TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Makauniyar soyayyah 55-56

 *MAKAUNIYAR SOYAYYA*πŸ’πŸ’–πŸ’ž



🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀🀦🏽‍♀



*STORY & WRITTEN*



*BY*



*MARYAM AHMAD PAKI*





*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*




_Masoya wannan littafin, ina ganin comment d’in ku, ba abin da zan ce muku sai godiya_


_Ina tare daku har kullum_


_Na baku wannan shafin kyauta_🀝🏽




*Rabbana atinah fid duniya, hasanatan, wafil akhirati hasanatan, wa qinna azaban nar*.


*Rabbana alaika tawakkalna, wa ilaika anabna, wa ilaikal masir*





*QUESTION OF THE DAY*


_Wane gida ne Mafi raunin gida da aka ambata a cikin Alkur'ani mai girma?_



 


55&56


Bayan ya raka Mus’ab gurin mota ne ya koma cikin gida ya wuce side d’in Momi.


Guri ya nema ya zauna yana ba ta labarin tafiyar da suka yi garin Adamawa da irin nasarorin da suka samu, sannan yaci gaba da ba ta labarin course d’in da aka tura su k’asar Uganda.


Murmushi kawai Momi ke yi jin ci gaban da d’an ta yake samu, tana alfahari da hakan.


Kallon shi tayi tace "Alhamdulillah Faruk, kullum ina maka addu’ar Allah ya kare min kai, ya baka nasara a aikin ka, ina rok’on Allah ya ci gaba da tallafa maka a al’amuran ka".


Cikin jin dad’in addu’ar da Momi ta mishi yace "Amin Momi".


Ci gaba tayi da cewa "Bayan nan sai maganar mu ta gaba shine maganar da muka yi kafin tafiyar ka, to yanzu ina son ka tsayar min da Magana, wace yarinya ce kake so, in kuma har yanzu ba da tsayayyar Magana da ita sai ni in za’ba maka, kasan wannan karan ba zan d’aga maka k’afa ba".


Wani irin yalwataccen murushi yayi sannan yace "Momi komai ya zo k’arshe tun da na dawo, ba kowace yarinya ce nake so ba illa Fatima".


Momi cikin rashin fahimta tace "Wace Fatiman kake magana".


"Fatiman gidan Abbu".



Shiru tayi kamar mai nazari sannan tace "Dama ka fad’a mata kana son ta ne ko sai bayan da ka dawo ne ka fad’a mata?".


"Tuntuni na fad’a mata, sai dai tace min in ba ta lokaci tayi tunani".


Cikin farin ciki Momi tace "Masha Allah, gaskiya naji dad’in wannan zancen, Allah ya za’ba mana mafi alkhairi".


"Amin ya Allah Momi" ya amsa mata.


Amma a ran Momi tana juya zancen ne a ranta cewa yarinyar dama yarinyar da  yake ta fad’ar yana so ita ce Fatima, amma zancen Dr Sadik da taji Anisa ta ce mata shi yake son ta fa, ko da yake mace da samari aka san ta, amma in haka ne mai zai sa Fatima ta tsaya sauraren Dr Sadik bayan tasan Faruk ne yake son ta? ganin ba za ta samo amsar ba yasa ta bar zancen a ranta.


A ‘bangaren Nana kuwa tun bayan gama wayar ta da Mus’ab da suka yi, tayi saving d’in number yaya Faruk a wayar ta.


Taso a ce sun gaisa da yaya Faruk, miskilancin ta ba zai ba ta damar yin hakan ba, duk da dai tace a gaishe shi, gaskiya tana yabawa da halin yaya Faruk.


Da daddare ta kunna data d’in ta, cikin sa’a tana chat d’in ta ga ya hau online.


Kamar ta share shi, amma wata zuciyar na umartar ta da ta mishi Magana.


Sallama ta tura mishi.


Sai da aka d’auki wasu ‘yan mintuna sannan ya turo mata reply da amsa sallamar.


"ka gane mai magana" abin da ta sake tura mishi kenan.


"No explain your self". Ya sake turo mata.


Ba ta ji dad’in haka ba, tana ganin ya kamata ace yayi saving d’in numban ta ko dan wataran.


"I by name Nana Khadija, a sister to Mus’ab".


Wannan karan bai d’au tsawon lokaci ba ya dawo mata da reply.


"Oh Nana, ya karatu? ya su Hajiya".


" Lfy lau, ya su Momi?


"Lfy lau, ki gaida Hajiya".


"Za taji"


"Gud night Khadija"


"Ok gud night yaya Faruk".


Suna gama wannan chat d’in yayi offline.


Ni kuwa tun san da yaya Faruk da abokin shi suka tafi, na dawo cikin falo d’in na nuna mata kud’in da abokin yaya Faruk ya ba ni, da kuma tsarabar da yaya Faruk ya basu, sannan na bud’e tawa tsarabar da ya min.


Gaskiya ko ni nasan yaya Faruk ba k’aramin kasha kud’i yayi ba, duba kalar kayayyakin da ya kawo min, ko ni a lokacin jiki na yayi sanyi da irin kasha kud’in da ya min, ko Ummu sai da ta jinjina tsarabar tana cewa yayi yawa, shi da ya tafi course zai tsaya kashe min wannan kud’in.


A lokaci d’aya kuma sai addu’a take yi ma yaya Faruk akan Allah ya bashi ladan zumuncin da yake yi da kyautata musu.


Ni dai ba ni da bakin Magana sai ma tattara kayan da nayi na tafi d’aki ina tunanin game d’in da za mu buga da yaya Faruk idan yazo gobe.


Lallai akwai badak’ala tsakani na dashi, koma mai zai je ya dawo, gwara ayi ta tak’are don hausawa na cewa "shure- shure ba ya hana mutuwa, kuma duk nisan jifa k’asa zai sakko".


Da wannan na samu k’arfin gwiwar ci gaba da harkoki na, ba tare da na bar fargabar da ke raina tayi tasiri a kaina ba.



Washe gari kamar yadda yaya Faruk yace zai dawo, hakan kuwa aka yi.


Ina zaune ina assignment naji rurin waya ta, ganin yaya Faruk ne na ji gaba na ya fad’i yau nake so na samar wa kaina mafita, amma na rasa me yasa nake jin kamar ban da wannan power d’in.


D’auka na yi muka gaisa.


"Ki same ni a gurin shak’atawa"

yana gama fad’ar haka ya katse wayar.


Tashi nayi na yafa veil a jiki na kasancewar rigar da nasa doguwar riga ne.


Yau cikin k’ananun kaya yayi, blue d’in T-shirt ne da bak’in jeans.


Sallama na mishi na samu guri na zauna.


Irin wannan kallon ya min da yake sa ni tsarguwa ya min, a lokaci d’aya yana sakar min sihirtaccen kallo.


Ganin kallon ba na k’are bane yasa na katse shi da cewa "yaya Faruk sannu da zuwa".


"yawwa Teemah".


Ci gaba yayi da cewa "Fatima kamar yadda kika ce in baki lokaci ki yi tunani, to na baki isasshhen lokacin da nasan ya isa kin zartar da hukunci game dani, ina kuma so ki fad’a min yadda kike ji na a zuciyar ki".


Yau ga dama na samu da zan fad’a ma yaya Faruk sirrin zuciya ta, sai dai abin takaici, zuciya ta na gargad’i na da kar in fad’a mai, gwara in bari da kanshi ya fahimci hakan.


"Amma anya in nayi haka na kyauta kuwa?".


Gaskiya ban kyauta ba, amma ina ganin wannan shine damar da zan samu in yi amfani da ita ba tare da ran kowa ya ‘baci ba.


Shawarar da na yanke shine in mishi tattausan lafazi, in yaso daga baya sai in fito in fad’a mishi.


"Yaya Faruk duk wanda yace yana son ka ya gama maka komai, ba abin da zan baka da zan saka maka da wannan Kalmar, kai d’an uwa na ne, ba yadda za ayi in k’i ka, ba abin da zance sai dai in ce Allah ya za’ba mana mafi alkhairi"



Hak’ik’a yaji dad’in wannan lafazin nawa, sai dai yaso ace na fito na fad’a mai cewa ina son shi, amma ya na ganin ko kunya ce ta hana ni fad’ar hakan, yasan da sannu zan fad’a mishi wannan Kalmar.


"Na gode Teemah, insha Allah zan ci gaba da son ki, fatana ke ma ki so ni kamar yadda nake son ki" yaya Faruk ya fad’a min cike da jin dad’i.


"Insha Allah" na bashi amsa a tak’aice.


Da haka yaci gaba da furtar min kalamen soyayya zafafa.


Bai d’au wani tsawon lokaci ba ya min sallama ya tafi da niyyar in an kwana biyu zai dawo.


Tun daga wannan lokacin yaya Faruk yaci gaba da nuna min so, sai dai ba na bashi k’ofar da kowa zai fahimci hakan.


 Bayan dawowar yaya Faruk daga gidan mu, ya samu Momi ya fad’a mata yadda suka yi dani, Momi ta ji dad’in haka, saboda a gaskiya tamu tazo d’aya da ita, tana d’auka ta kamar Anisa.


Daddy da ya dawo daga aiki Momi ke sanar dashi daddad’ar labarin game da yaya Faruk da ni.


Daddy yayi farin cikin jin wannan labarin, don haka Daddy yace zai samu Abbu suyi maganar dashi.



Da daddare yaya Faruk ne a falon Daddy, su na tattaunawa game da matsalolin da ake fuskanta a k’asar mu, da irin corruption da yayi yawa, fatan dai Allah ya daidaita komai.


Daddy ne ya canza hirar da cewa "Faruk, na ji kyakkyawan labari a gurin Momin ku, ta fad’a min Fatima ita ce yarinyar da kake so, gaskiya naji dad’in hakan, kaga ga kuma Anisa da Khalil, gaskiya wannan had’in yayi, sai dai muce Allah ya tabbatar da alkhairi, Insha Allah zan samu Ibrahim da maganar".


Lallai biri yayi kama da mutum, ya lura da kusancin da ke tsakanin Anisa da Khalil, yasan hakan za ta faru, ya ji dad’in haka saboda yasan Khalil kamilin mutum ne da ba shi da matsala, yayi murna da Anisa ta za’be shi a matsayin mijin aure.


"Daddy na gode, duk yadda kuka yi da Abbu d’in shi kenan, in na dawo sai a tsayar da Magana ko Daddy, plsss amma Daddy ba na so ya d’au time".


Dariya Dadi yayi yace "lallai Faruk kace da gaske kake son ‘yar tawa, kai da ake ta fama da kai akan maganar aure, kana kaucewa, yanzu da kan ka ke rok’on kar a ja time, to zan fad’a ma Abbun ka abin da kace, na fi so ne a had’a da na Anisa da Khalil, kaga service yake yi, na fi so sai mun samar mishi aiki, in hakan bai yiwu ba sai a fara naku".


Murmushi yaya Faruk yayi yace "Allah ya kaimu Daddy".


"Amin Faruk".


Haka suka ci gaba da hirar su, kana yaya Faruk ya ma Daddy sallama ya tafi side d’in shi.



Yau Daddy ne da Abbu a office d’in su dake Wagini motors suna tattaunawa game da bunk’asar da kamfanin yake samun ci gaba, da kuma irin nasarar da suke samu a harkar motocin su, sannan su ka gangaro yadda za su assasa kamfanin ya fi haka.


Daddy ne ya canza akalar hirar da cewa "Ashe d’anka duk wannan delay d’in da yake yi game da maganar aure, Fatima yake so".


"wace Fatiman?" Abbu ya tambaya.

"Fatima k’anwar shi".


Wani irin farin ciki ne ya kama Abbu, shi gani yake yi ma yafi kowa murnar da jin wannan labarin.


Yana son halin Faruk, yana d’aukar shi kamar d’an da ya haifa da cikin saboda yadda yake masa ladabi da biyayya.


Tabbas duk wanda ya samu suruki kamar Faruk yayi dace, don a wannan zamanin suna da wuyar samu.


Cike da farin ciki ya ce "gaskiya yaya naji dad’in wannan maganar, kuma ko b aka fad’a min ba, kai mai zartar da hukunci ne akan su, saboda haka duk yadda kayi daidai ne".


Dadi yaji dad’i yanda ya bar mishi wuk’a da nama, don haka yace mishi in yaya Faruk ya dawo daga Abuja za a tsayar da Magana.


Abbu na dawowa ya sanar da Ummu halin da ake ciki, ai tsakanin Ummu da Abbu, cikin su an rasa wanda yafi murnar da wannan zancen.


Ummu cewa take yi "Fatima ta samu miji na gari, wanda na dad’e ina mata addu’ar samun Kaman shi, Allah ya tabbatar mana da alkhairi ya kai mu lokacin".


Abbu kuwa amsawa yake yi da "Amin Aisha".


Kallon Ummu yayi yace "wani hanzari ba gudu ba Aisha, wannan Dr fa da yake zuwa gurin ta, har ta turo shi ya gaishe ni, shi kuma a me ta ajiye shi tun da tasan Faruk ke son ta".


Ummu ce tace "Alhaji a kira ta a a ji ta bakin  ta, ya kamata ta dakatar da wannan Dr d’in saboda yanzu maganar aure ce za ta shiga tsakanin ta da Faruk, in ban da ma wautar Auta, kana da wanda kuke soyayya sai kuma ka ci gaba da soyayya da wani.


Dariya Abbu yayi yace "Kin san ‘yan matan zamani, su suna ganin tsayawa da samari fiye da d’aya shine cinyewa, yanzu dai tun da shi wannan daman ba wai ya turo iyayen shi ba ne, sai a wa Fatima Magana ta bashi hak’uri don ban a son tara samari".


Abbu ne ya umarci Ummu da ta kira ni.


Samu na tayi ina kallon wani indian film mai suna "Kabhi alvidana kehna" Gaskiya film d’in akwai tausayi ga soyayya.


Ummu ce ta katse min kallon da cewa "Auta ana nan ana kallo ne".


Cikin shagwa’ba na ce "To ya zanyi Ummu, yaya Khalil ba ya nan bare muyi hira, film d’in ne zai d’auke min kewa, ina so ran weekend in tambayi Abbu zan je gidan su Anisa, daga nan sai mu je gidan su Anty Jidda da Aisha".


"Da ko kin yi zumunci".


Ummu ce taci gaba da cewa "Ki je Abbun ku na kiran ki".


"To Ummu" na amsa mata.


Bayan Ummu na bi muka shiga falon Abbu.


Kusa da Abbu naje na zauna a k’asar carpet.


"Sannu da hutawa Abbu, Ummu tace kana kira na".


"Yawwa Autan Ummu, ni nace Ummun ki ta kira min ke, saboda ina so muyi wata magana da ke akan wani labari da muka ji mai dad’i".


Shiru nayi ina sauraron jin Abbu yace labari mai dad’i za muyi Magana, wannan wane labari ne?


Abbu ne ya katse min tunanin da cewa "Fatima na ji dad’i dad’in labarin da na samu cewa Faruk shi yake son ki, hakan yasa nake alfahari da wannan familin namu, nasan Hajiyan mu in taji labarin nan za ta fi kowa da murnar haka, saboda haka ba abin da za mu ce sai dai Allah ya tabbatar mana da alkhairi, sai Magana ta gaba, game da wannan Dr da yake zuwa wajen ki, ina so ki fad’a mishi yanzu kina da wanda za ki aura, kin ga dam aba turo manyan shi yayi ba, in ban da wautar ki Auta, kin san kina da wanda kike so kuma ki ke tsayawa da wani, ban a son tara samari, yanzu in Faruk ya dawo za a tsayar da Magana".


Wani irin takaici ne ya tokare ni da naji na kasa bud’ar baki na in yi Magana, gashi ina so in fad’a ma Abbu cewa ni Dr Sadik ne za’bi na, sai dai nasan ban da damar fad’an hakan, baa bin da yafi ‘bata min rai sai jin cewa wai in yaya Faruk ya dawo za a tsayar da Magana, akan me yasa yaya Faruk zai sanar da su Abbu bai nemi shawara ta ba.


Abin da yasa ban fad’a mishi k’uduri na ba saboda ina son shawo kan matsalar ne a hankali, ashe ban san hakan zai jawo min matsala ba.


Abbu ne ya kalli Ummu yace "Aisha ko akwai abin da zaki ce".


"Ba abin da zance Alhaji, sai dai in ce Allah ya k’ara daidaita su, ke kuma Fatima ya kamata ki kula, ba yadda za ayi ki tauna taura biyu a lokaci guda, ki ba ma shi Dr Sadik d’in hak’uri, kar yaga kin yaudare shi, ki fito ki fad’a masa da wuri, ba ma kyau nema akan nema".


Duk wannan maganar da Ummu ke yi kamar tana k’ara sa zuciya ta na zafi, da ina da hali da na tashi na bar gurin ba tare da sun sallame ni ba, amma nasan hakan ba zai yiwu ba.


Abbu ne ya kalle ni yace "Fatima hakan ya miki ko, nasan in Faruk ya dawo lokacin kun yi exam, kin ga saura semester d’aya, sai a tsayar da bikin bayan kammala karatun ku".


Shiru nayi ban ce komai ba, don lokaci wani irin zugi nake ji zuciya ta na k’ara yi.


Ummu ce tayi dariya tace "Alhaji hakan ya mata tun da kaga tayi shiru, kasan yanzu auta ta girma".


Dariya dukkan su suka yi kana Abbu yace "za ki iya tafiya Fatima, Allah ya miki albarka".


"Amin Abbu"  na amsa a tak’aice.


Tun da na tashi na koma d’aki na, ko falo ban zauna naci gaba da kallon film d’in da nake yi ba, a lokacin ji nake yi komai ya fitar min a rai.


Ina shiga d’aki na fad’a kan gado ina zubar da hawaye mai d’aci.


Hawaye ne yaci gaba da zuba a ido na, ban damu da in goge ba saboda nasan ko na goge wasu ne za su ci gaba da zuba.


Me yasa sai yanzu da nake ganin na kusa samun nasara akan wannan lamarin, sai gashi wata badak’alar ta shigo, yaya Faruk ya wargaza min target d’ina, ba abin da yafi d’aga min hankali sai jin cewa in yaya ya koma aiki ya dawo za a tsayar da maganar bikin mu, kenan hakan na nufin rabuwar mu da Dr Sadik ya zo kenan.


Zuciya ta za ta iya hak’ura da Dr Sadik kuwa? "Ba za ta iya ba domin nayi nisa da son shi" zuciyata ta ba ni amsar hakan.


Ya kamata in bi komai a sannu dan ganin na samu abin da nake so ba tare da ran su Abbu ya ‘baci ba.


Fitowa in fad’a musu Dr Sadik nake so na nufin fuskantar hukunci daga kowane ‘bangare.


"Allah ka kawo min mafita cikin sauk’i, ba ni da inda za ni na nemi shawara don nasan ba mai goyon baya na, Allah kai nake rok’o ka kawo min komai cikin sauk’i".


Da wannan addu’ar na samu na tashi naje nayi sallar issha’i, ranar ko abincin dare ban tsaya na ci wani abun kirki ba.


Ko shi a yanzu ya rasa inda na sa gaba, duk hirar da zai min ban cika tsayawa ina bashi cikakkiyar amsar da ta dace ba, sai dai in bishi da eh ko a’ah, in ya tambaye ni me ke damu na sai dai in ce mai ba komai, ga abin da ke damuna a raina shine yadda na kasa fitowa in fad’a mishi ina da wanda nake so ko zai k’yale ni in huta, amma abin haushin na kasa. 


Yaya Faruk bai d’auki hakan da wata manufa ba, sai ma uzuri da ya min akan cewa yanayin d’an adam yana tsintar kanshi da rashin walwala.


Wannan time d’in yaya Faruk ya d’an dad’e a Kaduna, kusan 2 weeks yayi sannan ya koma Abuja.


Duk wannan abin da ya faru bai sa naji na rage son Dr Sadik ba, sai ma wani k’ara son shi da nake ji a zuciya ta, matsala ta dashi shine yadda yake kawo min uzurin bai samun zama ko lokaci, kamar akan shi aka fara aikin likita, ni kaina yanzu na rage zuwa asibiti gurin shi in muna free ba mu da lectures, a wani lokaci sweet word d’in shi ke wanke duk wani laifi da ya min.


Ko ya bani wani gift yanzu ba na nuna wa kasancewar na ga kowa a bayan yaya Faruk yake.


Na kasa fitowa in ce mai ya dena zuwa gidan mu in na tuno da danbarwar da muka yi dashi akan haka, dubara ce tazo min nace mun kusa exams, yanzu ban da wani time, mu dinga had’uwa shi a school kawai sai bayan exams.


Wannan lokacin bai min musu ba sai ma fatan alkhairi da ya min akan jarabawar da za mu fara.


Da haka na samu Sadik ya daina zuwa gidan mu, sai dai mu had’u a school, ko yazo department d’in mu, ko ni in shiga asibiti in bai da aiki.



Komawar yaya Faruk da kusan 3 weeks ne, Maryam ta haifo namiji.


Tun da aka yi haihuwar Nana ta tare a gidan, ko School ne sai dai ta tafi ta nan ta dawo.


Yaya Faruk ma yana shigowa ya d’auki yaro ayi hira dashi sannan ya tafi.


Ko wani sa’in in ya dawo daga aiki sai ya kira Nana ta kawo mishi yaron ya d’auke shi kafin ya tafi block d’in shi.


A wannan haihuwar Nana ta fara sakewa sosai da yaya Faruk duk da kasancewar su Miskilai, amma yanzu ba laifi suna hira.


Ran suna aka rad’a ma yaron sunan Dadin su Mus’ab wato Sa’id amma suna kiran shi da Asim.


Yaya Faruk siyayya yayi ta bajinta, kayan baby ya siyo masu yawa, sannan ya had’o da na mai jegon.


Mus’ab kuwa rasa bakin godiya yayi, sai jinjina halin Faruk yake yi na kyauta kamar bai san ciwon kud’i ba in ya tashi kyauta, fatan shi Allah ya k’ara dank’on amincin su da yaya Faruk, saboda yaya Faruk aboki ne na kwarai.


Yaya Khalil yana zuwa ya d’an yi kwanaki ya koma, ina kewar shi saboda shine abokin hira na.


Soyayyar su suke gudanarwa shi da Anisa cikin kwanciyar hankali ba sa tare da kowace matsala, su sun sami goyon baya ko ta ina, ni kuwa yanzu ba ni da damar yin haka.

Abin da ya bani mamaki shine yadda yaya Khalil bai min zancen yaya Faruk, hakan na nufin bai ji zancen ba ne, nasan yaya Khalil suna gaisawa da Sadik, amma in yaji kuma yaya Faruk yana so na, bayan shi zai bi, dama tuntuni yana bugar ciki na yaji ko akwai wata alak’a tsakani na da yaya Faruk in ace mai ba komai, ina ga yanzu in yaji zancen.


Dole na ja baki na nayi shiru ban mishi maganar ba.


Anisa ma ba ta min maganar ba, nasan cewa may be ba ta ji me ke wakana ba ne, nasan sai ta fi kowa zak’ewa akan maganar, in ba ta fi kowa ba, to ina jin ita ce a sawun gaba.


"Kin manta da Hajiyan Wagini ne?’ wata zuciyar tace min.


Nayi tuya na manta da albasa, Hajiyan Wagini ita ce ja gaba a ganin wannan auran ya gudana.


Kenan ba ni da tsimi ba ni da dubara, sai yadda Allah ya zartar da hukuncin shi 

a kaina.


Ko dai in fad’a ma Halima halin da nake ciki ne? ko kuma Aisha, duk wanda na fad’a ma wa a cikin su nasan za su bani shawara da kuma samar min mafita.


A ‘yan class d’in mu, akwai k’awaye da nayi basu wuce 3 ba, Akwai Fauziyya, Salma sai Halima, duk a cikin su mun fi shak’uwa da Halima, shi yasa na yanke shawarar fad’a mata halin da nake ciki tun da itama in tana cikin matsala tana neman shawara ta.


Da wannan shawarar nayi amfani bayan mun fito lectures muka samu guri muka zauna.


Halima ce ta kalle ni cikin kulawa tace "Fatima ya aka yi ne, nag a kamar ki na cikin damuwa".


Wata nannauyar ajiyar zuciya na sauke sannan nace "Ke dai bari Halima, ina cikin damuwa".


"Me yake damun ki" Halima ta tambaye ni.


Nan na zayyane mata duk abin da yake faruwa, har kawo yanzu da ake maganar in yaya Faruk ya dawo za ayi fixing d’in date d’in bikin mu.



"Gakiya kina cikin rikici kuwa Fatima, ni dai a ‘bangare na ina goyon bayan ki, gwara ki auri wanda kike so, da a zo kuma ayi aure abu yak’i dad’i, mutane bas a gane halin da mutum yake ciki in ya fad’a tarkon soyayya, sai a dinga ganin laifin ka akan cewa kai ka d’aura ma kan ka, bayan ita soyayyar ba ta shawara da kai a lokacin da za ta shiga, ni dai shawarar da zan baki shine ki fito ki fad’a ma shi yaya Faruk d’in abin da yake ran ki, sannan ki samu su Abbu ki musu bayani, nasan za su fahimce ki, kuma shima yaya Faruk d’in in har son gaske yake miki ai zai so ki samu farin cikin ki, shi kuma ya fawwala ma Allah lamuran sa, sai ki ga Allah ya masa za’bi nagari".


Sai a yau na samu wacce ta goyi baya na akan wannan maganar, hakan yasa na ji dad’in fad’a ma Halima da nayi, ko ba komai yanzu na samu mai bani shawara da share min hawaye na.


Cikin murna da shawarar ta nace "Na gode Halima da wannan shawarar da kika bani, insha Allahu zan yi amfani da ita".


"Ba komai Fatima, amfanin zaman taren kenan da kuma aminci".


Ci gaba nayi da cewa "Kin san me? ban san ta yadda za ayi in je in fad’a ma su Abbu wai Sadik nake so ba, nasan wannan maganar da zan fad’a mishi zai iya sa wa yayi fushi dani shi da Ummu, za kuma su iya d’aukar mummnar mataki a kaina".


"Ki bi komai a sannu ne Fatima, a hankali sai ki fad’a musu, nasan da yardar Allah za su yarda da za’bin ki".


Haka muka zauna a gurin Halima na ci gaba da ba ni shawarwari.


Sai da muka ga time d’in komawa class yayi sannan muka koma class.


Lokaci na ta tafiya, sai gashi har mun fara rubuta exam.

Kamar yadda muke jarabawar zango na d’aya a ND 2, sai ya zamana mun fi shan wuya akan sauran jarabawar.


Fatan dai Allah ya taimake mu ya kuma ba mu sa’a a jarabawar mu.


Bayan gama jarabawar mu naso muje Wagini mu d’an yi kwanaki tun da ba wani hutu mai yawa aka bamu ba, amma da na tuno da yanzu Hajiyan Wagini tasan abin da ke tsakani na da yaya Faruk, nasan idan na je matsa min za tayi akan maganar, shi yasa na hak’ura da zuwan.


Hutun zangon da aka bamu ba wani mai yawa bane, shi yasa nayi tunanin zuwa gidan su Anty Jidda in yi kwana biyu a can.


Yanzu ban cika son zuwa gidan su Anisa in kwana ba, saboda yanzu kulawar da Momi take ba ni tafi ta da, duk dama can tamu tazo d’aya, yanzu sai nake ji duk gidan ya fita kaina.


Duk zuwan da nake yi Momi ba ta kawo min zancen yaya Faruk, ko tayi hakan ne dan kar in dinga jin kunyar ta ina jin.


Ko a gidan yaya Aminu da na je yin kwana biyun, ban wani ji dad’in gidan ba saboda yadda yaya Aminu shi da Anty Jiddah suke zaunar dani sun aba ni shawarwari akan yaya Faruk, suna kuma k’ara jaddada min yadda yaya Faruk yake so na, bas u san duk wannan tunatarwar da suke min ba shi zai sa in canza k’udiri na, sai dai in ji su kawai, in da nake samun sauk’i ka ga dariya ta a gidan shine in su Humaira da Nabil muka had’u ina jan su da wasa, to nan za a ji magana ta.


A daddafe nayi kwana biyu na koma gida.


Mun koma zangon k’arshe a karatun mu, sai ya zamana duk wani hope namu yana kan wannan semester, tun da a shine muke sa ran final a karatun mu, don haka muka sake ba da himma dan ganin mun samu abun da muke so.


Ina kwance da yamma a gado na lumshe ido na kamar mai yin bacci, a zahiri kuwa tanini ne ya dabaibayi ganin har yau ban samo wa kaina mafita ba, gashi kuma banyi amfani da shawarar da Halima ta bani ba, da yanzu komai ya zo k’arshe.


K’arar sautin da ke tashi ne a waya ta na musamman da nasa a wayar yasa na gane Dr Sadik ne yake kira na.


D’auka nayi cikin shagwa’ba nace "Hello, My Prince Sadik".



"My Princess Zahra" shi ma ya fad’a.


Ci gaba yayi da cewa "gani a wajen gidan ku, ki fito ki same ni".


Duk da na ji dad’in zuwan shi sai da na ji fargaba, yanzu ban cika son yana zuwa ba tun da aka san me ke tsakani na da yaya Faruk, gashi Ummu da Abbu sun ja min kunne akan in dakatar dashi da zuwa, in fito in fad’a mishi yanzu ina da wanda zan aura.


Dr Sadik ne ya katse ni da cewa "Ki na ji na kuwa Zahra".


"Ina jin ka Dr, gani nan zuwa".


Jiki na duk ba laka na sa Hijab d’ina na fito, samun Ummu nayi a falo tana zaune.


Ganin Ummu a falo yasa na k’ara jin wata fargaba, duk da haka sai ban nuna hakan ba.


Ummu ce ta kalle ni da alamar tambaya tace "Fatima ina za ki na gan ki da Hijab a jikin ki".


Rasa abin da zance mata mayi.


"Ke fa nake tambaya Fatima" ta sake jefo min wata tambayar.


Cikin kame-kame nace "Dr ne yazo, shine zan je".


Tuni fuskar Ummu ta canza zuwa ‘bacin rai tace "Dama Fatima ba ki fad’a mishi yanzu ki na da wanda za ki aura ba, kin fi son ki dinga ‘ba ta mishi lokacin shi, to ba na son irin haka, in kin je ki fad’a mishi gaskiyar magana ki na ji na ko?".


"Zan fad’a mai Ummu" na fad’a da alamar rawar murya.


"Yawwa Auta ta, je ki tun da yana jiran ki".


Fita nayi amma duk ilahirin jiki na duk a mace yake, ganin tun a yanzu yadda Ummu ta fara min fad’a, ba abin da ke k’ara sakar min gwiwa in na ji ana maganar wai ina da wanda zan aura.


Da haka na k’arasa na bud’e k’ofa na fita, na nufi inda yayi parking a waje.


Bud’e min d’ayar k’ofar yayi alamar in shiga ta cikin motar shi.


Ba na so ya fahimci halin da nake ciki yasa na aro murmushi na yafa a fuskata.


Kallo na yayi yana sakin murmushi, a lokaci d’aya muna musanyar kallo ni dashi.


"Zahra ta, sai ki ganni unexpected ko".


"Na ji dad’i da ka min zuwan ba zatan, dan nayi missing d’in ka".


Murmushi yayi yaci gaba da cewa "Zahra ina ganin lokaci yayi da zan turo su Daddy na gurin su Abbu ko, ya kamat by now a ce akwai wata magana mai k’arfi a tsakanin mu, are my right" ya tsura min ido yana jiran amsa ta.


In akwai abin da nake jira, bai wuce a ce Sadik yace zai turo iyayen shi ba, sai gashi yau ya fad’a min amma ba ni da damar amincewa da hakan, tun da nasan abin da yake tafiya yanzu game da magana ta da yaya Faruk.


"Are you with me Zahra" Sadik ya fad’a ganin yadda na yi shiru.


Ajiyar zuciya na yi kana nace "gaskiya wannan shawara ce ka kawo, amma ina so ka d’an ba ni time, kaga ana so ne a had’a mu da yaya Khalil kuma yanzu service, idan ya dawo hutu sai in mishi magana a san yadda za ayi, sai in sanar dakai, ina hakan zai fi ko".


"Hakan ma yayi, bari in k’arasa gida in huta".


"Gaskiya kuna k’ok’ari, aikin likita ba hutu".



Dariya yayi yace "Haka za mu daure mu ci gaba da yi, Allah ne zai ba mu ladan".


"Allah ya taimaka"


"Amin".


Fito wa daga cikin motar nayi na jingina da window d’in motar.


"Ya aka yi ne Zahra".


"Ba komai Dr".


Cikin tsokana yace "Ko kar in tafi ne?".


"In da akwai hali sai in ce eh, amma ina so Sadik d’ina ya samu hutu, have a nice day".


"Thanks Zahra".


Sallama muka yi na bar jikin motar na nufi cikin gida, shi kuma Dr ya ja motar shi ya tafi.


A daidai wannan lokacin kuma yaya Faruk ne ya shigo da motar shi cikin layin.


Ganin ni ce na bar jikin motar yasa yayi tunanin waye a cikin motar na ke tare dashi, kau da wannan tunanin yayi ya k’araso gate d’in gidan mu.


Horn yayi mai gadi yazo ya bud’e mai ya shiga.


Sallama yayi ya shigo cikin falo d’in.


Saurin d’ago kaina nayi don jin muryar mai yin sallama da ban tsammaci zuwan shi a wannan lokacin.


Amsa mishi sallamar nayi ina mai sakin murmushin dole.


Zuwa yayi ya zauna a kusa dani yana murmushi yace "Teemah, I miss you a lot".


Maimakon in ba shi amsar da yake buk’ata, sai ma cewa nayi "Sannu da zuwa yaya Faruk".


"Yawwa Teemah, ina Ummu take?".


"Ta na ‘dakin ta".


"Ok".


Tashi nayi na d’akko mishi Table water da glass cup nazo na ajiye mai.


"Teemah yaushe za ki k’ara min Samosa da Spring roll".


A raina nace "Sai dai in maka dan darajar kai yaya na ne, kuma yanzu muna shiri, amma ba wai dan kana duba matsayin kai masoyi na ba ne".


"Ran da kake buk’ata sai in maka" na bashi amsa a tak’aice.


"Ok ran da nake so zan miki magana".


"Teemah wa na gani yanzu a mota kin dawo daga wurin shi" ya fad’a da zafin rai kamar ba shine ya gama min magana da sanyin murya.


Tsoro ne ya kama ni wanda in ka lura da ni sosai za ka iya gane hakan, amma sai na daure na ce "Oh wai Dr Sadik kake magana, a clinic d’in makarantar mu yake aiki, wani handout d’ina na manta dashi a office d’in shi, shine ya kawo min".


"Ya aka yi yasan gidan ku?"  ya sake jefo min wata tambayar.


Nasan in ba kare kaina nayi ba, zan iya ja ma kaina, don haka na shirya k’aryar da zanyi nace "Ai a bayan layin mu yake, rannan ne ya ganni na fito daga gidan mu, shine ya tsaya muka gaisa yake tambaya na dama a nan layin nake, na ce mishi nan ne gidan mu, yau da na manta hand out d’ina shine ya kawo min".


"Ya kamata ki kula, ina da kishi, ba na so wata mu’amala ta ci gaba da had’a ku in ba ta rashin lafiya ba da ya kama dole ki je in ba ki da lafiya, ki fad’a mishi ya daina zuwa gidan nan, dan ban ga amfanin haka ba".


Wani irin haushin yaya Faruk ne ya kama ni a lokacin, ya wani tasa ni ya na ba ni command kamar wani uba na, shi a ganin shi yanzu yana da matsayi biyu a gare ni da na matsayin yaya a gare ni da kuma wanda ake tunanin shi zan aura.


Ashe kuwa za muyi fito na fito dashi dan ban ga yadda zai ce in yanke huld’a ta ba da Dr.


Ko da yake bai san me ke tsakanin mu dashi ba, shi yasa yace haka, amma duk da haka saurin nuna ‘bacin rai ba nawa bane, da sannu zai fahimci Dr Sadik shine yake mulkar birnin zuciya ta.


Don haka cikin ladabi nace "Zan kiyaye yaya Faruk".


Murmushin jin dad’i ya saki sannan yace "that is my Teemah".


Ci gaba muka yi da hira amma ni duk zaman ya ishe ni, in na tuno yadda iyayen mu ke murna da wannan had’in sai in dinga jin raina yana ‘baci.


Mik’ewa yayi yace "Bari in je gun Ummu mu gaisa".


"Sai anjima yaya Faruk, nima d’aki zan shiga in yi karatu, akwai wani assignment da zan k’arasa".


"Sai mun yi waya kenan".


"Ok" na fad’a a tak’aice na tafi d’aki na.


Shiga gurin Ummu yayi suka gaisa kana ya fito ya tafi.


Yau kusan sati biyu kenan da zuwan yaya Faruk Kaduna, kasancewar ya fad’a min ya nemi hutu saboda yana so a gama komai akan maganar bikin mu dashi.


Gani nake wannan matsalar shi, koma hutun wata nawa zai d’auka wannan matsalar.

 

Yanzu had’uwar yaya Faruk da Dr Sadik kusan sau uku kenan, ban da wnada ya min gargad’i akan in yanke mu’amala dashi, tun yana tambaya ta ina mishi k’arya, har ta kai ya fara nuna min ‘bacin ran shi sosai.


Yau ma hakan ta kasance, muna tare da Sadik a k’ofar gidan mu kasancewar yanzu ba ya shigowa harabar cikin gidan mu, sai ga motar yaya Faruk ta shigo layin.


Wani irin tsoro ne ya kama ni da hakan ya nuna a fuska ta, nasan yau mai raba ni da yaya Faruk sai Allah.


Cikin kulawa yace "Zahra me ya faru ne, naga yanayin ki ya canza".


"Motar yaya Faruk ce na gani, kuma ya hana ni tsayawa zance".


Wani irin kallo ya min na tuhuma sannan yace "Akan wani dalili zai hana ki".


"Nima ban san dalilin shi nayin haka ba".


"In ba rami me ya kawo zancen rami, haka kawai ba zai ha na ki tsayawa da wani ba, dole yana da dalilin shi nayi hakan, ya kamata ki gano da dalilin yin haka, in kuma kin san dalilin shi nayin haka sai ki fad’a min".


Yanayin da ya min magana yasa nima na ji raina ya ‘baci dama ga kuma tsoron yaya Faruk da ya cika min rai, don haka nace "Ban gane me kake nufi da wannan maganganun n aka ba Sadik".


"Za ki gane ne in ki ka gano dalilin".


Ganin yadda Sadik yake fad’a min duk maganar da ya ga dama yasa nima na fita cikin motar ba tare da mun yi sallama ba, shi ma Sadik a lokacin ya ja motar shi ya tafi.


A lokacin kuma yaya Faruk ya ajiye motar shi a bakin gate ba tare da ya shigo da motar ciki ba.


Sauri nake in shiga cikin parlour saboda ba na so yaya Faruk ya tarad dani, dan nasan gamon mu dashi ba dad’i.


Takun tafiyar shi da na ji yasa na k’ara saurin tafiya ta, don ba na so ya tsare ni da tuhumar shi.


"Teemah!


Ya kira suna na da wata irin murya da ta razanar da ni.

Cak na tsaya da tafiyar da nake yi.








_Ni kaina 'yar mutan Paki zan so jin yadda za ta kaya tsakanin Teemah da Faruk_




Post a Comment

0 Comments