TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

SAKAYYAH page 71

 Tana wani sassayan tari, wanda take ta son danneshi, cikin sauri suka ƙara sa cikin ɗakin da sauri Dr Jameel yace.

“Ha'a ya dai?”.

Momy ce ta ɗago kanta tare da cewa.

“Kamar ƙwaruwa tayi”.

Cikin tsoro gami da damuwa Moddibo ya kalli Dr Jameel kana yace.

“Jifa tari take ba matsala ko?”.

Kai Dr Jameel ya girgiza tare da faɗin.

“A'a ba matsala bari nasa akawo mata wani magani tasha tarin zai bari”.

Ya ƙare maganar tare da kiran Line-line dake cikin wayar ya kira Pharmacy ya faɗa musu su kawo maganin jim kaɗan Norse ta kawo maganin karɓa yayi ya bata tasha cikin ikon Allah atake tarin ya bari.

Sai alokacin ta samu nutsuwa numfashi ta fesar kana ta maida kallonta kan Abualeey tare da cewa.

“Abu ina yini”.

Cike da kulawa yace.

“Lafiya lau ya jiki?”.

Ahankali tace.

“Da sauƙi ”.

Kai ya gyaɗa tare da faɗin.

“Masha Allah Allah ya raya abinda aka samu”.

Karɓan Jaririn yayi tare dasa mishi albarka kana ya miƙawa Waziri da Galadima dai-dai lokacin kuma kira ya shigo wayar Khausar Momy anutse ta duba ganin sunan Hajja Nana yasa ta ɗauka muryanta cike da farin ciki tace.

“Hajja Nana Alhamdulillah anyi Theater ancire ɗa namiji”.

Cikin jin daɗi da sauke ajiyar zuciya Hajja Nana tace.

“Alhamdulillah amma tana lafiya ko?”.

”Eh lafiya lau gata nan ma”.

Cewar Momy na miƙa wa Khausar wayar karɓa Khausar tayi suka gaisa cike da farin ciki Hajja Nana tace.

“Ƴar tsele da zaki kasheni azaune”.

Murmushi Khausar tayi cikin rashin jin karfin jikinta tace.

“Yaushe zaki zo?”.

Fuska ɗauke da farin ciki Hajja Nana tace.

“Kwanan nan in sha Allah kafin ayi suna”.

Murmushi Khausar tayi tare da maida kallonta kan Moddibo da idanunsa ke kan Jaririn tace.

“Ayiwa Hajja Nana shiri in Sha Allahu tana kan hanya zata zo”.

Kai ya gyaɗa mata tare da cewa.

“In sha Allahu”.

Akuma dai-dai lokacin Dija da Yah Aliyu suka shigo Murmushi Khausar tayi tare da cewa.

“Dija”.

Cike da farin ciki Dija tace.

“Na'am Khausar ai mu bamu sani ba Khausar baku faɗa mana ba”.

Still da Murmushi afuskarta tace.

“Kiyi haƙuri Dija gaba ɗaya abin ne yazo min atsorace”.

Dariya Yah Ali yayi tare da faɗin.

“Raguwa gaba ɗaya kin gigice kin gigita bayin Allah”.

Langwaɓar da kai tayi kana tace.

“Hmmm ba dole inji tsoro ba Yah Ali abinda ance wasu da yawa idan an musu kafin afito dasu ta can suke wucewa”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“A'a ke kam in Sha Allahu kina nan sai kin kawo wasu ƙannensa goma sha ɗaya sun zama Dozen”.

Idanunta ta zaro tare da faɗin.

“Goma sha ɗaya”.

Baki ɗaya ɗakin suka sanya dariya.

Raudat dake zaune gefen Asma'u ta ƙyalkyale da dariya kana tace.

“Addah khausy idan kika haifi Dozen sai ki bani biyun saman na riƙa kulawa dasu kar suyi Miki yawa ai Yah Moddibo zaku bani ko?”.

Ta ƙare maganar tana kallon Moddibo kai Moddibo ya gyaɗa yana Murmushi.

A ranan haka suka yini suna kula da ita.


Bayan sunyi kwana uku aka sallame ta suka koma gida.

 Haka Didi da Momy  suka cigaba da kula da ita suna bata kulawa na musamman...

Washe gari da safe Misalin ƙarfe 7:30 Asma'u ta zo zaune ta samu Lalla Khadijah, Rahama, na zaune kan lallausan Darduma Yayin da Didi,Momy,Innayi ke zaune gefe ɗaya Hajja Nana kuwa na gefen Khausar da Moddibo dake riƙe da Jaririn yana masa addu'a kana su kuma suna hira.

Ahankali Asma'u ta ɗago fuskarta ɗauke da Murmushi ta miƙa wa Khausar wayarta tare da cewa.

“Kalli wani special abu dana ajiye Miki wanda nake da yaƙinin sai kinyi min kyauta na musamman”.

Ɗan ware idanu Khausar tayi tana kallon Rahama dake cewa.

“Aikuwa dai Addah Asmeey muma dake gefe muna sa ran samun khauta”.

Dariya Khausar ta sanya kana tace.

“Aikam dai zanso gani”.

Ta ƙare maganar tana playing video

Da sauri ta zaro Idanunta waje ganinta kwance kan gado tana surutai.

Moddibo kuwa wani Amintaccen Murmushi ya saki ganin yanda ta zaro Idanunta waje sai kuma tayi saurin ɗaga kanta cike da kunya jin yanda suka ƙyalƙyale da dariya cikin tura baki ta kalli Asma'u tare da cewa.

“Asma'u Ni ko?,Aikuwa kin ci bashi sai na rama”.

Ta ƙare maganar cike da kunya ganin yanda suke maimaita maganar.

Asma'u kuwa Gwalo Asma'u tayi mata tare da cewa.

“Aikuwa sai dai ki rame yarinya dama can abinda ke Ranki kika faɗa”.

Khausar kuwa juyawa tayi jin Hajja Nana na cewa.

“Yoh ai gaskiya Asma'u ta faɗa ke da wannan mijin naki duk ba kunya ne daku idan ke baki cikin hayyacin ki kika faɗa ai shi yana sane bare keɗin ma kina sane”.

Rau-rau da idanu Khausar tayi ta shiga bubbuga ƙafa daga zaune tace.

“Didi kiji fa abinda Hajja Nana ke faɗa wai bani da kunya”.

Murmushi Didi tayi tare da faɗin.

“Rabu da Hajja Nana am Khausar ɗina kina da kunya sosai ai bada sanin ki kikayi ba”.

Momy kam Murmushi kawai takeyi.

Daidai lokacin Jakadiya ta shigo tare da sanarwa Didi tayi baƙi ƴan Barka.

Miƙewa Didi tayi kana tace.

“Toh ganan zuwa”.

Sai kuma ta kalli Momy dake cewa.

“Mu tafi”.

Atare Didi Momy Innayi,Niyna suka fice.

Kallon Rahamah kalla Khadijah tayi kana tace.

“Rahama muje ki tayani haɗa Alawar Madara da gullisuwa tun jiya naso yi kuma ina zirga-zirga”.

Murmushi Rahama tayi tare da miƙewa Lalla Khadijah kuwa har taje ƙofa ta juya ta kalli kana tace.

“Ƙanwata kema zo muje”.

Kai Asma'u ta gyaɗa tare da miƙewa suka fita.

Falon ya rage daga Khausar, Moddibo sai Hajja Nana da itama ta miƙe ta fita falon.

Cikin shagwaɓa Khausar ta kalli Moddibo tare da narke fuska kana ta tura baki tace.

“Yah Mu'allim”.

Murmushi yayi kana ya kwantar da jaririn ya janyota jikinsa bakinsa ya kai saitin kunnenta yace 

“Na'am Minha Viddaaaa ya akayi?”.

Ya ƙarashe yana jan sunan.

Cike da shagwaɓa tace.

“Jifa yanda na saki baki naita faɗan magana gabansu Momy da Didi kuma baka hanani ba”.

Murmushi yayi yana shafa bayanta yace.

“Ya za'a yi in hanaki fallasa min sirrin dake Ranki?,Taya kike tunanin bakina zai iya dakatar da zinaren kalaman da suke fitowa daga bakinki suna ratsa kogon zuciyata?,Kin kuwa san farin ciki da shaukin dana kasance alokacin?”.

Ya fesar da sanyayyan numfashi mai cike da zallan so da shauƙi yace.

“A lokacin ji nake tamkar ina yawo a gajimare ji nake tamkar nafi Mazan duniya Sa'a da samun Nagartacciyan mace irin ki kin nuna min so tun baki san menene so ba shin mai zanyi in biyaki”.

Cikin wani irin yanayi na musamman tace.

“Ka ƙaunaceni ka kuma soni fiye da yanda nake son kaina kada ka haɗa ni da kowa atare da kai idan kayi min haka kaga yimin komai Yah Mu'allim”.

Ahankali ya ɗago kanta tare da ɗaura lips ɗin sa asaman nata yashiga kissing ɗin ta...


 Alhamdulillah zuwa yanzu jikinta yayi ƙwari bazama ace Thearter  aka mata ba kullum Asma'u da Dija anan suke yini ana I gobe suna Dr Zakariyya, Asiya Hajja Nana, Abban Jameel, Lalla Hafsat suka zo.


Hajja Nana da Innayi ce zaune da Khausar aɗaki yayin da Innayi ta zuba mata abinci ta bata taci Momy kuma na riƙe da jiriri tayi masa wankan Yamma ta saka shi cikin wasu fararen kayan sanyu masu masifar taushi pink and white collar.

Anutse Moddibo ya shigo ya same su Kai tsaye bakin gadon ya wuce gefenta ya zauna.

Kallonsa hajja Nana tayi tare da cewa.

“Wai kai kam baka jin kunya ne?”.

Juyawa yayi ya kalleta kana yace.

“Kin iso da sa ido ko? Idon ki be iya gani bakinki yayi shiru ko?”.

Hararansa tayi tare da faɗin.

“Ba dole ba idan bani nake taka maka birki ba babu mai taka maka birki”.

Kallonta yayi tare da cewa.

“Toh sai kiyi mugani in birkin zai taku”.

Anutse Khausar ta kallesa kana ta kalli Hajja Nana tace.

“Yah Mu'allim rabu da ita”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Aima na rabu da ita?”.

Khausar kuwa nutsuwarta ta tattara kana tace.

“Yah Mu'allim gashi har gobe suna in Allah ya kaimu”.

Kai ya gyaɗa kana yace.

“Eh”.

Ahankali ta langwaɓar da kai tare da cewa.

“Kuma banji ka faɗa min sunan yaron ba”.

Murmushi yayi kana yace.

“Kuma tun a asibiti kafin ayi mishi wanka na masa huɗu ba tun kafin ki farfaɗo”.

Murmushi tayi kana ahankali tace.

“Kuma Yah Mu'allim baka faɗa min ba".

Juyawa yayi ya kalli Asma'u kana ya kalli Asiya dake cewa.

“Ai dai kam bamu san sunan yaro ba gashi har gobe Suna”.

Didi kam ido ta zuba mishi tana kallonsa Momy kuwa sunkuyar da kanta ƙasa tayi tana sawa Jaririn safan hannu tace.

“Toh menene sunan”.

Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya motsa laɓɓansa tare da cewa.

“Sunan shi Jameel”.

Cikin tsananin jin daɗi Asma'u ta kallesa tare da cewa.

“Allah sarki Yah Moddibo Ubangiji Allah ya saka da Alkhairi Allah yabar zumunci ayyah Yah Jameel ɗina Allah ya raya shi Allah ya mishi Albarka”.

Murmushi yayi tare da cewa.

“Ameen ya Allah Asma'u, Allah yasa ya biyo halin takwaransa”.

Ya ƙare maganar yana Murmushi.

Innayi ce ta amshi zancen da cewa.

“Naji Ibraahim kuna na kiranshi da *Keyan*”.

Kai Modibbo ya jinjina tare da cewa.

“Eh laƙanin kenan. Amman asalin sunan Jameel, Allah ya raya mana shi yayi nagarta irin ta mai sunanshi”.

Cikin tsananin jin daɗi Asma'u tace.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.

Khausar na Murmushi tace.

“Ameen ya Allah yasa ya biyo halin takwaransa Allah yasa yayi Ilimin takwaransa”.

Cikin jin daɗi Didi tace.

“Ka kyauta Babana Allah Ubangiji ya raya mana Jameelu”.

“Ameen ya hayyu ya ƙayyum ”.

Cikin tuno da Jameel Hajja Nana tace.

“Ameen ya Allah ai Jameelu mutumin kirki ne”.

Asma'u kuwa cikin sauri ta ɗauki waya tare da kiran Ummi Ummi na ɗauka tace.

“Ummi albishir”.

Daga ɗaya ɓangaren Ummu tace.

“Goro”.

Cike da farin ciki Asma'u tace.

“Yah Jameel ya samu takwara”.

Murmushi Ummi tayi tare da faɗin.

“Hmmm Asma'u kenan kece baki sani ba amma ainin tun ranan Aliyu ya faɗa min”

Murmushi Asma'u tayi kana tace.

“Ummi shine baki faɗa min ba ranan muna hira ina cewa Ala'andi wani suna za'a sawa yaron kikayi shiru ashe duk kin sani”.

Murmushi tayi tare da cewa.

“Na sani mana tun ranan ya faɗa min”.

Murmushi Moddibo yayi tare da cewa.

“Ai TOH na rigaki yin albishir ɗin”.

Dariya ta sanya tace.

“Wallahi Yah Moddibo Ina sauri in rigaka ashe ka rigani”.

Haka sukayi yinin ranan anata shirye-shiryen suna, nan washe gari suna akayi raɗin suna da hidindimu kamar yanda al'adan masarauta take. 


Bayan sallar la'asar manyan Fada ne a zaune saboda Aranar Abualeey yake son yin Murabus ya barwa Moddibo sarauta.

Bayan an zauna an cika a Fada anyi komai an taru Sarkin Al'adun Fada ne ya juya ya kalli Moddibo dake cikin wani irin shiga na alfarma da kawa da yayi masifar fitar da ainihin kyawunsa da ƙwarjinsa kana yace.

“Alhamdulillah kamar yanda al'adun Fada take sarki yana da dama da iko da zai yi Murabus tun yana da rayuwarsa ya danƙa Mulki a hannun ɗan sa da yake ganin zai iya gadon mulkinsa kana zai iya kula da Masarauta yanda ya kamata dan haka Sarki Youseef Mohammed Aliyu Mouley ma yayi alƙawari zai maida Sarauta ahannun ɗan sa Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley”.

Cikin jin daɗi Manyan cikin Fada da Manyan Masarautu na gefe-gefe wanda baki ɗaya sun san da Maganar an samu sa hannunsu  tun watanni hudu da suka wuce kowa cikin jin daɗi da farin ciki yake faɗin Alhamdulillah.


Cike da girmamawa Sarkin Fada ya juya ya kalli Moddibo tare da cigaba da cewa.

“Kuma a wannan ranane za'a ƙara wa Sarki Aleeyu Youseef Mohammed Aliyu Mouley mata kamar yanda atsarin Masarauta sarki bai kasancewa da mace ɗaya sai an masa biyu aranan da za'a danƙa mulki a hannunsa”.

Cikin sauri Moddibo ya ɗaga kansa ya kallesu sai kuma ya saki wani Murmushi dashi kaɗai yasan ma'anar sa juyawa yayi ya kalli Abualeey dake cikin matsanancin farin ciki kana ya kalli Sarkin Fada tare da cewa.

“Ina son magana da mahaifina”.

Kai Sarkin Fada ya gyaɗa kana yace.

“Toh shikenan ba damuwa”.

Kana suka shiga ɗakin Sirri Shida Abualeey, Waziri, Galadima Wambai Garkuwa...


A dai-dai lokacin kuma acikin gida Khausar ce cikin shiga ta alfarma sanye take cikin wani lafiyayyan Abaya Pinch colour mai masifar taushi da santsi da yasha duwatsu kana ta ɗaura Alkyabba ta Masarauta fari ƙall mai masifar taushi wanda al'ada ce ta Masarauta wanda ranan da za'a naɗa mijinka a Masarauta zaka sa.

Shima Jaririn sanye yake cikin shiga na alfarma wasu picnh colour kayane tausasa kana aka daura masa ƙaramin Alkyabba fari irin na jarirai.

Sai hotuna suke ta ɗauka dasu Lalla, Khadijah Lalla, Hafsat Asiya, Asma'u, Dija, Rahama, Raudat Asma'u kuwa kai tsaye take turawa cikin group ɗin su na class mate ɗin su da suka gama makaranta.

Nan da nan cikin group ɗin ya kace me da surutu kala-kala kowa na tofa albarkacin bakinsa wata ƙawarsu wacce lokacin da suke makaranta bencinsu ke kusa da nasu Khausar mai suna Hawwa  Idris ne tace.

“Ikon Allah wai Khausar ce haka🤔 girma yazo rawan kai ya gudu?”.

Tayi typing da emotion na mamaki dariya Asma'u ta tura mata tare da cewa.

“Gashi kuwa kinga zahiri”

Cikin Mamaki tayi voice dan gani take typing ɗin bai mata sauri kana tace.

“Masha Allah shiyasa akace arayuwa kada ka taɓa wulakanta mutum domin baka san baiwar da Allah ya mishi ba wai yau Khausar ce matar Sarkin Morocco kuma Malam Moddibo?”.

Hoton dariya Asma'u ta sake tura musu tare da faɗin.

“Aikam ikon Ubangiji yafi gaban haka?”.

Wata mai suna  Jidda ce tace.

“Aikuwa dai muma Allah yasamu Adamshin ku Asma'u ku kam kunji daɗin rayuwarku”.

Murmushin Samira Sani ta turo tare da cewa.

“Uhmmm kuma ku godewa Allah a yadda kuke ɗin”.

Da sauri Khadijah Sule tace.

“Sosai ma kam Samira am”.

Amin kuwa cikin sanyi da nadama tace.

“Alhamdulillah ai in Allah ya baka lfy ka gode masa”.

Haka dai suka cigaba da hira acikin group ɗin kowa na faɗin albarkacin bakinsa.


_Daga can gefe  kuwa su ne Rafi'a,Tutus kitchen, Mom sayyeed&Noor Tatti Dija chiroma,  ne da suka halarci wajen sunan ne suke ta Video da hotuna suna turawa cikin Group ɗin SAKAYYA Team Moddibo da Khausar kam baki yaƙi ruhuwa duk farin ciki ya cika su ganin irin gift da Khausar ta bayar akawo musu._


_Daga can gefe kuma ƴan karatun bati siddan na Allah ya isa kenan da basu biya kuɗi ba suke wiƙi-wiƙi da ido duk hakki ya hanasu sakewa da samun nitsuwa..._


Asma'u dake cigaba da hotuna da wayar Khausar wayar ya ɗauki suwwa ganin sunan Yah Mu'allim na yawo yasa da sauri ta nufi Khausar dake tsakiyar Didi da Momy suna hoto tayi saurin isa gareta kana ta tsugunna zata miƙa mata wayar kasancewar azaune suke haka yasa ta fito a hoton da yayi masifar kyau.

Asma'u kuwa cikin raɗa takai bakinta kunnenta tace.

“Gashi fa Yah Moddibo yana kiran ki”.

“Mu gani”.

Cewar Khausar tana karɓan wayar tare da kaiwa kunnenta tace.

“Assalamu Alaikum Yah Mu'allim”.

Cikin wani irin yanayin na musamman yace.

“Minha kizo ki sameni aɗakina”.

Kai ta gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Sai kuma ta miƙe tare da rungume jaririn kai tsaye ta nufi sashen bakinta ɗauke da sallama ta shiga falon nan ta samu Dr Jameel, Dr Zakariyya, Ibraahim,Yah Ali, da Yah Abba da sauran yan uwansa.

Yah Abba na ganinta yayi Murmushi tare da cewa.

“Mai jego kin sha ƙamashi”.

Murmushi tayi kana tace.

“Ai dai kam”.

Kallonta ta mayar kan Ibraahim tare da cewa.

“Ibraahim Yah Mu'allim fa?”.

Da hannu ya nuna mata bedroom ɗin kana yace.

“Yana ciki”.

Ahankali ta nufi bedroom ɗin kwance ta gansa akan gadon yana ganinta ya saki sanyayyar ajiyar zuciya tare da buɗe mata hannunsa.

Cike da begensa ta zauna kusa dashi miƙewa yayi ya haɗa ta da jaririn ya rungumesu ahankali ya riƙa kissing ɗin goshinta zuwa wuyanta da kuma sassan jikinta baki ta ɗan tura tare da cewa.

“Yah Mu'allim ka matsaneni kuma ɗanka ya matse min wajen Theater na”.

Cikin sauri ya saketa kana ya karɓesa ya kwantar dashi tare da jawota jikinsa ya rungumeta sai kuma ya saki sanyayyar numfashi kana ya ruggumeta tsam cike da kulawa da kuma ganin yanayinsa ta shafo sajensa tare da cewa.

“Yah Mu'allim lafiya meke faruwa?”.

Kanta ya tallofo kana ya kalleta ido cikin ido da mamaki take kallonsa ganin yanda idanunsa suka kaɗa sukayi jawur dasu cike da kulawa tace.

“Yah Mu'allim lafiya?”.

Sunkuyar da kansa ƙasa yayi kana ya ɗago ya kalleta tare da cewa.

“Minha na yiwa Abualeey laifi kuma har yayi fushi dani”.

Cikin sauri ta zare idanunta tare da faɗin.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim laifin me kayiwa Abualeey?”.

Araunane yace.

“Minha nayi mishi babban laifi naƙin bin Umarninsa”.

Cikin tsoro da kaɗuwa tace.

“Ya Ilahi Yah Mu'allim akan me baza kabi umarnin Abualeey ba?”.

Langwaɓar da kansa yayi kan wuyansa yace.

“Saboda kece ban bi Umarnin Abualeey ba!”.

Cikin sanyi da rauni tace.

“Ya Ilahi bana son jin wannan maganar sam maganar babu daɗin ji Yah Mu'allim Kabi Umarnin mahaifinka shine abinda ya dace kuma shine *SAKAYYAR* da zamuyi masa”.

Cikin rauni da karyewar zuciya yace.

“Bazan iya ba”.

Cike da mamakin shin wani irin abu ne me nauyi da girma agaresa da yasa har ya yiwa mahaifinsa gardama tace.

“Haba Yah Mu'allim ya za'a yi kace baza kayi abinda mahaifinka keso ba shin wani irin abu ne?”.

Cikin sanyi ya kalleta kana ya lumshe Idanunsa tare da cewa.

“Saboda yau yake so a bani mulkin Masarautar Mouley ahannuna”.

Cikin sauri da jin daɗi kana da Jimamin yanayin da yake ciki tace.

“Toh mene Yah Mu'allim mulkin ne baka son rikewa ko me meyesa zaka yi mishi gardama?Kuma ai nikam ma ina son mulkin nan meyesa baza ka karɓi Sarautar ba? Kawai ka karɓi mulkin shine abinda ya dace”.

Kai ya jujjuya tare da juya ƙwayar idanunsa acikin nata kana ya riƙo hannunta acikin nasa tare da cewa.

“Ba karɓan mulkin bane matsala Minha”.

Cikin rashin fahimtar abinda ke damunsa tace.

“Toh ka karɓi mulkin mana kayi mishi biyayya akai”.

Hannunta ya damƙe kana yace.

“Ki bari kiji ko menene”.

Fuska ta tsuke tare da cewa.

“Nikam babu abinda zanji Yah Mu'allim kawai kayi mishi biyayya akan abinda yake so ka karɓi mulki Allah ya tayaka riƙo ya baka ikon Adalci kai masa biyayya ka samu lada”.

Cikin sanyi da rauni yace.

“Cewa yayi an bani mulki bisa sharaɗin za'a bani Auren wata mata ya zama ina da mata biyu!”.

Da wani irin sauri ta dafe ƙahon zuciyarta da yayi wani irin harbawa cikin rauni da fusgar magana tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.

Atake jikinta ya fara rawa kar-kar-kar tamkar wacce aka watsawa ruwa ƙanƙara atsakiyar hunturun sanyi kana idanunta suka kaɗa sukayi jawur tamkar garwashin wuta lokaci ɗaya taji numfashinta na Up and down alamar yana shirin barin gangar jikinta jawota yayi ya riƙe ta da damuwa atare dashi yace.

“Kee ki tsaya mana ki nutsu me haka!?”.

Gaba ɗaya ta rikice numfashinta sai fusga yake alamun tana gab da suma saboda tsabar masifar kishi, cikin fusgar numfashi da ficewar hayyaci ta dafe ƙahon zuciyarta tare da cewa.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Yah Mu'allim Aure kuma?,Wata matar za'a Aura maka?,ita?”.

Sai kuma ta tsaya da Maganar jin numfashinta na shirin barin gangar jikinta alamar zata iya rasa numfashinta.

Moddibo kuwa cikin matsanancin mamaki tsoro gami da ruɗu yake kallonta tabbas yasan tana da kishi amma bai taɓa tunanin kishinta yakai wannan matsayin ba.

Cikin sauri ya rungumeta tare da riƙo hannayenta kana yana jijjiga fuskarta yace.

“Khausar Khausar ki nutsu mana ki buɗe idanun ki dan Allah ki tsaya ki fahimci abinda zan faɗa miki”.

Da ƙyar ta iya buɗe idanunta.

Cikin sauri da tsoro ya sake tallafe Fuskarta ganin yanda ta zazzaro idanunta sukayi wani irin ja.

Ahankali ya fara bubbuga kumatunta tare da cewa.

“Dan Allah Minha ki nutsu kiji abinda zan faɗa Miki”.

Cikin rauni murya da bugawar zuciya tace.

“Yah Mu'allim yanzu mata zasu ƙara maka innalillahi wa'inna ilaihi raji'un”.

Sai kuma ta kife kanta akirjinsa ta saki marayan kuka mai masifan cin rai da zafi kukan data sakene ya temaka wajen daidaiton numfashinta ya tsaya.


Ahankali ya tallafota jikinsa yace.

“Minha shine laifin da nace Miki na yiwa Abualeey saboda nace masa, in dai har sai an ƙara min mata za'a bani mulkin, ni na yafe bana buƙatar mulki abawa Ibraahim nayi alƙwari zan rayu daga Ni sai ke sai kuma ɗan mu da kuma wa'anda zamu haifa nan gaba”.

Khausar kam wani irin kuka mai tsuma zuciya da tsananin kishi take yi.

Moddibo kuwa cikin gaskiya da gaskiya ya cigaba da cewa.

“in dai akan mulkine zan yi Miki kishiya abawa Ibraahim in yaso a Aura mishi Mata huɗu a rana ɗaya, nayi alkawarin bazan yimiki kishiya a kan mulkiba Amman ban miki alkawarin cewa wai bazan Miki kishiyaba dan bansan ne Allah zai tsara a kanmuba a gaba”.

Da sauri ta tashi kana ta buɗe Idanunta cikin rauni da shesh-sheƙa tace.

“Mata fa kace zasu Aura maka”.

Cikin kwantar mata da hankali yace.

“Ba kiji mai nace Miki bane indai mulki ne na haƙura dashi a bawa Ibrahim abarni Ni in rayu dake da ɗana da abinda zaki haifa agaba”.

Ahankali ta shiga sakin ajiyar zuciya Moddibo kuwa cike da tarin ƙaunarta ya cigaba da faɗin.

“Na tabbar kun isheni farin ciki kun isheni jin daɗin rayuwa kun isheni komai batare da mulkin nan ba Ni na yarda zan kasancewa Ibraahim mai bada shawara abawa Ibraahim mulki shine abinda yafi min kwanciyar hankali hakan ya miki kinji daɗi akan haka”.

Cikin matsanancin jin daɗi da farin ciki tace.

“Na yarda in dai har Abualeey ya yarda Bama son mulkin mun bar musu mun yafe musu mulkinsu Mukam Bama so”.

Akuma dai-dai lokacin Jaririn yasa kuka cikin sauri ta kallesa cikin shesh-sheƙan kuka tace.

“Abu J ba ka jiba yana kuka shima baya so a yiwa Mimeeinsa kishiya”.

Cikin sauri ya rungumota jikinsa kana ya haɗa da jaririn ya rungumesu tare da cewa.

“Mu bar musu mulkinsu Minha ba ruwanmu suje can su ƙarata da mulkinsu, su riƙe abinsu abarmu haka mu cigaba da jin daɗi da kwanciyar hankali yafi mana”.

Dai-dai lokacin Ibraahim yayi knowking kana ya sanar masa zuwan Momy da Didi.

Suna shiga Didi ta kallesa Babu walwala atare da ita tace.

“Yanzu Aleeyu ka kyauta kenan ɓacin ran da kasa Mahaifinka”.

Cikin sauri ya mike kana ya tsugunna gaban Didi tare da cewa.

“Didi dan Allah kuyi haƙuri”.

Cikin sauri da rashin walwala Didi tace.

“Shi ya gama yanke hukunci amatsayin sa na Mahaifin ka Sarautace an riga da an baka ita sai kayi abinda kaga zaka iya akai”.

Da sauri cikin shesh-sheƙa Khausar tace.

“Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un Didi yanzu kuma harda Mata za'a ƙara mishi?,”.

Cikin tsuke fuska momy ta harareta tare da cewa.

“Dan Allah rufe mana baki, sokuwar banza sokuwar wofi, in ba'a Aure ke aka Auro ki baza ki taya mijinki yanda zai yiwa iyayensa biyayya ba, sai ki tsaya sokonci kina kuka kina cewa an ƙara masa mata matar kashe ki zata yi, ko kuma akan ki zata zauna?”.

Cikin rauni ta fashe da kuka kana ta jingina kanta da bakin gado cikin shesh-sheƙan tace.

“Momy ba zaki gane bane bazan iya rayuwa da wata mace tare da Yah Mu'allim ba”.

Ahankali Didi ta ɗagota kana ta dafa kafaɗarta tare da cewa.

“Kiyi haƙuri Sarauta ce an bashi Mata kuma tunda yace baiso da ɗaya zai zauna shikenan tun da dama bawai shariya ɓace ta tsara haka, al'adace”.

Ajiyar zuciya mai sanyi ta shiga saki tana jin nutsuwa na diran mata shi dai Moddibo kan sa na ƙasa Didi kuwa cikin kwantar mata da hankali ta cigaba da faɗin.

“Allah da kansa ya basu Umarni suyi Huɗu, Uku, Biyu idan kuma ba zasuyi adalci ba suyi ɗaya tunda yace ba zai yi adalci ba laifi.

 Mahaifinsa ya yarda an bashi Sarauta batare da anƙara mashi mata ba”.

Cike da matsanancin farin ciki ta mike ta rungume Didi kana tace.

“Nagode Didi Ubangiji Allah ya miki Albarka”.

Cikin sauri ta saki Didi kana ta tsugunna ta fuski Alƙibla tare da yin Sujudur Shukur ta godewa Allah kallonta ta mayar kan Moddibo dake Murmushi ta miƙa masa hannu tare da cewa.

“Yah Mu'allim Alhamdulillah ”.

Martanin Murmushi ya mayar mata yana mai jin wani irin nutsuwa na ratsa sassan jikinsa ganinta cikin farin ciki ahankali yace 

“Alhamdulillah”

Murmushi Didi tayi tare da riƙe hannun momy kana ta kalli Moddibo tace.

“Idan ka gama murnan ka tashi ka tafi Fada ana damƙa maka sarauta”.

Kai ya gyaɗa tare da cewa.

“Toh”.

Momy kuwa kallon Khausar tayi kana tace.

“Wuce mu tafi ”

Ta ƙare maganar suna fita.


Cikin sauri Khausar ta miƙe tare da faɗawa jikin Moddibo tayi masa wani Amintaccen runguma sai kuma ta tallafo kansa ta haɗe bakinsu ta shiga kissing ɗin sa ahankali ta zare harshenta cikin nasa tare da riƙe hannunsa Fuskarta ɗauke da maɗaukakin farin ciki tace.

“Ina ƙaunarka Abu J My life is nothing without you”.

Murmushi yayi kana ya lakace mata hanci tare da cewa.

“Shikenan kuka ya ƙare ko?”.

Dariya ta sanya tare da ɗaukan Jaririn tabi bayansu Momy da tuni suka fice kana shi kuma ya fita ya samu su Ibraahim suka wuce Fada.


Aranan aka naɗa masa Sarautar Mouley kana aka ɗaura auren Rahama da saurayinta kana matar da za'a Aura masa aranan aka Aura wa Ibraahim ita Ibraahim kam. baki har kunne cikin jin daɗi da farin ciki aka gama Shagali da daddare aka kaiwa Ibraahim matarsa.

Tun aranan Lalla Hafsat da wasu daga cikin baƙi suka tafi da Rahama kasan cewar ƙanin mijin Lallai Hafsat ne mijinta yasa aka wuce Mexico da ita baƙin suna kuma duk an watse lfy...


Haka rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar na samun kulawa mai kyau.

 ranan da ta cika sati Uku Alhamdulillah Thearter yayi gwaɓi sosai suka je asibiti aka sake dubawa a ranan sukaje asibiti Alhamdulillah aka duba akace babu matsala yayi kyau saboda jikinta yana da kyau yaro yayi kuɓul-kuɓul gwanin sha'awa Masha Allah.


A ranan da suka cika wata ɗaya da yammaci Khausar bayan ta fito daga wanka ta shirya cikin wani riga da skirt na less me kyau jikinta sai ƙamshi yake ɗan ta yayi kuɓul-kuɓul Masha Allah yayi ƙato gwanin ban sha'awa.

Zaune suke Khausar Innayi da Hajja Nana suke a bedroom.

Yayin da Momy da Raudat ke zaune Side ɗin Didi tana ta shirye-shiryen tafiya nan da kwana biyar masu zuwa.


Ahankali Moddibo ya shigo bedroom ɗin hannunsa riƙe da Jaririn dake tsala kuka kusa da Khausar ya zauna kana ya ɗaura mata yaron akan cinyarta kai ya langwaɓar cikin wata amintacciyar murya me cike da kulawa tare da tsantsar soyayya yace..

“Minha yunwa fa yake ji”.

Ashagwaɓe ta tura baki kana ta langwaɓar da kai tare da cewa.

“Yah Mu'allim ɗazu fa yasha kuma sai yaita tsotseni”.

Akasalance yace.

“Ki ƙara mishi”.

Fuska ta narkar tare da faɗin.

“Toh tunda ya daina kuka a bari sai anjima”.

Ahankali ya girgiza kai kana yace.

“A'a ki bashi yanzu”.

Miƙewa Innayi tayi tare da cewa.

“Khausar bari inje inyi Miki ɗan wake naji kina cewa kina son ɗan wanke tunda kika haihu baki ciba”.

Murmushi tayi kana tace.

“Yawwa Innayi na ayi min shi yaji yaji yayi daɗi sosai sannan asa min da  ƙwai da lemun tsami akai”.

“Toh".

Innayi ta amsa tare da ficewa.

Hajja Nana kuwa ido ta zubawa Moddibo lokacin daya zuge zip ɗin rigar Khausar ta baya.

Cikin Mamaki tace.

“Ohhhh ikon Allah”. Ta faɗa asanda taga yayi ƙasa da wuyan rigar  Nonon fito, kan yaron ya tallabe ya sawa yaron abakinsa.

Ta cigaba da cewa.

“Gwara ma ni in tattara mu koma in bar muku gidanku.  hankalin mu ya kwanta wai nan kai Sarki ne guda".

Juyawa yayi ya kalleta kana yace.

“Toh ce Miki akayi Sarauta anayinsa atsakanin Iyalai ne?

Ai sarauta iya kacinta Fada”.

Cikin taɓe baki Hajja Nana tace.

“Ohhh Allah ya kawo mu zamani ai kai ko A Fada idan zaka samu za kayi musu taɓara”

Murmushi yayi yana shafa sajensa yace.

“Toh Matatace fa,Ko ba matata bace?

Sadaki fa na biya”.

Hararansa tayi tare da cewa.

“Ka biya ko aka biya maka?”.

Dariya maganar nata ya bashi amma sai ya murmusa yace.

“Eh koma dai menene Matatace ni wlh kin isheni da gorin biya min sadaki akayi dan haka ni yau zan biya nawa sadakin”.

Ya ƙare maganar yana jan wayarshi tare da ƴan danne-danne.

Dariya ta sanya tare da cewa.

“Ohhh baki baya mutuwa ai da kai da ita duk bakin ku ɗaya ne”.

Khausar Murmushi take musu tana cigaba da bawa yaron Nono.

Sai kuma ta kalli wayarta jin sautin shigowar saƙo.

Hannunta na hagu tasa ta ɗauki wayar tare da buɗe saƙon.

Cikin tsananin mamaki ta zaro ido ganin alert ɗin 10 million da Modibbo ya tura nata da rubu a jiki.

*Minha ga sadaki na*.

Cikin kaɗuwa tace.

“Yah Mu'allim 10 million fa ka turo min me sanyi dasu, million goma”.

Sai kuma ta ƙare maganar da kallon Hajja Nana dake cewa.

“Da gaske”. Cikin tsananin jin daɗi Khausar tace.

“Wallahi kuwa gasu kin gani”.

Ta ƙare maganar tana miƙa mata wayar da kuma yaron sai kuma ta ruggumeshi tana saki kishi sassayan kiss tako ina a jikinsa.

Ganin yadda ta ruɗene yasa Hajja Nana yarda bawai dan ta fahimci rubutun alert ɗin ba.

Haka tai ta murna tare da godiya, kukan da Keyan ya sakan ne yasa ta saki uban ta karɓi ɗan kana taci gaba da bashi Nono.

Cikin dariya Hajja Nana tace.

“Daga yau ka huta da gori, kuma dole a bani million ɗaya a ciki”.

Murmushin yayi tare da cewa.

“Kawo account inki in baki naki sadakin tunda jikarki na gudun kishi sai in haɗata dake”.

Cikin dariya tace.

“Yoh ina ni ina aure ai na gama aure kam”.

Dariya sukayi baki ɗaya.

Bayan ta gama bashi da kansa ya mayar da Nonon kana ta mike tare da faɗin.

“Kizo muje ki gyara min Siff ɗina ya hargitse”.

Kai ta gyaɗa kana tace.

“Toh”.

Tare da miƙewa tabi bayansa da kallo Hajja Nana ta bisu sai kuma ta saki Murmushi tare da ɗaukan Jaririn tana mishi wasa.

  

     Suna shiga tsakiyar bedroom ya jawota jikinsa ya rungumeta yana shaƙan ƙamshin Kwalaccan Sirri da Humran _Aunty Aysha Aliyu Garkuwa_ da tayi amfani dashi sosai ƙamshinta ke zautar dashi yana masifar son ya riƙa shaƙar ƙamshin jinta yana masifar gigita masa tunani cikin wata kasalalliyar murya me cike da shauƙi da fitina yace.

“Minha yanzu dan Allah tsawon kwana nawa kika fara Sallah?”.

Cikin lumshe idanu da yanda lallausan tafin hannunsa ke yawo asassan jikinta ta fesar da sanyayyan numfashi tare da cewa.

“Yah Mu'allim nafi sati biyu da fara Sallah ”.

Ɗan ware idanunsa yayi kana muryansa can ƙasan maƙoshi yace.

“Kina tsoron kishiya kuma kina tsoron kyautatawa mijinki da ɗauke bukatarsa”.

Ashagwaɓe ta ƙyafta ƙwayar Idanunta cikin nasa tace.

“Yah Mu'allim nifaaaa”

Da sauri ya sake ƙanƙameta yana sakin ajiyar zuciya yace.

“Minha kin san dai ina da buƙata bazan  iya jiran abinda Likitocin nan suka faɗa ba”.

Cikin sanyi da ɗan tsoro tace.

“Thearter na fa kada ya ɓalle”.

Yana yawo da hannunsa aƙugunta yace.

“Bazai ɓalle ba”.

Ya ida maganar yana zama bakin gado kana ya zaunar da ita kan cinyarsa tare da zuge zip ɗin rigar ta yayi ƙasa dashi kana shima ya cire nashi blanket ya jawo ya rufe su tare da ɗaura bakinsa akan dogon hancinta yana tsotsa kana ya mayar kunnenta yana hura mata sanyayyar iskan bakinsa.

Sai kuma ya tsaya jin tana cewa.

“Yah Mu'allim ina tsoron Theater nafa”.

Muryansa can ƙasan maƙoshi irin na wanda ke cikin tsananin buƙatuwa yace.

“Na sani zan biki ahankali”.

Bai jira jin Abinda zata ceba ya shiga sarrafa ta cike da bege da kuma shauƙi yayin da ya shiga Binta hankali cikin shagwaɓa da tsoro tace.

“Wayyo Yah Mu'allim wajen Theater na zafi fa ina tsoro kar ka ɓalle min ɗinki?”.

Cikin ficewar hayyaci yace.

“Minhaaaaa bazan ɓalle Miki ba ki nutsu dan Allah”.

Ita kam cigaba da zuba masa shagwaɓa da raki tayi tana cigaba dace masa wajen Theater ta sai da ya ɗauki kusan awa ɗaya akanta kafin ya janye jikinsa daga nata ya janyota jikinsa ya rungumeta yana sa mata albarka sai kuma yayi Murmushi yace.

“Matsoraciya sai raki ɗinki ɗinki ɗinki sai raki da tsoro".

Cikin sauƙe ajiyar zuciya tace.

“Yah Mu'allim Allah tsoro nake ji kar ya ɓalle”.

Yana shafa shafeffen cikinta yace.

“Ba abinda zai ɓalla shi Minha”.

Miƙewa sukayi suka shiga toilet sukayi wanka atare bayan sun fito suka fara jiyo muryan Raudat na cewa.

“Assalamu alaikum.

Addah khausy”.

Da sauri Khausar ta ƙarasa jan Zip ɗin rigar ta ta nufi ƙofa kallonta Moddibo yayi tare da cewa..

“Kamar Raudat ko?”.

Kai ta gyada kana tace.

“Eh Itace kuma kamar Naji kukan Keyan”. atare suka fita yana gyara wuyar rigarsa yayin da take naɗe ƙasan rigarta.

Suka fita falon idanunsa ya sauƙa kan Raudat dake rungume da jaririn.

Ware idanu Moddibo yayi tare da faɗin.

“Ya Salam Aunty Raudhiy yanzu ke aka bawa Yaron nan?”.

Murmushi tayi tare da kallon fuskar Keyan tace.

“Yah Moddibo ai na iya riƙewa bazan kada shiba”.

Murmushi yayi tare da faɗin.

“Aikam ba zaki kada shiba kawo shi nan”.

Karbansa yayi ya bawa Khausar ta zauna tana bashi Nono suka zauna gefenta suna ta hira...


Bayan kwana biyar Momy suka wuce Saudi ita da Hajjaj Nana dan Modibbo ya biya musu umra, bayan sun gama aikin umrarsu ne suka koma Nigeria bayan komawar su da sati ɗaya akayi.

 Auren Amina da Baban Samira Sani cikin ikon Allah mai gadin gidansu Samira yace yana sonta fahimtar yanayin da take ciki kuma zuwa yanzu Alhamdulillah jikinta yayi sauki arana ɗaya aka ɗaura Auren Babanta ya bashi gida da jari kana ya nemi wani sabon mai gadi. 

Haka suka tare abinsu Samira da maigadinsu.

 ita kuma Amina tana rayuwarta da tsoho.


Hajiya Bunayya da Hajiya Lami kuwa na can Sycatry suna gallar rayuwarsu da girban abinda suka shuka.


Haka dai Rayuwa ta cigaba da tafiya Khausar kam Alhamdulillah yaronta ya kai wata shida yayi ɓul-ɓul dashi yana zama kana yana wangale baki yana dariya sosai.


A wannan lokaci kuma suka tafi aikin hajji, Ita da Modibbo da ɗan Jaririnsu da Hadimar dake kula dashi da kuma innayinsu, Asma'u da Dr Jameel, Asiya da Dr Zakariyya, Dija da Yah Ali, Yah Abba da matar daya aura wata biyu ɗaya wuce.

Sai Didi da Innayi da Abu Ali, da kuma Ibrahim da matarsa.


Watansu ɗaya a can suka dawo, bayan sun dawo da mako biyu suka je Mexico.

Sosai Lalla Hafsat da Rahama sukayi daɗin sosai.

Itama kanta Khausar Mexico tayi mata daɗi sosai.

Makonsu uku suka dawo.


Taraba. Nigeria Gembilan 

Yau ya kasance labari cikin ɓadda kama Uncle Naseer ya shigo cikin garin Gembila da niyyar kwashe Mahaifiyarsa da Mahaifinsa su koma Indi'a da zama.

Cikin dare ya shiga cikin unguwar su da sauri ya buɗe musu mota tare da cewa Mamansa da Babansa.

“Kuyi sauri kushi ga mu tafi”.

Kai Maman ta gyaɗa kana tace.

“Toh ai gwara ka kwashe mu mu tafi mu huta da jaraba da Sa idon mutanen gari da gulmace-gulmace”.

Ta ƙarashe Maganar tana shiga motar.

Shikam Uncle Naseer cikin sauri ya shiga motar yaja su.

Suka fara tafiya suna gab da fita garin Gembilan motarsu tayi tambul ta riƙa juyawa tana bugawa da tsaunukan gefen titi kafin ta kama da wuta sukayi mugun ƙonewa  sai ya Fuskarsu ce ta rage kana kuma b....

Post a Comment

0 Comments