ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»
TEAM----ZAFAFA BIYARπ₯ππ₯°π
ALLAH ka gafartama iyayenmuπππ».
[7/6, 9:39 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuΙi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haΖura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaΙa manaππ»_*.
No. 74
............“Dabarata ta jingina ciki ga Nu'aymah, da kawo hotonta ita da Yoohan shine burina Sooraj yay fushi yace sai Yoohan ya auri Nu'aymah. Ta hakanne kawai aurenta da Abdallah ko Naseer zai gagara. Duk da bana zargin Nasir da komai, amma inhar shi Nu'aymah zata aura tsugunne bata Ζareba kenan. Amma indai ta auri Yoohan inada yaΖinin zai bata kariya. Saboda alwashinsa na ranar da aka kirashi akan wannan batun ya birgeni. Ko bayan babu raina ina fatan ya zama garkuwa ga ahalin Firdausi. Sannan Nu'aymah ma zata samu lafiya ta dalilinsa tunda shine likitan da dama aka basu Number sa muka sace ni da Lurwan. Alhmdllh naci nasara, dan kuwa da bakinsa ya furta son auren Nu'aymah, duk da Sooraj bai bashi goyon bayaba a lokacin saboda jin nauyin Ζ΄an uwansa akan su Abdallah na tabbatar yanason bashi. Lurwan ya shiga ruΙanin ganin zai rasa dama ta biyu, hakan ne ya sakashi sake dawowa gareni mu haΙa kai a wannan karonma. Ya kuma bani haΖuri da tabbacin zaisa Abdallah ya maida aurensa da Adawiya da zarar anyi aurensa da Nu'aymah. Na nuna masa na amince dan na samu a gama maganar auren Nu'aymah da Yahya cikin kwanciyar hankali. Daga haka na cigaba da gayama ALLAH dan agareshi kawai nake hangen samuwar nasarar kubutar da Nu'aymah daga tarkon Lurwan. Hidimar aurar da Ζ΄aΖ΄a kawai nake a zahiri, a baΙini kuwa ba wannan bane a gabana sam, shiyyasa na samu Firdausi da shawarar duk yanda zatayi tayi kar Sooraj ya bama Abdallah ko Nasir Nu'aymah, gara a auramata Yahya bisa wasu dalilan dana lissafa mata a lokacin waΙanda Alhmdllh sunyi tasiri a gareta. Sai da ina shirin fitowane naga Sooraj tsaye bayanmu alamar yaji komai da muka tattauna kenan. Hakan yamun dadi, dan insha ALLAHU koba komai inada yaΖinin samun nasara”.
Ta share hakawayenta ga murmushi a fuskarta. Cigaba tai da faΙin,
Jin tabbatuwar Ιaura auren Nu'aymah da Yahya shine nasarata ta farko da kobayan nabar duniya inason Ζ΄aΖ΄ana su tuna suyi farin cikin aikin alkairi dana taΙa Ζullawa a rayuwata ta zaman gidan nan. Ko murnanr aurar da Ζ΄aΖ΄ana guda biyu a ranar banyi murnarsa da tsananin farin ciki ba kamar yanda nayi na Nu'aymah. Amma a baΙini nabar wannan nasarar tawa. A zahiri kuwa na shiga jerin masu shiga Ζololuwar tashin hankali kamar su Abdallah da Lurwan da rayuwarsu ke a gigice. Dan wlhy aranar da aka Ιaura wannan auren kaΙan ya hana zuciyar Lurwan bugawa a gidan nan. Ya kuma sake Ιaukar alwashi kala-kala akan koma ta halin ΖaΖa saiya samu cikar burinsa. Wannan furici nasane ya sakani saka Ζanwata bin Ζ΄an tawagar kai amarya. Sai da na tabbatar Nu'aymah ta shiga Ιakin mijinta lafiya ta hanyar ji daga gareta sannan hankalina ya kwanta. Duk da na tausayama yarinyar inda Ζaddara ta jefata. Amma sai nai mata fatan samun kariyar UBANGIJI da nasarar canjasu dalilin shigowar tata cikinsu. Daga haka na cigaba da Ιoyayyar jiyyar da mijinane kawai yasan inayi da duΖufa neman gafarar UBANGIJINA ko zan samu sassaucin raguwar zunubaina. Abinda yasa nabiku Austria ganin Nu'aymah saboda kozan samu na nema gafarartane. Ban saniba ko kafin ta dawo Ζasar ni na rasa raina. Ta Ιayan gefen kuma inason sakama Lurwan idone. dan a yanzu na daina sanin komai daga shirinsa saboda ya fahimci bana tare dasu a yanzu. Ko amincewa da zaman Adawiya da nai gidansa tanamin aikin sakamasa idone. Dan duk wani motsinsa itace ke kirana tana sanarmin batare da ita kanta tasan aiki takeminba dan ban fito fili na sanar mata manufataba”.
Wannan shine labarina, shine Ζaddarata, shine kuma son zuciyar SARAN ΖOYE dana aikata muku Firdausi, nasan bazaki taΙa yafeminba ke da zuri'arki, shiyyasama bazan matsaba wajen neman yafiyarku. Kai koma ke kin yafemin ALLAH bazai yafemin ba, dan nasan na cutar daku iya matuΖar gaya ta hanyar SARAN ΖOYE. na aminta ku kaini kowace irin kotu a yankemin hukuncin daya dace dani kafin naje na fuskanci babbar shari'ata ga babban alΖali”.
Ta Ζare maganar da fara tari mai tdanani. Sosai yanda take tarin guda gudan jini na faΙowa ya tada hankalin kowa a falon. Umm ta matsa gareta ta riΖeta sosai jikinta tana kuka. Da Ζyar aka samu tarin ya lafa. Duk da Yoohan najin zafinta har yanzu, dan shi baiji wani tausayin taba, duk da ΖoΖarin Ζulla aurensa da tai da Nu'aymah a Ζarshen Ιarnakun data tafka, amma sai ya bada shawarar a kwantar da ita zata samu sassauci daga yawan tarin. Da shawararsa akai amfani wajen kawo Ζaramar katifa aka kwantar da ita Ιin. Aiko sai tarin ya lafa sosai.
Murmushi tayi tana kallonsa, murya na rawa tace, “Nagode Yahya, ALLAH ya azurtaku da Ζ΄aΖ΄a nagari da zasuji Ζanku, ALLAH ya sauki Nu'aymah lafiya naga gudan jininku kafin nabar duniya”.
Uffan baiceba, baima nuna yaji mita faΙaba, amma jama'ar falon sun amsa mata da amin, duk da wasuma irin zuciyar Yoohan garesu basuji tausayin nataba.
Abban Abdallah da keji kamar ya tashi ya Ζarasa rayuwarta saboda zuciya data kumesa ya yunΖura zaiyi magana Hajjo ta dakatar da shi ta shanyar Ιaga masa hannu. Dole kuwa ya koma ya zauna yana zare idanu.
Tai gyaran murya sannan ta gyara Ζafarta mai ciwo da dubansu Ιaya bayan Ιaya ta fara faΙin, “Karma ka wahal da kanka wajen Ζaryata abinda duk Fauza ta faΙa Lurwanu. Idan bakai tunanin ana kallonku ba yau zan sanar maka cewar na jima da fahimtar kai da ita su wanene a cikinmu. Na barkune saboda na muku talalar zuwan wannan ranar. Na jima ina zargin akwai wani abu a zuciyar Lurwanu game da Ιan uwansa, dan yasha kawomin sukarsa akan miyasa kaza da kaza dole sai da umarnin Ιan malam akeyi a gidan nan?, sai dai ina nuna masa Ιacin rai. Amma ban sake tabbatarwa ba sai bayan tsaida ranar auren Abdullahi da Zainabu. Da kunnena naji dukkan abinda kuka tattauna akan soyayyar da Adawiya kema Abdullahi, tare da shirinku na bayan mutuwar Zainabu zai aureta. Hankalina ya tashi, dan zan iya cewa wannan shi e sanadin girmama samuwar hawan jini na ma. Na riΖe komai a raina na kasa faΙa har Ζ΄ar uwata tazo diba ni (Ananah) banso faΙa mataba. amma na fahimci dolene na samu shawara daga wani kafin lokaci ya Ζure. Dan wannan abune mai matuΖar sarΖaΖiya. haka na samu lokaci a wani dare mukai maganar. Itama hankalinta yayi Ζololuwar tashi dajin wnanan zance. Itace ta kawo shawarar ai tunda SARAN ΖOYE kukeyi muma yakamata mubi ta ZAGON ΖASA mu kamaku a hannu dumu-dumu. Itace ta kawo shawarar sace Zainabu ranar daren aurenta, dan hakanne kawai zai wargaza auren cikin sauΖi. A cikin shirinmu Ameer ya shigo rayuwar Zainabu matsayin abokin Abdullahi. Ameer kuwa abokin Naser ne, dan Naser shine mukaba aikin a hannunsa. Nice da kaina na shiga na haΙo kayan Zainabu a Ιakinta, na kuma jajjefa wasu ta taga. Ina cikin yi Yusrah ta shigo Ιakin da alama banΙaki zata shiga. Na tabbatar taga mutum, sai dai ban saniba kota gane waye ko bata ganeba. Abdullahi yaso lalata mana shiri a ranar saboda jan ra'ayin Zainabu da yay tayi akan suyi hira. Sai dai kuma ta dalilin Adawiya hirar batai tsaho ba. Naser ya samu damar Ιauke Zainabu ya kaita wani gida. Bamu dawo da itaba sai bayan sati biyu. Daga haka muka cigaba da bibiyar duk wani taku naku. Hatta da sace Number likitan da zaima Zainabu aiki naji a raina wani a cikinkune ya saceta, sai dai banida hujja shiyyasa nai shiru. Ina kan sani na amince da aurama Abdallah Adawiya saboda Ιana tarkon farko a gareku, inason kuma tabbatar da hannun Abdallah akan shirinku, kokuwa kuna amfani da shi ne kawai batare dashi kansa ya sani ba?. Na kuma hana Yusrah tarewa dan dama bazan yarda ta tare Ιinba. Tafiya da Zainabu Umrah yanada nasaba da son sake tabbatar da komai. Na kuma tabbatar Ιin. Waya da aka Ιagama Khadijah na hana Abdullahi zuwa Nigeria duk a cikin shirinmu ne. Munsa Nasiru ya dawo rayuwar Zainabu ne daman dan ya sake wargaza magar auren da Abdallah keta naci da son sake ganin ya Ζullu tsakaninsa da ita. Da kuma sanin da nai duk cikin shirinkune”..
“Maman Aaida data zama Ζawar Adawiya a saudia duk a cikin shirinmune itama. Mune muka sakata samun kusanci da Adawiya da Ιorata mataki-matakin kasancewa da Abdallah, a tunaninmu ko zaku dawo hayyacinku ku yarda da Ζaddara. Amma sai kuka sake tura kanku a cikin ramuka. A tarayyar maman Aaida da Adawiya ne ya bamu damar sake fahimtar bada sanin Abdallah kuke wani abunba. Dan ba komai kuke sanar masa akan shirinku ba, sannan lallai da gaske yana son Zainabu duk da ya raba hankalinsa biyu akan soyayyarta da dukiyar mahaifinta da kuka ΖwaΙaita masa a rai. Ta kuma hakane muka fahimci banzar sana'a da Abdallah yake ΖoΖarin jefa kansa a ciki. Amma Alhmdllh munyi ΖoΖarin maidosa hanya ta dalilin mijin maman Aaida Ιin, wanda ta hannunsa mukejin duk wani motsin Abdallah a yanzu haka. Maganar cikin Zainabu shine ya hautsina min tunani, saboda batare kukai aikinba yasa ban fahimci komaiba a ciki ba, duk da ina zargin kuΙinne duk da haka. Koda na tabbatar Zainabu takai mutuncinta gidan aure wannan ruΙanin na maganar ciki bai barniba sai yanzu da Fauza ta warware komai akan samuwar ciki da fitarsa. Na kai Uwaliya aiki Abuja ne dama dan Lurwanu yay yunΖurin yin amfani da ita kamar yanda Nasiru ya gano mana hanyar da sukebi wajen aamfani da Rabi itama. Na tabbatar alwashin da yahya ya Ιauka akan gano ko wanene bazai tashi a banzaba. Bakuma zai samu sauΖin ganowarba sai da wani a tsakani. Shiyyasa na tura Uwaliya ta fara sauka gidan Lurwanu ta kwana biyu sannan aka kaita wajen Zainabu. Ita kanta batasan amfani zamuyi da itaba, na Ιoyene saboda fahimtar idanunta a buΙe suke dasan kuΙu itama. Ko nawa Lurwanu ya bata lallai zata amince tai masa aikin daya buΖata akan Zainabu. Ankoyi sa'a shirinmu ya tafi dai-dai saboda Nasiru ma mutumne mai ΖwaΖwalwa da hikima. Hatta da yawan shigowa Najeriya da Abdallah ke yawan yi suna ganawa da Lurwanu duk mun sani dan duk inda yasa Ζafa Nasiru na biye da shi batare da yasani ba. Kai hatta binmu da Abdallah yayi Ζasar da akaima Zainabu aiki nasani. Dan ko a randa Yahya ya gansu suna magana shi da Lurwanu nima na gansu, sanin da nayi babu ta hanyar da zasu iya cutar da Zainabu saboda tsaron da take samu a wajen yasa na watsar da al'amarinsu. A yanzu haka mijin maman Aaida shine ya taso mana Ζeyar Abdallah zuwa Najeriya harya halarci wannan bikin duk da yazone a makare”.
Ta Ζare maganar da nuna inda Abdallah ke zaune kansa a duΖe tamkar munafuki. Harga ALLAH da yawan mutanen dake falonma sai yanzu sukasan da zamansa a falon. Hajjo ta sake gyara zamanta tana duban kowa.
“Nasan wasu zasuce miyasa duk nasan wannan amma na Ιoye matsayina na mahaifiya ga waΙan nan yara su duka?. Amsarku itace duk da ni mahaifiyace a garesu fitowa da lamarin kai tsaye dasa sabuwar fitinace da zatafi wadda muke ciki girmama. Dan inhar da tun a wancan lokacin na fiddo komai zasu kare kansu akan ba haka bane, su jefa zuciyarmu a ruΙani mu duka kokuma su canja salo, ko komai ya Ιaci duniya tasan halin da muke a ciki maΖiyanmu dake a waje su sami Ζofar yin kutse cikin wannan zuri'a su Ζarasa Ιarar da sauran abinda ya rage daga garemu. ΖyaΖyΖyawar rayuwar da aka gina tsahon shekaru zata wargatse ta lalace kowa ya fita a hayyacinsa. Idan hakan ta kasance banci riba ba. Sannan wahalar da malam ya sha akan son gina zuri'arsa baici riba ba kenan shima. Dukansu ni na haifesu, tun a Ζuruciya nasan halin kowannensu. Dama can Lurwanu hatsabibine tun yana ΖanΖaninsa, a cikin Ζ΄an uwan nan nasa babu wanda baisha wahalarsaba. Kaifin addu'a ne kawai ya ladabtar da shi, sai kuma kawaici da iya zama da su da Ιan uwansu yayi. Na yarda inhar ka samu ΖyaΖyΖyawar tushiya a cikin yabanyarka da izinin ALLAH zaka azurta da ΖyaΖyΖyawar albarka. Kasancewar Ιan malam Ιa nagari, mai haΖuri da kawaici, mai juriya da riΖe girmansa matsayin babba ga Ζ΄an uwansa shine ya taimaki wannan zuri'a da kaiwa haka batare da mutanen waje sunyi tunanin samun Ιarakar shigowa cikinmu su wargazamuba. ALLAH yayima Ιan malam baiwa da Ζyautar abubuwa da yawa. Ilimi, hankali, dattako, dukiya, sanin ya kamata, nasaba. Sai dai hakan ba yana nufin zai more rayuwarsa Ιari bisa Ιari ba tunda ya haΙa komai. Shiyyasa ALLAH ya jarabcesa da atsabibancin Lurwanu dana matar Ιan uwansa Mustapha. Suka dinga wajiga rayuwarsa saboda UBANGIJI ya gwada Ζarfin imaninsa. Koni da nake mahaifiya a garesa inajin sha'awar koyi da halayensa na haΖuri da juriya duk da zuciyarsa na Ζonuwa shi da matarsa da Ζ΄aΖ΄ansu. Wannan kawaicin da uziri shine ya kaimu ga matakin nasarar da a yau gashi su da sukecin dunduniyar sane a gabanmu suna faΙin tsiyatakun da suka aikata da bakinsu, miyafi wannan nasarar daΙi ga bawa kuwa?”.
Abban Adawiya ya share hawaye da fadin, “Babu inna, wlhy babu makamancin wannan nasara kuwa, dan hakan yana nuna mana duk mai haΖuri da tsayawa akan gaskiya, da adalci gana Ζasa da shi, ma'abocin bautar UBANGIJI, ALLAH bazai taΙa taΙar da shi ba, ALLAH bazai taΙa ΖasΖantar da shi ba. ALLAH bazai taΙa wulaΖanta rayuwarsa a hannun azzalumai ba. Ni shaidane akan hakan, dan Lurwan yaso jan ra'ayina sosai akan lamarin Yaya, kullum zancensa shine Yaya cutarmu yake a Ιoye. wai tayayama za'ai ace a raba mana gado tare, amma yazo ya fimu komai. Yafi kowa kaso mai tsoka a duka kamfanonin mu. Ga wasu harkoki da yakeyi kuma a gefe masu bala'in bashi kuΙi. Sannan kuma wai ai muduka munada ilimin addini amma tayaya za'ace kowa yafi sonsa da Ζaunarsa dajin maganarsa. Hatta mahaifiyarmu sai abinda Yaya yace takeyi a gidannan. Acewarsa wai Yaya ya asirce kowane kawai amma yake fakewa da malanta. Da farko na fara bin ra'ayinsa. Sai dai ba'ai nisaba ALLAH ya soni da rahamarsa ya fargar dani, danni dai ban taΙa ganin wani abu saΙanin Ζyautatawa ga yaya ba. Da kuΙinsa na gado ya tsaya mana mukai karatu duk da kuwa muma muna dasu. Da kuΙinsa na gado ya dinga mana hidimar rayuwa tamkar mahaifi. Idan mukai kuka shima sai kaga Ζwalla a idanunsa. Idan mukai ciwo shima sai kaga raΙaΙin a fuskarsa. Idan mukai dariya sai kuga tashi fuskar faΙaΙe da murmushi mai tsada. Shine ya nuna mana hanyar tashi mu nema na kanmu, dan shine ya fara shan wahalar kafa dukkan kasuwancin da ayanzu sune suke riΖe da duk wani motsinmu. Shine ya tsaya akanmu mukai karatu tuΖuri bayan ya tattare martabar mahaifinmu ya riΖe mana bai bada Ζofar da zamuyi sakacin da zata kufce mana ba. To miyasa son zuciya zaisa zamuyi sakaci ya sargafe tunaninmu?. Hakan yasani janye jikina daga wannan mummunar a Ζidar naita istigifari akan zargin da aka sakani nai masa babu gaira babu dalili. Ashe ya koma sun Ζulle da matata suna cutama yaya da zuri'arsa da basujiba basu ganiba. Minene laifin waΙan nan Ζananun yaran da basuma gama sanin rayuwarba balle daΙinta. Basai nace komaiba, dan Fauza azabarma da kike ciki ta isheki. kai ko Lurwanu ka jira naka sakamakon kaima, dan duk wanda yaci zalin gwani rabbi zai saka masa da alkairi a duniya ko a lahira”.
Abba Musbahu yace, “Tabbas haka zancenka yake Yaya Mustapha. Dan koni ma yaso jan ra'ayina. Sai dai fa ka sanni ni, a zuwan farko na shata masa layi duk da kasancewar sa yayana. Shine dalilin da yasa zama waje Ιaya a Lagos ya nema gagararmu sai da yabi ya lallaΙa yaya malam ta ΖarΖashin Ζasa aka maidasa Abuja aka buΙe masa company wanda ALLAH kaΙai yasan irin Ιarnar da yake a cikinsa shi da abokan aikin nasa. Domin a duk lissafin Ζarshen shekara idan mukayi sai mun tsamo yawan cuwa-cuwa da akai da kuΙaΙen company. Shi Yaya cayake daga ma'aikatanne. Niko nasan Yaya Rudwan ne dama wlhy. Nayi shiarune kawai dan ina fatan Yaya Malam ya kamashi da hannunsa dumu-dumu. To ashe aikin nasama ba anan ya tsayaba duk bala'in da ake kunnama Yaya malam da Ζ΄an Ζ΄aΖ΄ansa biyu da suka rage yanada hannu aciki. Wlhy ko alhakin Ζananun yaran nan bazai barku ku zauna lafiya ba balle kuma haΖΖin yaya malam da Umm-Muhammad da a kullum burinsu su Ζyautata rayuwar Ζ΄aΖ΄anmu a gidan nan. KaΙanma kuka fara gani yanzu kuma”.
Momyn Abdallah daketa kuka tun Ιazun tace, “Lallaikam yanzu suka fara gani Musbahu. Wannan wace irin cin amanace haka? Wane kalar son zuciya ce?. Ba yaya kaΙai kuka cutarba ai, muma kammu iyalanku kun cutar damu, kun shiga haΖΖinmu. Wace irin ni'ima ce ALLAH bai baku ba a rayuwa amma ku gaza gode masa har sai kun Ιaura Ιammarar shiga haΖΖin wani. Alhalin dukiyar da kukema zarin ma kunfi mai ita amfana da ita ku da iyalanku. Wai miyasa Ιan adam Ιin da ALLAH yayma ni'ima shike fin tsaurin idon rashin gode masa? ALLAH ya baku ilimi alhalin ga wasu can jahilai ko yanda zasu bauta masa basu saniba. Ya baku lafiya, ga wasu can a gadon asibiti kwance basu da kuΙin neman lafiyar. Ya baku muhallin zama. Ga wasu can suna raΙe-raΙe basu da ko kangon da zasu raΙa. Ya muku sutura. Ga wasu can tufafin da zasusa su rufe tsiraicinsu bai wadacesu ba. Ya baku mutunci da daraja a idon duniya, bayan akwai dubunku da suka fiku shekaru a ΖasΖance. Ya baku dukiyar da bama kuda iyalanku ba, waΙanda suka raΙu da ku zaku iya ciyar da mutum sama da Ιari a kowanne yini. Ga wasu can iyalansuma basa iya wadatawa. Ya azurtaku da Ζ΄aΖ΄a maza da mata, ga wasu can suna nema da miliyoyin kuΙaΙe basu samu ba. Ya azurtaku da iyaye na gari, bayan ga wasu can iyayen nasu a gidajen baΙala. Duk waΙan nan ni'imon kuka gagara godema ALLAH a kansu, to mikuke jira UBANGIJI ya muku kafin ku gode masan? Mi kuke nema kukuwa a duniya bayan duk waΙan nan tarin ni'imomin da yay muku. Bafa kunfi waΙanda basu da shi bane, ba kuma tsoronku yasa aka baku ba. Ba kuma ΖoΖarin ibadar kuce tasa aka baku ba. Kai jama'a kaicon hannu mai butilcin amsa ga mai bashi. Kaicon zuciya mai baΖin cikin cigaban mai Ζyautata mata, Kaiconku Rudwan, tabbas bazan yafe muku Ιoramin yaro akan mummunar aΖida da kukayiba........”
Kuka ya sarΖeta ta kasa cigaba da magana. Shi dai Abban Abdallah ya kasa koda ΖwaΖwaran motsi, kansa duΖe a Ζasa ya gagara kallon kowa. hakan yasa babu wanda zai iya cewa ga a yanayin da yake.
Baba malam ma dai kansa a Ζasa yake duΖe. Babu mai shaida yanayinsa. Umm kam ganin al'amarin take tamkar a mafarki zuwa anjima zata farka. Zuciyarta ta kasa gaskata komai akan Abban Abdallah da Fauza. Mutanen da sukafi kowa kusanci da su a gidan. Kai jama'a duniya ina zaki kaimu?.....
Jin kowa bai Ζara cewa komai ba yasa Jay yin gyaran murya. Kusan duk kallonsa sukayi. Ya furzar da numfashi na takaici da faΙin, “To inaga idan kun gama da su zamu kaisu station mu haΙa bayanansu sai mu miΖasu kotu su amshi hukunci kamar yanda shari'a ta tanadar”.
Tari Addah ta fara kaΙan-kaΙan, hakanne ya saka baba malam Ιagowa ya kalleta ya maida dubansa ga Jay. “Muhammad Jawaad mubar zancen zuwa kotu kaji. Ita wannan kuma miya rage mata a duniyarma gaba Ιaya. Ai wannan izayar da take ciki kawai ta isheta izina. Sai dai mu taimaketa mu miΖata asibiti kawai....”
Murmushi Jay yayi yana jinjina kai. “Duk da haka malam ai ya kamata su fuskanci shari'a kodan hakan ya zama ilimi ga Ζ΄an baya masu sha'awar sake aikatawa. Duk da tana cikin halin ciwo bashi ke nuna zata mutu ba, mutuwa ta ALLAH ce, takanzo a sanda taso ga wanda taso. Dan haka zamuje asibitin taga likita amma bisa ΖarΖashin kulawar hukuma. Shi ko zamu wuce da shi station”. Ya Ζare maganar yana nuna inda Abban Abdallah yake zaune.
Baba malam zai sake magana Hajjo ta katsesa da cewar, “Ζan malam hakan shine dai-dai kuma ya kamata. Kaga idanma da mai sha'awar aikatawa a nan gaba sai ya bada himma”.
Tarin Addah daya Ζara Ζarfine ya sakasu duk maida hankalinsu gareta. Da wannan damar Abban Abdallah ya samu ya sulale a hankali yabar sashen. Sauran jami'an dake a waje basusan yaya aka Ζareba shiyyasa basu hana Abban Abdallah bi ta gabansuba ya wuce sashensa yaje ya haΙa duk wasu abubuwa nasa masu muhimmanci ya zuba a Ζaramar jikka ya fito. A gaban jami'an ya shiga motarsa maigadi ya buΙe masa gate ya fita batare da shima yasan mike faruwa ba.
Daga ciki ma babu wanda ya farga da rashinsa sai bayan an fito da Addah daketa faman zuba aman jini aka saka a mota domin kaita asibiti. Suna wucewa su Jay suka koma kan Abban Abdallah sai yace ku Ιaukeni inda kuka ajiye. A take suka hau cigiyarsa a lungu da saΖo na gidan, sai daga baya sukeji daga bakin maigadi cewar ya fita a mota tun kusan mintuna talatin da suka shuΙe.
A razane Jay yace, “What?!!, shine kuka barsa saboda baku da hankali?!”. Yay maganar wa yaransa. Duk rawa jikinsu ya kamayi suka hau rantse-rantse su basusan mai laifi bane. Ai kota kansu Jay baibiba ya shiga motarsa shi da Bily da Little. Suma duk suka shiga a wacce sukazo. sai da suka tambayi maigadi motar daya fita a ciki da lambarta sannan suka fice a guje.
Wayar Jabeer Jay ya kira, yana Ιagawa ya ce, “Jabeer inason a baza zami'ai a kowacce hanyar fita garin kano domin tsaidamin mota mai Number..... Ruwan toka”.
Jabeer na amsa masa ya yanke kiran, C.P ya kira shima dan ya taimakesu.
__________★★
A gidan su Nu'aymah kam musalta muku halin da suke ciki Ιata lokacine. Dan motocin su Jay na fita a gidan Umm ta yanke jiki ta faΙi. Hakama Malam Ζarami shiΙe musu yayi. Ga kukan da su Adawiya keyi ya taru ya Ζara Ιaga musu hankali. Baba malam kansa dauriya kawai yakeyi dan gaba Ιaya jinsa yake kamar kansa zai tarwatse dan ciwo. Gashi su Yoohan sun wuce da Addah asibiti. Hakan yasa dole aka kwashi su Umm ma zuwa asibitin.
Ζangaren Abban Abdallah kam tunda ya fito anguwarsu kai tsaye hanyar Katsina ya Ιauka, shi kansa baisan mi yake shirin aikatawaba. Ceton kansa ko gudun kunya? Ko tsoro?. Gudu ya ke na hauka babu wasa a cikinsa. Musamman daya kasance ta gefe-gefen gari yake tafiyar, dan bai yarda yabi ta cikin gariba sam. Yana fara Ιaukar hanyar Ktn bayan ya gota Dawanau kaΙan ko mintuna goma baiyiba ya ga motar Ζ΄an sanda na binsa a baya. A take ya Ζara Ζarfin gudun motar tamkar ya manta da kasancewarsa Dattijo. Abu kamar a film suka fara rere tsakaninsa da jami'ai.
ALLAH sarki rayuwa, duk iyawarka baka isa zarce Ζaddarar UBANGIJI ba. Dan kuwa dai wannan Ζ΄ar tsere na Abban Abdallah da Ζ΄an sanda sunansa gudu akan igiyar Ζaddara. Dan kuwa bisa tsautsayi sukau taho mu gama da wata mota dake nufo cikin kano. A take waccan tayi gefen titi, shiko ta Abban Abdallah sai ta kife ta fara wuntsil-wuntsil daga titi ya gangara cikin gona. Tun suna jin yanda yake neman Ιaukin UBANGIJI har sukaji tsit, motar kuma ta bugi bishiyar dalbejiya ta tsaya cak.
Cikin sauri Ζ΄an sandan da dama tuni sun fito a mota suka nufi motar domin bashi taimako. Da Ζyar kuwa akayi kama-kamar Ιaga motar aka zarosa a ciki. Gaba Ιaya jikinsa yayi face-face da jini har ba'a iya gane inane ya bugu koma yanada rai ko ya mutu. Kasancewar sun kira sun sanar sai ogansu ya basu umarnin maza su Ιakkosa su dawo cikin kano asibiti. Bisa wannan umarnin ya sakasu Ιakkosa suka juyo a guje.
Kai tsaye babban asibiti suka nufa, cikin amincin ALLAH kuma akai sa'a can aka kai Addah da su Umm suma. Su baba Malam na tsaka da tashin hankalin abinda ya faru sabon labari akan haΙarin Abban Abdallah yazo musu. A take na gida dana asibitin suka sake harmutsewa.
A yanda Yoohan yaga al'amarin ya kasance sai da yaji nadamar shigewa gaba wajen wannan bankaΙe-bankaΙe. Sai gashi da idanunsa ya ga baba malam na rusar kuka. Nu'aymah kam ai sai allurar barci ya danna mata saboda yanda ta birkice kamar dai ΖwaΖwalwar ta bata gama dawowa dai-dai ba.
Lallai wannan ranace da waΙaΙan nan ahali bazasu taΙa mantawa da itaba a jerin tarihinsu. SauΖinsu ma har yanzu ainahin labarin bai fita kunnuwan jama'ar gariba. Sai dai kawai ana maganar Sheikh Rudwan Hashim jibiya yayi Accident a hanyarsa ta zuwa Ktn yanzu babu jimawa. A take mutane suka shiga jera masa addu'ar ALLAH ya tashi kafaΙa, musamman ma mabiyansa.
Zan iya ce muku yanda wannan ahali sukaga yinin wannan rana haka sukaga dare. Duk da kuwa Alhmdllh zuwa dare an tabbatar da Abban Abdallah bai rasuba. Ya dai samu karaya a kafaΙunsa duka biyu da kafafu. Sai manyan raunika da sukai masa kaca-kaca da jiki. Itako Addah barci suka sakata yi. Umm ma Alhmdllh ta farfaΙo ita da malam Ζarami. Hakama Nu'aymah ta farka.
Sai kusan tara na dare suka bar asibitin, ba kuma a barsu sunga Abban Abdallah ba dai. Yoohan da kansa ya fiddo Nu'aymah da ga Ιakin office Ιinsa daya sakata barci. Ananah ta taimaka mata suka Ζarasa shiga mota. Baba malam yaso su Yoohan su bisu can gidan su kwana amma suka bashi haΖuri akan zasu zauna anan asibitin ne. Badan yaso ba ya barsu.
Yoohan na ganin motocinsu sun gama wucewa ya sauke ajiyar zuciya mai kauri, A Ιaya daga kujerun dake a waje ya zauna hannayensa duka dafe da kansa. Sai yanzu komai ke dawo masa a ΖwaΖwalwa tamkar almara. Dan Ιazun su Addah na bayani ne little na fassara musu shi da Umar, duk da shi yana Ιan jin hausarma kaΙan-kaΙan yanzun.
Kusa da shi Umar yazo ya zauna shima yana sauke nasa ajiyar zuciyar. Yoohan bai motsaba balle ya kallesa. Shima sai bai damuba ya fara magana a hankali. “Haka mafi yawancin mutanen da suka samu Ιaukaka suke. Sai kaga na nesa da su na matuΖar sonsu da begen kasancewa da su. Amma waΙanda ke tare da su mafi yawancinsu ba son gaskiya suke musu ba. Ζaso Ιaya bisa uku a ciki zaka samu suna musu Ζauna ta tsakani da ALLAH. Kaso biyun kuwa sai kaga suna raΙe da sune bisa wannan Ιaukakar da ALLAH yay musu. A zahiri kuwa su zugasu da nunama duniya babu kamarsu, a baΙini sune masu musu SARAN ΖOYE. lallai waΙanan mutanen masu zagon Ζasa suna Ιaya daga cikin jarabawar masu mafi yawan Ιaukaka”.
Ajiyar zuciya Yoohan ya sake saukewa. Ya Ιago ya dubi Umar a karon farko, idanunsa sunyi jajur. Ga barci ga yunwa ga gajiya. Shi kansa Umar Ιin a galabaice ya ke. “Zancenka haka yake Umar, bazan Ιoye makaba al'amarin mutanen nan ya sake saka tsoro a zuciyata gaba Ιaya, nasake jin tsoron halin mutum da ayyukansa. Wannan wane irin bushewar zuciya ne haka? Su da ya kamata su zauna suyita godema ALLAH bisa ni'imar da yay musu ta rayuwa, su dinga ibada sai suka zama masu butulcewa ta hanyar cutar da wanda shi ya kusan Ζare tasa rayuwarne a Ζyautata tasu da ta Ζ΄aΖ΄ansu. Umar wai miyasa Ιan adam keda manta alkairi da yawan butulci ne?. Miyasa Ιan adam yafi yarda da biyayya wa huΙubar shaiΙan akan dokar ALLAH ne?. Miyasa Ιan adam yafi yarda ya zama mai samu bamai sadaukarwa ba? Miyasa mafi yawan mutane sunfi sha'awar cutar da wanda suka Ζyautata musu amma sunajin tsoron mai munanasu?. Ko addu'a mutum zaiyi, sai kaji yace ALLAH ka tsareni daga sharrin masu sharri. To miyasa bama addu'ar ALLAH ya karemu da aikata sharri ga masu Ζyautata mana ne?”.
“Wannan shine halin Ιan adam Ιin da ake faΙa Dude, munada son kanmu, duk kuma mutum mai son kasa zakaga shine kullum a cikin wahalar nema da faΙuwa. Dan bazai taΙa doguwar nasara ba. Daya samu take kufece masa. Amma saboda bushewar zuciya gobe ma sai ya koma sake neman sa'a. Kowane addini akwai na banza akwai na gari. Irin waΙan nan mutanen suke ja ana zagin addinin islama bayan shi kuma addinine mai koyar da Ζyawawan Ιabi'u. Ko shekara banyi da shiga musilinci ba, amma wlhy Yoohan na fahimci babu wani addini dake gogayya da shi akan koyar da ΖyaΖyΖyawar rayuwa. Komai musilinci ya haΙa. Amma ka duba su da keda ilimin sani a tsahon shekaru sunfi zaΙar su saΙama ALLAH bisa son zukatansu”.
Sosai zukatansu Yoohan suka Ζara rauni da wannan al'amari. Imani da tsoron ALLAH ya sake shigarsu a zuciya da Ιargo. Suma kansu dai a wannan dare sunyi barci ne kawai badan jin daΙi ba.
*_WASHE GARI_*
Washe gari aka bama su baba malam damar shiga su duba Abban Abdallah. A lallai duniya abin tsoro. Bawa daina cikama rayuwa baki kai ba komai bane. Duk damar da kaga ka samu a rayuwa da ga rahamar ALLAH ne. Amma wlhy idan yaso ko Ζyaftawar ido baka isa gittawa ba. A jiya iyanzu shine zaune tare da Ζ΄an uwa da iyalansa. Amma yau gashi babu ko Ζyan gani a fuska saboda tsabar jigata da rayuwarsa tayi. Ita kanta Addah jikin nata babu daΙi.
Duk wanda ya shiga duba Abban Abdallah sai kaga ya fito da kuka. Hakan yasa dama Yoohan bai bar Nu'aymah a wajenba. Suna zuwa ma ya jata wai tazo suje wajen awo. Bata fahimci wayo yake mataba ta bishi. Sai ya kaita office yasa aka kawo mata abinci. Duk da tace masa ta Ζoshi, dan basu fitoba sai da Umm ta bata abinci ya dage sai taci. Dole taci kaΙan dan ya barta. Sauran kuma ta bashi dan ta fahimci shima yana buΖatar a tsaresa yaci abincin.
Zuwa ranar dai dukan ahalin gidan sunsan halin da ake ciki, Ζ΄aΖ΄an Addah dake aure da Ζannen Abdallah ma duk sunzo. Ansha sabon kuka dai kam yau ma. Daga Ζarshe baba malam dake ta ΖoΖarin danne tasa damuwar yay musu nasiha da nuna musu muhimmancin Ζaddara. Ya tabbatar musu da cewar hakan jarabawane. Dan bazai yuwu dama a rayuwa a rayuwa babu jarabawa ba. Ya hana kowa kakkausan lafazi akan su Addah, dan kuwa shi a take ranar ya tabbatarma da kowa cewar ya yafe musu. Sai su cigaba da musu addu'ar ALLAH ya basu lafiya kawai.
Baba malam ya Ζara kima a idanun iyalan Addah da Abban Abdallah. Musamman ma Abdallah da har ran yakejin tsanar mahaifinsa da Addah. Sunso su gurΙata masa tunani ALLAH ya hana hakan. Dan bayan Addah ta Ιale a cikinsu Abbansa sake zaunar da shi yay ya Ιora masa sabon karatu akan maido da Nu'aymah rayuwarsa koda ta Ζarfin tuwo ne. Wannan shine dalilin da yasa dinga bibiyar rayuwarta. Ko a randa ya bisu shopping mail Ιin nan da nufin kidnapping Nu'aymah ya je. Sai akai rashin sa'a Yoohan ya gansa tun lokacin da suke faΙansu da Aymah harta faΙa a jikinsa. Dai-dai lokacin da yake cemata ta tara musu mutane idonsa ya sauka akan Abdallah Ιin. Har suka shiga mail Ιin kuma yana sane da shi. Sannan yana akan sani yabar Aymah a wajen ita kaΙai dan yaga mi Abdallah zaiyi?.
Lokacin da Nu'aymah taji Ζamshinsa da gittawar mutum Abdallah ne, yana gab da isa gareta Yoohan ya jasa baya da Ζarfi ya toshe masa baki suka koma ta bayansu. Cikin fushi Abdallah ya hakaΙe Yoohan Ιin yana faΙin. “Kai shasha minene haka?”.
Murmushi Yoohan yayi sannan ya haΙe fuska. Cikin ΖanΖance ido ya nuna Abdallah da faΙin, “Idan ka bari gangancinka ya Ιora zuciyarka bisa dokin shiga gona ta. Na rantse da ALLAH Abdallah sai na dawwamar da rayuwarka a dana sani. Na fika hatsabibanci fiye da yanda kake tsammani. Dan haka ka kama kanka kafin na ajiye mutuncin ahalinka da nake gani gefe na Ιata rayuwarka. Karka zata bansan wanene kai ba da ubanka. Ka kiyayeni kona fallasaku duniya ta sanku da aiyyukanku akan ahalinku”.
Yana gama faΙa yabar wajen, shine yaje yaja Aymah suka wuce wajan biyan kuΙi.
Tabbas kalaman Yoohan sun girgiza Abdallah. Hakan yasa ya janye daga bibiyar Nu'aymah. Dan dama can shi mutum ne da a rayuwa bai son yawan matsawa kansa, sannan baison fitina sam. Wannan halayyar tasa tasa lokacin yana yaro ake ganinsa matsoraci a cikin yara Ζ΄an uwansa. Dan da gaske tabbas yanada tsoron faΙa a rayuwarsa. Dai-dai da film Ιin faΙa Abdallah baya zaman kallonsa sam saboda baya ra'ayin fitina, daya zama saurayune ma dai ya fara canjawa. har zuciyar tasa tai tauri saboda zuciyar gidansu ta gado.
Ζin faΙama Abbansa zancen yayi. Amma yayi Ζudirin janye jikinsa daga bibiyar Nu'aymah. Daga bakin Abbansa yaji samuwar Uwaliya, dan a randa aka kawota a ranar Abbansa ya tattauna da ita tun a office kafinma a kaita gidansa. Uwaliya akwai son kuΙi. jin maΖudan ΖuΙin da Abban Abdallah ya tabbatar mata zata samu akan kaso masa auren Nu'aymah da kawo musu dukkan bayanai a kanta yasa ta amince zatayi. A ranar ya bata rabin kuΙin, sauran kuwa sai aiki ya kammala.
Tasha murna a ranar, ta kuma tabbatar da lallai ta shigo Abuja da Ζafar dama. Yo ko Yoohan Ιin sukace ta bibiya akan waΙanan kudin ai ta halakashi kuwa.
Wannan shine dalilin da yasa ta fara musu aiki. Sai dai abinda bata saniba suna amfani da wayar Rabi da muryartane idan suka kirata.
Lokacin da aka wuce da Nu'aymah Austria da gaske Abdallah yaje dubatane saboda son da yake mata. Sai dai baiso Yoohan da su baba malam su gansa. Shine yaso su fara haΙuwa da Abbansa. koda suka haΙun Abban ya dinga masa faΙan da har zancen Nu'aymah ya shigo ciki saboda Addah da tazo taga Abdallah ta zata cutar da Aymah zasuyi. Anna ne Yoohan yaji da Hajjo sukaji, abinda kuma basu saniba shine baba malam ma ya gansu, ya kuma jisu. amma sai bai taΙa nunawa ko da Umm ba balle su..........✍
[7/6, 9:39 AM] +234 913 412 2711: *_LITTAFIN nan na kuΙi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haΖura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaΙa manaππ»_*.
0 Comments