TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Babu so page 66

 *_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*

jimawa, Anaam dafe da kanta dake mata ciwo


saboda kukan da tasha ɗazun, ga jikinta har


yanzu sam baya mata daɗi irin na shiga


sabuwar rayuwar da ba'a saba ba. Aysha ce ta


amsa masa sallamarsa, ya ƙaraso ciki idonsa


akan Anaam. Ya miƙama Aysha dake masa


sannu ledar hanunsa.


 “Ita wannan lafiya kuwa?”.


“Kanta ne ke mata ciwo, nayi-nayi tasha


magani kuma taƙi”. Zaune yakai kusa da ita,


ya janye hanunta dake dafe da kanta. Kasa


kallonsa tai, dan haka kawai take jin wani irin


matsanancin kunyarsa. Shiko ya matuƙar


shagala ne a kallon kwalliyar dake zane akan


fuskarta, a kasalance yakai hannunsa kan


haɓarta ya ɗago fuskar da ƙyau, hakan sai ya


tilasta mata ɗago nata idanun dake cike da


ƙwalla ta kallesa. Ba ƙaramin jarumta yay


wajen jawo numfashinsa dake neman


kufcema ƙirjinsa ba, ya matsota jikinsa tare


da ɗaura hanunsa saman goshin nata.


 “Wannan idon naki kinyi kuka da shi, ko


muje asibiti ne?”.


Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Kanta ta


girgiza masa da ƙara lafewa a jikin nasa har


hakan ya so bashi mamaki. Dan yasan dai


koshi ya ringumeta turesa take kota janye


jikinta, amma yanzu ga saɓanin hakan yanagani, koda yake tunda abin nan ya faru ya


fahimci ta zama wata shiru-shiru, tsiwar taɗan


ragu kaɗan ko likimo ne, mata sunji maza


kenan. Fitowar Aysha ta sakata janye jikinta,


shima sai ya miƙe yana faɗin, “Bara na watsa


ruwa sai a samo miki magani”.


 Baki ta ɗan tura masa da kaiwa kwance. “Ni


basai nasha magani ba fa”. 


 Juyowa yay daga niyyar barin falon da yayi,


“Oh tunda hakane tashi na fasa barinki anan


ɗin”. 


 Dole badan taso ba ta miƙe, dan ya tsuke


fuska babu alamar wasa, duk da dama dai


tunda ya shigo babu fara'ar tattare da shi.


Aysha da tuni ta koma kitchen yay kira. Fitowa


tai da sauri tana amsawa. 


 “Gyaramin fruits ɗin nan”.


“To Yaya. Ko'a haɗa salad?”.


“Duk yanda kikai is ok”.


Kanta ta gyaɗa masa, shi kuma ya kama


hanun Anaam suka fice. Ta bisu da kallo


murmushi bayyane akan fuskarta. Tana fatan


ALLAH ya hana su Mommy raba wannan


auren har abada. Dan sun kasance abin


birgewa best couple ever matuƙa”.


 Koda suka iso sashen nasa a falon ya zauna,


ya riƙota saman cinyarsa ya zaunar. Yanzun


ma cikin mamaki yaga ta lafe a jikinsa. Ya ɗan


murmusa da shafar fuskarta idonunsa na binfuskarta dake ƙwaɓe alamar rashin jin daɗi


da kallo. 


 “Kodai har yanzu garden ɗin na zafinne?


Noorie!?”.


 Kanta ta sinne a ƙirjinsa da riƙo hanunsa


dake kaiwa jikinta, dan zuwa yanzu ta fahimci


mi yake kira garden ɗin. “Yaya Please ka


daina”.


 “No Aunty babu wannan zancen”.


Ya faɗa cikin kwaikwayon muryarta.


Murmushi ya kufce mata tare da ƙara cusa


kan nata cikin jikinsa. Dan yanda yay maganar


ya matuƙar bata dariya. Shima murmushi yay


da kaima wuyanta kisses. Tsoro ne ya kamata,


tai ƙoƙarin jan jikinta baya amma ya hana


hakan. 


 “Wayyo kaina zai fashe Yaya”.


Dakatawa yay daga ƙoƙarin cusa hanunsa


cikin rigarta. Ya riƙo kannata. “Ayya. Sorry,


sorry”. Sake langaɓewa tai kamar gaske. A


ƙasan ranta kuwa dariyace ke taso mata tana


dannewa. Da gaske kan nata na ciwo, amma


yanda takeyi ɗin yanzu harda pretending. Yin


hakan kuma shine mafita a gareta saboda


ganin yana neman sakin layi, itako a yanzu in


ba giyar wake tasha ba mizai kaita sallama


masa ya kasheta. Ai anyi kenan babu ƙari


tunda abun azaba kawai akesha a ciki. Ita jiya


tunaninta gaba ɗaya akan tayaya wasu matanke iskanci a cikin wannan wahalar? Ko kuwa


su basajin abinda taji da bazata taɓa


mantawaba har duniya ta tashi.


 Zaunar da ita yay a kujerar ya shiga bedroom


ɗinsa. Dai-dai nan Fadwa tai sallama. Anaam


tai kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa


ciki-ciki. Sam Fadwa bataji an amsa ba, sai dai


sanin halin mai sashen da kuma halin da suke


ciki na fushi da juna ya sata shigowa a ganinta


kobai amsa ɗin ba zata shigo. Turuss ta ɗanyi


na ganin Anaam, sukaima juna kallon cikin


ido kowacce ta janye da takaicin ƴar uwarta


da tsagwaron kishi.. Basuyima juna magana


ba, Fadwa ta nema waje ta zauna. 


 Fitowarsa ta saka Fadwa ɗaga kai tana


kallonsa, shima ita ɗin yake kallo da mamaki


a ƙasan zuciya, sai dai a fuska babu ko ɗigon


hakan sai ma janyewa da yay cikin halin ko'in


kula ya nufi Anaam dake kallonsu ta ƙasan


ido. Ita dai bata san sunada wata matsala ba a


gidan. Dan haka bata kawo komai a ranta ba


game da ɗaure-ɗauren fuskar tasu. A hanun


kujerar da take kwance ya zauna, 


 “Tashi kisha. Kimmaci abinci kuwa?”.


 Sai da ta ɗan saci kallon gefen Fadwa sannan


ta ɗan tura baki da narke fuska. “Ni banajin


ci”. 


 “Uhhm baƙya son ci, yarinyar nan ki ragetaɓaran nan naki, yanzu abincin ma sai kin


nuna masa hali? Yanzu dai kinga ba'a shan


magani sai da abinci, faɗamin mi zaki ci?”.


 Kallonsa ta ɗanyi da juya ƙwayoyin


idanunta, sai kuma ta narke fuska da girgiza


kai. “Da gaske bana son ci, barci nakeji kawai”.


 “Uhm-uhm fa, bana son zama da yunwa


sam! Ki dai sha ko fruits ɗin can ne idan Aysha


ta kawo. Zakisha ko?”. Ya ƙare maganar da


ranƙwafowa kanta yana sinsinar wuyanta. Ta


gefen ido ta saci kallon Fadwa, sai taga su


take kallo fuskarta ciɗin-ciɗin kamar zata


fashe har wani jajaja takeyi na alamar ɓacin


rai abunka da fari. Murmushi tai mai sanyi


dakai hannu ta shafi fuskar tasa a ranta tana


faɗin (Ashe kin san akwai ciwo ni kike yi masa


kiss a gabana, zan koya miki iya zaman


duniya). Hanunta da take neman janyewa ya


cafke da sauri yana maidashi akan tattausan


gashin kumatun nasa. “Kin yarda zaki sha?”.


 “Ni dai ɗan kaɗan”.


Ta faɗa a shagwaɓe.


Da ƙyar ya iya jan numfashi, dan shagwaɓar


tata ba ƙaramin susutashi take ba. “Good


girl”. 


 Murmushi tayi da janye hanun. Riƙeta yay, ta


marairaice masa. “Nifa fitsari zanyi”.


 “Okayy to ana buƙatar abokin rakkiya?”.Ta faɗa da zille masa tana ƴar dariya.


Bedroom ɗinsa ta nufa batare da ko sashen


Fadwa ta kallaba. Tana shiga ta zube a


gadonsa dan babu wani fitsari dama. Kawai


dai taba Fadwa space ne. Domin rama abinda


tai mata bashike nufin bazata mata adalci ba.


Kuma koba komai yanzu kawai ta nuna mata


cewar alwashinta tabbatacce ne akan mantar


da Yaya MM ita in har tana a tare da shi.


 


 Shiko daga can da kallo ya bita har saida ta


shige, a hankali ya haɗiye murmushi kan


fuskarsa. Miƙewa yay kamar zai bar falon.


Tasan idan tai wasa da wannan damar zatafi


haka shan wahala. Kamar yanda Mama


(Gwaggo halima) ta faɗa mata ba haka ake


buƙata ba, taje ta shirya dashi kodan


kasancewar gobe ne zata amshi girki, suna


buƙatar tai aiki da wasu fitinannun maganin


mata da aka kawo dominta tun daga ƙasar


sudan. 


 “Dan ALLAH kayi haƙuri” ta faɗa da sauri


tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da tun ɗazun


take son su zubo ko zata samu sassauci.


Ratseta yay zai wuce tai azamar riƙosa. Bai


juyoba amma ya dakata. Ta share hawayenta


hanunta riƙe da nasa. “Dan ALLAH kayi


haƙuri, nasan nayi kuskure. Amma wlhysharrin shaiɗanne”.


 Ransa a ɓace ya dubeta da wani mugun kallo


daya matuƙar neman gigitata. Saurin sakinsa


tai da girgiza masa kai. “Nasan nayi kuskure


amma dan ALLAH kayi haƙuri haka bazata


sake faruwa ba”.


 “Tashi kibar min falo”.


“Please Soulmate dan ALLAH”.


Sallamar Aysha ce ta sakashi haɗiye maganar


bakinsa, ya koma ya zauna da amsa mata.


Itama hawayenta ta shiga sharewa idonta na


satar kallon ƙofar bedroom ɗinsa, dan


zuciyarta raya mata take Anaam na wajen


laɓe tana saurarensu. Sosai takejin raɗaɗi da


ɗacin hakan, amma taci alwashi komi zai faru


a yanzu ɗin bashi ne Anaam ɗin zataci itama


zata rama.


 Aysha ta dire tray ɗin hanunta a gabansa,


fuskarta da murmushi ta gaida Fadwa da taƙi


kallonta saboda kar Aysha ta fahimci tayi


kuka. Kanta kawai ta jinjina mata. Ayshan


bata damu ba, dan tasan halin Fadwa wani


lokacin itama akwai yarfi. Hankalinta ta


maida akan Share!, “Yaya a zuba?”. Kai ya


girgiza mata alamar a'a, sai kawai tai musu


sallama ta fice a ranta tana ayyana akwai


matsala gaskiya, sai dai rashin ganin Anaam


yasa taji wani iri.


 Kusa da shi ta taso ta dawo, “Soulmate......Hannu ya ɗaga mata a fusace. “Fadwa! leave


me alone. Tashi ki fita”.


 Idanu ta tsura masa zuciyarta na mata


raɗaɗi, tasan a cikin fushi yake, kuma shi baya


son yanke ma mutum hukunci cikin fushi. Jiki


a saɓule ta tashi ta fice wasu hawaye masu


zafi da jin matuƙar tsanar Anaam na ƙaruwa a


ranta. Dan a ganin duk an mata hakane


saboda Anaam, ta kuma tabbatar ba haka


iyayen Anaam suka bar Share! ɗin ba kamar


yanda Mama ta sanar mata yanzun.


 Ya jima zaune a wajen zuciyarsa na masa


raɗaɗi da ƙuna, baya son ɓacin rai da


damuwa, yama rasa ina zai kama da halin


matan nasa. Ya samu ita Anaam ɗin ta sakko


ya fara samun kwanciyar hankali ita kuma


Fadwar na neman rikita masa lissafi. dole ne


ya musu sabon shiri na zama da kowacce da


halinta. Yasan duk abinda Anaam zatai tana


yinsane a karan kanta sannan bata da ɓoye-


ɓoye. Fadwa kam ya fahimci akwai zugar


mutane baibaye da ita, dan tun zuwan Anaam


gidan ya fahimci ta ajiye wasu halayenta na


zahiri ta aro waɗansu daban, idan bai tashi


tsaye a kanta ba zasu iya laɓewa a bayanta su


tarwatsa masa farin cikin gidansa, shi kuma


harga ALLAH yana sonta itama. Ya furzar da


numfashi mai ɗaci, tunawa da Anaam dakecikin bedroom ya sashi miƙewa ya nufi


bedroom ɗin. Da mamaki yake kallonta


kwance a gado har tayi barci, ya tsugunna


saitin fuskarta yana sakin murmushi da kai


hannu ya shafa kanta. “Dama fitsarin ƙarya ne


kenan?”.


 Idanu ta buɗe a hankali dan dama barcin


baiyi nisa ba, sai kuma ta maida zata lumshe


da ture masa hannu. Hannun nata ya riƙo


cikin nashi, fuskarsa gab da tata, “Tunda kin


tashi muje kisha fruit ɗin”.


 “Ni na ƙoshi barci nakeji Yaya”.


 “Ni kuma ban yarda ba idan kika sha sai kiyi


barcin”.


 “Uhhum-uhhum”. Ta faɗa tana noƙe


kafaɗarta. Miƙewa yay yana murmushi, ya


ɗagata gaba ɗayanta. Watsal-watsal ta farayi


da ƙafafunta. “Wayyo Yaya! Wayyo Yaya ni ka


saukeni na ƙoshi”.


 “Wayyo Aunty! Wayyo aunty ni bazan


saukeki ba sai kinsha”. Ya faɗa dai-dai suna


kaiwa falon.........




Post a Comment

0 Comments