TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MIN QALB 🥰 PAGE 34-35

 Littafin Nan na kudine kabiya ka karanta cikin nutsuwa da aminci.**_MQ 34_*






Fuska kawu ya sake bayan isowar MD yace"


MAHMOUD sannu da qoqari mungode sosai Allah yasaka yayi muku albarka duk ku duka Allah yaji qan Khalilu yayi Masa rahama tareda albarkar Abinda yabari a baya.


Amin kowannensu yace jiki a sanyaye kafin umme ta Dora da fadin"


MAHMOUD kayi Magana da kawu Dan Allah yabar Amatu harta haihu tukuna ayi maganar tafiyarta.


Miqawa zarah takardar dake hannunsa Wanda Fatima tabayar kafin ya kallesu cikin rashin son Jan dogon zance yace"


Kutafi zamuyi mgn da kawun Zan wuto da ita idan angama.


Kallonsa umme tayi tana miqa dukkanin yardarta akan cika maganarsa na zai dawo da Amatun zabeera idan sun barta.


Ahankali ya gyada Kai Yana Dan rufe Ido.


Kallon Amatun umme tayi jiki a matuqar mace tace"


Ina jiran dawowarki Amatu.


Gyada Mata Kai tayi tana murmushin Bata qwarin gwiwa kafin ta kalli anty zarah da ita tayi wani iri tace"


Anty ZARAH saki fuskan Mana saikace Rabin ranki ne akace za'a tafi dashi.


Guntun murmushi anty zarah din tasake tana Dan hararar Amatun tace"


Kina tunanin MAHMOUD zai barni yatafi wani gurin bayan tafiye tafiyensa?

Kece dai abin jimamin sbd ba'a shiga Zabeera family a fita saidai mutuwa""taqarasa tana dariyar Amatun qasa qasa.


Tafiya sukai suka bar Amatun taredasu iyami dasu kawun Nan kawun da MAHMOUD suka kebe sukai magana sai gashi sun wuce a motar Salman sun barta tareda MAHMOUD din 

Batareda yayi Mata kallo biyu ba ya nufi motarsa bayan yace suje.


Drivernsa ita yafara budewa mota tashiga kafin ya zagaya ya budewa MD din yashiga ya rufe yafada motar shima ya tayar sukabar gurin.


Jinginar da kanta tayi baya tareda lumshe ido ta sauke numfashi ahankali sbd imperial majesty dinsa daya gaurayu da AC dakuma qamshin motar saiyake Bata nutsuwa sbd dadinsa.


Shikuma wayarsace datai ringing ya dauka yafara waya cikin nutsuwa a harshen turancin dayasata Dan bude Ido kadan ta saci kallonsa sbd ya tuno Mata da Dr khalil dinta idan Yana turanci zaunawa takeyi ta zubawa bakinsa Ido cikin burgewa da son koya sbd abin na matuqar burgeta tana sha'awar zama Yar gayun Yar Boko me zuba turanci Wanda tasan da Dr na Nan da yanzu tafara karatu Inshallah.


Ajiyar zuciya ta sauke afili Wanda yasashi Dan waiwayowa kadan ya kalli gefenta kafin yaci gaba da wayarsa.


Har bakin qofar palonsu motar ta tsaya direban yafito da sauri ya zagayo ya bude Mata batareda ta juyo ta kallesaba tace"


Nagode""ta fice ta shige palon tana sauke numfashi sbd atakure take cikin motar ko dogon motsi bakada ikon Yi kamar an takura Masa ne shiyasa ko matarsa zarah wata ran basa kwana tare sbd yawan juye juyenta da motsi Wanda ke hanasa bacci ko kadan hakan Kuma na saka Rabin kansa ciwo.


A palon ta tararda anty salamatu na qoqarin ajiye abincinda tafito dashi daga kicin akan dinning itada shafa'atu me aikinta.


Wecewa tayi dakinta Kai tsaye tayi wanka da ruwan dumi sosai kafin ta fito ta sanya jallabiya tayi sallar magriba da akayi suna hanya tayiwa mijinta addua sosai cikin farin ciki da walwala take sbd cikin jikinta ya dawo da duk wani farin ciki datake tunanin ta rasa Dan kuwa Dr khalil dinta Jin take kaman yadawo sbd tasamu Abu mafi soyuwa daga garesa.


Shafa cikin tayi bayan ta miqe ta zauna bakin gado ahankali ta tuno da cikin qaryarsu Wanda shauqin abin alokacin yayita shigarsu itada Dr Ashe ita kadai zata qarar da zuwan ranar,

Idan namiji na Haifa baida sunan daya wuce na mahaifinsa inshallah.


Wayartace tayi ringing ta juya ta kalla screen din wayar taga sunan USI 

Tasaki murmushi me Fadi tana daukar wayar kusan atare sukace"


Lallaima.


Dariya suka saki lokaci daya Jin bakinsu yazo daya tace"


Allah USI nakusa gayawa kawu ya yafewa Yan can Kai,

Yanzu duk yinin yau sai yanzu kake kirana.


Dadina dake masifa ko numfashi bazaki Bari mutum ya saukeba,

Yaya jikin to?

Nayi waya dasu kawu yace ansallameki sunkoma gida.


Eh da magribar Nan nadawo.


Amah nayi Magana da kawu akan Zaki koma gida sbd zaifi Mana sauki harzuwa lokacin haihuwarki tunda ko haihuwa Kikai bana sakaran zasu karba Abinda aka Haifa din saiyayi wayo sosai kokuma idan Zaki koma makaranta

Dagani har kawu Amatu karatu yanzu mukeson kiyi.


Numfashi ta sauke tareda gyara zamanta tace"


USI Nima naso komawa gidan saidai Kuma yanada wuya su Bari nabar Nan din shiyasama kawai nabari Bayan haihuwar saina koma gida tunda koba komai Ina haihuwa na fita takaba ba sauran dalilin zamana anan din Amma dai kawu yace zaizo gobe zasuyi Magana dasu Modibbon idan sun Bari din zankoma gidan idan Kuma sun buqaci na zauna harna fita takaban duk Babu illa tunda dai lokacin zaizo.


Numfashi ya sauke cikin nutsuwa yace"


To Allah ya saukeki lafiya shine fatanmu akan komai.


Amin ya furta afili kafin suka shiga cikin zancen karatunsa dayayi nisa yanzu gashi Yana bada himma sosai Dan tuni ya goge cikin masu qoqarin makaranta.


Da daddare umme da kanta tazo tayi musu fira har kusan qarfe goma kafin ta tafi anty zarah dai ce Bata sake gani ba sai washe gari anacan ana soyewa da Rabin Rai.




Washe gari qarfe goma sha daya na Rana kawu ya iso zabeera tareda Dr Salman dayaje ya daukosa akan maganar komawar Amatu gida

Dama Suma su Modibbon suna jiransa sbd tun jiyanma da MAHMOUD yayi musu bayanin Abinda kawun ya buqata sukaso zuwa har gida su samesa tun cikin Daren saigashi yace yace zaizo a yau din.


Babban palon Andi suka Isa inda andin da Modibbo ke jiran isowar kawun

Gaidasu kawai dr Salman yayi ya ficewarsa ya barsu suka Fara tattaunawa.


Cikin nutsuwa Andi ya kalli kawu zaifara Magana saiga MD yashigo batareda yasan kawunma naciki ba.


Cikin nutsuwarsa da girmamawa ya gaidasu tareda sanarda Modibbo zaiyi tafiyane yau takamasa Kuma zai kwana biyu kafin yadawo.


Kallonsa Andi yayi cikin nazari harya miqe zai fice yace"


MAHMOUD dawo ka zauna Magana zamuyi akanka da Dan uwanka marigayi tareda Abinda yabari.


Maida kallonsa yayi Kan kawu cikin nuna Masa girma amatsayinsa na mahaifin 'yar dasuke son abarta cikin zuriar 'ya ko 'dan da zata Haifa yace"


Mal Saleh tun jiya nakejin saqonka bakin MAHMOUD 

Da tun jiyan mukaso ganinka saikuma dai muka Bari yau din tunda yace kace zakazo din akan maganar,

To Mal Saleh munji zancenka amatsayinka na mahaifin AMATULLAH Kuma bamu katsi hanzarinkaba amma maganar barin AMATULLAH kwata kwata zabeera Bata tasoba sbd koba komai dai ga rabo Nan ya ratsa a tsakani Kuma bayan hakan ma tun asali zabeera shiyasa ba'a auren waje sbd irin hakan duk da qaddara ce da Babu me gujewa saidai kuma tunda AMATULLAH tashigo zuria mezaisa ta futa Dan mijinta ya rasu bayan munada Wanda zai Kare mutunci da haqqin iyalin 'dan uwansa ko ayanzu da babu ran nasa?,


Mal Saleh Kai ubane,bazaka so 'yarka Takoma gabanka ta Dora sabon zama na zawarci duk da Allah ne yaso hakan shiyasa muke fatan kaima kazabi barin 'yarka a killace cikin inuwar aure sabanin komawarta gabanka,

'yayanmu idan mazajensu sun rasu suna fita takaba da qanqanin lokaci muke aurar dasu ga Yan uwa mafi kusanci na mazajensu sbd dorewa acikin aure shiyasa ba alfahariba bamada tarin zawarawa acikin zuria sbd zawarcin ba Dadine dashiba,


Maganar aure ga me takabar dake cikin takaba haramun ne shiyasa bazamuyi maganar auren AMATULLAH ayanzu ba Amma dai muna roqonka a matsayinka na mahaifin AMATULLAH daka barta anan tayi renon cikinta ta haihu bayan haihuwarta zamu nemawa Dan uwan mijinta mafi kusanci agaresa aurenta wato MAHMOUD Wanda Inshallah aranar sunan Abinda ta Haifa tareda radin suna zamu daura musu aure Inshallah idan harka bamu dama tare Kuma da amincewa.


Numfashi me qarfi kawu ya fitar a fili tareda jinjina Kai sbd shima kamar yanda suka fada duk duniya Babu ubanda zaiso yarsa tadawo gabansa ta zauna ta dasa sabon zaman zawarci sai abisa qaddara,


Qaddara ce ta saukarwa Amatu Kuma Dole sunkarba hannu bibbiyu saidai tunda tasamu wani tayin auren gskia bazaiqi amincewa ba tunda dama suna tunanin tattarawa ne subar gidan sukoma inda Amatun zatafi sakewa da Abinda zata Haifa to tunda har mutanen nan na qaunarta harda basa iya barin ta fita wani gurin dabam tayi aure Babu Abinda yafi Masa wannan saidai tunda ba halaccin maganar neman aure akanta ayanzu zai tafi da ita still idan lokacin haihuwarta yakusa tunda zata dawo daga baya.


Aje numfashi yayi tareda koro musu nasa bayanin bayan amincewarsa akan idan takusa haihuwa Zata koma gida ta haihu gaban uwarta.


Ba wani dogon sharhi suka amince akabar maganar akan Babu Wanda za'a sanarwa yanda aka aje zancen sai bayan haihuwarta idan lokacin Daurin auren yayi.


Komai bai iya cewa ba sbd zancen baiyi Masa Kama da zai yiyu dinba idan har za'a tambaya ra'ayinsu kafin Daurin auren idan lokaci yayi.


Sallama yayi musu tareda 'yar godiyar da batakai cikinsa ba ya fice Yana duba agogon hannunsa sbd yakusa lattin Isa airport.

##Mamuh#


*_Dan Allah kuyi hkr kuyi manage inada uzurin fita ne amma Inshallah next pg saikun gaji da karantawa sbd tsayi_* 😁*_MQ 35_*


Godia kawu yasake kafin ya sake gyara zama bayan fitar MD yace"


To akwai 'yan burirrika dakuma kamar sharadi zance kokuma dai nace alfarma damuke nema bayan auren.


Cikin jinjina Kai Andi yace"


Muna sauraronka Mal Saleh Allah yasa me dubuwace wannan alfarmar ko sharadin.


Eh wato gskia Amatu dai na sha'awa dakuma ra'ayin zurfafa karatun zamaninta wato na bokon Nan 

Tajima da wannan burin bama ita kadaiba wannan burinane akansu tun suna Yara gaskia saidai Kuma Hali na rayuwa baibari tasamu ilimin bokon ba sosai,

Shi kansa mijinta Allah yaji qansa kafin aurensu yayimin alqawarin barinta tasamu wadataccen ilimi bayan aurensu saigashi Allah bai basa iko ba Dan haka nake bayarda wannan buqatar ta barinta ta ilmantu acikin Boko Dan shi na addini Banda haufi akanta tasamesa yanda yakamata Inshallah,

Wannan shine buqatata 

Idan MAHMOUD daku iyayensa zaku Bata wannan damar to Ina godiya da hakan.


Tsit sukayi suna nazartar zancen nasa sbd maganar haqiqanin gaskia yaransu Mata basa karatu anan musamman masu auren sbd qasarmu na daya daga cikin qasashen da Basu dauki Mata da daraja ba idan angansu suna yawon neman ilimi makaranta musamman akan matan aure da akafi buqatar fasikanci dasuba ayanzu akan 'yan matan shiyasa suka zabi gwara sukai yaransu qararda ba'a sansu ba suyo karatunsu su dawo,

Amma babbar matsalar anan itace ana maganar karatun Amatun ne bayan aure Kuma har wata qasar.


Muskutawa Modibbo yayi ya kalla Andi cikin nutsuwa yace"


Inaga Babu wata illa ko abin damuwa musamman tunda shi MAHMOUD din nada gida acan yawancin qasashen saita zaunama acan din shikenan.


Numfashi Andi Yakuma saukewa kafin ya jinjina Kai ya kalli kawu yace"


Yanxu duk ba lokacin wannan neba yanxu idan lokacin yayi zamuyi maganar insha Allah.


Sake goggodewa juna sukayi tareda maganganu dangane da gadon da Khalil yabari shidai kawu baida tacewa hakadai suka kammala kafin aka Kira Salman ta waya yadawo ya daukesa Dan maidashi gida.



***Ahankali tasanyawa kanta hkr ta rungumi qaddarar rasuwar mijinta tareda rungumar Abinda Allah yabata ta maida hankali gurin renon cikinta Wanda kusan yanzu tsakanin itada umme da iyami da anty zarah sai oga kwata kwata MD ZABEERA ba'a San yafi qwallafawa cikin Rai ba,


Iyami tuni tafara siyan robar wankan jariri dasu kujeran zaunawa akai ayi Masa wanka harma dasu kayan yajin abincin me jego Wanda kullum lissatafinta kenan,


Umme ma Kam tuni akai nisa gurin tariyar kayan jarirai hardasu kayan wasansa,

Anty zarah kuwa kayan me jegon tafi maida hankali gurin Dan siya 


Sai oga MD ZABEERA Wanda ya damesu ya shanye gurin Tara siyayyar kayan jarirai har wainda sai ya iya tafiya da gudu kafin yayi amfani dasu dan sunfi qarfin jariri Wanda daki guda ake Tara kayan acikin sashen Amatun duk yayi tafiya yadawo scan ake Kai kayan Wanda yasa Tunanin Yama fisu zautuwa wannan Rabin ran Anty zarah din.


Tsakaninta dashi gaisuwa ne shima sai idan anci sa'a sun hade by mistake sbd saitayi fiyeda wata ko wata biyuma Bata gansa ba sbd sosai yanzu yarage zama sai yawan tafiye tafiye,


Dr Salman kuwa yayi tafiya baya qasar tun cikinta na wata hudu yayi tafiyar Amma kusan kullum ayini shida USI batasan Wanda yafi wani kiraba,


Cikinta yanzu Yana wata na bakwai Wanda yayi girma Dan daidai ba laifi Wanda yasa qafafuwanta Dan kumbura kadan shiyasa ma kullum ake fita da ita haraba tana Dan zagayowa sbd Dr Fatima tace taringa motsawa tana Dan zagayowa.


Duk wani bayani da update Akan lafiyar cikin Dr Fatima MD ZABEERA take Fara Kira sbd agurinsu tamkar shine mahaifin Abinda za'a Haifa din and kowa yasan irin shaquwarta da qaunar dake tsakaninsa da 'dan uwansa kafin ya rasu so koba a fada musu ba sunsan Babu Wanda zai dauki responsibilities na cikin Bayan shi barema Kuma shine yabada wannan odar ta komai asanar dashi har ranar haihuwar ma'ana EDD dinta duk yasani.


Zaune suke apalo itada anty salamatu da sai umme datazo dubata and kwana biyu tunda tashiga wata na takwas take fama da ciwon Kai me tsanani Dr Fatima tayita dubata ta sanar musu da tana fama da matsalar high BP ne Wanda Dole suyi monitoring dinsa sbd idan bai sauka ba yakoma normal to yanada wahala ta iya haihuwa da kanta saidai CS.


Magani umme ta miqa Mata ahankali ta karba tareda karbar robar ruwan dake gabanta ta bude ahankali tana Dan lumshe ido sbd ko Ido ta bude sosai kanta kamar zai tsage,

Maganin ta shanye tana ajiye robar daidai Dr Fatima na shigowa palon daukeda sallama suka juya dukkaninsu suka kalleta suna Mata sannu da zuwa Banda Amatun data kasa ko bude idanuwanta dake lumshe sai kawai taji hancinta na shaqo Mata qamshin imperial majesty sama sama,

Bata bude idanuwanta ba sbd tasan baitaba shigowaba Kuma tasan baida dalilin dazai sashi shigowa din dan Daman da cikin yadamu bawai ita ba to Kuma Dr Fatima ma kafin tafada musu komai dangane da cikin saita fada Masa tuntuni haka suke Dan haka Bata sakaran akwai Abinda zai taba sanyashi shigowa....


MAHMOUD Kaine da kanka yau?""maganar umme data sanyata bude rufaffun idanuwanta cikin rashin sa'a sai acikin nasa daya zuba Mata akaro na farko daya kafeta idanuwansa Yana kallon cikinta daya Gama girma.


Cire idanuwanta cikin nasa tayi akaro na farko wata irin tsananin kunyarsa ya kamata sbd ganin irin kallon dayakewa cikinta

Ta 'dan muskuta ahankali tareda Dan Jan wuyar rigarta sama sbd budadden wuyane Dan doguwar rigace Mara nauyi Sam hannunta ma qarami ne irin na shimi.


Ahankali ya dauke kansa Yana zaunawa a kujerar dake fuskantar Tata ya kalli umme ya bude baki cikin yanayinsa na nutsuwa cikin sauti me taushi yace'


Barka da yau umme,

Na sameku lfy?


Lafiya kalau,

Yaushe kadawo ne Dan last time Dana tambaya zarah tacemin kana Turkish.


I came back this evening.


Allah sarki to sannu da hanya.


Thank you umme""ya furta cikin qaramin sauti sbd Sam kwata kwata rayuwarsa bai Saba da a nuna Masa kulawaba musamman daga gareta shiyasa yaji abin wani irin har baisan Yaya zai amsa Mata dinba Bayan da qananan kalmomi.


Kallon anty salamatu data kawo Masa drinks yayi tareda Dan girgiza Kai Yana cewa''


No thank you bana buqatan komai am ok.


Maida kallonsa yayi Kan umme cikin nutsuwa batareda ya kalli Amatu ba yace"


Umme Dr Fatima tayi bayanin komai dangane da yanayin da ita take ciki wanda yakamata asan asalin menene yasa takasa kwantar da hankalinta kodan sbd lafiyan Abinda yake tareda ita,

Meyasa bazaku fada Mata ta kwantar da hankalinta ba sbd high BP dinnan is a very serious issue and I can't.....sai yayi shiru yakasa qarasa fada ya 'dan kalli gefenta kadan tareda maida kallonsa Kan Dr Fatima yace"


Please make her understand illolin BP game ciki please.


Kallonsa Dr Fatima tayi kafin tajuyo ta kalli Amatun datake mamakin yanda Ashe dama Yana Magana haka sosai saidai maganar tasa tafi Kama da kamar ransa A 'dan bace yake.


Cikin damuwa ma umme itama tace"


Hakane kam Amatu Dan Allah ki cire damuwar idanma damuwar tsoron haihuwar kika saka aranki ki cire Zaki haihu lfy munanan munata Miki addua.


Idanuwanta be suka ciko da hawaye har suka Fara gangarowa Wanda yasa kowa zuba Mata idanuwansa cikin mamaki da damuwa,


Dr Fatima ce ta Kama hannunta tajata  daki tareda ce musu karsu damu zata Magana da Amatun zataji matsalarta.


Daki suka Shiga tareda rufo qofa suka bar su ummen zaune tsit cikin tsumayi.


Kiran wayarsa akayi ya miqe ya fice a natse tareda daukar wayar Yana Magana kamar bayason Yi ya nufi hanyar sashensu.


Kallon Amatu Dr Fatima tayi cikin nutsuwa da kulawa tace"


Amatu karki damu ni likitarki ce duk Abinda na tambaya kada kiji komai karki boye ki fadamin sbd lafiyanki da abindake cikinki mukeso Kuma kema nasan bazaki so komai yasameku ba, kinada matsalar da kikeji ne dangane da cikin?

Kokuma a jikinki?


Numfashi ta sauke tareda sauke kallonta daga Dr Fatima din ta bude bakinta dayayi nauyi tace"


Dr Fatima kaina ne ke tsananin ciwo sai Kuma kamar na daina Jin motsin cikin tun jiya.....


Kallonta Dr Fatima tayi da sauri cikin 'yar razana amm zamtowarta likita saita saki murmushi cikin kulawa da kwantarwa da Amatun hankali tace"


Jiya tun yaushe ne bakiji motsin ba?


Tun da yamma danaji bansake ji ba.


Sake wani murmushin me sauti tayi tareda dafa hannun Amatun tace"


Kinga wannan ba wani matsalane babba ba zamu duba mugani inshallah baby lafiyansa kalau 

Bayan wannan menene Kuma matsalar?


Dagowa tayi ta kalleta kafin tayi qasa da Ido cikin damuwa tace"


Ciwon Mara saikuma gashi dazu Naga jini kadan kadan kaman Yana zuwa.


Kama ne kokuma kingani din?


Nagani""tafada Kai tsaye tana bayyanarda damuwarta.


Ok Amatu kinaji karki damu sosai Dan akan wannan insha Allah yanzu zanje dake asibiti zandubaki acan sbd Kinga gskia lokacin haihuwarki bai Isa yiba ana haihuwane at 36weeks zuwa 40weeks harma fiye amma ke Kinga yanzu kina cikin 33weeks atleast Koda za'ayi haihuwar gaggawa ne Kikai ko 35weeks haka so yanxu zanje dake asibiti zamu duba matsalar mugani Amma kema saikin taimaka kin rage damuwar komai aranki sbd Kinga damuwace tasaka BP dinki rising and hawan BP Kuma na iya leading to komai so please Amatu kicire damuwa inshallah komai zaizo yanda ake so ake Kuma fata kinji ko??


Ajiyar zuciya ta sauke ahankali kafin ta daga Kai tana cewa Inshallah Dr.


Dr Fatima ce kawai ta fito tabaro Amatun cikin daki dan tashirya tafito su tafi.


Zama Dr Fatima tayi ta fuskanci umme data zuba Mata Ido tana tsumayin jiran Abinda zata fada musu  

ta Dan sauke numfashi cikin yanayi na damuwa kadan tace"


Gskia akwai matsala dangane da yanda tace batajin motsin cikin gakuma zuban jini datace Dan haka inaga asibiti zamu Bata gado ta kwanta mufara monitoring BP dinta da lafiyar babyn har musamu takai lokacin haihuwar saidaima bazance ga komaiba yanzu sainaje asibiti munyi scanning munkuma dubata mungani musan meye abinyi.


Ajiyar zuciya umme ta sauke jiki a mace yace"


To Allah yasa miji alkhairi

Min barwa Allah komai 

Allah yayi Mana jagora.


Amin anty salamatu da Dr Fatima sukace Suma jiki amace.


Dr Fatima ce ta miqe tafara ficewa tana latsa Kiran MD Dan sanar Masa halinda ake ciki.


Cikin doguwar rigar jikinta ta fito sai dogon hijabin data sanyo.


Fitowa sukayi umme na riqeda hannunta sbd qafafuwanta dasuka kumbura sosai daqyar take takasu ga mararta datai nauyi tana Mata ciwo.


Baqar JUGUAR RANGE ROVER suka tarar pake a bakin qofar palon akunne sai qyalli take tana aiki duk da Basa ganin Wanda ke ciki kowannensu Saida ya ayyana MAHMOUD ZABEERA ne sbd shikadaine ke dukan irin wainnan motacin a zabeera duk da kowa na dukan kalar nasa arzikin.


Shine da kansa yake tuqa motar 

Umme ta bude baya Amatun tashiga ahankali Yana kallonsu ta mirror kafin anty salamatu tashiga

Umme tace suje zataje ta shirya zatazo daga baya.


Jan motar yayi suka wuce Yana tuqin ahankali kamar Wanda ya dauko me naquda.


Koda suka Isa Dr Fatima ta shirya komai Nan take aka karbeta akai nufi labour room da ita Dan acan zasu dubata suyi Mata scanning.


Anty salamatu ana Shiga da Amatun ta daga waya takira kawu tafada Masa tana kashewa saiga Kiran iyami cewa gatanan zuwa.


Tashin farko suna Gama dube dubensu suka gano ruwan dake riqeda babyn saura kadan su Gama tsiyayewa gashi lokaci baiyiba Dan ko kadan Bata Fara budewar haihuwa ba suna saka ran saidai CS gashi Kuma lokaci baiyiba da saura Dan haka mun yanke zamu riqeta anan muna kulawa da lafiyarsu har zuwa Nanda sati biyu tashiga 35to 36weeks sai ayi aikin saidai gskia babyn zaizo ba qwari muna fatan yazamto rashin qwarin kawai sbd irin hakan babies din yawanci na zuwa da matsaloli"""Dr Fatima ce take fadawa MAHMOUD ZABEERA hakan acikin office dinta bayan tabaro Amatun gurin nurses suna shifting dinta zuwa dakinda zasu ajiyeta.



Zanyi tafiya Nanda 5 days but Inshallah I will be back before time din yacika Just do the best you can atare matsalar.


Karka damu Mr zabeera Inshallah zaka dawo kasamu both the mother and the baby lfy.


Thank you"yace tareda miqewa Yana dorawa da cewa''


Stefan zaiyi clearing bills na komai zuwa anjima.


Kamar zaije dakin datake saikuma ya dakata tareda kallon qofar kawai ya wuce daidai isowar su iyami suka gaisa ya fice asibitin gabaki daya.



Da daddare iyami ce kawai ta kwana tareda ita anty salamatu ranar gidansu ta wuce dan dama tanada niyyar zuwa gidan yau yin wani Abu saiga zuwa asibiti ya kamasu.


Umme da Haj maryam ne suka Zo da daddare suka kawo musu abinci

Anty zarah ma tazo takawo wa Amatun furar datake so,

Gaba daya Kwanakin busy take da hidimar gidanta data MAHMOUD da yanzu ta dage sosai take farautar soyayya da kulawar mijinta Wanda Amatun ke sake zugata da Bata qwarin gwiwa Kuma alhmdlh tana samun ci gaba Dan ko last month tare sukaje UK sukaga wani likita Akan matsalar rashin haihuwar ta Wanda itace ta nuna tanason ganin likita cikin sauki kuwa ya amince Mata sukaje UK din daga can Sudan suka wuce Saida sukai kusan wata daya kafin suka dawo wanda tafiyar tasa tafara fuskantar asalin irin rayuwar da mijinta MD ZABEERA takeso wato rayuwar turai shida iyalinsa Wanda duk wayewarta ita Kuma takasa koyawa kanta sbd Sam ita saka qananun Kaya basa gabanta tafi ganin kyan kanta da burge kanta idan ta hade cikin kayanta na yarenta har gwara dogayen rigunan jallabiya taba sakawa sosai saigashi taga yanda yake rayuwa kamar asalin bature idan yabar qasarsa wato wasu irin personalities garesa boyayyu na burgewa ga wasu irin kyawawan manyan 'yan Mata masu aji dasuke huldar business dashi suna jansa da fira sosai Kuma ba laifi Yana 'dan sake musu shiyasa ta Raina kanta suna dawowa tafadawa Amatu damuwarta Wanda hakan ya sanyaya jikin Amatun itama saita Fara zugata akan ta zabure tafara duk Abinda tafara lurada yanaso tunda harta Fara samun C

Post a Comment

0 Comments