Maryam da Nuratu sun shigo sashena bayan shigowar su Khalil????


Da sauri cikin tashin hankali duk suka zubawa shafar Ido jiran amsarta 

Tace"

Eh da Kuna ciki sun shigo Amma.......


Bata qarasaba Salman ya juya da mugun gudu Yana cewa'"


Innalillahi-wainna ilaihirrajiun.....


Da sauri Dr khalil ya juyo ya kalli umme da zufa ya katse Mata ya kalli Amatu da tuni qafafunta suka Fara daukar rawar tashin hankali ya riqo hannuwansu duka su biyun cikin qoqarin bawa kansa nutsuwa Dan kwantar musu da hankali yace"


Umme duk tsanani karku Fadi asalin abinda yafaru na gskiar Abinda yafaru tsakaninku Kika kawo Amatu zabeera,

Amatu komai zai faru karki bude baki kiyi magana nine zanyi Magana ok???


Kallonsa umme tayi da sauri tana cewa''


Ta yaya Zan tsaya Ina kallonka ka dauki hukuncin Abinda bakaine kayiba...


Umme please kuyi kawai Abinda nace ku koma ciki Bari nabi bayansu tun kafin su Isa.


Da sauri yabi bayan su Yana share zufan goshinsa akaro na farko dayaji yanawa wani fatar faduwa ya Suma sbd Jin yake inama Nuratu kafin takai tafadi ta suma a hanya..


Kasa hakuri ummi tayi takasa komawa ciki ta tsaya gurin tana zarya cikin tsoro da fargabar Abinda zai biyo baya....



Bakin qofar shiga momy tayi nasarar damqe Nuratu da sauri tana sauke numfashin wahala da tashin hankali tace"


Nuratu kidawo hayyacinki kada kiyi Abinda masifarsa zata qare kanmu sbd wannan alamarin ba Abune me sauqi ba dazamu Bari Modibbo yaji daga garemu ba bare Andi

Maza kawo takardun Nan mukoma muyi Magana a nitse......


Qwacewa tayi tareda tura qofar palon zata shiga har lokacin kuka takeyi sosai tace"


Momy yau idan ban tona asirintaba duniya tasan ko ita wacece ba hankalina bazai taba kwanciyaba 

So nake ta dandani 'dacin rabuwa da Abinda kakeso....


Fixgota Salman yayi da qarfi Yana qoqarin kwace envelope din ta fizge da qarfi tana cewa'' 


Kaima bayanta zakabi aci gaba da barin karuwa tana rayuwa acikin zabeera?

Me take Baku da duk mazan zabeera kuka haukace akanta??

Abinda take bawa sauran mazan waje........


Wani wawan Mari salman ya sauke Mata Wanda yasata haukacewa cikin tsananin firgici da masifa tace"


Wlh ka sake dasamin tsanarta me tsanani Koda Zan rasa Raina saina tabbatarda Andi da Modibbo sunsan karuwace ita,

Barauniya ce,

Yar bola ce,

Me aikin karuwanci a gidan abinci.......


Ba zata Marin dayafi na farko zafi da qara ya sauka akan inda Salman ya mareta 

Wannan karon radadin yayi tsananin data kasa riqewa saidata zube a qasa ta dago ta kallesa idanuwanta na qarasa rinewa hawaye masu tsananin zafi da baqin ciki suna gangaro Mata murya na rawa tace"


Khalil duk akan wannan karuwar ce??


Cikin tsananin bacin Ran dabasu taba ganinsa aciki ba ya bude baki zaiyi Magana akai gyaran murya daga bakin qofar Shiga palon kusan duk atare suka juya cikin firgici da tashin hankali sukaga Andi ne da kansa a tsaye Modibbo na gefensa kowannensu kallo daya zakayi Masa kasan dukkanin fushi da bacin ransu a bayyane yake 

Cikin nutsuwa Modibbo ya qaraso gaban Nuratu da itama tashiga firgici ya sanya hannu ya zari envelope din hannunta batareda yace qala ba ya juya yadawo gefen Andi Yana bude envelope din Wanda yasa tuni kowannensu ya shiga rawar jiki musamman momyn tuni ta durqushe qasa tan neman sakin kuka 

Andi yayi wa gefenta kallo daya take ta hadiye kukan batareda yafitoba yakoma tana rawar jiki.




Duk inda tashin hankali da sanyin jiki yake Yana tareda Amatu da umme sbd kowannensu yakasa samun nutsuwa ta ja qafafunta dasukai nauyi ta nufi hanyar sashensu idanuwanta na sake kadawa bayan kumburin dasukayi na kukan data gama sha,


Tana shiga palon da anty zarah dake zaune tana qoqarin kiranta tayi saurin miqewa ta qaraso gabanta cikin tashin hankali da tsoro take Kiran sunanta tana tambayarta lafiya.


Kasa motsi tayi bare Magana sai kawai ta fashe da sabon kuka me shiga Rai tana zubewa qasa...


Innalillahi-wainna ilaihirrajiun" anty zarah ke maimaitawa tana zubewa qasan itama cikin tashin hankalin ganin irin kukan da Amatun keyi cikin rudu muryarta na rawa tace"


Amatu meya sameki kifadamin tun kafin kisa zuciyata fashewa itama Dan Allah,

Kukanki na bani tsoro tareda sani cikin tsananin firgici Dan Allah kiyimin mgn.....


Dagowa tayi ta kalli anty zarah din jajayen idanuwanta na tsiyayo da hawaye masu zafi tanajin tausayin kanta Dana zarah din sbd tasan lokacin rabuwarsu ne yazo,

Abinda Bata saniba shine zarah din zata tsaneta idan taji Abindake faruwa?

Koda zata tafi zatayiwa anty zarah adalcin fada Mata gskia da bakinta ko Dan zallar qaunarta gareta.


Wasu hawayen ne suka Kuma tsayayo Mata ta rintse ido zuciyarta na radadin Abinda zata fada ahankali tace"


Anty zarah ki gafarceni na zamo babbar butulu me mayarda alkhairi da cin Amana,

Na cutatar dake ta hanyar wahala akan Abinda Kika saka Rai da burika akansa,

Na hanaki bacci da sukuni gurin dawainiya Dani akan qarya yaudara...

Anty zarah banida ciki ajikina,

Bantaba daukar cikiba,

Bantaba sanin namijiba bare nayi Abinda zaisa nasamu ciki,

Dr khalil ba Mijina bane.........



Sakinta anty zarah din tayi cikin tsananin firgici da mamaki tayi baya tana zaman 'yan bori idanuwanta na silalo hawayen tsoro da karyewar zuciya ta Fara girgiza Kai tana son yin Magana takasa sai hawaye....


Anty zarah bantaba sanin a duniya akwai masu irin tsarkakakkiyar zuciya irin tasu kawu ba sai Dana hadu da Dr khalil dake da salman kuka kawo wani irin farin ciki da sanin mutuncin Kai arayuwata Amma Babu Abinda nakawo Muku sai yaudara da damuwa.....


Cikin rawar murya anty zarah dake rawar jiki gaba daya cikin firgici tace"


Idan duk Abinda Kika fada hakan ne to meya kawoki cikin rayuwarmu????


KUDI"""""tafada Kai tsaye tana sauke Kai hawayenta na qaruwa..


Son kudi da burin samunsu kota halin Yaya yasani shigowa rayuwarku

Saidai bayan haduwata daku na fahimci samun mutanen dake sonka da son farin cikinka tareda zama acikinsu shine asalin farin ciki da walwala Wanda kudi baya siya maka suba,

Anty zarah girmanki da qaunarki alqawarine da bazai taba gogewa azuciya da rayuwataba,

Anty zarah idan lokaci yayi Zan fada Miki gaskiyar duka Amma ayanzu iya Abinda Zan fada Miki kenan.



Miqewa tayi da sauri ganin irin hawayenda anty zarah din keyi tana bin cikinta da kallo burirrikanta akan cikin suna tarwatsewa daya Bayan daya,

Cikinda akai alqawarin Bata Abinda za'a Haifa Wanda tuni tafara kallon kanta amatsayin uwa Nanda lokacin qanqani.


Buga kofar da akayi da qarfine yasasu kallon kofar tun kafin su motsa aka sanarda saqone Andi nayiwa Amatu Kiran gaggawa.


Rintse idanuwanta tayi hawayen ciki suka gangaro ta juya ta nufi qofa.





A tsaitsaye suke Babu Wanda yasamu damar motsawa daga Inda yake sbd tashin hankali kusan mintuna suka share ahakan sbd shock dinda su Andi suka Shiga Bayan Gama sanin wacece Amatu dakuma irin qazamtacciyar rayuwar karuwancin datayi qarshe ta qare acikin zuria mafi tsafta da mutunci,


Umme da sauran manyan yaran Andi da Modibbo da tuni aka kirasu suka qaraso Babu wanda ya zauna duk tsaye suke cikin tashin hankali da jimanin abinda zai biyo Andi kawai ake jira yayi Magana.



Dagowa yayi cikin wani irin yanayi na tsanani yayiwa Khalil kallon dayasa kowa sake Shiga firgici cikin amo me firgitarwa yace"


Kowace tambay amsa daya nakeso,

Ka auri wannan yarinyar??


Aa,


Acikin takardan Nan anrubuta cewa

Ita din Mara asali ce,

Yar bola ce,

Karuwa ce,

Barauniya ce,

Gidajen abinci,hotels da gidan rawa take aiki,

Babu police station dinda batayi zamaba har gidan yari

Gaskia ne ko qaryane???????


Cikin tsananin firgici da tashin hankali muryarsa na rawa yace"


Gskia ne Amma Banda.......


Hannu Andi din ya daga Masa fuskarsa na nuna dukkanin fushinsa da bacin ransa.


Take yace kowa ya watse ya sallamesu ya juya yayi ciki 'yayansa na binsa abaya.


Kasa motsi kowa yayi sbd sanin abin bazaiyi kyauba.


Daga ciki kuwa kallon alhaji qarami yayi Kai tsaye yace"


Yarinyar da mariqanta a daukesu a rufe a central station dinda Khalil zaifi shekaru goma Yana nemansu baigansu ba a sanarda commissioner laifin datayi ta yanda zasusan girman laifin Bata sunan zabeera.

##Mamuh#

Post a Comment

0 Comments