TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sanyi da zafi page 77

 EPISODE 77

Wuraren 3 yafarka da strong erection tashi yayi yazauna idanunshi sunyi ja, yajuya ya kalli Haleema dake bacci she’s not the one he wants, wai wats wrong with him ne? Over a year kenan he’s married to Haleema all this abubuwan bayajinsu, dan ijiyan zuciya yasauke sannan ahankali yatashi bayi yashiga yayo wanka yafito Wasa wasa yau 4days kenan Ammi tahanashi ganin Rashida, kai koshi Munir dake kwana da tashi a flat din baiganta ba, the only one person dake shiga da fita adakin nan is Ammi sai Dr dake dubata dudda yaune second kwananta duk a side na Ammi yake shigowa yaci abinci but wlh baiganta ba Ammi tahana abun yasa hardan rama yafara, duk Ammi na kallon take takensa tayi banza dashi.Today is the 4th day da Maimoon take kiran wayanta nonstop, ganin she keeps calling wayan nata dake hannunshi yasa saiya daga yakai wayan kunnenshi dasauri Haleema tace “Dr Rash mesa baki zuwa clinic, I’ve been calling you baki amsawa wlh duk na damu, are you okay?” Kaman Riyad bazai amsaba anatse yace “this is her husband speaking, batada lafiya” faduwa gaban Maimoon yayi daman Rashida nada miji dasauri tace “ayyah ina yini ya aiki, in sha Allah zanzo na dubata” kaman bazaice wani abuba yace “she’s not in that house muna family house” cikeda damuwa Maimoon tace “dan Allah inane family house din? Can I come and see her”? Shiru Riyad yayi chan yace “okay” cikeda damuwa tace “wannan driver nata ya sanni, yanzu mun fito break na sallan azahar, I can come basaina koma clinic ba” dan shiru Riyad yayi tun ranan daya fara ganin yarinyar yayi running background check on her dan baison any kind of mutum tareda matarshi, yarinyar batada matsala and again an gayamai ta taba aure tanada baby but mijinta yarasu a Maiduguri a hannun boko haram he’s a military man, anatse yace “k” ya katse wayan.Ammi na zaune a falo akai sallama Ammi tace “come in” ahankali Maimoon tabude kofa tashiga Ammi tabita da kallo ganin lab coat ajikinta ga gyale ta nannada akanta looking so decent, da sauri Maimoon ta zube gaban Ammi ganin babban mace, ahankali tace “ina yini Anty, sunana Maimoon ni friend din Rashida ne, inata kiran numberta ba’a dauka, yau sai mijinta ya dauka yake sanar dani ba lafiya shine yasa aka kawoni na ganta” murmushi Ammi tayi sosai ganin Rashida nada friend mai hankali haka, cikeda tattausan murya tace “Stand up stand up” dasauri Maimoon ta tashi, Ammi tace “ya school? Hope wani test ko assignment be wuceta ba?Muje na kaiki wajenta” Maimoon dake murmushi tace “a’a babu wani mahimmin abu daya wuceta, kawai attendance mark nata ne zaiyi gibi da log book nata, but that’s not really a problem, next week zamuyi all test nan da 2weeks zamu fara exams” Ammi dake tafiya Maimoon na binta abaya har sama zuwa dakinta tace “Allah yabaku sa’a”ahankali Ammi tabude kofan ta shiga dakin Rashida na kwance kan gado dudda ba bacci takeba wayan Ammi ne a hannunta tana kalle kallen pictures na ciki, tayi wani irin kyau bana wasaba, takara haske kaman mai bleaching, dakin na lafiyayyen kamshi turaren da ake turarata dashi, tana sanye da soft gown na cotton material mai kyau tadan rame alamun ciwo but then takara kyau da ja, wajen gadon Ammi tayi ta dagota ahankali ta tashi ta zauna gently kaman irin yanda matan da suka haihu suke zama cikeda so Ammi tace “look who is here your friend” tayi pointing kofa dasauri Rashida tajuyo takalli kofa Maimoon tagani dake kallonta tana murmushi, Ammi tace “bari na barku naje kasa” tawuce tayi kofa tafita tareda maida musu da kofan tarufe takira wata yar aikinta tasa aka hadamu Maimoon’s kayan abinci da drinks da snacks aka kaimata sama.Yanda Maimoon ke kallonta yasa Rashida ta sauke kanta kasa cus gani take kaman duk wanda ya kalleta zai gane abinda yasameta, asanyaye tace “Maimoon” zuwa Maimoon tayi ta zauna gefen Rashida da sauri saikuma tarike hannunta tace “Rashida daman kinada aure shine baki taba gayamin ba”? Batare da Rashida ta kalleta ba making innocent face tace “bansan yanda ake gaya bane nima” dasauri Maimoon tace “kinsan shine yasa aka kawoni nan naganki, driver ki ya aiko” ahankali Rashida ta kalleta itama Maimoon kallonta take saikuma chan tace “Rashida wlh I really like you as a friend, I understand you, nasan bakida friends bama kisan ya ake friendship ba, but you can trust me, I know that nima bantaba gayamiki anything about me ba but nima nataba aure for almost 2yrs mukai tare, I have a son Ameer, he’s 3yrs yanzu, mijina soja ne, but….” Tadanyi shiru saikuma muryanta ta karaya ahankali tace “yarasu!” Dasauri Rashida ta kalleta ganin yanda hawaye ya taru a idanunta, cikin sanyin murya Maimoon tace “kasheshi akayi, he went to battlefield bai dawo ba saidai aka kawo mana gawansa” Rashida jitayi wani abu ya taso mata, wani ciwo a zuciyanta barinma datace kasheshi akayi she just remembered Mama sai itama hawaye ya cika idanunta, ahankali Maimoon tace “Rashida I know so many things are going on with you, nima I’ve been there, akwai lokutan da har depression saida ya kamani, my point is learn to share kidena rike abu aciki most especially to mutanen dakikaga they genuinely care about you” ahankali Rashida ta rungumeta sai kawai suka fashe da kuka tare cikin muryan kuka Rashida tace “I’m sorry about your husband Maimoon Allah jikanshi, I’m sorry for not telling you anything about me yau zan fada miki” sakin Maimoon tayi tafara bama Maimoon labari komi game da rayuwanta harda Mama da yan gidan nan da abinda yafaru ranan even though bata fadan mata sex part dinba.

Ahankali Maimoon tace “did he took virginity naki? Meya miki daya kaiki dakin?” Dasauri Rashida ta dauke kai saikuma ta sauke kanta kasa tashiga wasa da kumbanta, ganin taki amsa tambayan sabida kunya da nauyi yasa Maimoon tashare tambayan cus is even obvious jinyan datakeyi kenan. Harga Allah tazo gidan nan taga genuine love Ammi has for her, and shi mijin dudda bata sanshi ba but tasan shine mutumin data gani ranan, the act na ya tura aka daukota aka kawo ta shows yana sonta, and kome yayi mata yayi ne sabida kishi, ko ita yanda Bilal yamata ranan batasoba kowa yasan Bilal fa playboy ne akanme tanada aure zata kula wani? Banda haka is not fault nasu ai, wayanda sukayi crime ba bata rayuwan Mama an kamasu suna hannun yan sanda and again akwai wani abu she noticed wlh Rashida nason mutumin nan, inhar shine mutumin ranan nan data gani agidan nan wlh Rashida na sonshi, data furta yanada kyau saida mood din Rashida ya chanza, she was so jealous like hell. Hannunta takai ta taba kafadan Rashida tace “yanzu yazakiyi?” Ahankali Rashida takalleta murya tace “ni banson shi, awajen Ammi zanyi zamana zata rabamu banso na kara ganinshi tsoronshi nakeji” dan murmushi kadan Haleema tayi tace “to shikenan I hope zaki iya” Dasauri Rashida ta kalleta saikuma tadauke kanta dasauri kawai she’s not comfortable gani take duk wanda ya kalleta zaiga abinda ya sameta murya chan kasa tace “ni kidena kallona” dariya sosai Maimoon tayi tasa hannu tadauki abincin da aka kawo mata tafaraci, tana gamawa taciro books nata da komi dasukayi ta nunnunama Rashida wanda yawanci ta iya but still tai snapping da wayan Ammi, sunyi hira da Maimoon dudda yawanci Maimoon ke maganan but she was so happy to see her, she promised zata koyama Rashida alot bari ta warke tukunna, 6 ta tashi tana daukan jakanta tace “bari kiga natafi” ahankali Rashida tamike ta tsaya tadan dafa bango Maimoon tabita da kallo saikuma tai murmushi dasauri Rashida cikeda masifa tace “me haka?” Dan dariya Maimoon tayi tace “sannu kinsha wuya wlh” dauke kai Rashida tayi dasauri saikuma ta koma ta zauna tajuya mata baya tace “wlh nafasa rakaki tunda ni kallona kike” dariya Maimoon tayi tace “eh nima banso da wannan gwalallun kafan naki” dasauri Rashida tadauki filo tajuyo ta jefamata kaman zatai kuka Maimoon tabude kofa tafita da gudu tana dariyan Rashidan da taga ashe tanada this mugun kunyan. 

 Baiwar tazube gaban Ammi tace “Ammi ga matan mai Martaba Sarki Riyad tazo gaidaki!” Abu kawai Rashida taji ya chaki zuciyanta sai kawai kaman an tsikareta ta mike zata wuce hannunta Ammi takama tarike tace “dawo ki zauna” batare datai musu ba tadawo ta zauna ahankali gefen Ammi tadauki wayan Ammi kawai ta shiga daddannawa, Ammi tadanyi shiru yau shekara daya da watanni matar Riyad bata taba zuwa wajenta ba ta gaidata is as if batamasan itace asalin mahaifiyar Riyad ba so wat is she doing today anan? Kallon baiwan Anmi tayi tace “kumata iso”. Bayine suka fara shigowa guda shidda saikuma ga Haleema tashigo sanye da crazy alkyabba daya hadu jakadiyan ta namata fifita tasa wani exclusive super wax dake jikinta, tunda tashigo take kallon wata jan yar budurwan yarinya dake kusa da Ammi tana daddanna waya batare data dago kanta ta kalleta ba kotama nuna tasan da an shigo dakin, kujeran da bayin suka shiga sharemata da zannuwan jikinsu tazauna kujeran na facing wanda Ammi take zaune tareda Rashida dake game abinta, wani kaluluwa Haleema taji ya tsaya mata awuya cus tana kallonta tasan itane matar Riyad ce dan ancemata daman fara ce, ga kyau ga gashi, part of abinda yakawota flat din is tazo taga wacece matar da Riyad ya aura dinma, wani arnen kishi taji yarufeta takalli Ammi tareda kakalo murmushi tace “Ammi ina….” Hannu Ammi ta daga mata strictly tace “sallami mutanenki sujiraki awaje” jitayi ranta yabaci amman saitai murmushi ta danne tama Jakadiya alamun su fita sannan cikeda makirci tace “Ammi wai nayi missing period dina ne, Mai Martaba yakamata yakaini hospital tun shekaran jiya but gynea dina bata kasan gobe zata dawo, shinefa yace nadena komi adinga kula dani cus lafiya gobe ciwo, Babe ya tsani ya ganni ina rashin lafiya saisa nake yawo da bayi incase of emergency” hakanan Rashida dakejin komi kawai taji zuciyanta yakama da wuta, game din datakeyi ma bata ganewa kuma, Haleema tace “Ammi ina yini” anatse Ammi tace “lafiya lau yasu wajen Mamanki da Babanki hope you’re hearing from them”? Cikin shedanci tace “yes I think Babe yakira Mamana ma this morning cus inata amai duk hankalinshi yatashi saida tafadamai wani orange remedy yahadamin sannan ya tsaya ma” sosai Ammi ke kallon Haleema sabida taga Rashida take kafidirin nan cus ita bata isa tamata hakaba, ikon Allah Ammi kawai tasaki baki tana kallon kwainane, Haleema tasake sakin murmushi tace “Ammi Riyad is so happy about this our baby, kinsan yanason yara I can’t wait na haifa babyboy me kama dashi, Ammi kin kusan zama grandmother” daidai lokacin aka bude kofan falon, shigowa falon Munir tareda Riyad sukayi, hannun Riyad rikeda paper bag din cold stone ice cream, dakin yabi da kallo kafin idanunshi su sauka kan Rashida dake playing game da wayan Ammi, kamshin turarenshi kadai Rashida tajiyo da sauri ta dago kanta ta waigo wajen kofan da sauri, hada ido sukayi a mugun firgice takama hannun Ammi daya ta rike tashige jikin kujeran tai lamo gabanta na faduwa ba kakkautawa kaman wacce taga dodo. Anatse yashigo cikin dakin Munir biyedashi dawani irin sauri Haleema ta taso ba kunya uban kowa na dakin tawani shige jikinshi ta kankameshi tace “Baby how did you know I was craving ice cream? You understand my pregnancy cravings so well” hayaki Rashida taji yataso mata tundaga kirji yazo mata wuya yamata hake hake, ganin yanda Haleema tawani rungume Riyad.Abala’in kunyace dan Riyad na mugun kunyan Ammi yadan tureta batare dayayi magana ba dasauri ta dago kanta takalleshi ganin yanayin kallon daya mata yasa ta saken mishi murmushi takai hannunta ta karbe ice cream bag din daga hannunshi tace “thank you Baby” Rashida jitayi idanunta sun juya ganin ita da ice cream dinta wata ta karbe, Ammi bata ankara ba taji kawai tamike dudda yanda tafiya ke mata wahala amman saida takai wajen dasauri daga Riyad har Haleema suka juyo suna kallonta yanda ta taho kaman zakanya, gaban Riyad Rashida tashige batai wata wata ba tasa hannunta ta fizge paper bag na ice cream dinta tace “ai kinada Ammi kema, kije kisa taki Ammi ta aika mijin naki ya sayo miki niki ice cream din but this is mine! And I don’t share!” Daga Ammi har Munir baki suka sake suna kallon Rashida dashi kanshi Riyad din daya tsaya yana kallonta da ita kanta Haleeman dake kallon Rashida jiyake kaman ta shake Rashida itama, watsa mata lafiyayyun harara Rashida da manyan idanunta da saida tsoro ya shiga Haleema ganin yarinyar barkono ce tawuce fuuuu tayi staircase tafiya daya biyu tayi tai baya zata fadi dasauri Riyad yayi wajen yace “Jewel” daidai yana tarota tafado jikinshi afirgice takalleshi.




Post a Comment

0 Comments