πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»
*GIMBIYA HAKIMA*
πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»πΈπ»
*πMANAZARTA*
*WRITERS ASSOCIATION* ππ️
*M. W. A*
```Kungiya d'aya tamkar da dubu. Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta ta kuma Nishad'antar da masoyan ta. π€π»```
________________________________
_STORY AND WRITING_ _BY_
_Jameelah jameey π_
*(Yar mutan kankiaπΈπ»)*
*BISSIMILLAHIR RAHMANIR RAHIM DASUNAN ALLAH ME RAHMA ME JINKAI*
_Wannan labarin kagaggen ne, duk wanda yazo daidai da rayuwarshi a kasi ne._
```NASADAUKAR DA WANNAN LITTAFIN GA FATIMA ABUBAKAR
BELLO, ALLAH YA BAR KAUNA YAR UWA RABIN JIKIππ```
71&72
Tunda Hakima ta tafi shashen Gimbiya Yakumbo nan suka zauna suka fara magana.
"Daughter kinga Hakim ko."?
"Eh naganshi Momy kuma yayi Allah dai ya albarkaci Aurenmu."
"Amin ya Allah, daman nasan kuna ganin juna zaka amince da juna saboda ba Ζaramin dacewa kukayi da juna ba."
"Gaskiya ne Momy, yana da hankali ga dukan alamu dan jiya kawai muka fara ganin juna amman naga hankali a taitare da shi."
*{kunji Hakima da wata sharaton wai jiya suka fara ganin juna π€£π€£}*
"Ai haka yake kuma gado yayi waje biyu daga uban har uwar, nidai Daughter dan Allah karki bamu kunya ku zauna lafiya keda wannan baiwan Allahn, Allah yayi maku albarka."
"Amin Momy, insha Allah ba zan baku kunya ba, "haka nike san ji ai ga wannan ya kawo da kudi dubu Ιari biyar."
"Wooow! Momy gaskiya nagode, amman ban ansar kudin nan sunyi man yawa ina da kudi sosai."
"Kinga a haka akayi ma kowace mace indai gidan sarauta ta fito sai uwar miji ta bada tukuncinta na fara zuwa neman aure kuma kw zakiyi amfani da komai da aka kawo wanan ne zaki nuna kin gode."
"To Momy nagode, na zan wuce na fara jin bacci, "to Daughter Allah ya kaimu, "Amin ya Allah."
Azima ta anshi kayan hannun Gimbiya Hakima sanann ta wuce dasu su kuma su Bilkisu suka take mata baya zuwa shashen ta, tunda Azima ta anshi kaya sai da ta kaisu kowane shashen dake cikin masarautar baki Ιaya sanann ta dawo wajen Gimbiya Hakima.
"Allah ya taimakeki, gaskiya Yarima Hakim yayi koΖari dan tunda nike ban taΙa ganin irin wanan kyautar ta ganin farko ba sai gunku."
"Uhmmm! Azima ku riba kuΙin ga duk wani bawa dake shashena sai kuyi hakuri ba yawa, sai ku fara shirin bikin kafin na baku abunda zaku bukata su kuma wanann super aura da wanann laces Ιin akai ma Ιikin fatan kinjini."?
"Allah ya taimakeki yanzun zani cika Umirninki, muna godiya Gimbiya Hakima Allah ya Ζara tsawancin kwana ya raba ki daga shirin maΖiya."
"Amin, ku wuce ku ban waje ina bukatar na huta, "to mun barki lafiya."
Haka suka tafi suna murna, ranar bayin shashen Gimbiya Hakima sunyi murna daman basu wuce su bakwai ba aiko sunsha kudi, Gimbiya Hakima ko tasha addu'oi kala-kala.
Bayan tafiyar su Lantana, Hakima online ta hau direct *JAMEEY NOVEL FAN* ta shiga nan suka fara comment da shirhi na novels Ιin Jameey dan suna gani koΖarinta wajen yanda take baje basira take Nishad'antar da masoyan ta, bayan sun gama sannan ta sauka online ta kwanta bacci.
*SOME DAYS LATTER*
Tunda Hakim yazo bai Ζara waiwayar Hakima ba itama bata damuba dan daman ita ba jiran wayarshi take ba balle zuwanshi, hidimar gabanta take balle biki yanzun saura sati Ιaya dilkar da halawar da ake yi mata sun ma isheta dan jike kamar ta kurma ihu da gyaran jikin da ake yi mata.
Gimbiya Yakumbo yanzun bata da lokacin zama dan gyara Hakima take ciki da waje, dan tace idan kana da kyau to ka Ζara da wanka shiyasa ta ko ina gyara Hakima take dan yanzun Hakima ta dawo shashenta da zama baki Ιaya.
Daga can bangaren kuma Gimbiya Yakumbo tsaye take tana ba Hakima maganin kariya daga shirin shidanu sannan kuma tana Ζara janjamata ta riΖe Allah dan shine gatan ko wani bawa.
Shiri suke ba kama hannun yaro, cikin lokaci Ζalilan Hakima ta koma kamar balarabiya dan baka gane ta sai tayi magana, maganar ma idan tayi sai ka kyaleta sosai zaka gane Gimbiya Hakima ce saboda ta chanza baki Ιayan ta.
_____________________________
*×ZARIA×*
Itama Gimbiya Fulani Kubrah ba abarta a baya ba dan ta zage tayi ma Gimbiya Hakima lefe nagani da buΙe, duk da Maimartaba Sarki Abdulmatalak ya bada kuΙi amman itama ta Ζara da kuΙinta banda kuΙin da Hakim shima ya bada, dubai taje itadasu Maryama suka haΙo ma Gimbiya Hakima Lefa set 42 akayi mata banda gana most go guda shidda ba abunda ke cikinta sai bags da dai sauransu.
Bata damu da fidda hannu da su Gimbiya Zulaha suka yi ba, daman tasan haka zai faru shiyasa taita hidimar gabanta badamu da abunda suke ba, ta ba banzaye ajiyarsu.
Su kuma su Gimbiya Kilishi bakin ciki kamar ya kashesu, ba kamar yanda sukaga iyayen lafe su duk a tunaninsu Maimartaba Sarki Abdulmatalak shi ya bada kuΙin duka akayi wanann lafe ga kuma sunga dubai akaje aka haΙo su hakan ya Ζara tun zuramasu zuciya.
Gimbiya Kilishi abun ya isheta kasa zaune tayi hakan yasa ta Ιauki hanyar shashen Gimbiya Zulaha hankali tashe dan batada wata kwanciyar hankali gani take dukiyar Maimartaba ce duka Gimbiya Fulani ta ansa taje tayi ma Hakim wanann Ζarya injisu ba.
"Gimbiya wai kina ganin abunda ke faruwa cikin masarautar nan."?
Hmmm! "Ina gani Kilishi, daman tuni nasan Abdulmatalak yana nuna mana banbanci tsakaninmu da Kubrah, yafi sonta a kanmu kuma asirine kawai tayi mashi shiyasa baya saurarar kowa sai ita."
"Ina wallahi bazai saΙuba budunga a ruwa, ya zama dole muma idan su Hamad suka tashi aure ayi masu fin abunda akayi ma wance gawar, suna wahalar banza basu san saura shekara Ιaya ya mutu ba."
"Ai ni harda haka yasa na kwantar da hankali na su gama wahalar banza saura shekara Ιaya ya mutu kinga komai suka saya Hamad za'aba shi duka harda ita matar dasuke rawar Ζafa a kanta."
"Aiko dai hakane kawai mu samasu ido suka gama haukansu wawaye kawai dasu, ai gobe ne zamu kai lefe ko."?
"Eh gobe ne, "ok muna jiran goben tayi zamu kai lefe yanda take bukata mudai musan karshen lefen namu ne."
"Ehmana, kedai bari Kilishi ni kawai sama Kubrah ido nayi tagama bikinta da dariyarta nan da shekara Ιaya kuka zatayi sannan tanaji tana gani za'a Ιaura Hamad mulki na maida ta baiwa ta bikin ciki zaiyi ajalinta."
Uhmmmm! Abunsa Kilishi tace kenan ta tafiyarta dan ita kaΙai tasan abunda zatayi ma Gimbiya Zulaha, nan da shekara Ιaya itama zatayi kuka karshe bikin ciki zaiyi ajalinta itama, dan gaban idonta za'a Ιaura Humad mulki, haka tai ta tunaninta daga karshe ta kama dariya dan gani take komai ya kusa zuwan mata karshe tana haka bacci ya kwasheta ba tare da tayi addu'a ba, to ina ma zatayi addu'a matar da ko sallah batayi.
*{yan uwa muslmai wallahi muji tsoran Allah ita wannan duniyar ba matabbata bace, duka nawa duniyar take da zakiyi ma Yar'uwarki hassada da bakin ciki bayan kunsan cewa hassada ga mai rabo takiceπ€π°, to maiye abun yi ma mutun hassada bayan Allahn da baya mutun shi zai baki idan kina da rabo wanda kike ma hassada karki manta bashi ya ba kanshi ba, Allah ya bashi dan haka nidai shawarace tawa sisters murage yi ma junanmu hassada kaima kayi addu'a Allah yabaka abunda zai zamaka Alkhari ka nema Alkharin Allah, Allah yasa mudace Amin}*
_By Jameelah Jameey✍π»_
0 Comments