ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»
TEAM----ZAFAFA BIYARπ₯ππ₯°π
ALLAH ka gafartama iyayenmuπππ».
[7/8, 10:16 PM] Sweet Sis: *_LITTAFIN nan na kuΙi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haΖura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaΙa manaππ»_*.
No. 76
.............Gaba Ιaya gidan ya hargitse. Su Naser dai sunbi motar data Ιauki Yoohan a mota, sai dai babu tabbacin zasu iya cimmasu, musamman daya kasance dare ne.
Afrah da yake tazo wajen sunan ce tai azamar kiran Jay ta sanar masa, shima kansa hankalin nasa ya tashi matuΖa, amma sai ya shiga kwantar mata da hankali akan karta damu, indai da waya a jikin Yoohan gano inda ya ke abune mai sauΖi, ya kuma tabbatar a duk inda za'a kai Yoohan Deen na wajen insha ALLAH.
Suna yanke wayar yay kiran su Aliyu ya sanar musu. Tare da tura musu Number Yoohan dan yana son a bibiyesu da sauri kafin suyi tunanin yadda wayar a wani waje ko wani abu daban. Haka kawai a ransa ya kejin wannan aikin papa ne.
Lallai hikimar Afrah na saurin kiran Jay ya taimaka ainun. Dan cikin amicin ALLAH kuwa ta hanyar bibiyar wayar Yoohan Ιin da ke a jikinsa suka samu nasarar sanin inda aka kaisa.
_______★
A Ιangaren Yoohan kuwa an shammacesa ne. Dan yana tsaka da firgicin jin cewa ba'aga Deen ba, da cewar Nu'aymah ta suma juwa ta nema kwasarsa. Yana dafe kansa kawai yaji an jasa ta Ζarfi an tura a mota, al'amarin kamar wani wasan yara. Suna sakashi a motar suka Ιora masa bindigu. Binsu kawai yay da kallo Ιaya bayan Ιaya ya girgiza kansa. Kafin yace wani abu Ιaya a cikinsu yace, “Indai kana buΖatar Ιanka a raye ka bimu salin alin”.
Guntun murmushi kawai yayi ya Ιauke kansa. Papa yana Nigeria kenan, dan a take ya gama fahimtar su Ιin yaran papa ne. A ransa yake tunanin shin da papa na buΖatar ganinsa sai ya bi ta hanyar sace masa yaro kenan? Minene amfanin yin hakan to?. (tsoron a kamashi mana) zuciyarsa ta raya masa. ‘To ashe kuwa shi da kansa zai damΖa papa a hannun huku yau ba sai gobe ba’.
Ganin baice komaiba yasa yaran Ιauka yayi ladab ne. A haka suka iso wani hotel. Duk maida bindugunsu sukayi a jiki daga su har Yoohan suka fito a motar. Yaji a ransa zai bisu kamar yanda suke buΖata. Sun shiga cikin hotel Ιin babu wani alamun rashin gaskiya tattare da su. Hasalima sun shiga a rarrabe ne. Yoohan tare da Ιaya a cikinsu, suma sauran biyun suka shiga su kaΙai.
Shi Yoohan sun wuce cikin hotel Ιin direct, sauran kuma suka tsaya reception kamar dai wani suke jira. Yoohan dai yanata bin hotel Ιin da kallon nazari har suka Ζarasa Ιaki mai lamba 23 vip section. Knocking Ζofar yayi sau Ιaya, sai ko gashi anzo an buΙe. da ido yayma Yoohan alamar ya shiga. Yoohan yay masa wani gajeren murmushi ya shige Ιakin, sai y bisa a baya yanayin Ζwafa. Dan yaji haushin murmushin Yoohan Ιin har ransa.
Ko kaΙan Yoohan baiyi mamakin cin karo da Momy a Ιakinba. Dan dama ai su zuciyarsa take raya masa gani Ιin. Ya kauda kansa daga kallonta saboda shegun kayan dake jikinta bata da maraba da tsirara. Takowa tai gabansa tana kwasar dariya da tafa hannaye ta shiga zagayesa.
Hannayensa kawai ya tura cikin aljihun wandon shaddarsa ya rumtse idanunsa. Sai da ta zagayasa sau kusan uku kafin tazo gabansa ta tsaya daf tamkar zata rungumesa. Ko motsi kuwa baiyiba, bai kuma buΙe idanunsa ba.
Cikin raΙan maganar shaΖiyanci da jin alfahari madam Chioma tace, “Abin mamaki ko my boy, haka muke ni da papanka kullum cikin bama mutane mamaki”. Sai kuma ta ΖyalΖyale da dariya mai cin rai tana ja baya. Komawa tai bakin gado ta zauna tana wani lashe baki da banΖaro Ζirji. Tare da jan rigarta sama sosai cinyarta Ιaya ta fito waje idonta akan Yoohan da har yanzu nasa idanun ke a rufe. Cike da salon iskanci ta sake narke idanu tana lasar laΙΙanta.
“My boy karka takura kanka da tunani, dan baka buΖatar hakan musamman akan soyayyar jaririnka, oh sorry jikana nefa ashe”. Ta kwashe da dariya sanna ta cigaba da faΙin, “Yi haΖuri my boy na mantane. Ta hanya Ιayane kawai zaka iya cetar my grandson John. Dan nice kaΙai zan iya kaika inda zaka samesa. Hakan kuma bazata kasance ba sai ta hanyar biyamin buΖata ta. Hhhhhh My lovely john dolene fa na ΙanΙani zumar nan taka da kaketa min rowa, dan itace burina tun kana shekaru sha takwas a duniya. Hhhhhh kaga kuwa ai bai kamata nasha wahalar dakon lokaci ba, kaima nasan zaka tausaya min dear soooon”. Ta Ζare maganar da wani salon iskanci tamkar zatai kuka. Sai kuma ta taso zuwa gabansa ta tsaya tana matso hawayen da suka cika mata idanu.
Hannayenta ta Ιora akan Ζirjinsa ta fara Ιalle maΙallin shaddarsa tare da cigaba da faΙin, “Karka damu duk ma na yafe maka wahalhalun dana sha a waΙancan shekarun kaji baby. Dan wannan daren kawai ya wadatar da cike gurbin duka sauran dararen da suka shuΙe”.
Duk wannan iskanci da madam Chioma keyi Yoohan na tsaye tamkar gunki, har yanzu idanunsa a rufe. Sai da takai Ζarshen duka maΙallansa tana sambatun haukan zantukanta, ta tura hannunta cikin rigar ta fara shafa Ζirjinsa ta saman singlet Ιinsa. Wani irin cije baki yayi ya hankiΙata baya da iya Ζarfinsa.
A take ta saki wani irin wahalalliyar Ζara saboda da gaske ta bugu. Da sauri yaran da suka kawosa wajen suka zagayesa da bindugu. BuΙe idanunsa dake a matuΖar jazur yayi akansu, ya wani Ιauke kai irin ba kune a gabana ba ya maida kan madam Chioma dake kwance Ζasa wanwar tana numfashi da Ζyar saboda azaba.
A hankali ya fara takawa gareta fuskarnan kanta tayi jazur kai kace aman wuta zatayo. Suko yaran madam Chioma na biye da shi da bindiga abin nasuma abin dariyaπ.
Ζafarsa ya taka a samna gadon ya ranΖwafo kanta. Wani murmushin tsantsar tsana ya jefeta da shi tare da nunata da Ιan yatsa. “Na tsaneki, har cikin raina na tsaneki, tsana irin wadda ban taΙama wani mahaluki ita a wannan duniyarba. Indai nine zaki mutu da takaicin rashin samuna har Ζarshen numfashinki. Nayi takaici mai yawa akan kasancewarki mahaifiya a gareni. Bakuma zan taΙa yafe miki ba har abadan tunda ke karya ce wadda sam bata da zuciya a Ζirjinta balle ΖwaΖwalwar tunani. Badan ke uwata bece da yau na tabbatarma duniya ke Ιin dabbace, a cikin dabbobinma kina jerin aladu dan sune basu banbance junansu wajen neman kansu. Wlhy kinji na rantse ko tabon Ζwarzane na samu a jikin yarona saina halakaki da wannan hannun nawa”. Ya kai Ζarshen maganar yana wara yatsun hannunsa da jujjuyasu akan fuskarta.
Da gaske tsoro ya shigi Madam Chioma, dan tunda take a rayuwarta bata taΙa ganin irin wannan fusata da fushin na Yoohan ba. Tsaye ya miΖe yana zuba mata wani mummunan kallon tsana da Ζyama.
Da sauri ta zabura ta miΖe duk da azabar da bayanta ke mata. Tace, “Ku Ιauremin shi, wlhy koda Ζarfi saina lashi zumarka John. Kaje kaita tsanar tawa kai ya dama wannan kuma, ni ban tsaneka ba. Ba kuma zan tsneka ba”.
Kafin Yoohan yay wani yunΖuri kuwa suka dabaibayesa da igiya, duk yanda yaso kuΙutar da kansa ya gagara hakan sam, dan tsam suka Ιauresa a tsaye sannan suka kamashi suka ajiye a kujera suka sake Ιaurewa suna dariyar yanda sukaga yana wani irin huci na zafin zuciya.
Itama kanta Madam Chioma dariyar take tayasu da iya Ζarfinta. Ta tashi tsaye da Ζar tana riΖe Ζugu. Gabansa tazo ta tsaya tana cije baki. “John kana wasa dani ko? Na fika hatsabibanci yaro. dan tunkan asan za'a haifeka nake da taurin kai. Ai tunda nayi alΖawarin saina cikama rayuwata”.
Lokacin da su Yoohan ke wancan dabi shi da madam Chioma su Nu'aymah suna shigowa cikin hotel Ιinne tare da jami'an tsaro. Dan tuburewa tai akan saita biyosu. Ganin yanda ta rikice Ιinne ya saka Omar bada shawarar aje da ita Ιin. Sai da jami'an tsaron sukai magana da manager Ιin hotel Ιin sannan suka nufi cikin hotel Ιin kamar yanda alama ke nuna musu dai-dai inda wayar Yoohan take. Wadda toshewar basirar madam Chioma baisa ta kawo a ranta sanadin wayar ballinsu zaiyi ruwa ba.
Dai-dai madam Chioma ta Ιora kanta saman wuyan Yoohan tana shinshina kamar wata mayya ko tunkiya, hannayenta duka biyu na akan jikinsa. wani irin masifar tafasa zuciyar Yoohan keyi tamkar zata faso Ζirjinsa ta fito waje. Sai ko faman taunar lips nashi yake da masifar Ζarfi, a Ιaure yake, bashi da wata damar Ιaukar mataki akan uwar tasa.....
Da sauri ta Ιago saboda jin an buΙe Ζofar. Hakama yaranta dake tsaye a gefe kawunansu a Ζasa duk zabura sukayi suna rarumar bindugunsu...
“Ζasa gaba Ιayanku, duk wanda ya taΙa wata bindiga anan kuwa a bakin ransa”.
Ζaya daga cikin jami'an ya faΙa a tsawace yana nuna yaran madam Chioma. Da sauri ta fiddo tata Ζ΄ar Ζaramar bindigar jikinta ta Ιora bisa kan Yoohan daya buΙe idonsa a hankali ya sauke su akan Nu'aymah da ke shigowa tare da Jami'an.
Cikin rawar jiki data murya Madam Chioma tace, “Ku fita a Ιakin nan kona tarwatsa masa kwanyar kai duk da kasancewarsa Ιana”.
Da sauri Nu'aymah tace, “Ζarya kike munafuka azzaluma. K! Ba mahaifiyarsa bace ba. Yah Yoohan wlhy ba itace mahaifiyarka ba Ζarya takeyi”. Tai maganar da fashewa da kuka tana zaro hoton nan daga envelope ta nuna masa balarabiyar nan. “Kaga mahaifiyarka nan Yah Yoohan, wlhy ba wannan shaiΙaniyar bace. Bana tantama akan har mijinta ba shine ya haifeka ba, akwai abinda suke Ιoye maka. Iyayenka na gaskiya bazasu sace maka Ιanka ba. Mahaifiya ta Ζwarai bazata so tarayya da Ιanta ba koda kuwa bata da addini, sai dai idan dabbace ita mai juyayyen tunani..........”
“Hhhh da Ζyau tsagera”. Madam Chioma ta faΙa tana dariya har yanzu bindigarta na akan Yoohan da zantukan Nu'aymah sukema kai kawo a rai. Ta cigaba da dariya da faΙin, “Ashe tsaurin idon naki ya kai haka? Ko da yake ashefa kinsan zafin haihuwa ko? Hhhhhhh. Ashe kuwa za'a kwashi gawa da yawa a hotel Ιin nan yau”. Tai maganar da haΙe fuska ta nuno Nu'aymah da bindigar.
Cikin kaushin murya Umar yace, “Kibar wannan haukar da kikeyi ki ajiye bindigar hannunki kawai madam”.
Kallonta ta maida garesa. Cikin yatsina fuska tace, “Richard kake kowama? Kai kuma a suwa shiga family issue?. Maza kama kanka wannan ba shigarka baceba.....”
Kafin ta rufe baki taji an hankaΙata, sai ga ta ita da bindigar Ζasa wanwar. Da sauri Ιaya a cikin Ζ΄an sandamln ya Ιauke bindigar, wani kuma yazo ya danna mata ankwa ta baya. Yaran nata ma duk an kamesu. Nu'ayma kuwa da gudu ta Ζarasa jikin Yoohan dake a Ιaure ta rungumesa tana fashewa da kuka. Biyota Umar yayi ya fara warware igiyar da suka Ιaure Yoohan Ιin da ita, itama Aymah sai ta miΖe tana taimaka masa. Suna gama kwancesa ya rungume abarsa yana shafa bayanta. Sai dai bakinsa ya kasa furta komai saboda irin tafasar da zuciyarsa ke masa. Hoton hannun nata ya zare ya kafe balarabiyar jiki da kallo tare da papa dake gefenta. Jiyay wani abu na tsarga masa tun daga zuciya har zuwa tafin Ζafa. Ya kafe fuskar papa yana nazari sosai akansa batare da su Nu'aymah sun fahimci abinda yake nazartarba. A hankali ya janye Aymah a jikinsa yana miΖa mata hoton, gaban madam Chioma ya karasa. Babu wani kace nace yasa Ζafa ya taΙe Ζafafunta sai gata a Ζasa ta zube. Kasancewar hannayenta Ιaure suke ta baya da ankwa sai ta faΙi a rubda ciki. A take goshinta da hancinta da baki suka fashe, haΖoran gaba guda biyu sai gasu a Ζasa.
Wata wahalalliyar Ζara ta saki. Yoohan yasa hannu ya birkitota ta dawo rigingine. Gaba Ιaya fuskarta ta gama damewa da jinin raunukan data samu, “Ina Ιana?”. Wannan itace kawai tambayar daya jefa mata batare da ya damu da yanda jini yayma fuskarta jage-jage ba.
Kanta ta shiga girgiza masa, cikin rawar murya da laΙΙa tace, “Nima ban saniba John, Please ka yarda da ni”.
Uffan Yoohan baice da itaba, sai bindigar hannun Ιan sanda Ιaya ya fisge ya Ιora mata a goshi. “Humm ke Ζaramar Ζ΄ar iskace ashe. Idan kika cigaba da min gardama ba shakka zan tarwatsa Ζaramar ΖwaΖwalwarki da harsashin cikin bindigar nan. Idan kinada taurin kai tun kan haihuwata, ni ki Ιauka bayan haihuwar tawa na damaki na shanye. Da kika ganina anan tsageran kainane nima wlhy. FaΙamin ina Yarona yake?”.
Wutar bala'in da madam Chioma ke hangowa cikin idanun Yoohan ya sata saurin faΙin, “Zan gaya maka, amma ka taimakeni ka cikamin burina nima, kayi tarayya dani koda sau Ιaya ne naji sanyi a raina John. Ka tausayama wahalar danasha a kanka ta tsahon shekaru”.
“Lallai k! a tumakin ma balama ce”. Yoohan ya faΙa yana cije baki da Ιana kunamar bindigar ya maida bisa tsakkiyar kanta.
Jikinta karkarwa ya farayi, tana kuka tace, “Kayi haΖuri karka kasheni zan faΙa maka Jonh. Na rantse zan faΙa maka. Yaronka na a hannun Papanku acan wani gida dake cikin G.r.a, nima ya sakanine na kai masa kai, shine nai amfani da wannan damar domin fara cikama kaina burina a kanka na tsahon shekaru. Na biyo da kai tanan kafin na miΖaka wajensa. Miracle ita aka saka ta sace maka yaro a wajen bikin da kukeyi, dan dama muna biye da duk wani motsinku.......”
Duka ya kai mata a fuska Ιan sanda yay saurin riΖesa. “Cool down Mr Yoohan. Karka damu dolene ta kaimu har inda suke ai. Kwantar da hankalinka kaji”.
Huci kawai Yoohan ya keyi, tsabar zuciyar dake cinsa sai ga hawaye sharrrr suna sakkowa. Matsowa Nu'aymah tayi ta riΖe masa hannu batare da tayi magana ba. Da sauri ya jawota jikinsa ya rungume ko zaiji sassaucin zuciyarsa.
An tattara yaran madam Chioma zuwa police station da su. Su kuma su Yoohan da sauran jami'an suka shiga motar da aka sato Yoohan tare da madam Chioma bayan an sakata kiran papa ta sanar masa cewar gata ta samo Yoohan harda Nu'aymah ma. Wani ihun gigitacciyar dariya papa ya saki har su Yoohan na jiyosa. Umar da Jami'an sun rufe fuskokinsu tamkar su Ιinne yaran madam Chioma. Itace ta dinga nuna musu hanya har suka isa anguwar. A daidai Ζofar gate Ιin gidan suka tsaya. Maigadi na leΖowa yaga motar sai ya buΙe da tunanin su madam Chioma sun ciyo nasara suma.
Yoohan da Nu'aymah aka sakama ankwa a hannu suka fara shiga, jami'an tsaron da fuskokinsu ke a rufe na biye da su a baya. Umar ne Ζarshe da madam Chioma a gabansa. Acan waje dama tuni Ζ΄an sanda sun gama zagaye gidan dan dama babban burinsu shine kama papa da sauran mutanensa. Abinda suka share watanni biyu suna nema ga dama ta samu a lokacin ΖanΖani.
Da sauri Papa dake zaune cikin kujera su Joshua zagaye da shi duk suka miΖe sabida ganin Yoohan da Nu'aymah. Deen na kwance akan centre table Ιin falon cikin showal Ιinsa. Yayi kukan wahala har ya gaji yayi barci. Gefensa an ajiye sharΙeΙiyar wuΖa.
Cike da wata irin mahaukaciyar dariya papa ya shiga tafa hannayensa yana kallon su Yoohan.
Ya tako gabansu a hankali batare da tunaninsa ya haska masa cewar waΙanda ke bayansu ba yaransu bane ba. Da dariyarsa ya shiga faΙin, “Oh my Son & Darling daughter in-low Ιina. Welcome to my new land. Nice meeting you my guys”.
Da ga Ayma har Yoohan dai kallonsa kawai suke. Papa ya kalli jami'an da yake tunanin yaransa ne yana fa faΙin, “Ku cire musu ankwa amfaninta ya Ζare ai. Dan game zamu buga da su mai zafi”.
Babu musu Ζ΄an sandan nan suka cirema su Yoohan ankwa. Komawa papa yay ya zauna a kujerar daya taso. Ya Ιan taΙe bakinsa da dora Ζafa Ιaya kan Ιaya ya Ιauki kofin giyarsa ya kurΙa yana kallon su Yoohan. “John badan inada Ζarancin lokaci ba dana baka wani labari mai ban mamaki da al'ajabi. Amma share kawai muje ga game Ιinmu. Idan lokaci ya rage mana a cikinsa sai na baka labarin. Daughter in-low karki tada hankalinki kinji, Ιanki yana lafiya, kingama barci yake abinsa”. Yay maganar da tasowa daga kwanciyar da yayi jikin kujera ya yaye showal Ιin da deen yake ciki yana lakatar hancin yaron da Ιan yatsa. “Daughter kin iya haihuwar Ιa fa”. Ya faΙa yana kecewa da dariya su Mike na tayasa. Giyarsa ya kwankwaΙa ya ajiye kofin yana haΙe hannayensa waje guda. “Oh Sorry my son karka fusata na sanka da zuciya”. Takardun dake a gefen Deen ya jawo ya tura Ζarshen tebirin ta sashen da su Yoohan suke. “Wannan takardun sune game Ιinmu tare da Ιan jinjirinku ΖyaΖyΖyawa. John kanada zaΙi biyu. KuΙutar da yaronka ta hanyar yimin signing a duk takar dunnan, ko kummaaaaa nai masa yannnnnkan rago da wannan wuΖar tawa a wannan lallausar fatar tashi”. Ya ΖyalΖyale da dariya yana Ιora wuΖar bisa cikin Deen dake barci a binsa yanata sakin ajiyar zuciyar kukan da yasha.
Ko motsi Yoohan baiyiba, haka ma Nu'aymah duk da hankalinta a tashe yake kallon papa kawai take zuciyarta na tunanin anya kuwa wannan mutumin ma mahaifin Yoohan ne?
Hannunta taga Yoohan ya saki tare da takawa a hankali zuwa gaban papa yana wani ΖyaΖyΖyawan murmushi, dan cikin Ζ΄an sandan nan Ιaya yay masa alamar yaje. Zuwa yanzu sunsan sauran Ζ΄an uwansu sun gama tattare yaran papa gaba Ιaya dake cikin gidan. Sannan sun gama nazarin su papa kaf babu wani makami tare da su anan sai wuΖar dake akan Deen. Babu wani alamar damuwa a fuskar Yoohan balle tambayar papa ba'asin yin hakan. Yazo gaban tebirin ya zauna akan Ζaton tum-tum dake kusa da shi yana murmushi. Cikin kwanciyar hankali ya Ιauki pen Ιin dake saman takardun ya rike a hannu. Shafin farko na takardun ya karanta cike da nazari. YaΙan Ιago ido ya kalli papa da shima ke kallonsa. Murmushi Yoohan ya sakar masa da taune lip Ιinsa na Ζasa ya Ιage gira Ιaya da lumshe idanunsa ya sake buΙewa akan takardun. Har cikin jini Murmushin Yoohan ya daki zuciyar papa da su Mike. Amma sai basuyi magana ba. Ζaya bayan Ιaya Yoohan ya fara signing takardun. Yana gab da gamawa Mike da ya farga babu Madam Chioma. yace, “Brother wai nikam ina madam ma ne? Ta kawo mana su amma banga ta shigoba ita”.
Da sauri Papa ya kalli Mike, sai kuma ya kalli Yoohan dake signing yana murmushi da taunar lip dinsa na Ζasa. “John mikake kullawa? Ina matata?”.
Ko motsi Yoohan baiyiba balle ya kalli papa. Sai da ya gama signing Ιin duk takardun sannan ya kalli papa da tsoro ya fara bayyana masa a fuska. WuΖar kan Deen ya dauka yana faΙin, “Ashe kuwa inhar wani abu ya samu matata saina halaka wannan yaron”.
Murmushi Yoohan ya sakeyi har haΖoransa na bayyana. Ya miΖe tsaye hannunsa Ιauke da takardun da yay Signing. YaΙan sosa pen din a gefen wuyansa yana duban papan. “Oh my sweet papa ya da karaya haka da wuri?”. Yay maganar da wani shegen murmushin yaΖe. Sai sukaga ya girgiza kansa yana Ιan buΙa hannayensa. “Karfa ka damu papa. taya zan cutar da mahaifiyata. Guys Please ku kawo masa matarsa”. Ya juya yana kallon Ζ΄an sandan nan. Umar dake can Ζofar falon bai shigoba ya turo madam Chioma ta fara shigowa bakinta a Ιaure. Bindiga a bisa kanta.
Wani irin zabura papa yayi jikinsa na rawa. Kafin yay magana Yoohan yay Ζ΄ar dariya yana faΙin, “Oh my sweet papa relaxxxxx!!. Idan ban mantaba kace zamuyi game ko? So karka damu bazan canja ba zamu buga ai. Nasan kana son matarka, ba kuma zakaso rasata ba, gata Ζ΄ar ΖyaΖyΖyawa kuwa”. Yay maganar da wata shegiyar dariya. Sai kuma ya gimtse fuska da haΙe hannayensa waje guda yace, “Oh sorry papa bazan sakeba. Ga takardu na maka signing kamar yanda ka buΖata. Sai dai kana da zaΙi. Matarka ko waΙanan takardun. Idan su kafi buΖata, zan baka, amma zan tarwatsa kwanyar matarka a gabanka. Idan kuma matarka kafi bukata, zaka bani Ιana, na kuma wuce da takardun nan a gabanka. Wannan shine game Ιin Yahyaaaaaa! Muchπ! muchπ!!, I love you my papa!!”. Suka kwashe da dariya a Ζarshen maganar shi da Nu'aymah tare da tafawa.
Wani irin huci papa ya fara fitarwa kamar zai shiΙe. Ya kai hannu zai fisgi wuΖar nan Yoohan yay saurin faΙin, “No! no! no no no no!!!! Pastor goshpower. Karka fusata da yawa fa, kasan Ιan naka mai faΙa da cikawa ne. Ai yanzun game ya tashi daga tsakanin takardu da yarona, ya koma tsakanin takardu da matarka ok?”.
Kafin papa yace wani abu Yoohan ya fisge handkerchief Ιin da suka Ιaure bakin Chioma da shi. Wani wahallalen Ζara ta saki da fashewa da kuka. Cikin roΖo tace, “Please Darling ka basu yaronsu, ka taimakeni, na rantse john zai iya kasheni, kagafa yanda ya ciremin haΖwara, karkai jayayya dasu nan duk jami'an tsarone ba yaranmu ba”.
“What!!!”.
Papa da su Mike suka ambata a firgice. A take duk jami'an tsaron da Omar suka janye abinda suka rufe fuska. Sai ga wasu na shigowa suma akai ma su papa zobe. takawa Yoohan yayi gaban papa yana dariya ya Ιauki Deen ya rungume a jikinsa tare da sumbatar goshin yaron. Da sauri Nu'aymah ma ta matso garesa ta haΙashi shi da yaron ta rungume. Umar kuwa ya damkama Ζ΄an sanda Madam Chioma ya matso ya Ιauki takardun da Yoohan yayma Signing yana dubawa.
“Kai!! Dude!, anya kuwa mutumin nan ma shine mahaifinka kuwa?”..
Ζagowa Yoohan yayi daga sumbatar kumatun Deeen, yasa hannu ya share hawayen da suka cika masa ido yana miΖama Nu'aymah yaron. Yace, “Goyashi akwai sanyi”. Babu musu Aymah ta juya ya Ιora mata Deen a baya ta goyashi, ya gyara mata hijjab Ιin jikinta sannan ya dubi Umar da yay tambayar da furzar da zazzafan huci.
“Bana zaton haka Umar, dan abubuwa da yawa sun banbanta tsakaninsa da wanda ke a hoton nan. Sannan waΙanan takardun mallakin kaddarorine a cikinsu wanda alamu suke nuna ba nasa bane sam. Dan signing Ιin cikinsu ba irin nashi baneba. Akwai sirrin da yake Ιoyema duniya a kaina........”
“Sirri mai girma kuwa”.
Muryar da basuyi zato ba ta karaΙe kunnuwansu a bazata. kusan gaba Ιayansu suka dubi bakin Ζofar inda maganar ta fito. *Jawaad Abdul-aziz Yusuf* ne tsaye cikin Ζananun kayan da suka rage masa shekaru, sai dai duk wanda yasan shekarun girma ya kallesa yasan shiΙin bana wasan yara bane, (Duk ya girmi masu karatu yanzu, duk da a gabansu aka haihesaπππ€£π).
Bayansa jami'ai ne biye da shi. Cikin falon ya karasa shigowa ya zauna a kujerar da ke kallon papa dake a durΖushe bisa gwiwoyinsa yanzu shi da su Anthony saboda zagayesu da akai da bindugu.
Ζafa ya Ιora Ιaya kan Ιaya yana wani shegen murmushi, yace, “Hii Goshpower, sai kuma gaka. Hhhh ALLAH sarki. Haka rayuwa take ai, duk iya gudun mai tsere bai isa zarta Ζaddararsa ba. Dama naji a jikina dole ka dawo, dan yanzu da dukiyar da wannan takardun kawai kake tunanin ka tsira. Kafa birgeni, dan da gaske ka iya wasa. Kana da basira Ζwarai da gaske. Sai dai kuma kanada daΖiΖanci a wajen kuskuren lissafi. Da ace bakabar Yoohan a raye ba da lissafinka bazai taΙa Ιata ba. Sai dai kash a dalilin ΖwaΙayin abinda baka taraba ka saka kanka a tarko tsahon shekara talatin da biyu. Tsem! Tsemm tsemmm!!! Gaskiya ka bani tausayi. A farkon labarin dai cike yake da birgewa da Ζayatarwa ga marubucinsa. Sai dai a Ζarshe an samu dagulewar ΖwaΖwalwa ga marubucin. Mai makon yanda aka fara da nasara a Ζare da nasarori sai aka Ιige da faΙuwa Ζasa wanwar. Kash matsalar tunani ko Mr goshpower”.
Jay yay maganar Ζarshe yana Ιage gira da sakin dariya. Ya cigaba da faΙin, “Oh sorry bara na taΖaita, dan ka sani tafiyar da ban shiryaba a daren nan daga Abuja zuwa kano ga uban sanyi. Maganar gaskiya ma ban yafe ba. Ζ³an jarida ku shirya kayan aiki”. Ya faΙa yana shafar girarsa da nuna hanyar Ζofa.
A take kuwa suka shigo kusan su shida. Duban Yoohan da Nu'aymah da Umar yay ya nuna musu kujerun alamar su zauna suma.
Zama sukai a sanyaye kamar an doke gwiyawunsu da Ζarfuna.
Jay ya kalli agogon hannunsa sannan ya dubi papa. “Mr Goshpower bamu da isashen lokaci, dan awoyi uku da mintuna ashirin da Ιaya suka rage alfijir ya keto. Bana son wasana da kai yay tsamari a wannan gaΙar dan daga ni har kai mun jigatu, inason sanin wanene Yahya? Su wanene kuma waΙanan na jikin hoton?”.
Shiru papa yayi ya Ζi magana, hakan yasa Jay Ιinma bai sake magana ba, sai kawai Ζarar bibdiga su Aymah sukaji da Ζarar papa. RuΙewa Aymah tayi ta ΖwaΖume Yoohan jikinta na rawa. Ga Deen dake bayanta ma ya farka da wani irin firgitaccen kuka. Taimaka mata Yoohan yayi ta sakko da shi, ya rungumesa a jikinsa yana jijjiga shi. Da kallon papa da Jay yayma harbi biyu a duka Ζafafunsa saboda tsabar Ζwarewa a iya harbi.
Jay ya girgiza kansa da dafesa. Yace, “Oh kana neman fusatanine Mr Goshpower. Gashi ni kuma hannayena ΖaiΖayi sukeyi. Na faΙa maka a jigace nake matuΖa, karka jani da nisa ana idar da sallar asuba nake son komawa Abuja”.
Cikin magautar raΙaΙi papa ya fara magana. Ga wata irin zufa ta jiΖesa a take duk da uban sanyin da ake zubawa a garin. Yace, “Shima sunansa Goshpower, shi Ιin twin brother Ιinane. Wannan kuma matarsa ce”.
“Yayi Ιan gari, haka nake buΖatar jinka. Omar a cire masa bullets Ιin nan”.
Da sauri Omar yace, “Okay Uncle ”.
Tsabar son azabartarwa Umar sai ya Ιauki giyar da papa yasha ya rage ya zuba masa akan harbin. A take kuwa ya saki wata wahalliyar Ζara ya suma. Ko a jikin Omar. Ya amshi First aid box a hannun wani jami'i da sukazo da shi ya cire bullets Ιin cike da rashin tausayi. Sai da ya kammala komai sannan aka zubama papa ruwa ya farfaΙo.
Sai da suka bashi damar hutun kusan mintuna biyar ya daidaita sannan ya fara bada labari.
“Ni da shi twins ne. Muna tsananin kamanni har takai jama'a basa iya banbantamu inba mahaifiyarmu ta faΙa ba. Duk da itama wani lokacin rikicewa takeyi. Suna Ιaya iyayenmu suka saka mana wato Goshpower. Takai inhar ka kira Ιaya a cikinmu sai mu amsa maka mu duka. Mamanmu ta taΙa faΙa mana kaifin basira da muke da shi da farar fata tasa har ana dangatamu da wasu sunaye. Wasuko na tsoronmu da faΙin mama debora ta haifi waΙanda ba mayu. Wannan ba sabon a bu bane daga hallayar mutanen Ζabilarmu da yankinmu wajen danganta mutum mai fari da Ζyawun jiki da suna na tsoro. Mutane basu fara samun basirar banbantamu ba sai da muka fara girma halayenmu suka fara banbanta tsakanina da Ιan uwana. Mu duka munada kaifin basira da wayo, sai dai kowa da yanda yake gudanar da tashi. Duk inda gaskiya take zaka samu Ιan uwana a wajen, niko saΙanin haka shine zaΙi na. Kullum cikin takalo rikici nake wa iyayenmu, Ιan uwana kuma bai gajiya da bayyana gaskiya idan an tambayesa. A duk lokacin kuma da nai niyyar cutar da shi akan wannan abu da yakemin sai bana samun nasa. Dan ko faΙa zamuyi yafi Ζarfina. A haka dai muka kammala primary, akwai shaΖuwa mai Ζarfi a tsakaninmu, amma bamu cika zaman lafiya ba da zama waje Ιaya na dogon lokaci. Bayan secondary skull muka wuce jami'a, inda anan mabanbantan halayenmu suka sake bayyana. Duk da mu duka muna karatu ni a koda yaushe hankalina nakan mata, sannan duk wani abokin banza zaka samu nawane. Hakan na Ιatama Ιan uwana rai, tun yanamin nasiha da faΙamin gaskiya har yayi zuciya ya daina, daga Ζarshema muka raba Ιakin kwana, dama ba department Ιinmu Ιaya ba. Haka dai muka cigaba da tafiya, kafin mu kammala jami'a na zama riΖaΖen mara jin magana dan har harkar Ζwaya na fara, sannan na shiga cikin Ζ΄an Cult. Mun kammala degree Ιinmu na farko, ta hanyar ogan babanmu muka samu taimakon tafiya Ζasar Italy Ζaro karatu. Daga nan ne labarin canjawar komai ya fara. Dan watanninmu biyar kacal a makarantar na sake canjawa daga duk yanda aka sanni. Idanuna sun sake buΙewa sosai harna fara harkar cocaine. Ta hanyar wanda na fara harkar Cocaine ne idanuna suka sake bushewa. Ya kutsa dani cikin manyan mutane konace tantirai dake juya duk wani iya shege na duniya. Nasha wahala ba kaΙanba wajen karΙar horo daga garesu har takai makaranta ma na daina shiga duk da yawan damuwa da kirana da Ιan uwana keyi, tare da yawan ΖoΖarin son sanin abokan mu'amulata. Muna shekarar Ζarshe daya kamata mu kammala degree Ιinmu na biyu Ιan uwana ya haΙu da matashiyar Balarabiyar saudia mai suna Anum. Itama karatu tazoyi, wannan kuma shine zangonta na farko. Sun fara rayuwa kamar abokai a hankali suka rikiΙe zuwa masoya. Sam bansan da wannan soyayya tasu ba sai da tai nisa, muna ma gab da kammalawa. ko nace Ιan uwana na gab da kammalawa. Danni tuni na yaye kaina daga zuwa makaranta. Sai dai nakan shigo lokaci-lokaci saboda harΖallar dake tsakanina da Ιalibai ta kayan shaye-shaye. A wani shiga da nai cikin makarantar ne na haΙu da Anum, wadda ina cikin tafiyata tazo tasha gabana, a zatonta Ιan uwana ne. Da farko na harzuΖa matuΖa, sai dai Ζyawunta yayma idanuna barazana da danne fushina. Cike da tsokana take kallona tana dariyar wai yaushe nasai kayan jikina?, ita dai basu mata ba. Naji haushin kalamanta amma saina fuske na barta akan Ιan uwan nawa ne. Kiran wayata da ogana yayine yana min neman gaggawa yasa na sulale nabar Anum da nufin zan dawo gareta. Daga haka bansan yanda ta Ζareba bayan taga Ιan uwana. Shin ya warware mata mu Ζ΄an biyu ne, kokuwa ya karΙa mata matsayin shine ni?. Kwana biyu da yin haka na dawo cikin skull neman Anum sai dai na samu labarin cewa sun wuce saudia ita da Ιan uwana. Samakon zuwa da yayunta biyu sukai suka ganta da Ιan uwana daba musulmi ba”.
“Duk da bana shiri da shi hankalina ya tashi matuΖa, dan kodai babu komai shiΙin Ιan uwanane ai. Duk zatona ko zasu cutar da shi ne? Naso binsu duk da bansan ina suka nufaba sai kuma wani aiki ya sake taso mana zuwa Ζasar Germany. Haka na tafi al'amarin Ιan uwana na damuna a cikin rai. Kamar wasa sai ga wannan tafiya ta jani tsahon wata huΙu, lokacin da muka dawo Ζasar Italy saina samu munyi graduation, course mate Ιina duk sun kama gabansu har Ιan uwana. Na bincika Anum sai na samu wai itama tabar makarantar. Daga jin haka sai kawai na nufi Nigeria, a zatona Ιan uwana ya koma gida. Amma kash sai na iske saΙanin tunani. An dai tabbatar min yazo wata biyu da suka gabata wajen rasuwar mahaifinmu, nima anta nemana amma ba'a sameniba. Ko damuwa banyi da mutuwar babanmu ba, sai dai jin ogan babanmu ya bama Ιan uwana maΖudan kuΙin aikin da mahaifinmu yay aiki a ΖarΖashinsa dan yaje ya juya hankalina ya tashi na bukaci sanin ina Ιan uwana yake?. Mamanmu bata saniba, abinda kawai ta sanarmin shine ya sake barin Ζasar, bakuma susan ainahin Ζasar daya tafi ba. Yadai bar musu kuΙin da zasu ishesu, tare da musu alΖawarin nanda shekara guda zai dawo musu da daddaΙan labari. Nayi Ζwafa kawai bance komaiba. Daga haka na tattara kayana zan koma. Sai dai kafin na wuce na haΙa harΖalla da abokaina akan zanke turo musu kaya insha ALLAHU suna saidawa su tura min kuΙin. Sunko amince tare da min alΖawarin bazasu bani kunyaba. Daga haka na tattara na koma inda na fito, babu wani zancen nasarar da naci a karatuna dana zauna naima mahaifiyarmu. dan koma ban faΙaba nasan Ιan uwana ya gama tona mata dukkan zance a kaina”.
“Ban sake sanin ina Ιan uwana yakeba, ba kuma mu sake haΙuwa ba sai bayan kusan shekara, ana gab da zai cika alΖawarin daya Ιaukama iyayenmu na komawa garesu da daddaΙan albishir. A lokacin naje kai kaya Ζasar Syria ne. Kwatsam zamu shiga wani shopping mail ni da abokin tafiyata sai ga twin Brother Ιina tare da balarabiyar yarinya dana taΙa haΙuwa da ita a Italy a bazata. Da gani har shi babu wanda baima Ιan uwansa kallon mamaki ba. Hakama mafi yawan jama'ar wajen kallon mamaki suke mana da al'ajabi. A zahiri dai gashi muna tsananin kamanni, amma a shigar sutura da yanayi bama muyi kama da Ζ΄an yanki Ιaya ba. Ni na fara sakin murmushi ina kallon jaririn dake rungume a kafaΙarsa, sannan na kalli Anum na sake kallonsa. Goshpower kaine anan kuma?”.
“Shima Murmushin ya saki a karo na farko yana girgiza min kai, yace my twin bro, wannan suna yanzu na bar maka. A yanzu sunana IBRAHEEM ne, wannan matatace Anum, ga yarona Abdul-Maleek. Woow!! Na faΙa ina dariya da tafa hannu, kafin na miΖa hannun ya Ιoramin jinjiri Abdul-maleek. Yaro ΖyaΖyΖyawa mai tsananin kama da mahaifiyarsa, sai dai ya kwaso kamannina nima ni da Ιan uwana kaΙan. Ganin dai da gaske munsan juna abokin tafiyata ya barni tare da su yana faΙin mu gaisa shi zaije ya kai kayan zuwa anjima saimu haΙu. Na amsa masa da jin daΙi, dan koba komai ina buΖatar keΙancewa dama da Ιan uwana dan naji yaya batun kuΙin daya amso a Nigeria suke. Dan ko kaΙan banji wani damuwa da fahimtar ya koma musulmi ba. Kamar ya shiga raina kuwa. Sai ya buΖaci mizai hana muje gidansa kawai, ashe nan yake da zama yanzun. Mun shiga danΖareriyar motarsa dani da ke wahalar nema da shiga haΙarin rayuwa ko wadda bata kamitaba bani da ita. Wannan abu ya sosamin rai, amma sai ban nunaba muka shiga, suna gaba shida matarsa niko ina baya tare da jaririnsu a hannu. Al'amari bai kuma tadamin hankaliba sai da muka isa Ζaton gida da yaji kayan more rayuwa a matsayin wai nashine. Lallai nasha kallo, cikin mintuna kalilan kuma matarsa ta gama cika gabanmu da kayan ciye-ciye. Sai bayan munci mun Ζoshi mukai gaisuwa da tambayar bayan rabuwa. Bai Ιoye min komaiba daya shafesa bayan rabuwarmu”.
Yace, (Ζan uwana kamar yanda na sanar maka wannan itace matata, mun haΙu a jami'ar Italy dakaΖi nutsuwa ka Ζarasa. Da farko tsakanina da ita abota ce, sai daga baya muka fahimci muna son juna. Sai dai ta tabbatarmin babu yanda aure zai kasance a tsakaninmu saboda addinimu ba Ιaya baneba. Hankalina ya tashi domin ina tsananin Ζaunarta. Nai alΖawarin inhar zata yarda mu zama ma'aurata zan koma addininta. Ta sake tabbatarmin indai saboda aurenta ko soyayyar da nake matane zan zama musulmi wannan bazaisa ta yarda ta aureniba. Na musulinta kawai domin ALLAH badan tarayyarmu ba. A hakanma na yarda na amince, a randa muke shirin zan karbi shahada aranar Ζ΄an uwanta biyu sukazo dubata. Sun nuna mata tsantsar Ιacin rai nayin tarayya dani, harma yanda ake musalta musu a cikin makarantar mun zama tamkar wasu miji da mata. Dagani har ita hankalinmu ya tashi muma. Dan tunda nake da ita ko maganar banza bata taΙa shiga tsakanina da itaba. Bata taΙa yarda ko zama gab da juna munyiba balle akai ga aikata wani abu mara Ζyau. Ni bamma taΙa kawo wani mummunan al'amari tsakanina da itaba kamar yanda nasan itama hakanne daga gareta. Kawai dai ALLAH ya haΙa jininmune kawai, kuma ina koya mata karatu. Duk yanda mukaso su sauraremu sunki, daga karshe ma suka tattarata wai zasu wuce da ita. Banyi Ζasa a gwiwa ba wajen tattara duk abinda nake da shi na bisu batare da sun saniba. Sai da muka dira Ζasar saudi-arebia suka fahimci jirgi Ιaya ma muka shiga da su. Sun nuna jin zafin binsu da nayi, amma sai basu hanani na bisu har gidansu ba. Koda muka isa gidansu sunma iyayensu bayani akan dukkan alaΖar dake tsakanina da Anum. Maimakon nai zaton za'a koreni sai naga saΙanin hakan, dan kuwa sun yarda da bukatata ta zama mai salla. Amma babu zancen aurena da Anum, dan suncemin yarinyarsu karatu takeyi. Duk da na shiga tashin hankali saina amince a hakan zan musilinta Ιin. A take kuma na amshi shahada. Komawata musulmi ya sake canja komai, dan kuwa sunmin gagarumar Ζyauta maiban mamaki ta maΖudan kuΙaΙe wai na riΖe kaina, tare da haΙani da wani malami dazan dinga Ιaukar ilimi a hannunsa a Ζasar Italy. Satina biyu a saudia na dawo saboda karatuna. Amma daka ganni kasan bana cikin hayyacina saboda rabani da akai da masoyiyata. Duk na rame na fita hayyacina, amma hakan baisa nayi sakaci da karatuna ba. Na cigaba da neman ilimin addini da zana jarabawar Ζarshe data rage mana na tsahon watanni biyar. Har muka kammala jarabawa banji labarin kaba. Na bincika ance bakaje Nigeria ba. Hankalina ya tashi matuΖa. Amma yaya zanyi. Bayan yin graduation Ιinmu na tattara zan koma gida Ζasata. Amma maimakon nayi 9ja direct saina kasa haΖuri na nufi Saudia wajen Anum. Nayi mamakin tarbar dana samu daga iyayen Anum da ita Anum Ιin kanta daya kasance tazo hutu, dan lokacin karatunta ya dawo nan Ζasar Syria. Albishir na farko da suka faramin shine bani auren Anum, ashe dama sun gwadanine dan suga da gaske nakeson komawa addinin islama kokuwa dan son Ζ΄arsu?. Shiyyasa suka haΙani da malamin dake koyar dani batare da nasan bayanai yake basu ba a kaina. Nayi farin ciki nayi kuka dan daΙi. Sai dai da aka nema na gabatar da iyayena na fito fili na tabbatar musu akwai matsala. Dan nasan kaf danginmu babu wanda zai amshi canjawata matsayin musulmi balle kuma auren musulma kai tsaye. Naji tsoron Anum zata sake kuΙucemin sai gashi ba hakaba. Dan duk da abinda na sanar musu sai gashi sun amince sun bani aurenta. Bayan Ιaurin aurena da Anum an bamu wajen zama kafin ta koma makaranta. Watanmu Ιaya da tarewa ta koma makaranta, ni kuma naje gida Nigeria, sai dai kowa ya tambayeni ina kake sainace kanacan baka Ζarasa naka karatunba sai next year. Na tarar jikin babanmu yayi tsamari, amma sunki kaisa asibiti. Inada kuΙaΙe masu nauyi a accaunt dana samu saboda musilintar da nayi, dan haka nai amfani dasu wajen kaisa babban asibiti aka fara bashi kulawa. Sai dai kash, kwanakinsa huΙu a asibiti ya rasu. Bayan rasuwarsa da kusan sati biyu nace musu zan koma domin yin kasuwanci. Ananne ogan daddy ya bani kuΙaΙen daddy, wai yace a bamu idan munzo, tunda mune manyan Ζ΄aΖ΄ansa maza. Na amsa kuΙi na basu wanda zasu wadacesu na koma saudia. Mahaifin Anum shine ya Ιaurani akan harkar kasuwanci acan Ζasar Syria, ya bani shawarar na koma can kusa da matata ina kasuwancina tana karatunta. Naji daΙin wannan shawara kuwa. Tafiyata Syria ta zama tushen nasarata, dan ina zuwa na iske matata na laulayin ciki. Nayi farin ciki matuΖa, harma bansan yaya zan musalta makaba. Haka na zauna kulawa da ita tare da fara kasuwancina. Cikin amincin ALLAH sai gashi dan danan na haΙaka. Saboda na farane da kuΙaΙe masu nauyi. sannan kuma ta hannun babban mutum irin mahaifin Anum. A haka cikin Anum ya shiga watan haihuwa, tana gab da haihuwa na sayi wannan gidan da nake ciki, tare da motar hawa. Sannan na zauna na banbance dukiyar da take matsayin mallakina, na kuma fidda wadda ta kasance ta mahaifinmu. Kwanaki uku da yin haka Anum ta haihu namiji, wanda yaci suna Abdul-malik. bansan yaya zan bayyana maka Ιunbin farin cikinaba Ιan uwana. Amma babu abinda zancema ALLAH sai godiya. A yanzu haka watan Abdul-maleek uku a duniya, muna shirin zuwa Saudia ne domin nunasa ga dangin Anum dan babu wanda ya taΙa ganinsa sai mahaifinta da yazo mana nan sanadin harkar kasuwarsa. Daga Saudia kuma zamu wuce Nigeria na nunata ga dangina, na kuma sanar musu na zama musulmi duk da a tsorace zuciyata take. Dan yanzu haka maganar da nake makama nayi cinikin wani gida a Lagos, idan munje can zamu Ιan zauna kafin hutun Anum na Ζarshen shekara ya Ζare. WaΙanan takardun sune takardun shaidar company na dana mallaka da dukiyata. Insha ALLAHU kuma zan mallakashi ga Abdul-maleek ne. Dan haka kaima inason ka zama shaida, kaimin signing anan wajen, a duk lokacin da yakai shekaru talatin na girma zan mallaka masa shi. Wannan kuma sune takardun dukiyar mahaifinmu, idan nazo Nigeria mu dukanmu zamu haΙu mu saka hannu alamar tabbatarwa da banawa bane ni kaΙai).
“Rungumesa nai a lokacin, na nuna masa tsantsar jin daΙina da wannan ΖoΖari nashi, tare da bashi goyen baya akan zamansa mai sallah. Yaji daΙin yanda na bashi goyon, hakama matarsa. Sai dai ni a cikin zuciyata Ζulla ta yanda zan kwashe waΙanan takardun nakeyi, tare da damfare duk wata dukiya da yake fankamar ya tara. Banbar gidanba sai dare, na tafi da Ζudiri kala-kala a cikin raina da zuciyata”.
“Washe gari ma naje na samesu, shine ya Ιaukeni ya zagaya da ni duk inda companys Ιin suke guda biyu. Na Ζara girgiza da wannan al'amari, dan dukiyace bata wasaba Ιan uwana ya tara. Tofa sai tunanina ya Ζara faΙi da girmama. Dan koda nabar wajensu a ranar kasa barci nayi, har takai na fito na bayyanama abokin tafiyata. Yace na bashi dama zaiyi tunanin ta yanda dukkan wannan dukiya zata zama tawa, amma sai nan da kwana biyu mun gama abinda ya kawomu zai faΙamin hukuncin daya yanke. Naji daΙi, na kumayi murna. Sai dai wayewar garin ranar al'amari ya canja salo, dan bamusan yaya akaiba aka kama wanda muka kawoma kayan cocaine. Har bincike yazo ta kanmu. Da farar safiya mukaji jiniyar motocin Ζ΄an sandan Ζasar. Hankalina ya tashi matuΖa ni da abokin tafiyata, cikin zafin nama muka samu nasarar tserewa ta bayan gidan kafin Ζ΄an sanda su gama shigowa gidan. Muna barin gidan muka rabu nida abokina, domin wannan gudune na ceton rai, kuma hakan abune da kowa ya sani daga tsagera. Idan bala'i ya tunkaro kowa takansa yakeyi. Ba'a sauraren dukiyar da aka tara balle abokantaka. Cikin kiΙima na nufi gidan Ιan uwana, dan duk da wannan bala'i da nake a ciki ban manta da batun takardu ba. Ina isa na samesu a tsakar gida suna hutawarsu cikin kwalliya. Dakewa nai daga ruΙanin da nake ciki na amshi jaririnsu, tare da faΙama matarsa nifa inajin yunwa. Dariyar tsokana suka dinga min, Ιan uwana na faΙin to nazo nayi aure, yafimin wannan gararin, danshi sofa yake na dawonan tare da shi mu haΙa Ζarfi wajen kula da kasuwancinmu. Murmushi kawai nayi, na shiga daga ciki Ιauke da yaron. Matar ta shigo ta bani abinci. Tana kammala haΙamin komai Ιan uwana ya shigo, kallonta yay cike da so da kauna, yace tunda ga bro yazo kizo muje muyi shopping Ιin nan da bamuyiba jiya, sai mubar Maleek tare da shi dan harmu dawo da wahala ya farka. A take ta amince da shawararsa. Yayinda ni kuma kaina ya kawomin wuta a take. Jacket Ιin jikina na cire jin yana faΙin bara ya karo riga a saman kayansa. Nace bro indai rigace ga wanann ka saka nasan zata maka Ζyau, dan yanzun nan dazan fito na ganta a wani shago na siya. Nama tambayi biyu akace babu. Cike dajin daΙi ya amsa, dan shi mutumne mai saukin kai. Sannan bashi da saurin zargi. A gabana matarsa ta taimaka masa ya saka suna dariya da yaba Ζyan da rigar tai masa. Murmushi nayi ina dubansa na ajiye yaronsu na tashi ina gyara masa rigar, cikin dabara na saka masa wayata da wallet Ιina a aljihu, na zare tasa wayar da wallet ni kuma. Sunmin sallama sun wuce bayan sun tambayeni abinda nake buΖata a siyomin nima, dan yace idan ya dawo zamuyi magana akan zamana a gidan. Suna fita na kulle Ζofar falon, na bar yaron anan na shiga cikin Ιakinsu binciken takardu dama duk wani abu mai amfani. Duk kuwa da a raina ina addu'a da fatan tarkon dana Ιana musu ya zama sanadin tafiyarsu har abadan. Komai na gansa, dan haka na tattare tsaf na hada a jikka, na fito falo inda yaron ke barci na ajiye tare da zaman jiran sakamako”.
“Mintuna talatin kuwa ban rufa da zamaba saiga babban labarin da nake jiran gani daga television. Ζan jaridan dake bada rahoto ne ke magana cikin tsantsar sarΖewar harshe, akan samun nasarar kama mutane biyu da suka shigo daga Ζasar Italy da hodar ibilis. An samu nasarar cafke Ιaya a airport, Ιaya kuma daidai traffic light tare da matarsa. Sai dai bisa kuskuren guduwa da sukayi na gardamar su basusan komaiba Ζ΄an sanda suka harbesu, wanda bisa tsautsayi suka matu har lahira. Sai ga gawar Ιan uwana an nuno tare da matarsa kwance cikin jini. Hannayensu riΖe dana juna. Ga Ζ΄an sanda na lalube wallet din dana saka masa tare da wayata anata faman bincike. Ko Ιar banji a raina na nadamar yin hakanba, dan koba komai asirina ya rufu, zan fara sabuwar rayuwa. A take na Ζarasa haΙa duk wani abu mai muhimmanci dake gidan, tare da kayan yaron na shiga mota na fice a gidan. Na tabbatar yanzu bazan fuskanci kowacce irin matsalaba, musamman daya kasance hankalin jami'an tsaron ya koma gaba daya akan nasarar cafke masu laifi. Aiko banci karo da kowace matsalaba wajen barin Ζasar ta mota. Duk da naci uwar wahala ga yaro nata zubamin kuka ban damuba. Haka nai nasarar fita a Ζasar zuwa Ζasar dake maΖwaftaka da su, acan kuma nabi jirgin ruwa, inda anan ne na haΙu da Chioma, itama tsagerace ta kanta, dan kuwa kusan duk irin harkokina shi takeyi, sai dai ita oganta a Nigeria take. A dai takaice na samu nasarar komawa Italy tare da jariri da Ιunbin dukiya da takardun kaddarori da taimakon Chioma. Ogana yayi farin cikin ganina dajin labarin ta hanyar dana kuΙuta, dan haka yaymin alΖawarin taimakona ta hanyar tabbatar duk waΙannan kaddarori na Ιan uwana a tafin hannuna. Yanda Chioma ke taimakona da rainon jariri dana canjama suna da John ne yay sanadin Ζulluwar soyayya mai Ζarfi a tsakaninmu har mukaima juna alΖawarin aure. Ta matsa matuΖa muyi aure sannan mu koma 9ja dan haka na amince mata saboda nima ina sonta. Bayan aurenmu muka nufi Ζasar haihuwarmu cikin danginmu. Wanda zuwa yanzu labari ya gama zuwa kunnen danginmu na rasu ta hanyar kamani ina safarar hodar ibilis ni da wata, dan a haka labarin keta yawo. Kowa kuma yana Ιauka ni aka kashe, saboda kowa yasan halina. ni kuma nine Ιan uwana. Munzo Nigeria ne dama da shirin hutu mai dogon zango, dan ogana ya tabbatarmin dolene inyi nesa da shiga kowacce Ζasa. Inba hakaba kuwa babu makawa sai an bankaΙo ainahin gaskiyar nine mai laifi ba Ιan uwanaba. Nayi amfani da wannan shawara kuwa, dan haka na yada zango a Lagos gidan da ya sanarmin ya saya ta hanyar abokinsa. A labarin nanfa da nake baku kowa ya Ιauka dama nine aka kashe, dan ansan nine tsagera, Ιan uwana kuma shine ni. Dan haka na canja sosai wajen Ιaukar Ζyawawan halayyar Ιan uwana na yafama kaina akan dole. halena kuma na Ιoyesu, dagani sai matata muka sansu. Ban wani cika burin Ιan uwana ba na mallakama mamana da Ζannenmu dukiya ba, sai dai naja Ζ΄an uwan nawa a jiki wajen sakasu cikin harΖallolina. Bansan yaya akai Godwin ya fahimci banine twin bro Ιina ba, sai kawai rana tsaka ya fuskanceni da wannan zance shi da Mike. Na matuΖar tsorata da firgita, amma sai Chioma ta bani dabarun maidasu a hankalinsu ta hanyar Ζara jansu jikina da rufe bakunansu da dukiya mai tsoka da kuΙaΙenta. Danni a lokacin bawani kudine da niba. Sunko bi sun tsuke bakunansu kuma, tun daga nan suka zama sunsan kowacce irin harΖallata, sun kuma san John ba Ιana baneba”.
“Abinda ya faru baisa na daina harΖallataba, sai harkokine suka sake buΙewa sabbi dan yanzun dukiyar Chioma muke juyawa, nazama jan wuya anan Nigeria, ta hanyar turomin da kaya da ogana yakeyi. Cikin shekara huΙu kacal na shahara, na kuma sakeyin kutse cikin addini har saida na zama Pastor a wata Ζaramar church duk da babu wani ilimi da nake da shi. Zuwa lokacin John ya fara wayo, yanada shekara huΙu, dan ko ina zuwa yake, ga surutu a bakinsa ba'a magana. Yanda yaron ya shiga ranmu muke tarairayarsa bazaka taΙa kawowa a ranka ba dΙanmu bane, dan soyayya ta gaske Chioma ke nuna masa. hakan yasa na Ζara sonta a raina, dukda kaf dangina basa sonta dan ta rainasu, su kuma gani suke ta Ζwaceni ta hanani taimaka musu bayan kuma dukiyarsuce tunda dai kallona suke a matsayin twin bro Ιina. Dukiyar Ιan uwana tazo hannuna, sai dai ba dukantaba, dan wata an tabbatar da dolene sai John ya girma sannan nasoba kuwa dole na haΖura, na cigaba da juya abinda ke hannuna ta hanyar harΖalla daban-daban. A wannan lokacin ne naje Ζasar France yin wani couse na watanni tara, dan rashin yawan ilimi nason min tangarΙa akan zamana pastor. inda acanne muka haΙu da Sooraj Hashim Jibiya. Bayan korarsa da akai a makaranta sanadin dukan da yaymin nai jiyya kusan ta watanni uku, da Ζyarma na kammala abinda ya kaini na dawo gida cike da alwashi kala-kala akan Sooraj dama yankin daya fito gaba Ιaya. Dan nayi alΖawarin sanadin abinda ya aikata mani saina tarwatsa duk danginsa da jama'ar yankinsa. Wannan shine dalilin farkon fara sato yara daga yankinsu ana kawomin ina cinikinsu. Sai dai na gaza lalubo a ina Sooraj yake? Dan ko'a wancan karon dama bansan taka-maimai shi Ιan ina bane, nadai san musilmine Ιan arewa. a zahiri kuma na lulluΙe True color dina da rigar addini, babu mai cewa ni shege ne. Cikin kanΖanin lokaci na shahara, dukiya da girma suka zauna saina tattaro na dawo Abuja. Wani halaye da John ya fara nuna mana na Ζyamar addini da wasu abubuwan namu duk da ΖanΖantar shekarunsa yasa hankalina tashi. Dan da alama yaron yanada wata baiwa dake nuna ya fahimci kamar muΙin ba iyayensa bane. Mike ne ya bani shawarar zuwa gidan boka a kulle tunanin Yoohan gaba Ιaya, koda ya girma bazai taΙa kawo a ransa muΙin ba iyayensa bane koda yaga rashin kamansa da Chioma. Naji daΙin wannan shawara, nakumayi amfani da ita. Bayan munje wajen boka ya amsa zai mana aiki, sai dai aikin zai zama sanadin saka ciwon rashin barci ga John lokaci-lokaci. A take kuwa muka amince, akai asiri John ya koma tafin hannunmu sosai. Duk abinda muka sakashi babu tantama yake mana, sai dai ban taΙa yarda yasan Ιoyayyar harΖallataba Mamana ma da sauran Ζ΄an uwana nasa akai musu asirin da bazasu taΙa tunanin ko kawowa a ransu niΙin ba Ιan uwana bane. Ana haka Chioma ta haihu twins itama, Gebrail da Joy. Nayi farin ciki sosai da samuwar nawa Ζ΄aΖ΄an, amma samun nawa baisa naji tsanar Yoohan ba. Bayan su Joy Chioma bata sake yarda ta haihuba sai da John ya shiga jami'a ta sake haihuwar Victoria. Ta sake Abraham wanda cikinsa yazo mata babu shirin hakan, dan tace daga yaΖ΄a uku ta gama. To ashe da rabon zuwan Abraham. Abinda yasa nasaka Solomon kullum yake tare da John tun bayan gama karatunsa, saboda tsoron kar wajen yawon Ζasashensa da aiki ya tilasta masa yin gamo da wani dangin mahaifiyarsa ΖwaΙata tayi ruwa. Shiyyasa dukkan motsinsa sai na sani ta hanyar Solomon”.
“Abu mafi Ιagamin hankali daya faru shine tarayyarsa da Sheikh Sooraj. Lokacin dana san wannan alaΖa hankalina yayi Ζololuwar tashi, na kumayi murna dan sanadin John maΖiyina dana Ιauki shekaru ina bulayin nema ya bayyana. har Ζauye naje mukai zaman meeting da sauran mutanena, dan saboda gudun irin haka yasa na cusa masa Ζiyayyarsu tun yana yaro, amma daga Ζarshe sai gashi abinda nake gudun ya auku. John ya xama musulmi kamar mahaifinsa. Ranar nayi tamkar mahaukaciya a gidan nan, harma na yanke hukuncin kashesa kawai na huta bayan na sakashi ya sakamin hannu a takardun da naketa a jiya tsahon shekaru, dan company Ιin yanata haΙaka zuwa yanzun, sai dai ina mamakin ta hanyar wa hakan ke faruwa?. Su Mike ne suka haΙu wajen bani shawarar mizaisa na damu da musilincinsa. Sun san dai babu ta yanda za'ai ya iya gano shiΙin wanene saboda asirin da ke a kansa. Sooraj kuwa amfani zamuyi da kusancinsa da John Ιin mu yashe masa asusunsa tsaf mubarsa da Ιimautar ΖwaΖwalwa da bugawar zuciya. Amma wai koda na tuntuΙi John akan mike alaΖarsu sai ya nunamin wani aiki yakeyi akan Sooraj Ιin. Nafa yarda da shi har cikin raina. Saboda nasan irin horon danai masa tun yana yaro akan wannan yanki. Har raina daΙi nakeji zai Ιaukamin fansa akan abinda Sooraj yaymin tsahon shekaru, dan duk da korar da akai masa a makaranta wancan karon baisa na huceba, na kuma daΙe ina addu'ar haΙuwarmu amma hakan bai yuwuba sai yanzun. Ban fahimci John folani yake a kwalayeba sai akan aurensa da Ιiyar Sooraj, idan nace zan bayyana muku halin dana shiga ni da matata dasu Mike a wannan tsakanin Ιata lokacine, da Ζyar Godwin ya kwantar min da hankali akan na amince da auren, bayan anyi mu kashe yarinyar yanda Sooraj zaiji ciwo sosai a ransa kafin kuma mu yashe masa asusunsa. Wannan shawarace ta kwantarmin da hankali na amince akai aure batare dana yarda na nunama Yoohan nasan ya musulintaba, sanann matata ma ban taΙa faΙa mata ya zama mai salla ba dan nasan tana son John sosai fiyema da Ζ΄aΖ΄anta, kodan shita fara samu matsayin Ιa ne kafin ta haifi nata oho. Shigowar Ιiyar Sooraj cikinmu ta sake ruguza komai na shirinmu, dan yarinyace hatsabibiya. takai ko ganinta nai sai naji matsanancin tsoro na shigata. Bala'in kwarjini takemin kamar ubanta, gata bata da tsoro. Ban sake tabbatar da yarinyarnan abar tsoro bace sai randa ta shigar min Ιaki, ta kuma nuna ba ita bace. Da gaske nima Ιin na yarda ba ita Ιin bace a lokacin, sai daga baya na gane itace ta hanyar cctv dake a falona wadda ko matata batasan da zamanta ba duk da kuwa harΖalla Ιaya mukeyi, kai hasalima na sakatane domin ita dan haka harkarmu take a kullum bama yarda da juna. Bawai ina tunanin itama zata cutar dani bane, dan ina tsananin Ζaunarta, na kuma yarda da ita. Ina tsoron kar dai cikin abokan harΖalla wani yay amfani da ita ya cutar dani ne dai. Sosai hankalina ya tashi da lamarin yarinyar, da kuma tunanin mahaifintane ya turota leΖen asirina. Sai kawai na shirya yanda Doctor Ιin da zasu mata aiki zasu kashe min ita ta cikin sauΖi kafin na dawo kan John Ιin shima. Naji daΙin abinda Gebrail yay mata, dan nasan nesa tazo kusa akan aiwatar da aikina a kanta, sai dai kash Dr Mateo ya lalatamin burina. Naji takaici, naji ciwo, na kuma yanke shawarar halaka John da yarinyar gaba Ιaya da zarar sun dawo Ζasar nan. Zan fara halakata ita da duka danginsu da ubanta kafin shi ma na juyo kansa. Amma taurin kai irin na John da bani da tantama wajen ubansa ya gada sai ya sake ruguzamin shirina. Ya koro Solomon, ya kuma Ιauketa daga Austria ya canja mata Ζasar da bani da damar shiga, dan tuni aka hanani lasisin shiga Ζasar U.S. Wamnan shine dalilin yimin katanga a garesu, na zauna dakon jiran dawowarsu ko zuwansu Ζasar a tare. A randa John ya dakarmin yaro wai ya shigar masa Ιaki naji kamar shima na halakashi da hannuna. Amma na taushi zuciyata dan nasan a tafin hannuna yake. Shina ΖanΖanin lokacine ya rage masa ai. Na tattara komai na ajiyeshine ban masa magana a kaiba dan banason ya zargi komai a kaina har sai randa ya sakamin hannu a waΙannan takardun, ya kuma kawomin shegiyar matarsa Ζasarnan. Dan nagama shiryawa tsaf akan yanda zan yashe asusun ubanta kaf na maidashi sifili. Wai kawai kwatsam rana tsaka saiga yarannan da ciki sunzomin gida. Lallai naga baΖar rana kuwa, dan da gaske ranar susucewa nasoyi gaba Ιaya. Randa na gama shirya Ζudirin aikata lahira suka baro Abuja batare da ko John ya sanar minba da yake shima tantirin Ζwallon shege ne. Nasa a biyota kanon, a daren da zasuzo bisa jagorancin Solomon kuma Ζ΄an sanda suka ritsamin yaro a hanyarsa ta kawomin kaya daga Ζasar Cameroon. Da Ζyar yasha zuwa abuja, duk sun fasa masa jiki da bullets, amma sai yayi ΖoΖarin zuwa ya isarmin da saΖon na gudu, dan da gaske wanann tarkone babba aka Ζulla a kaina tsahon lokaci. wannan shine sanadin tserema Ζ΄an sanda da nayi, sai da na bada Ζafa ta watanni biyu na dawo da baya saboda jin matar John ta haihu ta hanyar wani Ιan leΖen asirina. Na fahimci lokaci yayi da zai sakamin hannu a takardu, daga haka na kama gabana bayan na kasheaa shi da Ιan da matar tasa. Sooraj kuwa zan dawo masa da nasa shirin bayan Ζura ta kuma kwanciya.......”
Kallonsa kawai kowa keyi a falon kamar sun sami television. Dan shi kansa Jay makircin na Goshpower ya matuΖar rikitashi. Ashe shine sanadin halakar Ζanwarsa da mijinta. Iya bincike sunyi bayan faruwan wancan al'amarin amma suka gagara sanin gaskiya, dan sudai basusan mijin Anum da wani twin Brother ba. Ba komai yaja hakaba sai sakacin rashin bincike danginsa koda a Ιoyene, duk da dai shi yaso yayi binciken a lokacin mahaifin Anum Ιin yace a barsa darajar gaskiyar yaron, a bashi dama har ya bayyana mana danginsa suma ya bayyana musu mu. Tunda dai shi sun gwadashi ta hanyoyi da dama basu samesa da wani mummunan hali ba. A lokacin haushi shi Jay yaji yace ya cire hannunsa akan batun, dan ya rasa wane irin so sukema mijin Anum Ιin. Ganin yanda ya dage da harkar nema da neman ilimin addini yasa shima Jay din Ιaga masa Ζafa ya bashi lokaci zuwa sanda Anum zata haihu, dan yayi alΖawarin da zarar ta haihu kosu Ummu sun yarda ko basu yardaba dolene yasan dangin mijin Anum ta hanyar tasa Ζeyarsu har Nigeria aje tare da shi. Sai gashi a dai-dai gaΙar da take shirin kawo musu ribar auren nata su gani su kuma je ga dangin mijin nata wannan al'amari ya bayyana. Wanda ta sanadin haka suka rasa Ζ΄ar uwarsu da mijinta da Ιanta. Suka kuma rasa ainahin gaskiyar zance akan zargin da akema mijin nata. Haka suka haΖura badan zukatansu sunsoba, suka Ιauka wannan itace Ζaddararta kuma. Tare da mahaifinta sukaje suka amshi gawarsu wajen Ζ΄an sanda bayan ansha gwagwamaya suka sallacesu aka kaisu makwancinsu. Sai dai basuga gawar yaronba, sai suka Ιauka wani ya Ιauke gawar a cikin wannan rubibi. Sai dai a binda ya Ιaure musu kai rasa muhimman takardun mijin Anum a gidansa. Bayan wasu watanni kuma akazo musu da batun an Ζwace duka kaddarorin nasa dake a Ζasar ta Syria. Basu da ikon nuna rashin yarda tunda sunsan hakan shine dokar Ζasar ga duk wanda aka kama da irin wannan laifin. Badan zukatansu sunso ba daga haka suka rufe babin Anum da duk abinda ya shafeta. Sai kuma gashi kwatsam bayan tsahon shekaru sunci karo da mai tsananin kamanni da ita a Nigeria, tare kuma da mai tsananin kamanni da mijinta matsayin ubansa. Wannan abu ya rikita Jay matuΖa, harma yaji a aransa inama Ummu da mahaifin Anum na raye su tayasa wannan al'ajabi.....
Ta Ιasan da Jabeer yayine ya sakashi dawowa hayyacinsa daga tunanin daya tafi, Jabeer ya nuna masa agogo da faΙin, “Boss asuba fa na gab da shiga, muyi abinda ya dace kafin masu Ζarfin faΙa aji suce wani abu”..............✍
0 Comments