*_ALLAH ka gafartama iyayenmu😭🙏🏻_*
jimawa, Anaam dafe da kanta dake mata ciwo
saboda kukan da tasha ɗazun, ga jikinta har
yanzu sam baya mata daɗi irin na shiga
sabuwar rayuwar da ba'a saba ba. Aysha ce ta
amsa masa sallamarsa, ya ƙaraso ciki idonsa
akan Anaam. Ya miƙama Aysha dake masa
sannu ledar hanunsa.
“Ita wannan lafiya kuwa?”.
“Kanta ne ke mata ciwo, nayi-nayi tasha
magani kuma taƙi”. Zaune yakai kusa da ita,
ya janye hanunta dake dafe da kanta. Kasa
kallonsa tai, dan haka kawai take jin wani irin
matsanancin kunyarsa. Shiko ya matuƙar
shagala ne a kallon kwalliyar dake zane akan
fuskarta, a kasalance yakai hannunsa kan
haɓarta ya ɗago fuskar da ƙyau, hakan sai ya
tilasta mata ɗago nata idanun dake cike da
ƙwalla ta kallesa. Ba ƙaramin jarumta yay
wajen jawo numfashinsa dake neman
kufcema ƙirjinsa ba, ya matsota jikinsa tare
da ɗaura hanunsa saman goshin nata.
“Wannan idon naki kinyi kuka da shi, ko
muje asibiti ne?”.
Ya faɗa a hankali cikin kunenta. Kanta ta
girgiza masa da ƙara lafewa a jikin nasa har
hakan ya so bashi mamaki. Dan yasan dai
koshi ya ringumeta turesa take kota janye
jikinta, amma yanzu ga saɓanin hakan yanagani, koda yake tunda abin nan ya faru ya
fahimci ta zama wata shiru-shiru, tsiwar taɗan
ragu kaɗan ko likimo ne, mata sunji maza
kenan. Fitowar Aysha ta sakata janye jikinta,
shima sai ya miƙe yana faɗin, “Bara na watsa
ruwa sai a samo miki magani”.
Baki ta ɗan tura masa da kaiwa kwance. “Ni
basai nasha magani ba fa”.
Juyowa yay daga niyyar barin falon da yayi,
“Oh tunda hakane tashi na fasa barinki anan
ɗin”.
Dole badan taso ba ta miƙe, dan ya tsuke
fuska babu alamar wasa, duk da dama dai
tunda ya shigo babu fara'ar tattare da shi.
Aysha da tuni ta koma kitchen yay kira. Fitowa
tai da sauri tana amsawa.
“Gyaramin fruits ɗin nan”.
“To Yaya. Ko'a haɗa salad?”.
“Duk yanda kikai is ok”.
Kanta ta gyaɗa masa, shi kuma ya kama
hanun Anaam suka fice. Ta bisu da kallo
murmushi bayyane akan fuskarta. Tana fatan
ALLAH ya hana su Mommy raba wannan
auren har abada. Dan sun kasance abin
birgewa best couple ever matuƙa”.
Koda suka iso sashen nasa a falon ya zauna,
ya riƙota saman cinyarsa ya zaunar. Yanzun
ma cikin mamaki yaga ta lafe a jikinsa. Ya ɗan
murmusa da shafar fuskarta idonunsa na binfuskarta dake ƙwaɓe alamar rashin jin daɗi
da kallo.
“Kodai har yanzu garden ɗin na zafinne?
Noorie!?”.
Kanta ta sinne a ƙirjinsa da riƙo hanunsa
dake kaiwa jikinta, dan zuwa yanzu ta fahimci
mi yake kira garden ɗin. “Yaya Please ka
daina”.
“No Aunty babu wannan zancen”.
Ya faɗa cikin kwaikwayon muryarta.
Murmushi ya kufce mata tare da ƙara cusa
kan nata cikin jikinsa. Dan yanda yay maganar
ya matuƙar bata dariya. Shima murmushi yay
da kaima wuyanta kisses. Tsoro ne ya kamata,
tai ƙoƙarin jan jikinta baya amma ya hana
hakan.
“Wayyo kaina zai fashe Yaya”.
Dakatawa yay daga ƙoƙarin cusa hanunsa
cikin rigarta. Ya riƙo kannata. “Ayya. Sorry,
sorry”. Sake langaɓewa tai kamar gaske. A
ƙasan ranta kuwa dariyace ke taso mata tana
dannewa. Da gaske kan nata na ciwo, amma
yanda takeyi ɗin yanzu harda pretending. Yin
hakan kuma shine mafita a gareta saboda
ganin yana neman sakin layi, itako a yanzu in
ba giyar wake tasha ba mizai kaita sallama
masa ya kasheta. Ai anyi kenan babu ƙari
tunda abun azaba kawai akesha a ciki. Ita jiya
tunaninta gaba ɗaya akan tayaya wasu matanke iskanci a cikin wannan wahalar? Ko kuwa
su basajin abinda taji da bazata taɓa
mantawaba har duniya ta tashi.
Zaunar da ita yay a kujerar ya shiga bedroom
ɗinsa. Dai-dai nan Fadwa tai sallama. Anaam
tai kamar bazata amsa ba sai kuma ta amsa
ciki-ciki. Sam Fadwa bataji an amsa ba, sai dai
sanin halin mai sashen da kuma halin da suke
ciki na fushi da juna ya sata shigowa a ganinta
kobai amsa ɗin ba zata shigo. Turuss ta ɗanyi
na ganin Anaam, sukaima juna kallon cikin
ido kowacce ta janye da takaicin ƴar uwarta
da tsagwaron kishi.. Basuyima juna magana
ba, Fadwa ta nema waje ta zauna.
Fitowarsa ta saka Fadwa ɗaga kai tana
kallonsa, shima ita ɗin yake kallo da mamaki
a ƙasan zuciya, sai dai a fuska babu ko ɗigon
hakan sai ma janyewa da yay cikin halin ko'in
kula ya nufi Anaam dake kallonsu ta ƙasan
ido. Ita dai bata san sunada wata matsala ba a
gidan. Dan haka bata kawo komai a ranta ba
game da ɗaure-ɗauren fuskar tasu. A hanun
kujerar da take kwance ya zauna,
“Tashi kisha. Kimmaci abinci kuwa?”.
Sai da ta ɗan saci kallon gefen Fadwa sannan
ta ɗan tura baki da narke fuska. “Ni banajin
ci”.
“Uhhm baƙya son ci, yarinyar nan ki ragetaɓaran nan naki, yanzu abincin ma sai kin
nuna masa hali? Yanzu dai kinga ba'a shan
magani sai da abinci, faɗamin mi zaki ci?”.
Kallonsa ta ɗanyi da juya ƙwayoyin
idanunta, sai kuma ta narke fuska da girgiza
kai. “Da gaske bana son ci, barci nakeji kawai”.
“Uhm-uhm fa, bana son zama da yunwa
sam! Ki dai sha ko fruits ɗin can ne idan Aysha
ta kawo. Zakisha ko?”. Ya ƙare maganar da
ranƙwafowa kanta yana sinsinar wuyanta. Ta
gefen ido ta saci kallon Fadwa, sai taga su
take kallo fuskarta ciɗin-ciɗin kamar zata
fashe har wani jajaja takeyi na alamar ɓacin
rai abunka da fari. Murmushi tai mai sanyi
dakai hannu ta shafi fuskar tasa a ranta tana
faɗin (Ashe kin san akwai ciwo ni kike yi masa
kiss a gabana, zan koya miki iya zaman
duniya). Hanunta da take neman janyewa ya
cafke da sauri yana maidashi akan tattausan
gashin kumatun nasa. “Kin yarda zaki sha?”.
“Ni dai ɗan kaɗan”.
Ta faɗa a shagwaɓe.
Da ƙyar ya iya jan numfashi, dan shagwaɓar
tata ba ƙaramin susutashi take ba. “Good
girl”.
Murmushi tayi da janye hanun. Riƙeta yay, ta
marairaice masa. “Nifa fitsari zanyi”.
“Okayy to ana buƙatar abokin rakkiya?”.Ta faɗa da zille masa tana ƴar dariya.
Bedroom ɗinsa ta nufa batare da ko sashen
Fadwa ta kallaba. Tana shiga ta zube a
gadonsa dan babu wani fitsari dama. Kawai
dai taba Fadwa space ne. Domin rama abinda
tai mata bashike nufin bazata mata adalci ba.
Kuma koba komai yanzu kawai ta nuna mata
cewar alwashinta tabbatacce ne akan mantar
da Yaya MM ita in har tana a tare da shi.
Shiko daga can da kallo ya bita har saida ta
shige, a hankali ya haɗiye murmushi kan
fuskarsa. Miƙewa yay kamar zai bar falon.
Tasan idan tai wasa da wannan damar zatafi
haka shan wahala. Kamar yanda Mama
(Gwaggo halima) ta faɗa mata ba haka ake
buƙata ba, taje ta shirya dashi kodan
kasancewar gobe ne zata amshi girki, suna
buƙatar tai aiki da wasu fitinannun maganin
mata da aka kawo dominta tun daga ƙasar
sudan.
“Dan ALLAH kayi haƙuri” ta faɗa da sauri
tana ƙoƙarin haɗiye hawayen da tun ɗazun
take son su zubo ko zata samu sassauci.
Ratseta yay zai wuce tai azamar riƙosa. Bai
juyoba amma ya dakata. Ta share hawayenta
hanunta riƙe da nasa. “Dan ALLAH kayi
haƙuri, nasan nayi kuskure. Amma wlhysharrin shaiɗanne”.
Ransa a ɓace ya dubeta da wani mugun kallo
daya matuƙar neman gigitata. Saurin sakinsa
tai da girgiza masa kai. “Nasan nayi kuskure
amma dan ALLAH kayi haƙuri haka bazata
sake faruwa ba”.
“Tashi kibar min falo”.
“Please Soulmate dan ALLAH”.
Sallamar Aysha ce ta sakashi haɗiye maganar
bakinsa, ya koma ya zauna da amsa mata.
Itama hawayenta ta shiga sharewa idonta na
satar kallon ƙofar bedroom ɗinsa, dan
zuciyarta raya mata take Anaam na wajen
laɓe tana saurarensu. Sosai takejin raɗaɗi da
ɗacin hakan, amma taci alwashi komi zai faru
a yanzu ɗin bashi ne Anaam ɗin zataci itama
zata rama.
Aysha ta dire tray ɗin hanunta a gabansa,
fuskarta da murmushi ta gaida Fadwa da taƙi
kallonta saboda kar Aysha ta fahimci tayi
kuka. Kanta kawai ta jinjina mata. Ayshan
bata damu ba, dan tasan halin Fadwa wani
lokacin itama akwai yarfi. Hankalinta ta
maida akan Share!, “Yaya a zuba?”. Kai ya
girgiza mata alamar a'a, sai kawai tai musu
sallama ta fice a ranta tana ayyana akwai
matsala gaskiya, sai dai rashin ganin Anaam
yasa taji wani iri.
Kusa da shi ta taso ta dawo, “Soulmate......Hannu ya ɗaga mata a fusace. “Fadwa! leave
me alone. Tashi ki fita”.
Idanu ta tsura masa zuciyarta na mata
raɗaɗi, tasan a cikin fushi yake, kuma shi baya
son yanke ma mutum hukunci cikin fushi. Jiki
a saɓule ta tashi ta fice wasu hawaye masu
zafi da jin matuƙar tsanar Anaam na ƙaruwa a
ranta. Dan a ganin duk an mata hakane
saboda Anaam, ta kuma tabbatar ba haka
iyayen Anaam suka bar Share! ɗin ba kamar
yanda Mama ta sanar mata yanzun.
Ya jima zaune a wajen zuciyarsa na masa
raɗaɗi da ƙuna, baya son ɓacin rai da
damuwa, yama rasa ina zai kama da halin
matan nasa. Ya samu ita Anaam ɗin ta sakko
ya fara samun kwanciyar hankali ita kuma
Fadwar na neman rikita masa lissafi. dole ne
ya musu sabon shiri na zama da kowacce da
halinta. Yasan duk abinda Anaam zatai tana
yinsane a karan kanta sannan bata da ɓoye-
ɓoye. Fadwa kam ya fahimci akwai zugar
mutane baibaye da ita, dan tun zuwan Anaam
gidan ya fahimci ta ajiye wasu halayenta na
zahiri ta aro waɗansu daban, idan bai tashi
tsaye a kanta ba zasu iya laɓewa a bayanta su
tarwatsa masa farin cikin gidansa, shi kuma
harga ALLAH yana sonta itama. Ya furzar da
numfashi mai ɗaci, tunawa da Anaam dakecikin bedroom ya sashi miƙewa ya nufi
bedroom ɗin. Da mamaki yake kallonta
kwance a gado har tayi barci, ya tsugunna
saitin fuskarta yana sakin murmushi da kai
hannu ya shafa kanta. “Dama fitsarin ƙarya ne
kenan?”.
Idanu ta buɗe a hankali dan dama barcin
baiyi nisa ba, sai kuma ta maida zata lumshe
da ture masa hannu. Hannun nata ya riƙo
cikin nashi, fuskarsa gab da tata, “Tunda kin
tashi muje kisha fruit ɗin”.
“Ni na ƙoshi barci nakeji Yaya”.
“Ni kuma ban yarda ba idan kika sha sai kiyi
barcin”.
“Uhhum-uhhum”. Ta faɗa tana noƙe
kafaɗarta. Miƙewa yay yana murmushi, ya
ɗagata gaba ɗayanta. Watsal-watsal ta farayi
da ƙafafunta. “Wayyo Yaya! Wayyo Yaya ni ka
saukeni na ƙoshi”.
“Wayyo Aunty! Wayyo aunty ni bazan
saukeki ba sai kinsha”. Ya faɗa dai-dai suna
kaiwa falon.........
0 Comments