TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Sanyi da zafi cmplt nvl

  💫 SANYI DA ZAFI 💫

BISMILLAHI RAHMANI RAHIM


 ✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣


Anatse yayi sallama yashiga wani babban falon wanda suke kira da Shakallo dan sirri kadai kesa a shigo cikin falon, wani irin kirar samfarin gini akama dakin kaman wani museum, yanada fadi da kirma dakin ga wasu ado na gwalagwalai sai babban carpet daya lullube ko’ina a girman falon, sai filoli na tumtum dasuke jejjefe akan carpet din na kishingida anmai ado na sarauta a jikinsu.

Mutane biyar ne zaune a falon maza hutu sai mace tsohuwa guda daya, Mai Babban daki wacce take tsohuwa ta manyanta dan akalla zatai 76 da idanunta sukai jazur tana sanye da Alkaybba hannunta rikeda tissue dakuma charbi tanaja, sai Waziri, Wambai, Makama dakuma Sarkin dawaki, chan kuma saiga wasu Manyan dattawa maza guda biyu dake kama da Mai Babban daki sun shigo sun zauna suma, dan faduwa gabanshi yayi dan haduwan mutanen nan wanda bayan sarki sune masu fada aji a fadan nan kasan babban abune, karasowa yayi tsakiyan dakin sannan yasami waje yazauna yakalli Mai Babban daki yace “Gwaggo kene kika aika akirani”? Girgiza kai tayi kafin ahankali tasa tisssue saman fuskanta tashare hawayen tasss sannan tace “aminan mahaifinka sukasa akiraka amatsayinka na babban dan sarki Kabeer” dasauri yadagokai yakallesu sauran jama’an dakin dake kallonshi yace “tooh” anatse babban cikinsu Makama yace  “kannenka duka sun iso? Dan karfe hudu zamukai Sarki makawancin sa” cikeda kamala dakuma natsuwa yace “Yarima Halilu, Ibrahima, dama suna nan, Munir yanzu yakirani jirginsu ya sauka a Abuja, shikuma Umaru yanzu haka jirginsu yatashi daga lagos din shikuma…..” yay dan shiru, atare dukansu yan dakin sukace “Yarima Riyad fa”? Adan hankali yasauke yar boyayyen ijiyan zuciya yace “nakirashi ba adaddi bana samunshi” salati mai Babban daki tasaki tace “bantaba ganin gantalallen yaro irin Riyad ba, yau yana Egypt, gobe yana Cyprus, jibi yana Oman gata yana zanzibar, citta yana China ko Iceland, ohh ni Shatu, chanake yau yana France ka gwada number shi ta chan kuwa Dan Buri? Idan baka da number kaje wajen Fulani ka amsa” cikin murya mai laushi Dan buri (Kabeer) yace “Gwaggo kema kinsan baitaba yin cikakken wata daya agari dayaba yabarta yatafi wata, kuma har ita mahaifiyarshi Fulanin batasan inda yayi ba dan nasameta itama tana kiranshi baya shiga, ni narasa mecece matsalan Riyad da ya gwammace yayta yawon duniya daya zauna akasarshi inda aka yankemai cibiya, ya girma baisan…….” Hannu sarkin Wambai yadagamai yace “ya isa” yadan sauke ijiyan zuciya yace “yanzu dai sabida shi bazamu jinkirta yima sarki abinda yakamata ba, nasan duk inda yake aduniyan nan zaiga news na rasuwan mahaifinshi dan haka zamu ganshi, yanzu tashi katafi” tashi yayi ahankali yamike yawuce yafita yanajan dan tsaki aranshi bayan yakai waje.

Cikeda bacin rai daya daga cikin jama’an dake falon yace “Gwaggo I’ve said this time without number to Mai Martaba he should call Riyad to order, duk cikin yaran Sarki babu gantalalle kaman Riyad, yaki zama ya koyi komi na al’addun mu, yanzu me za’a gayama jama’a akaga shine kawai bayanan” kowa na dakin binshi yake da kallo sai dayan dake kusada shi da ake kira da Usmanu yace “a’a Yaya Riyad yarone mai natsuwa dukanmu nan munsani sana’o’inshi ke kaishi kasashen nan kuma Mai Martaba shiya ya aminta da hakan ya bashi go ahead tunda yaga yaron nada passion for business, Riyad yaro ne mai matukar kyawun hali ga tausayi dukkan mu anan munsan da hakan” cikeda zuciya yace “kai ina magana harka isa kabani amsa Usmanu” cewan yayan da ake kira da Hambali, zasuhau gardama Mai Babban daki tace “shup! Hambali Usmanu kunsan dan uwanku ya rasu kuwa? Fada kuke kokarin yi sabida danshi?” Shiru duk sukayi basu kara magana ba…


Direct flat din mahaifiyarshi Dan Buri yayi wacce take uwargida, wani irin babban gidane da is as if daga inda yake zuwa side din zaije wani anguwa ne, kana ganin Masarautan kasan akwai kudi bana wasaba, dudda ga mata ana koke koke bai hanashi yawuce su yashiga cikin flat dinsu ba. Tana zaune tsakiyan mabiyanta tana kuka yamata alamu da idanu datazo yayi sama, mikewa matar da akalla zatai 48yrs tayi tana gyara lullubi tabishi idanunta sunyi jazur, dakinta yabude kofa yashiga dasauri itama tashigo yamaida kofan yarufe yana manna key, cikin rage murya irin ta munafukai kaman ba itace ke kuka afalo yanzun nan ba tace “ya akayi? Me suka cemaka” Dan murmushi yayi yace “har yanzu ba’a sami Riyad awayaba Mama, abin yamin dadi” dasauri ta dunkulle hannu tawani watsa a iska tace “da kyau Alhamdulillah! Nifa dama Riyad ne kadai matsalata Dan buri dan duka yaran sarki kafisu kudi, kafisu ilimi sannan kafisu connection, gaka kafito daga tsatso mai kyau tsatsona, kuma kai akafi sani afadan nan, Riyad shikadai ne zai nuna maka arziki dakuma kwalin karatu tunda yanada PHD yanzu, amman banda haka meyafika dashi yaron da ko mata baidashi anata gulma ma ana cewa ba lafiya gareshi ba yanda yaki yayi auren nan, kowani Bafade ko jama’an Babbanka za’a tambaya wasukafi so yazama Sarki kowa cha zaiyi kai kai akafi sani kaine jagoran gidan nan kuma dan sarki na fari kasha kuruminka kaman kazama sarki kagama, yanzu dai bari a bunne sarkin anjima dakaina zanje wajen Mai Babban daki anjima, banda Riyad Baffanku Hambali shine mayen kujeran kuma zanyi komi na kaudasu, yi maza wuce katafi waje sabida jama’a su ganka ashaidaka, duk wani kaninka ko kanwarka dazasu iso ka tsaya ka rungumesu kanuna musu soyayya, kazama kaine tsaye akan komi kana kula da komi kaji hakan zaisa kasake farin jini, yanzu tafi tafi ko me ake ciki kadinga fadamin kodako awayane kaji, Mai Martaba yariga ya garzaya saidai kuma mu hadu alahira Mulkin nan kuma tun kafin akaishi makwanci zan fara shige da fice saka akai, kaine d’ana dan fari kaine kuma magaji” Murmushi yamata sosai harda dan dariya yace “Mama kinyi ne arayuwa” da sauri ta shafa fuskanshi tace “kaga daina nuna farin ciki yi fuskan nan ne kaman kai kadai akama mutuwan nan agidan nan” gyadamata kai yayi yakoyi sakwa sakwa da fuska uwa zai fashe da kuka nan ko ranshi fess yawuce yafita daga dakin.


Komawa yayi waje inda dubbanin jama’a suka taru ga kannenshi su Halilu, Ibrahim, Shu’ibu duk sun iso da Iyalansu da akai cikin gida dasu Munir shine last person daya iso wajajen yana zuwa wajen da Babban wan nasu ke zaune yayi cikin jama’a tareda yayyinshi kafinma ya gaidasu yace “Dan Buri kasami Riyad?” Girgizamai kai yayi kaman salihin  nan yace “no tunda kun iso yanzu za’a sallaci Baba bazamu jirashi ba kodama yana hanya ne sabida shi bazamu bari Baba ya kwana ba” Munir baice komiba yajuya yafito zuwa wani waje da ba mutane sosai yaciro wayanshi yashiga kiran Riyad danko jiya sunyi waya wuraren 1 nadare but numbershi baya shiga yanzu harzai maida wayan kunnenshi kaman wanda yatuna wani ba yashiga email nashi ya aikamai sako sannan yawuce yakoma ciki akai Alwala aka sallaci mai martaba aka bunneshi nan cikin fada.

Magana sai yawo yake kan duka yaran sarki sun sallaci mahaifinsu banda Yarima Riyad dan Sarki na biyar cikin yaran sarki maza guda shidda ran Dan Buri fess har wani kara haskakawa yake jin yanda rumors din ke flying.

Cikin gida Munir yashiga tareda yayyinsu zuwa babban falo da duka matayen Marigayiya Sarki ke ciki kowacce zaune sanye da hijabi idanunsu jazur ga yan uwa da abokan arziki duka aciki, wajen Fulani suka fara zuwa dukansu yaran anatse suka gaisheta amsa musu tayi suka wuce wajen Fulani 2 suka gaidata itama ta amsa su suka wuce wajen ta uku itama ta amsa ta hudun suna gaida aka dan zauna akai addu’a aka shafa sannan suka fice suka koma wajen maza dan karban manyan baki top politicians manyan kasa from across the world.





💫 SANYI DA ZAFI 💫

   EPISODE 2️⃣

✍🏻M SHAKUR



Kusan gudu gudu, sauri sauri yake tafiya acikin airport din bai damu da bala’in gajiyan dayayi ba sabida economy ticket yasamu bama business ko first class ba, tunda aka haifeshi yaune first time daya taba flying economy, kafafunshi sun sandare abunka da mai tsawo sunma kumbura. 

 Fitowa yayi daga arrival yafara tafiya dan zuwa wajen parking motoci wasu mutane biyu biye dashi abaya dake sanye da suit bakake da glasses akan idanunsu, lift yashiga harya danna 2nd floor kofan zai rufe mutane biyun suka  sako hannunsu ciki kofan yakoma yabude dan dago kanshi yayi yaga wani black mutum ne yana sanye da suit baki ga wanima exactly irin kayanshi suka  shigo elevator din suka danna boturin dazai rufe kofan, kofan yarufe yafara moving sama, dauke kanshi yayi daga kallonsu yadaga hannunshi dake daure da agogo na Rolex dan duba karfe nawa yanzu hakanan yaji bai natsuba amman yadake yana tsaye inda yake rikeda bag pack din dake rataye shoulder nashi that is very fine and unique dan babu kalan su ma a Nigeria, hannu daya daga cikinsu yakai ya danna lock elevator ya tsaya chak tareda juyowa yana zaro wani wuka daga bayanshi in seconds yakai zai chakamai aciki chak Matashin yarike hannunshi yana kallonsu cikeda fargaba da tsoro da komima, dayan mutumin shima yaciro tashi wukar yace “au gardama zakayi bazaka bari mu kasheka ba salin alin mu karbi ragowan payment dinmu” shima yaciro wata karaman wuka zai chakamai kwasheshi yayi da kafa yafadi akasa wukar tafadi zai dauka yatake hannunshi da boot din kafanshi, yawani lankwasa hannun wanda yarike tareda sa kafa yadakeshi a balls dinsa cikeda azaba gayen yayi ihu yayi baya yakama gaban wandonshi yanaji kaman zai mutu da sauri guy din yasa hannu yabude kofan elevator din baimasan wani floor bane suke kawai yafice dagudu gudu sauri sauri dayan dake kasa yatashi yace “call the rest bari nabishi” yafice yabar wanda ke rike da gaban wando yana kokarin kiran waya, yashiga gudu shima yana binshi abaya, sosai yake gudu ganin daya yabiyoshi yanakai hannunshi cikin wando dan ciro wayanshi yakasa kawai yahau staircase yashiga sauka yana kallon baya jin gudun sahu dayawa ana biyoshi dudda baya ganinsu dan basu riga sun hayo benen ba ganin wani kofan restroom na mata dan ansa ladies ajiki yasa kawai yabude kofan yafada jiki wani kalan mugun karo sukaci dan tana shirin fita ne tai tangal tangal zata fadi da bala’in sauri ta dafa bango shikuma yajuya ya tura kofan bayin dasauri tareda saka sakata na sama da kasa yana kara murza jam lock sannan yajuyo daidai tana dagowa tana shafa goshinta cikin tsananin fushi dan tadan buge kuma taji zafi zatai magana, cikin a very soft yet anxious voice guy din yace “please ki boyeni some guys naso su kasheni ne and call the police” dudda taji zafin bigewan datayi amman ware manya manyan dara daran idanunta tayi kaman fitila tana kallon mutumin dayashigo cikin bayin mata da ranan nan Allah yaso ba kowa ciki ma, farin guy ne bawai irin fari sosai dan zata fishi haske but yanada normal fair skin not black skin, dogo wanda akalla zaiyi 34-35 ko 36yrs hakanan, baida kiba at the same time baida rama, yana sanye da riga na latest collection na Dior fari yadaura wani leather brown jacket asaman sa da yabar boturan abude bai rufe ba hakan nasa kana ganin farin rigan ciki, saikuma yasa  jean na Rick Owens, sai wani boot dake kafanshi brown na Tomford mai bala’in kyau da agogo daure a writs nashi na rolex, yanada very very dark hair dake nan kwance so wavy, dark eyebrows da eyelash nashi yamafi na wasu mata yawa, ga dan gemu dayake dashi da saje acike dudda gemun baida tsayi sosai looks like yana trimming gemun dan hair na wajen gabaki daya na dsame length, lips nashi are full irin asalin masculine lips that are a bit pinkish, idanunshi sunyi jaaa sosai, ganin yanda take kallonshi yasa yace “call security” hankalinshi atashe yadanna kofan da hannunshi yana kallon kofan jikinshi nadan rawa kana gani kasan da gaske he’s in trouble jin gudun mutane dayawa haka ga maganan su yana tashi kasa kasa “baku ganshi ba? We have to kill him ance kar mubari yakai gida araye wannan kofan fa kunduba ciki ko ya boye wajen”?  Hankalinshi atashe yajuyo yana dan zaro idanu hakan yasa itama gabanta yafadi bayin tashiga kallo kafin idanunta su sauka kan cart din garbage can dake wajen wanda take juye dattin bayi aciki ta gungura tafito dashi takai bola, daga kafanta tayi without making sound taje ta tsaya kusada can din tasa hannunta ahankali tabude marfin sannan tadago kanta daidai sun fara knocking kofan zaro idanu yayi da sauri ta nunamai can din da hannu alamun yazo yashiga nan da sauri yazo ya tsaya kusada ita yakalli bolan cikin can din wani kalan yatsinewa cikinshi yayi yaji kawai amai yatasomai da sauri yadaura hannunshi kan bakinshi jin aman zai fito, tazaro idanu tana kallonshi yau da babuma wani bolan kazanta sosai ma shine zaiyi amai lallaima, daidai an kara knocking dasauri da murya kasa kasa tace “kaga idan bazaka shigaba nifa ba ruwana, kafita ni nacigaba da aiki na, I don’t have any security number I don’t work here yau kawai an kirani nai replacing wata ne just for today” juyo da kanshi  yayi yakalleta itama kallonshi tayi da manyan idanunta kusan iya kirjinshi tsayinta ya tsaya daidai anyi mugun knocking kaman za’a balle kofan baisan lokacin dayay tsalle yafada cikin trash dinba yasa hannunshi yana kama hancinshi lekowa tayi takalli ciki yanda yakeyi yasa tai dariya dayasa fararen  hakoranta suka bayyana more of dariyan mugunta tace “yi bacci toh” kallonta yayi yanda take dariya dimples nata na lotsawa bama ta tsoro yanda kasheshi akeso ayi, bama ta tsoro tana mace itama sujimata ko su illatata, he’s just staring at her da suprise, jakanta dake kan slap ta kalla saita wuce da sauri tabude taciro wani black gyalenta na abaya tazo wajen ta warware ahankali ta yafa kanfuskanshi, wani irin lumshe idanu yayi jin kamshi mai sanyi daya sauka kan fuskanshi mai ni’ima in this moment na wari dayake ciki sai kuma ya sauke gyalen da sauri ya kalleta yace “wat are you doing?” Tana kallon kwayan idanunshi itama ba kunya ko shakka tace “datti zan watsa akanka yanzu so brace up” takai hannun tadauki thrash can dake kasa wanda bata riga tajuye dattinshi ba kawai tajuye  asaman kanshi tana murmushi ganin yanda yake kallonta kaman zai rufeta da duka tace “I am saving your life here it’s your choice” wani kalan ijiyan zuciya yake saukewa tsigan jikinshi natashi da kyar yaja gyalenta yarufe fuskanshi dashi yana rufe idanun duka dan yakasa standing dattin datake watsamai akai ta ijiye can din tasa hannunta dake sanye da working glove nata ta kwashi sattın ta rurrufeshi da kyau sannan ta rufe marfin tadan sauke ijiyan zuciya cike da karfin hali tawuce tai wajen kofan tabude cikeda masifa tace “wai waye ke knocking haka ina aiki”? Ganin maza kusan biyar yasa tadan koma baya kadan ta tsaya chak tana kallonsu dudda gabanta na faduwa bata nunaba dukansu kallonta suke ganin wata yarinya da akalla zatai 22yrs haka tana sanye da cleaners uniform riga da wando ash color tasa wani karamin farin hijabi daya tsayamata iya kirji hannunta sanye da glove kafafunta sanye da rain boot, cikin rashin tsoro tace “baku iya karatu bane duk girmanku ku gane ladies restroom ne nan”? Dukansu kallonta suke ganin yanda take musu magana gata wata kalan kyalkyawan yarinya fara sol saidai akwai uban baki ga rashin kunya ga muryanta shegen zaki kaman zai fasa dodon kunne, babban ne yahade rai yace “ke wani bai shigo nan ba”?  Wani kalan matsiyacin kallo tamai tace “kai nan wajen yamaka kama da inda wani zai shigo”? Dukansu baki suka sake suna kallonta daya daga cikinsu yace “ke kinsan waye mu kike mai rashin kunya”? Tana kallonshi tace “kai kasan wayeni zakuzo ina tsakiyan aiki na bayan nayi stating agaban kofa working no entry kunzo kuna bubbugamin kofa kuna maza toh ubanme kukazoyi nan kuje men restroom mana, I will call security wlh” kallonta Oga yayi this loud girl can ruin work nasu ta tara musu jama’a yanda take this vocal ma killing her will never be easy still saita tara jama’a, they don’t want scene hakan yasa yace “please let her be she’s crazy, I don’t want problem, ku rarrabu kuje mu nemoshi ni nasan yana floor din nan” tsaki tayi tace “mahaukata kawai” dukansu su shiddan juyowa sukayi suka kalleta wlh ko dar batajiba tasa hannu ta maida kofan ta buga tarufe tadauki wayanta ta danna waka tamaida earpiece tacigaba da mopping kasan wajen wanda shiya rage mata dama tariga tagama wanke cikin bayukan yanda takebin wakan tana aikinta bata missing any verse wlh zaka dauka mawakiya ce kuma da karfi take wakan abinta..….



Dudda yanajin warin bolan dayake ciki kaman zai kasheshi ga tsoron dayakeji but hakanan muryanta da yanda take wakan hold on na calming nashi down sosai, muryanta yamafi na asalin wanda yayi wakan dadi, what a voice! Tass tagama aikinta ta jingine komi inda zata jingine sannan tadauki jakanta tarufe tagoya abaya tasa hannu tabude kofan bayin hada ido tayi da maza biyu daketa sintiri awajen ta ballamusu harara tacire board na close dake gaban kofan bayin takoma ciki ta ijiye sannan ta gunguro garbage can din da kyar sabida nauyi amman ta daure tafita tafito dashi ko kallonsu batayiba saima wakanta data cigaba dayi abinta tawuce tasauka har kasa tazaga baya inda suke ijiye dattin saida ta jujjuya ganin babu kowa yasa tabude marfin bolan batare data kalli cikiba tace “you are safe yanzu you can come out” kafinma ya yunkuro tajuya abinta tahau tafiya dan sauri take is already 3:30 by 4 zata shagon abinci gashi this whole drama yabata mata lokaci, da kyar ya iya ya lallaba yafito daga bolan sai amai duk wani abu dayaci saida ya amayar dashi sai kakkabe jikinshi yake yadago zai mika mata gyalenta daidai tanashan kwana harta tafi, he wanted to say thank u dudda she’s a crazy wicked girl tana zubamai dirt tana murmushi but she helped him, hannunshi yakai aljihunshi yataba but baiji wayanshi ba kuma baisan a ina ta fadi ba wlh kuma shi bazai duba bolan nan ba, daidai wani cleaner na gunguro nashi bolan dasauri yace “please bani aron wayanka nakira” binshi yayi da kallo ganin kaman ba lafiya yasa yabashi wayanshi Munir yakira kafin yayi magana yace “Munir kazo ka daukeni a airport pls karka fadama kowa kana zuwa katambayi wajen zuba bola ina wajen” kafin yayi magana ya katse wayan yabama yaron yazauna awajen kawai feeling terribly sick kusan 1hr yana wajen  jikinshi yadau mugun zafi ga tsigan jikinshi na tashi kaman zai mutu yana zaune ahaka yaji ance. “Riyad” dasauri yadago kanshi da gudu gudu sauri sauri Munir yataho wajen yace “what happened to you like this? Wat are you doing here? Why are you so dirty”? Tashi yayi yana kokarin yima Riyad magana yace “someone tried to kill m…..” kawai ya sume da kyar Munir yasamu wani cleaner yazo kawo datti shima aka tayashi daukanshi suka tafi mota aka sashi sai gida bayan yakira Mom akira Dr.


Tawani special secret gate Munir yabiyo aka budemai already ga mutane tsaitsaye Gwaggo (Mai Babban daki) gawata black beauty mata dake sanye da hijab mai dan kiba (Mom), Wambai, Waziri, Kabeer da su Halilu, Ibrahim da Shuaibu, Baffa Mujitapa dukansu suna wajen da family Dr nasu, yayi parking agurguje Munir duk sukai wajen fashewa da kuka Mom tayi tace “what happen to yarona Munir? Wakeson kashemin shi daga shigowanshi garin nan? How did they even know ya shigo? Gwaggo jini a hannunshi look, Doctor do something” Mom tai maganan tana kama hannunshi ashe wukan ta yankeshi dazu, atare dukansu mazan suka ciccibeshi zuwa wani dabkareren flat na Mom Gwaggo tace “meya sameshi haka Munir? Jibi jikinshi? Meya faru Munir”? Dasauri Munir yace “Gwaggo nima bansani ba but kaman he was attacked ne, yana kokarin fadamin wai ana kokarin kasheshi ya sume ba wayanshi taredashi, shi babu akwati, akusa dashi, awajen bola naganshi da bag pack yana mota dawani dan kwali black, kafin yafadamin komi kuma yasuma” gam Mom tarike hannunshi har daki kan wani taskeken gado aka kwantar dashi Dr yashiga dubashi yanda skin nashi da fatanshi keyin wani bororo dahar wani motsi suke yasa yace “a chanzamai kayan jikin nan nashi maza, ku goggogemai jiki with clean towel, allergy ke damunshi, he’s allergic to dirt da kazanta right from small, kuyi sauri pls” fita kowa yayi daga dakin akabar Munir da Mom, Waziri da sauran duk suka zauna a falo yace “wazai attacking yaro daga durowan shi kasan nan?” Anatse Wambai yace “call the police I think sai anbincika airport din maybe ta CCTV za’a gani” faduwa gaban Kabeer yayi amman yadaure yaranshi always do a clean job he hope bazasu kwofasashi ba, fitowa Munir yayi yace “Dr an gama” dukansu komawa ciki sukayi Kabeer sai tsaki yake aranshi shida yakeso kowa yaji haushinshi amman jibi yanda kowa ke nan nan dashi, attention yakoma kanshi ma infact, skin nashi gabaki daya yakoma so red, drip akamai fixing da allurai ciki Dr yakalli Mom datafi kowa damuwa adakin yace “anjima kadan zai farfado don’t worry” dan murmushi tayi tareda gyadamai kai Waziri yace “ki zauna dashi” Gwaggo tace “nima ina nan kome za’a kawomai kowa zaizo yadubashi saina ganshi inga uban waye keso ya cutar mini da jika, bangama kukan mutuwan d’ana ba yanzu halakamin jika za’ayi  wlh jinina yasha karfin kowa” kallon Munir Mom tayi ahankali tace “thank you Munir” gyadamata kai yayi yawuce yafita daga dakin hakan yarage daga Gwaggo sai ita, dafata Gwaggo tayi tace “ki tsare yaron nan ki dage da addu’a akanshi, tun ranan da aka haifi Riyad akace yanada taurari masu kyau kuma babban mutum ne shi, kiduba kigani yaran marigayi maza shidda amman shi kadai akeso ahalaka tun yanzu kenan bama asan waye zai gaji kujeran sarautan ba kenan amman so ake akasheshi balle kuma ace shine zai gaji sarautan ki tashi tsaye Maryama, saikin tashi tsaye, kinyi zaman gidan nan basai na fadamiki hadarorin dake cikinsa ba, inde kalubale ne yanzu Riyad yafara gani, idan kuma yazama Sarki yadinga ganin kalubale iri iri kenan har abada, ki tsare yaron nan, kizama idanunshi kunnuwanshi uwa uba kizama inuwarsa dakuma lullubinsa” gyadama Gwaggo kai Mom tayi takama hannun Riyad tarike gam tana kallonshi tace “Gwaggo meya musu Riyad dako zaman gidan nan baiso, na tabbata baimason ya gaji kujeran nan, dan bata gabanshi” Gwaggo tace “kwarai” Mom tace “shi kadai Allah yabani, shi kadai gareni, Riyad kadai Allah yabani yau ana kokarin rabani dashi” kankame hannunshi tayi tace “Gwaggo zan iya zuwa bangon duniya sabida Riyad! Kuma nayi alkawari duk Wanda yace zai cutar da yarona saidai yafara dani dan daga yanzu zan zama shamaki tsakanin Riyad da komi na duniyan nan, zan zama inuwa hazo zan lullubeshi nakuma kareshi daga duk wata hari” sosai Gwaggo take kallonsu sai kawai tai murmushi tadauki charbi ta tacigaba da ja itama bini bini tana tofama yaron addu’a aka.


💫 SANYI DA ZAFI 💫

EPISODE 3️⃣

 ✍🏻M SHAKUR



4 daidai tashiga wani babban kanti na abinci irin local restaurant din nan, wata katuwar mata dake zaune a tsakiyan shagon kan kujera ga lalitan uban kudi a hannunta tana kirgawa ne ta kalleta tace “Allah yasoki baki latti ba” batace komiba kai tsaye tace “ina wuni Maman Miwa” batare data amsaba tace “nidai je ga wanke wanken ki chan na jiranki” bata damu da yanda tamata maganan ba dudda akwai mutane a shagon sunacin abinci tace “bari nai salla naje nayi” bata jira amsanta ba tawuce ciki chan bayan gidan shagon bayi taje tacire kayan jikinta tafito da dogon riga na abayan dake jakanta tana neman gyalen ta tuna tabawa mutumin nan tsayawa tayi chak sai kawai taja gajeren tsakiya saurin datake tazo nan yasa ta manta bata amsaba, karamin farin hijabin tasaka ta dauro alwala tafito tasami waje tai salla sannan ta cire hijabin tasa kan igiya fari ne batason ruwan wanke wanke ko mai ya bata mata taje gaban makwarara, ga wanke wanke zaka dauka na gidan biki ne ga manya manyan tukunyan abinci, omo ta dauka ta tara ruwa abaho dukta kawo sannan ta dauki wayanta kirar vivo duk taci screen tasaka earpiece ta danna waka ta soke wayan aljihun dogon rigan tashigayin wanke wanken da sauri sauri dan tanada kuzari sosai batada kasala ko son jiki.

Wata yar budurwa ce tazo wajen ganinta tana wanke wanke tana waka kasa kasa like zero worries dinnan yasa ta harareta tajuya tafito tadawo cikin shagon tazo gaban mahaifiyarta dahar lokacin take kirga kudi tace “wai Mama Yar gidan HIV dinchan kikesa take mana wanke wanke har yanzu banace ki sallameta ba gashi gashi abinda ake cewa ita da Mamanta sunada shi” batare da maman ta kalletaba tace “koyar gidan kanjamau ce ba HIV ba ina ruwana ko kinada wanda zaki samo dazatamin wanke wanken nan ta share ko’ina har zuwa katon shagon nan akan dubu biyu kullum aduk fadin garin kanon nan?” Baki yarinyar tabude zatai magana Maman Miwa tace “kinga ki kyaleni fa, nagadai nace kiyi aikin nan bayi zakiyi ba” dasauri yarinyar tace “Mama ni kyamanta nakeji wlh, sunada HIV tana mana wanke wanke” dasauri Maman Miwa tace “wai sau nawa zan gayamiki Maman ta kedashi ba itaba yarinyar datake karatun likita, to koma tanadashi me ruwana nagadai ciwon nan ajini yake kuma baya kwarara acikin ruwan wanke wanke ko? Miwa dan Allah ki barni na kirga kudin nan kinatasa ina mance abinda na kirga” tsaki yarinyar tayi tawuce tafita daga shagon cikeda bacin rai.

Kafin 1hr tagama wanke wanken nan tass, tukunyoyin har bayansu ta wanke kal sai kyalli suke ta share ko’ina tashigo shagoma ta share tsaf tai mopping lokacin biyarda rabi sannan takoma baya tasa hijabinta tadauko jakanta ta goya abaya tafito tazo gaban Maman Miwa tace “nagama” kallonta Maman Miwa tayi tace “ohh kudinki ko”? Gyadamata kai tayi, kudin hannunta Maman Miwa tashiga kirgawa taciro 10k tabata tace “gashi na litinin zuwa yau juma’a” murmushi tayi for the first time dan gaskiya she hardly smile kaganta tana murmushi ko dariya to sai in tana tareda Mamanta, takirga kudin tass dubu goma chip chip tace “nagode Allah yabiyaki” tajuya tawuce kallo Maman Miwa tabita dashi ance duk muguntan ka kaji an maka wani addu’an saikaji ranka ya sosu harta fita waje Maman Miwa tace “Rasheeda!” Dasauri yarinyar tajuyo jin an kirata, komawa cikin shagon tayi tace “na’am gani” kallon sales girl dinta Maman Miwa tayi tace “samata shinkafa da tuwo a takeaway takaima Mamanta” wani kalan murmushi tayi dayasa wani hot dimples suka lotsa a kumatunta Ya Allah! She looks damn beautiful dasauri tace “nagode sosai, nagode nagode” Maman Miwa sai kallonta take dan wlh today is the first time in almost 3months data fara musu aiki take ganinta tana murmushi, yarinyar kam badai kyauba, ta tabbata badan cutan su ba da tuni wani babban Alhaji ya aure ta, kawomata abincin akai a leda ta amsa wannan karan saida ta duka tace “nagode sosai Maman Miwa” murmushi Maman Miwa tamata tace “sai Allah yakaimu  gobe” gyadamata kai tayi tafice Maman Miwa tabita da kallo wani zubin she wants to be wicked amman kuma indai kai ba shaidan bane u can’t be wicked to this girl cus zata maka aiki tsakani ga Allah dabazaka taba ganin abinda zakai complain akai ba, wanke wanke take maka tsaf, tai shara tai moping kaga ko ina na kyalli, banda haka  daidai da tsinke bata taba sata a shagon ba wlh ko kwayar magi bai taba bataba dudda ko basudashi, kowa ya tsaneta kowa kyaranta yake sabida Mamanta but if u look at it ciwo nakan kowa, zata gudu tabar mahaifiyarta ne sabida tabada HIV? No, ba HIV ba ko HIVVV uwarta kedashi uwarta ce, dudda ma taji labari ance mai kudi mahaifiyarta ta aura but taje tai fasikanci tasamo HIV yakorota yace cikin ma ba nasa bane, hmmm tasauke ijiyan zuciya tace “Allah ya kyauta dai”.


Tafiyan datayi zaiyi nisan tafiyan inda zakaje kabiya 200 ko 300 kan adaidaita sahu amman akafa tai tafiyan nan tana shiga layinsu ta tsaya gaban wani chemist ta kirga 6500 tabashi tace “ga kudin maganin nagode” karba yayi yace “an dawo daga aikin Rashy” gyadamai kai tayi batace komiba ya karbi kudin yana kokarin kirgawa daidai ta juyo zata fito wasu maza guda biyu na zuwa wajen daya daga cikinsu yakalli mai shagon yace “kai Bala nagaya maka idan kana bari yarinyar nan na shigowa shagon ka bazaka taba yin ciniki ba ni nama fasa sayan abinda nazo saya mtswww yawa kake wlh gaye” yajuya harya fara tafiya Rasheeda tace “ko dabba yafi jahilin namiji mara ilimi daraja tirr, adaije makaranta akaro ilimi katon banza” chak saurayin ya tsaya saikuma ya juyo yanuna kanshi yana kallonta kur itama Rashida ke kallonshi yace “dani kike”? Dasauri Mai chemist din Bala yazagayo yana daga marfin kanta yafito yace “badakai takeba Rashida tafi gida kudin sun cika nagode” wani kalan kallo tama mai chemist din tace “akanme zakace badashi nakeba Bala? Inba dashi nakeba waye yamaka kama da jahili awajen nan”? Wani tahowa gayen yayi azuciye zai daketa yace “zan sumar dake wlh ke” dasauri Bala yatareshi yace “me haka kai Sani dukan mace zakayi”? Wani kalan dariyan daru Rasheeda tayi tasauke jakanta dake goye abayanta ta ijiye ledan abincin hannunta duka akasa tanuna kanta tace “nizaka daka?” Tasake dariyan keta tace “billahillazi yauka tabani saidai uwarka ta haifo wani zan gwada maka ni dakake gani kaman maza dari ce anan, try me I will make sure namaka abinda baxaka so ka karabin hanyan danake bi ba” tai maganan azuciye cike da fushi da masifa da rashin tsoro, dasauri Bala mai chemist yakalli abokin Sani yace “please rikeshi ku tafi dan Allah Kamal” kamashi abokin yayi yace “muje Bros shareta pls ba riba a fada da mace” Rasheeda tace “kasan Jahili baida ilimin sanin hakan wannan dahar yanzu ake raba shayin safe dashi agida” haba wani kalan fizge kanshi yayi yakawo mata duka da duka karfinshi kaucewa Rashida tayi da sauri yasami bango batai wata wataba ta daga kujeran dake wajen na zaman mutum plastic chair ne ta rapkamai a fuska kafan kujeran ya yakushi bakinshi haba bakinshi sai jini ganin jini abakinshi yayo kururuwa zaiyo kanta da sauri abokinshi da Bala mai chemist suka rikeshi, itama Rasheeda cikeda fitina ba tsoro azuciye tace “ku sakeshi yazo bakaga komiba duk bakin dazai kokarin bullying dina wlh saina fasa bakin, kai kayi kadan kahanani sakewa agarin nan sabida ka ganka namiji, akan wani dalili zaku hanani sakat bazan iya zuwa nasai abubu? Shaguna nawa nadena zuwa na layin nan? Wannan danake zuwa yanzu shima kuce ban isaba sabida wani dalilin ku na banza da wofi, cuta nakan kowa, babu wanda yasan karshen shi, yes Mamana nada HIV and so what? Kubi duniya a sannu kai kanka bakafi karfin kasami cutan ba dakiki kawai mahaukaci, katon banza wanda ake gutsurama buredi agidansu har yau akasa dashi da kannenshi sabida baida zuciyan nema, kar Allah yasa ka kara zuwa shagon siyan abu, jahili kawai” cika shagon akayi da mutane sabida yanda Rashida ke zubamai zagi shikuma yana kokawa dasu Bala asakeshi ya daketa ganin yanda ta fasamai baki, cikin taron mutanen wani dan tsoho ya leko ganinta sai kawai ya shigo cikin shagon yakai hannu ya karbe kujeran ya ijiye gaisheshi mutanen wajen sukahau yi. “Barka da yamma Baba Liman” cikeda hikima na manya ya dubi Sani yace “ayakuri Sani, kekuma wuce mutafi” hannunta yakama yace “wuce mutafi” batai musu ba akumbure cikeda taurin kai tace “ni jakata” sakinta yayi yana kallonta taduka tadauki jakanta ta goya abaya da ledan abincin tarike a hannu tana nishi kaman kirjinta zai fashe sabida fushi saikuma ta dago azuciye dan tanada naci wani zubin kaman mayya, takalli uban mazan dake wajen duk ana kallonta tace “Baba Liman kagayama yan anguwan nan su kiyayeni nida mahaifiyata, bamu shiga gidan kowaba munyi sata, Mama harni baya shiga gidajensu sabida yanda kowa ya kyamace mu, bamu rokesu kudi ba, banzo nacema kowa yabani kaza zankai mahaifiyata asibiti ba dan haka su fita daga rayuwata dana mahaifiyata Baba, sufita na gayamusu, I am enough for Mamana! ni kadai zan iya kula da ita, nayi girma kuma Alhamdulillah inada karfin yimata komi kowa yafita harkana, ban nemi fadan kowaba ban shiga hurumin kowaba dan haka duk wanda yashigo tawa koshi waye wlh sai inda karfina yakare kagaya musu Baba Liman” tayi maganan with a sound warning, ahankali tsohon yace “ya isa!” wucewa tayi fuuuuu tafice daga shagon kowa na wajen jikinshi yayi sanyi wani dakeda shago kusada na chemist yakalli yaron yace “kudaina abinda kukeyi mutanen nan ba akanku suke zaune ba, wlh Allah zai iya saka musu, shidai cuta nakan kowa, yau dauka fasikanci matan tayi tasamu Allah masani amman ina mai tabbatar muku, gulma, keta, rashin mutunci da sa’ido da menene menene kukema matan da yarta kadai ya kore zunubansu” anatse Baba Liman yace “muji tsoron Allah, mun kyamaci mutanen nan shi kadai ya isa wlh kudena takura musu kar Allah yakamaku, kar Allah yakamaku” yawuce shima yatafi, dasauri Bala yace “nima kada ka kara zuwan mini shagona kaje wani chemist din” tsaki Sani yayi yace “ka dinga shiganmata ko zaka mutu iyayyenka dai damuka sani bazasu taba barinka auren tijararriyan yarinyar me kanjamau dinchan ba” yayi maganan yana ficewa dağa shagon abokinsa na binsa.


Gidansu na wajajen karshen layin, wani dan karamin gidane sosai ciki da falo daya ne sai bayi ba kitchen a tsakar gidan suke girki, ko’ina kal kal agidan, maida kofan tayi tarufe tasa sakata tasauke ijiyan zuciya sannan tai murmushi dan bataso Mama tagane ranta yabaci daganan zaure tai shouting “Mamaaaaa, Mama nadawo” tai ciki da gudu labule ta daga Maman na zaune kan dadduma kaganta kamansu daya sak da Rasheeda itama tanada haske but ba kaman Rasheeda ba, batada kiba ko kadan ta rame ta bushe sosai, duka duka bazata wuce 40 ba but she looks kaman wacce ta tsufa, tana zaune kan dadduma tanajan charbi, ijiye kayan hannunta Rasheeda tayi saikuma tai tagumi tana leka fuskan Mama tace “Mama kiyi sauri kigama kimin sannu da zuwa niii” tafadi a shagwabe, hannu Ammi tasa ta shafe addu’an datakeyi sannan tajuyo kawai saita kama kunnenta ta saman hijabin jikinta tace “dan kaniyanki ba alwala yakamata kiyo ba kizo kiyi salla ba” dariya sosai tayi tana yarfe hannu tace “wayyooo kunnina Mama zai cire” sakin kunnin Mama tayi tana murmushi looking so happy tace “imaza to jekiyo alwala kafin lokacin magrib yafice baki salla ba” tashi tayi tafito tsakar gida alwala tayi tadawo tai salla kusada Mama sannan tadauki jakanta tabude taciro kudin tasa a hannun Mama tace “Maman Miwa tabiyani, hotel din nan gobe suma zasu biyani kuma manager tace nakawo zanen tagani idan na iya sosai zasu saya” karban kudin Mama tayi tana kallo tana murmushi Rashida tashiga fito da abincin tace “nabiya nabawa Abdul kudinshi Mama ga abinci Maman Miwa tace nakawo miki” bubbude komi tayi ta tashi tafita dasauri tadauko ruwa a bowl tadawo tazauna takama hannun Ammi tasa aruwan tace “wanke hannun muci” wanke hannunta Ammi tayi ta ijiye kudin agefe ta gutsuro tuwon instead takai bakinta bakin Rasheeda takai dasauri Rasheeda tace “Ammi ke kici” ahankali tace “ni naci abinci namana shinkafa, keko nasan tun safe bakici abinci ba banda karin dakikayi ko kinci wani abu”? Hadiye tuwon bakinta tayı tana fikifiki da ido most of the time idan tana aiki mantawa da abinci take, hararanta Ammi tayi tace “bude bakin, kidena wasa da abinci kinji Doctor” gyadama Ammi kai tayi tana murmushi Ammi nasa mata tuwo abaki tace “ko biscuit ne buy and eat kinji” sake gyadamata kai tayi, haka Ammi tadinga feeding nata kuma sosai taci ita bama tasan takusan cinye tuwon ba saida takalli takeaway dasauri tace “Ammi  nacinye miki tuwon” murmushi tayi tace “haka nakeso dama Doctor” tass tacinye tuwon Ammi kuma taci shinkafan ba sosai ba dan batajin yunwa, sannan ta tashi taje tayo wanka da alwala tareda Mama sukai salla ta shiga tattara yan kwanukan zata wanke Mama tace “kibarshi jekiyi zanen ki zanyi wanke wanken” dasauri tace “Mama ni kidaina aiki, bayawa yanzun nan zanyi nagama zanyi zanen” kafin Mama tai magana tafice daga dakin biyota Mama tayi dudda haka tana wankewa Mama na dauraye wa suka gama suka dawo daki tayata Mama tayi ta kwaso board na zanen da colors nata da pen ta zuzzuba tafara zanen kome takeso Mama na mikamata suna cikinyi aka dauke wuta torch light Mama tadauka ta kunna Rasheeda tai murmushi tacigaba dayi sai wajajen 12 tagama tabarsu su bushe gobe zata sasu acikin frame, zama tayi anan danta huta kafin suje su kwanta sai bacci itakuma Mama na tattare brushes din tana dauraye mata su aruwa, munsharin ta da Mama taji yasa tajuyo takalleta ganin yanda take baccin azaune kanta na lilo.


💫 SANYI DA ZAFI💫

 ✍🏻M SHAKUR

EPISODE 4️⃣



She just wished all this ayyukan wahalan da suffering da yarinyarta yar karama keyi just to take care of her itane keyi mutane bazasu gane rahama ne Allah yamaka lafiya sannan yabaka karfin nema ba gashi tana neman wannan karfin ita tafita tayo aiki ta kula da diyarta daya tak a duniya tarasa, Rasheeda ce zuwa ayyukan shara da wanke bayuka, da wanke wanke just to get paid suci abinci ga school duk ita kadai dan yanzu ma suna hutun school, yarinyarta batasan menene dadin rayuwa ba tunda ta taso sai wahala, Rashida doesn’t deserve to be born like this, ta zaman ma yarta bakin tabo arayuwanta waye zai taba auren Rashida yanzu? Ko anzo ma gulman yan anguwan nan koransu suke, babu kalan sherin da ba’a musu, kowace budurwa irin Rashida nada kawaye ita batadashi kota fara kawance iyayen yaran zasu raba abotan sabida ansan diyar mai HIv ce, yar fasika ne gantalalliya dan haka babu iyayen dakeson yaransu suyi mu’amala da yarta, hawaye masu dumi ne suka gangaro daga idanunta dasauri takai hannunta ta share fuskan tass tareda sauke ijiyan zuciya ahankali tace “Allah na yarda ka kasheni da ciwon nan, Kama karomin cuta daban daban duk na yarda, amman Ya Allah kabama diyata farin ciki arayuwanta, Ya Allah ka kawomata karshen wahalan nan, Ya Allah idan mutuwata zai zamto abinda zaisa Rashidana tadena aikin wahalhalun nan just to take care of me Ya Allah ka dauki raina dudda banson na barta, Ya Allah spare my daughter this harsh way of living and take me instead” tasake share hawayen dasuka zubomata sai kawai tadaura kasan rigan atampanta kan fuskanta tai shiru takai 2min ahaka sannan ta mike taje inda take tallabota tayi tace “Raudah oya muje ki kwanta” ina batamasan anayiba baccin yayi nisa gajiya kuma kesata baccin kaman tamutun nan, kamata Mama tasakeyi tace “tashi muje kinji Rish-rish din Mama” Mama tai maganan tana dagata da kyar ina bamata iya tafiya kaman matatta, kakkamata Mama tayi tasata ajikinta tana tafiya da ita ahankali tanajan kafa kaman irin wacce tasha giya tai tatil din nan, uwar dakin babu komi banda wata yar katifa datake a gyare akasa sai kuma manyan ganamasgo guda biyu na kaya sai dan rio na kayan kwalliya da wasu kodaddun hodon makeup da gorunan turaren humra suke ciki saikuma wata benci haka da littafai ne cike na school akai saikuma lab coat da aka makala a nail na bango jikin aljihun an rubuta Dr Rash ajiki Mama ta kwantar da ita ahankali.



Karfe 4:30 daidai tabude idanunta adduan tashi daga bacci tayi sannan takalli Mama wacce taganta kan dadduma idan da sabo ta saba agurguje ta tashi waje taje tahura wuta tadaura ruwan wanka sannan tashare tsakar gidan taje ta wanko bayi ta watsa ruwan sanyi ita tafito tai alwala tazo ruwan yayi zafi tahadama Mama a bucket tadawo daki dan kaita bayin dan kafafunta na bala’in damunta tace “Mama muje kiyi wanka” tana rike da Mama har bayi Mama tace “karki jirani jeki salla” batai musu ba salla taje tayi sannan tafito ta daura tuwo a wuta ta kwashe kayan da Mama tasa sharp sharp ta wanke ta shanya tasake wucewa hanyar bayi tadawo da Mama dakin dahar ta gyara tafita waje takarasa tuwo tai miya tazuba komi a kula takawo daki sannan ta shirya cikin wani dogon rigan abaya baki wanda stones din duk sun ciccire tadau gyalen zata yana kenan ta tuna jiya saitahau dariya Mama dake shafa mai tace “ke lafiyanki kike dariya ke kadai?” Dasauri tajuyo ta taho wajen Mama tace “Mama wani dan gayun mutumi nasa a bola na zuzzubamai shara bakiga yanda yake makyarkyata ba kaman da zinare aka yishi ba kasa ba” yanda take murmushi tana dariya  yasa Mama tace “wa kikasa a bola Doctor?” Dan tsagaita murmushin tayi tabama Mama labari kunnenta Mama taja tace “Rauda wai mesa bakiji ne inda sun kasheki ke fa dakike musu rashin kunya ina kikeso nasa raina why mesa you are always putting yourself in trouble ne eh? Mesa bakiji wai kin dauka wani karfi gareki wai sabida wani baitaba chasaki ba ko” kaman zatai kuka tace “Mama yakuri to kisaki kunnena” sakejan kunnenta Mama tayi dudda bada karfi sosai ba tace “saina cireshi duka, wai mesa bakiji eh? Why wat if wani abu yasameki?” Ganin yanda takeyi da fuska kaman zatai kuka alamun jan kunnen namata zafi yasa Mama tasaki kunnen ahankali saikuma takama kafadanta cikeda damuwa sosai tace “Doctor kinason duk idan kin fita yanzu hankalina yadena kwanciya ne?” Dasauri ta girgizakai, ahankali Mama tace “to yimin alkawari u will not put kanki in any trouble again” murmushi tayi tace “I promise Mama bazan karaba” ijiyan zuciya kawai Mama tasauke dan tasan is impossible cus Rashida and trouble are besties, tashi tayi tawuce takarasa shiryawa ta yana gyalen akanshi ta kwashi uniforms nata tasa ajakan ta sannan tazauna tahada zanen tasaka musu frames Mama sai kallonta take kawai saida tagama tass sanan tazo kusada Mama lokacin 7 daidai tace “Mama maganin safe” tadauko magani bama Mama maganin tayi sannan tacire yar wayanta daga chaji tadauki earpiece dinta tace “Mama bari inje” cikin kudin data kawo jiya Mama tazare 1k tace “ga wannan kihau abin hawa kidena tafiya da kafa hotel din nan da nisa” dasauri ta girgiza kai tace “Mama ki ijiye duk nazuwa asibiti ne next week ni dakafata zan taka ai ba nisa ko ciwon kai kikaji ki kirani zanbar kome nakeyi na dawo zanyi aiki a hotel har karfe daya biyu yau ba airport zandaiga alert, sai karfe 4 ina wajen Maman miwa bye Mama na” dasauri Mama tace “to baxaki daure ko Lipton kisha ba tunda baki iyacin abinci dasafe” dukowa tayi ta rungume Mama tace “Mama zanyi latti ne nakai zansha a hotel din ai ana bamu coffee da biscuit bye Mama kinji” ta shafa fuskan Mama tana kallonta saikuma ta manna ma Mama kiss a goshi tace “Mama kinyi kyau wlh atampan nan zaki bani ita” dan maketa kadan Mama tayi tace “ba Dr yace kidena min irin abubuwan nan ba saina shafamiki ciwo” haderai Rashida tayi sosai tai sauri zata tashi hakan yasa Mama tarike mata hannu tace “zo to fushi kikayi banso kibar gida da fushi yakuri bazan kara miki maganan ba” hawaye idanunta suka tara saikuma tahadiye hawayen saikawai ta rungume Mama tsamtsam kaman yar yarinya tace “Mama ko duka ciwon duniya kikedashi ni zan fiso su dawo kaina ke naganki lafiyanki kalau, Mama kome kika dawo ko menene ajikinki you will always be Mama na nikadai, koda zan samu I don’t mind ni ko mutuwa yazo nafiso mu mutu tare ma” dasauri Mama ta daki bakinta tace “bazaki mutu yanzu ba sainaga yaranki jikokina” turobaki tayi tasaki Mama tace “Mama ni banson maganan nan I hate maza to the core bazan taba aure ba, dana auri miji irin wanda kika aura danni ba Babana bane gwara na mutu ahaka banyi aure ba, matsiyac…….” “Doctor!” Mama takirata azafaffe hakan yasa tai shiru tadauke fuska, ahankali Mama tace “karki kuskura ki zagi Babanki” kallon Mama tayi irin why are you still protecting him sai kawai tayi hanyar fita daga uwar dakan cikin sanyin murya Mama tace “he’s your father” jakanta tadauka ta goya tace “Mama he’s not my father ko sunanshi dakikasa nake amfani da dan babu yanda zanyi ba, Mama na tsani mutumin nan and I hate all men naduniya, nidai mudaina maganan banmasan maisa kikemin maganan maza ba to mezasumin? Akwai wani hanyar neman kudi daban iyaba? Mama namafi mazan karfi laaaa nama manta ban daga karfe ba yau” tajuya dasauri zata fita daga dakin Mama tace “kika daga karfen nan saina mammakeki wlh waike namiji ne yau naga bala’i a hannun yarinyar nan” dariya Rashida tayi ta tsaya daga bakin kofa tana kallon Mama tace “Mama bakiga saisa babu me kawomin raini ba sabida ansan inada karfi Mama dan Allah kibari nadaga kinji Mama 2mins” da hannu Mama ta nunata tace “wlh zanci kaniyanki, sokike ki mummurde ki koma namiji? Wannan harkan karfen wlh bazan yarda dashi ba jira nake rannan lahadi idan Lawali yazo ince yatafi dashi” dasauri Rauda tace “wlh Mama karki bayarmin da abuna da kyar nasamu mutanen garejin nan suka saidamin da abin nan dubu uku” baki Mama tabude tace “yanzu bakisa dubu uku kin sayi sutura ba sai karfe kikaje kika saya agareji tafi aiki ki dawo zaki gamu dani wlh agidan nan” dariya tayi sosai saikuma ta buga kafa tace “to kice bazaki bayarba wlh Mama kowa kikaba sai naje na karbo abuna kota katanga ne saina haura” haba Mama tarike tace “to wani daban zan bamawa ba Lawal ba sai inga idan tsafi zakiyi ki gane wana bamawa,  wuce kitafi” tace “bye Mama na, Mamana kyakkyawa mai gashi, Mama haryau gashina yaki kamo naki narasa maisa” kaman jira Mama take tace “sabida kin soma daga karfe ne saisa” dariya Rashida tayi harda kama ciki tace “laaaa Mama wlh wannan zuki tamallo ne” baki Mama tasaki tace “ni Mamanki ke karya Doctor”? Dan sosa kai tayi kaman mara gaskiya tace “uhnnn” kwapa Mama tayi tace “wuce kitafi zan gamu dake kika dawo ai anan zakizo ki sameni” nokekai tayi tana danne dariya tawuce tafita Mama itama tai murmushi ta daga murya daganan daki tace “ayi addu’a dai kafin afita daga gida Allah bada sa’a” tsayawa tayi tai addu’a sannan tabude kofa tafita abinta tana rike da frames na artwork datayi guda uku ga jaka abayanta she’s just a young lady da kana ganinta kaga strong, bright hardworking young lady, Nisan daga gidansu zuwa hotel din kusan tafiyan awa daya cur tabar gida bakwai takai hotel din by 8, Babban hadadden hotel ne shima gyare gyaran daki take da da bayika su wata wata suke biyanta 30k office na wajen da uniform nasu taje ta chanza kayanta taciro uniform din tana sawa Riga da wando ne tana kokarin saka karamin farin hijabinta wata tashigo dakin hakan yasa dasauri tajuyo hada ido sukayi da yarinyar tana ganin gashinta tace “Innalillahi Rashida kinasa attachment ne”? Dan zaro manyan idanunta  Rashida tayi dan bama tasan gashinta ya warware ba hannunta yarinyar tadaura kan gashinta bakin kirin gashi da sulbi ga tsayi sosai tace “wlh gashin kine Woww Rashida hala ku ba yan Nigeria bane” fizge gashinta Rashida tayi kaman fada tashiga parking tace “kada ki kara tabani” baki yarinyan tasaki tace “ohhh nidai bantaba ganin masifaffiya irinki ba daga na yabi gashinki Rashida sai fada” saka hijabinta tayi tace “aiki kikazo yi ko yabon gashi”? Tana maganan ta kwashi frames din tabar wajen yarinyar tabita da kallo har cikin ranta tanason tai kawance da Rashida but Rashida irin mutanen nan ne mafadata and too protective is as if batason mutane su shigo space nata because she don’t wanna get hurt oho, u can’t complement her, u can’t say anything to her fada but batada neman tsokana, bata shiga mutane ba ruwanta da kowa itadai tazo tayi aikin datazo yi lokacin tafiya nayi ta tafi ko minti daya bata karawa.


Sosai manager ke kallon zanen saikuma ta kalli Rashida tace “anya kene kikai zanen nan kodai satowa kikayi”? Zaro manyan idanunta tayi tace “tunda nake bantaba sata arayuwana ba idan baki yarda ninayi ba bani paper da pen da color namiki exactly irinshi agabanki” murmushi manager tayi takalli abin saikuma tace “zan saya akan 10k each sannan ki dingayi kina kawomin ko guda nawa ne zan saya” bakaramin dadi Rashida tajiba dudda zanen zane ne da har 100k zaa iya saya awani waje but bata damuba 10k is huge 30k ta kirgo tabata sosai Rashida taji dadi bata taba sanin zata iya saida zanenta ba kaman fa wasa taji ana maganan sayan frames tace ta iya manager tace takawo tagani jibi anbata 30k akan guda  uku anatse tace “nagode Ma Allah kara arziki” dan tabe baki matan tayi tace “tafi kifara aikin ki” wucewa tayi tafita manager ta kalli frame din tace “zan gayawa Oga 150k each nasaya wayyooo this girl is talented bata sani ba inhar Oga yasosu zance muyi ma all rooms na hotel namu nabama yarinyar tamin I will be fucking billionaire nabata 10k each ni na karbi 150k for each awajen Oga wow look at her work”.



💫 SANYI DA ZAFI 💫

  ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 6️⃣

Wallahi kanshi ma sarawa yafarayi jin maganganun da Mom kemai, first of all duk wani abun na sarautan su bayaso saisama baya iya zama agarin, baison hayaniya baison how they do things cus is always fighting, makirci and politics, and baijin tunda ya girma yatabayin cikakken 2months like good 60days agidan ba bini bini yabar country, lokutan salla ne yasan dole yake dawowa sabida yanda Baba ya maida abin mandatory yanason duka yaranshi to be home sabida hawan salla and other activities na al’adu, shi mutum ne da baisan mulki he prefer business nashi, he derive joy a business, it gives him purpose, for aure kuma dudda yasan culture nasu ne amaka aure abaka mata but shi kwata kawata baitaba sanin Mom zatamai hakaba cus Mom is highly educated and expose, itama bata cika biyema culture ba saisa ma take barinshi to live his dream life, ko kadan bai shirya aure ba cus bayason commitment for now, his plan is nan da 2yrs zaiyi aure yanzu kawai aure baya lissafinsa, dukawa yayi ahankali gaban Mom yadafa kafanta kaman zaiyi kuka yace “Mommmmm” ahankali itama Mom tana kallonshi tace “Riyaddddd! You don’t have to say abinda zaka fadi kasan nasanka sama da kowa aduniya ko?” Gyadamata Kai yayi Mom tace “I know how you despise sarauta, mulki infact bakamasan komi akaiba, I know for auren zakace baka shirya ba bakasan damuwan mace da sauransu” sai kawai takai hannuwanta tai cupping face nashi cikin tattausan lafazi tace “dama akwai abinda zan taba so aduniyan nan dabaza ka iyamin ba Riyad”? Ahankali Mom tace “I thought nine number 1 dinka like you always say”? Dasauri cikin raunin murya Riyad yace “Mom u are my number 1 kema kin sani” kai tsaye Mom tace “inhar nine number one din naka then karka karamin gardama kan maganan nan it’s an order allow me to do everything am I clear?” Yadade yana kallonta yanda take kallonshi babu wasa kan idanunta yasa ya sauke kanshi kasa alamun dai baiso but baice komiba, baya iyama Mahaifiyarshi gardama, cikin fushi Mom tace “kamin shiru? Ban isa dakai bane ko ban isa nace maka haka nakeso kayi kayiba”? Tai maganan tana shaking leg in anger, abu yahadiye awuyanshi har saida taga motsin adam apple nashi asanyaye yace “okay” tsayarda shaking leg din tayi tai murmushi sai kawai ta matso ta mannamai peck agoshi tace “I wish kowacce uwa zata sami d’a mai mata biyayya kaman Riyad dina data zama very very lucky, Allah maka albarka kaji, Haleema is a good girl tana matukar sonka tun tana yar yarinya, she will keep my son happy I’m sure of that, so karka damu, zancen sarauta kuma I will teach you everything and you will do well kaji”? Gyadamata kai yayi zuciyanshi duk ba dadi duka duka kwanan Babanshi nawa da rasuwa but kowa is after kujeranshi, look at matayensu kaman ba mazajensu ne suka rasu ba dukansu kokarin daura yaransu kan Sarautar suke sunma manta da rasuwan shima yanzu yazama sarkin one day haka matarshi zatayi kenan itama yana mutuwa all focus dinta will be yanda danta zai gajeshi bamatada lokacin yimai addu’a tashi kawai yayi yajuya yayi kofa.


Mom tabishi da kallo ranta fess, dolema Riyad dinta yadinga intimidating kowa, yafi duka yaran sarki kyau ga kwarjini ga haiba ga natsuwa, ga jan aji, ga kudi, ga rashin magana, ga rashin shiga mutane, gashi baida kallon mata shi kadai keda qualities na sarki and bazata hutaba saita maidashi sarki wannan alkawari ne!.


Dakinshi yashiga Munir dake danna laptop yabishi da kallo ganin yanda mood dinshi ya chanza tashi daya,   Wucewa yayi yafada gado yakife cikinshi tareda lumshe idanu Munir baicemai komiba yacigaba da abinda yakeyi abinshi.


Yana fita Mom ta daga wayanta takira matan Waziri da ake kira da Mariya ringing daya ta daga wayan tace “ranki shi dade Uwardakina, Allah yaja zamaninki Umman Riyad” dan murmushi Mom tayi kafin cikeda isa da jiji dakai tace “dole gobe Haleematu zata koma makaranta ne”? Dasauri Mariya tace “ai Uwardakina ko makarantan kikace karta kara zuwa saita zauna” jinjina kai Mom tayi tace “tom inaga bazata tafi goben ba dan zan turo Riyad yazo ya ganta inaso nahada su aure inyaso bayan yaganta zata iya tafiya” wani ihu Mariya tayi cikin waya saikuma ta zube kaman tana gabanta tace “nagode nagode Uwardakina da wannan karamci naki, kidubi kowa na gidan nan amman kuka zabinma Yarima Riyad Haleematu nagode, namiki alkawari bazaki taba samin matsala damu ba, I will forever be loyal to you, Haleema zata bautamiki Uwardakina, kuma da yardan Allah kujeran sarautan nan ta Yarima Riyad ce ai naji jita jita, da yardan Allah shine magajin sarki” dan murmushi Mom tayi tace “Waziri ya shigo yakirani” tana maganan ta katse waya wani ihu Mariya tayi tamike da gudunta tafice zuwa dakin  Haleematu kai tsaye tabude kofan yarinyar na zaune sanye da rigan bacci tana kokarin hada kaya Maman kawai ta dagata tana juyawa tana rawa abinma saiyasa Haleematun dariya tace “Mommy menene kike murna haka”? Cikeda jin dadi tace “yanzun nan Sarauniya Maryama takirani tace tanason hada aurenki da Yarima Riyad gobe ma zata aikoshi gidan nan” wani kalan zaro idanu Haleema tayi she can’t believe abinda taji tun tana yar yarinya takeson Yarima Riyad yahadu ne over wlh, lips nata rawa suka fara farinciki yahanata magana tace “Mommy mekikace? Yarima Riyad mene? Dan Allah maimaita”?Kyalkyacewa da dariya Mama tayi tace “dalla cewa nayi za’a aura miki Riyad zaki zama matan sarki dan ina mai tabbatar miki shi za’a bawa Sarautan” ihuuuu tayi tareda wani kalan tsalle ta rungume Mamanta sai kawai tahau tsalle sosai lekowa dakin Waziri da shigowan shi kenan yayi ganinsu yayi murmushi waya na kunnenshi Mama zatamai magana yadaga hannu yace “inajinki ranki shi dade” wucewa falo yayi yazauna Mama da Haleema suka biyoshi a speaker yasaka wayan dashi da Mom ke magana suna shirya komi kaman ba mutuwa aka musu ba, planning auren da yanda zasu sami kujeran suke hankali kwance.

**



Wuraren 10 yafito daga dakinshi yana sanye cikin wani farin yadi da akamai dinkin jumper yamai kyau sosai sai kamshi yake zubawa kaman zaije gasan turare, binshi da kallo Mom tayi tana murmushi tace “Son katashi? Munir yashigo yakai sau uku nacemai bai isa yatasheka ba, bayan kunyi sallan asuba tare a mosque” karasowa yayi yazo kusadab da ita yazauna ahankali yace “morning Mom” as usual pecking nashi tayi a goshi tareda shafa kumatunshi tace “morning Riyad, yaya jikin? Zakai breakfast yanzu ne”? Girgiza mata kai yayi alamun no, dasauri tace “to maza je Gwaggon ku ta aiko dazu akiraka kadawo saikai breakfast kafin kafita fada ko”? Dan gyadamata kai yayi yatashi ahankali yayi kofa haryasa hannu zai bude kofan tace “idan tamaka maganan auren Haleema kai naam” dasauri yajuyo da kanshi ya kalli Mom dauke kai tayi kafinma yamata wani maganan, dan jim yayi sannan yabude kofa yafita ma’aikata fada sun cika wajen yawanci Mom bata barinsu falo so anan waje suke yashe kaman kaya, gaishe gaishe da kirari sukahau mai ya wuce abinshi ko kadan baison zuwa wajen Gwaggo shi kadai hakan yasa yaciro wayanshi daga aljihu dailing number Munir yayi ringing daya yadaga yace “kana’ina”? Daga dayan bangaren yace “ganinan daure da towel wanka zan shiga” dan yatsine fuska yayi yace “be fast to” ya katse wayan baiso ya koma ciki dan baiso Mom tasan baijeba kuma baison yayita tsayawa awajen hakan yasa yawuce flat din su Munir wanda da dan tafiya sai gaidashi ake bai amsa kowa har gaban flat din tsayawa yayi jimmm awajen sai chan yasa hannu yabude kofan da sallama ahankali hada idanu yayi dawata mata dake zaune a falon sanye da hijab da charbi a hannunta kaganta kaman ita tai kakinshi ta tofar sunyi kama sosai, itama tanada haske kaman shi, sauke kanshi yayi kasa da sauri sannan ahankali yashiga ciki tareda maida kofan yarufe yama kasa magana, tadade tana kallonshi sannan tasauke kanta kasa tace “Munir nasama kaje ka sameshi” gyadamata kai yayi sai chan kaman me tsoron magana yace “ina kwana Mami” batare data kalleshi ba tace “yajikinka dafatan basu maka komi ba”? Dan dago kanshi yayi yakalleta ganin kanta akasa yasa shima ya maida kanshi akasa yace “I’m fine” daidai lokacin Munir yaleko daga sama daure da towel yace “ina fitowa daga bayi naji kamshin turarenka wlh daukomana breakfast kataho dashi” mugun kallo yamai saikuma kawai yawuce dinning din yazauna yana bude warmers din saman table din,  ganin shayi dayaji kayan kamshi mai zafi dasauri ya zuba a cup ya debi waina da pepper soup yadade rabon dayaci traditional food kawai yahauci bini bini Mami na dago kanta tana kallonshi dudda yabama falon baya, sosai yakecin abincin dan yanada ci yana cikin ci wayanshi yahau ringing ganin Mom yasa yahadiye wainan bakinshi da sauri yakai wayan kunnenshi kafin yayi magana cikin kakkausan murya strictly Mom tace “kana ina Riyad?” Kasa magana yayi yay shiru cikin masifa sosai Mom tace “okay sabida na barka tareda Munir shine yanzu gidansu kake zuwa kasan nida matan nan bamayin juna but you keep going there kana ganin gidan nan kowani yaro najin maganan uwarsa ni ban isa kaji nawaba ko ai shikenan kayi duk yanda kakeso…..” “Mommm!” dip ta katse wayan dasauri yatashi yajuyo sauke kanshi kasa yayi cikeda girmamawa yace “Mami bari naje in Munir yafito yasameni awajen Gwaggo” ahankali Mami tace “okay” kofa yayi dasauri yabude yafita tabishi da kallo sai kawai ta sauke ijiyan zuciya, wajen Gwaggo yawuce, Babban flat ne uwa gari guda, ga hayaniya ana shiga da fita masu aiki sai gaidashi ake kaman anga sarki amman ko kallon mutum daya baiyiba harya shiga dankareren falon Gwaggo, dudda dakin yacika da mutane yana shiga Mai Babban daki ta sallami kowa falon yarage daga ita sai shi yawuce wajenta yazauna yayi shiru, fuskanshi Gwaggo ta taba sannan takama hannunshi tabi da kallo tana dube dube tace “yaro jiki uwa na baturai kai kenan baka isa kaga kazanta ba” murmushi yayi ya fizge hannunshi yace “Gwaggo ni na warke kidena dubamin jiki dan Allah” tsuki tayi tareda hankadeshi tace “kaga shashasha” Hararanshi tayi tace “ni shiga dakina ka dauko huran dana dama maka daga babanka sai kai kap cikin jikokina keson furana” jikinta yayi sanyi shima haka sai yayi shiru ganin yanda yayi yasa da sauri tai murmushi tace “bance kamin fuskan mara lafiya ba, Allah shiya bani babanku kuma shiya amsa Alhamdulillah d’ana yayi abubuwan alkhairi da dama aduniya yayi shukoki daban daban, ya gina makarantu, rijiyoyi, gonaki dan haka banda nadama Allah ubangiji yakai haske kanarinsa jeka dauko” tashi yayi ahankali yadauko kwaryan fura yazo yazauna yafarasha anatse tana kallonshi harga Allah itama zatazo Riyad yazama sarki cus yarone mai tausayi mara hayaniya ga kwarjini ga biyayya sannan ga kwazo, baida sa ido, shine yaro na farko kap yaran sarki daya fara neman nashi da kanshi, tun ana gulma ana cecekuce but marigayi yace abarshi yayi abinda yakeso dudda kalan kudi dayake dashi baitaba raina wani ko yadingaji yafi kowaba gashi da tausayi ya tsani yaga wani na fushi ko kunci sanadiyanshi dan haka itama Riyad ne zabinta daman tariga ta jefamai kuri’a. Ahankali tace “zabinka ne diyar Waziri ko zabin Mamanka Maryama dan nasanta da tsinannen taurinkai, dason saka kabi ra’ayinta sabida taba Allah ya yoka me biyayya, kaika zabi Haleematu”? Abu yaji ya tsayamai awuya but ya daure ya gyadama Gwaggo kai batare dayayi magana ba, Gwaggo tace “ai shikenan za’ai magana idan anyi bakwai na babanka muji, zanma Baffan ka Muji magana nama kirashi daman” daidai nan Munir yashigo yana zama akai sallama Mujitapha yashigo yana sanye da manyan kaya daya fito da katon teban daya ijiye sai kyalli shaddan jikinshi yake kana ganinshi kasan yasha kudi ya koshi waje ya samu ya zauna hakan yasa daga Munir har Riyad suka gaidashi atare. “Ina kwana Baffa” binsu yayi da kallo shikebin mahaifinsu yanason yaran wanshi baida matsala dasu, yanason ya gaji sarautan but then again idan baisamu ba no big deal idan any of yaran wanshi suka samu, adai dauko wani sarki ne daga cousins nasu da sauransu shine bazai yarda ba, anatse yace “kai yajiki? Kasami lafiya?” Gyadamai kai Riyad yayi Baffa yace “har yanzu ana kan investigation koma su waye sukai kokarin kasheka za’a kamasu, so don’t worry, it’s good zakai aure koda bakai maganan ba ma yana cikin plan dina nace kafito da mata you need to settle down shi lokaci baya jiran kowa mutuwa ake kullum” Munir ya kalla daketa sunnar dakai yace “kaikuma fa yaushe zaka fito da taka matar?” Dasauri Munir yadago kanshi saikuma ya nuna kanshi foolishly yace “Baffa ni” akufule Baffa yamai dakuwa yace “a’a ni” Gwaggo ta zubamai rankwashi tace “dan kaniyanka kaima kafito da mata akace” kabar da hannun Gwaggo yayi yana turo baki yakalli Baffa yace “toh Baffa zan fara nema daga yanzu” gyadamai kai Baffa yayi yace “kutashi kuje toh lemme speak to Mama” tashi sukayi suka fice daga dakin.

Direct dakin Mom yayi yana bude kofa Mom tace “get out Riyad” gaban kofan ya tsaya yace “sorry Mommy please Munir naje kirafa yarakani wajen Hajiya”



Cikin fushi Mom tace “tell me Riyad akwai abinda kataba so daban maka ba? You showed me duk cikin yan uwanka Munir kakeso dudda ban shiri da mahaifiyarsa but nabarka dashi but na gayamaka kadena zuwa side dinsu banso banso yare nake maka daka kasa fahimtata eh?” Ahankali yafara tafiya yakai inda take sai kawai ya rungumeta ashagwabe yace “I am sorry Mommyyyy bazan karaba kinga banda lafiya karki fushi dani please am missing Dad already abin zaimin yawa” shiruu tayi saikuma ahankali tace “okay nahakura but baka ba ita that woman is the reason har Babanku ya rasu baya shiri dani she come between ni da shi, allow me to plan your wedding and coronation in peace kaji” sakinta yayi sai kawai ya daura kanshi kan cinyanta ahankali yace “Mom kimin auren na yarda but please Mommy banson nazama sarki dan Allah I am too young to be Sarki, Mom I want to tour round the world with my wife in peace” cikeda fada tace “kaje sama da 58 countries wani tour round the world ne yarage bakayi ba? Is time kayi taking responsibility naka Riyad, you are royalty Riyad, kai Royal blood ne ba normal samari out there ba, duk wanda aka haifa a royal family akwai high possibility zai iya zama king so accept your calling, and Babana zai turo bodyguards dazasu dinga binka anywhere and everything” dasauri yatashi yace “Mom banso wlh banso” wani kalan kallo tamai tace “did you even know su waye da waye ke kokarin kashe ka?” Kallonta yayi yace “suwaye?” Tana kallonshi tace “I don’t know but my gut is telling me Yayanku from the way yake eye service dan he’s everywhere, da yarinyar nan bata cecekaba I don’t know what would’ve happened” dan ijiyan zuciya Mom tasauke cike da damuwa tace “kullum bana baccin dare sabida tunanin wasu out there are trying to kill my son” dan lumshe idanu Riyad yayi ahankali yace “Mom lemme see the footage” iPad dake gefenta agadon tadauka ta bashi daidai lokacin akai sallama yar aiki ta gayamata tai baki tashi tayi tawuce tafita shikuma ya kwanta ahankali kan gadon tareda playing footage din da aka samo daga airport din yana kallo kusan footage biyar ne daban daban tun na shigowan shi arrival hall dana elevator saina bayin wanda shine na ukun, tsare cleaner yarinyar da ido yayi, a lokacin da abin yafaru bai wani kalleta ba dan yana cikin tashin hankali sai yanzu yake kallonta on this footage dudda is not that clear video karkar dinnan but yanda ta turashi cikin sharan yakala da yanda tarufe da how she handled everything ahankali yace “who is this feisty gurl”? The way takebin music yake kallo, he was actually watching the footage to see kozai gane criminals din but yana fara kallo attention nashi kawai yadawo kan cleaner, har footage data kaishi wajen dumping shara yakala da yanda take tafiya sai kawai yayi pursing video tareda zooming face nata yace “who are you? You saved my life.”

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 5️⃣

Ahankali yake bude idanunshi kadan kadan sama sama yaji ance “Son” dudda idanunshi akulle but ahankali bakinshi ya furta. “Momm” shafa mai kai matan tayi ta duko ta manna mai kiss agoshi cikeda tsantsan so tace “gani nan yarona open yourself Riyad no one is gonna hurt you again” gently yake bude idanunshi kafin ahankali ya saukesu akanta gently ya yunkuro ya shige jikinta kaman dan karamin yaro yace “Mommm” bayanshi ta shafa tana murmushi tace “meya sameka what happen? Who did this to you”? Murya chan kasa yace “wasu mutane wanted to kill me….” Kankameshi tayi sosai tace “babu wanda ya isa ya cutarmin dakai ko yadauki rayuwanka as long as ina raye, u are safe already ana investigating abun sai inda karfina yakare” takara kankameshi kaman dan karamin yaro tace “I love you Riyad kaine kadai sanyi idanuwa na”lumshe idanu yayi saikuma ya yunkuro yatashi daga jikinta yakalleta da muryanshi da bata fita sosai yace “Baba”? Kallonshi tayi saikuma ta sauke dan ijiyan zuciya tace “tashi kaje kai wanka ka shirya kafito ka gaggaisa da mutane idan zaka iya, sannan kaje kama Babanka addu’a a makwancin sa” dan runtse idanu yayi abin yamai ciwo yaso Ya sallaci mahaifinshi, fuskanshi Mom ta taba hakan yasa yabude idanunshi dasukai ja yakalleta murmushi kadan tamai tace “nasan yanda kakeson mahaifinka but he’s in a better place yanzu trust me, all abinda yake bukata awajenka is addu’a, jekai wanka za’a kawo maka kayayyakin dazakasa” gyadamata kai yayi agajiye yace “Mom please ke kikawomin banson hayaniyan kowa” tsayawa tayi ta kalleshi ahankali tace “tom zan kawo maka da kaina” dagoshi tayi yatashi tsaye ahankali yawuce bayin dake nan bedroom din, girman bayin yayi girman wani gida, wanka yayi yayi brush yadaura towel yafito yana kallon saman gadon inda tundaga kan takalmi har zuwa kan agogo an jeramai akan gadon tsaf dazai saka wasu kayan sarauta ne masu kyau sunsha aiki, anatse yake komi ya shirya cikin kayan da aka musu aikin royalty ya feffesa turare yadan juya yakallo kanshi amadubi yayi wani irin kyau na ban mamaki hulan dayasa yasake maidashi wani cikakken mutum bude kofa yayi yafito daga bedroom din wasu bayi ne ma’aikata a falon suna ganinshi suka duka dukansu. “Takawanka lafiya Yarima Riyad, taho a sannu dan kwalisa abin begen Sarauniya Maryama, barka da fitowa, Allah yakara maka lafiya, makiyinka fadawanka, duk wanda yaja dakai ya shirya yasha kasa….” Wucewa yayi fuuuu yafita danshi bayason wayan nan surutun nasu, da Munir yaci karo yana kokarin shigowa flat dinsu hakan yasa ya tsaya yahade rai kaman suna fada Munir yace “katashi, are you feeling better can you walk”? Gyadama Munir kai yayi yay gaba kawai, Munir yabishi abaya direct inda aka binne sarki yayi yana zuwa ya shiga wajen batare da an hanashi ba yayi shiruuuuu idanunshi sukai ja, almost everyday indai Mai Martaba baida wani uzuri saiya kirashi da daddare yaji yayake ina kuma yake, kullum cikin fada yakemai daya daina yawon kasashe yakan yawan cemai yanda yake gudunma gidan nan da alamu shine wanda gidan nan zai rike kuma gam, ana cewa sarakuna basu da lokacin yaransu shidai mahaifinshi nada lokacinshi, Baba ya fara koyamai business how to make 1naira yakoma billions, Baba guides him through everything, duk business dazai fara saiya kira Baba, sai Baba ya amince zai farayi, kuma bai taba takura mishi ba, hawaye yaji sun taru a idanunshi da sauri ya runtse idanun yana fuzar da iska dan baiso suma zubo but he’s deeply hurting, da ace yasan Baba zai rasu dabaiyi tafiyan nan ba, sosai yama mahaifinshi addu’a sannan yafito Munir yagani awajen da Kabeer dasu Shaibu yan uwanshi dukansu yajiki sukamai ya amsa sai kallonshi suke Kabeer yace “kasha magani kuwa you still look sick? Ko zaka koma ka kwanta ne”? Gyadamai kai yayi ahankali yace “nasha, I’m fine thank you” dannewa Kabeer yayi ganin yanda yakemai magana kaman alfarma yakemai dayake amsashi yadai daure yace “to mutafi fada” atare dukansu suka wuce fada, sauran yayyinsa da yan uwansa natamai hira da uhm a’a kawai yake amsasu cus gashinan ne kawai, gaida mutane sukayi sai yima Riyad gaisuwa ake ana kiran sunanshi shi baimasan ya akayi akasanshi hakaba dan baicika zama ba, su Waziri dai duk suna kallon komi, kowa yazo saiyamai gaisuwa amai yajiki, yanda ma ake kallonshi sai abin yasa yaji sabon zazzabi na nema ya lullubeshi.


Mom nazaune afalonta tana jan charbi ita dawasu kawayenta wanda suke mata Sarkin daga wasu garin dasuka kawo mata gaisuwa aka shigo flat din Matan Waziri ne da babban diyarta Haleema da ake kira da Lims, tana sanye da doguwan riga abaya black ta yana gyalen akanta, tanada tsayi da dan jiki kadan duka duka bazata wuce 24, 25 ba, tana shiga dasauri tawuce wajen Mom kafinma Mamanta tai gaisuwa tace “Mom ina kwana” takalli sauran matan wajen cikeda girmamawa tace “ina Kwanan ku” amsawa sukayi Mom tamata murmushi tace “Halima ba kina school ba yaushe kika dawo”? Mahaifiyarta tace “nima ganinta nayi agida da safen nan ta iso daga London wlh na aika driver yaje yakawota tunda taji rasuwan Mai Martaba hankalinta yakasa kwanciya” sosai Mom ke kallonta akunyace Haleema ta sunnar dakai Mom tace “school fa idan kikai missing exam ko test fa” Maman ta tace “project ma fa takeyi this month zasu gama komi da komi” babu wasa kan muryan Mom tace “kibi first available flight ki koma school gobe kinajina” gyadama Mom kai tayi ahankali tace “to Mom” Mom bata sake cewa komiba tacigaba da magana da manya, ahankali Haleema kebin dakin da kallo gabanta na faduwa addu’a take Allah yasa suhadu ta ganshi, Allah yakawoshi side din nan dudda tasan ba lallai yadawo ba barinma yaji da baki adakin amman tasan inhar yana gari yafi zama wajen Mom da bangarensu na samari.

Kallonta Mamanta tayi tace “tashi kije wajen su Batul mana” juyowa Mom tayi takalleta tace “tashi kije wajen yan uwanki” batai musu ba tashi tayi tawuce tafita Matan Madaki tabita da kallo tace “yarinyar akwai natsuwa ga kunya ga kawaici ta dace da Riyad sosai yanda shima baida maganan nan” wani kalan dadi Matan Waziri taji Mom tai dan murmushi batace komiba.


Ahankali take tafiya ita kadai tana danna wayanta kamshin turaren dataji yasa ta dago kanta dasauri Riyad tahango yafito daga fada yana shigowa nan compound din Mom wlh kusan duka yaran sarki tasansu da yaran yan uwa dan afadan nan aka haifeta anan ta girma bata taba ganin yaro mai kyau da farin jini da aji irin Riyad ba kap gidan nan babu wanda yakaishi kyau, ga tsayi ga gayu ga jidakai ga miskilanci ga kudi kudinshi na kanshi bawai kudin Baban su ba dan babu wanda yakaishi kudi a yaran sarki, gashi Mai Martaba na sonshi, ga kakanshi na bangaren Mom Attorney General yafi kowa tsatso mai kyau da gata ayaran sarki. 


Faduwa gabanta yayi sosai amman tadaure ta tsaya awajen jikinta har bari bari yake, tahowa yayi wajen batare daya kalle inda takeba zai wuce dasauri tace “Yarima Riyad!” Tsayawa Riyad yayi chak batare daya juyoba dasaurinta Halima taje ta gabanshi ta tsaya adan kunyace tace “ina yini ya hakuri?” Dan kallonta yayi trying to remember waye ita, shifa wasu kannin nashima ba saninsu yagamayi ba dan baya shiga lamarin gidan nan baison komi game da sarautan, dauke kanshi yayi ganin yanda take murmushi tana kallonshi, kaman ance dole yayi magana yace “who are you”? Wow the way he talks is super adorable, da kyar ta iya controlling zuciyanta dake neman fitowa ta danne kome takeji tace “Haleema” dan kallonta yayi irin kallon okay but still baigane ta ba and he doesn’t care din nan yajuya zai wuce dasauri tace “Ya Riyad sabida kai nazo gobe zan koma school” dan tsayawa yayi wannan karan yajuyo kalleta da kyau shifa har yanzu bai santaba and sabida shi tazo? Akan wani dalili? Are they related in anyway? Infact baida karfin bude baki ma yayi all this questions hakan yasa yadan tabe baki yace “thanks” kawai yawuce ya shiga flat din Mom……


Jin akwai baki abangaren Mom yasa yajuya yagazaya ta baya yashigo gidan yaje ya kwanta.



Yana zaune adakinshi dashi da Munir har yanzu bai gamajin sauki ba yana sanye dawani 3quater da singlet wayanshi yahau ringing kallon wayan yayi ganin Mom yasa yadauki wayan kai tsaye tace “kazo dakina ina son ganinka” ahankali yace “okay Mom” tashi yayi ahankali Munir dake taba wayanshi yace “ina zaka?” Slippers yashiga sawa yace “Moomm” yadauki wani farin t-shirt yasaka kawai yawuce Munir daya gane abinda yake nufi wato Mom nakiranshi hakan yasa yacigaba da abinda yakeyi ahankali yabude dakin Mom tana zaune kan couch din dake dakinta ganinshi yasa tanunamai gefenta tace “taho nan” shigowa yayi ya maida kofan dakin yarufe yataho wajen kujeran zama yayi saikuma ya kwanto yayi filo da cinyanta he’s really feeling mutuwan mahaifinshi so duk walwalanshi bayanan, hannunta Mom tadaura saman kanshi ta shafa tai shiru kafin tasauke ijiyan zuciya tace “kasha magani kuwa? Dr zai zo anjima” ahankali yace “nasha” dan ijiyan zuciya tasauke tace “da banson namaka maganan nan yanzu cus nasan kanajin mutuwan Babanka, I know how much you love mahaifinku Riyad but I have to dan kowace matan sarki maganan da datake ma danta maza kenan, nima dole nama nawa” dan dago idanunshi yayi ya kalli Maman nashi baice komiba, ahankali tace “inaso kai aure Riyad!” dawani irin sauri Riyad yatashi zaune daga jikin ya kalleta yama kasa magana cus maganan yazo mishi ne bagatatan, Mom dake kallonshi itama looking damn serious tace “and bakowace kalan yarinya nakeso ka auromin ba Riyad, inaso ka auri yarinyar da zuciyana ta aminta da ita yarinyar da nice na zabeta, all yammatan zamanin nan yanzu burinsu is suyi aure su raba yaro da mahaifiyarshi I will never allow you marry such girls, I have a girl a mind dina gaskiya” haderai yayi kana ganin fuskanshi kasan bama yason maganan dasauri yace “Mom aure!”? Wani mugun kallo tamai tace “kaga Riyad banson shirme don’t even start all abinda kakeso kace, I supported you duk yawace yawacen dakake kana touring round the world bantaba hanaka ba dan nasan it’s your hubby, bantaba takuraka ba dudda normally normally ba tun yau yakamata kai auren ba, but yanzu lokaci yayi it’s an order you have to settle down, aure zakayi and i have a girl danakeso ka aura diyar Waziri Haleematu, ita nakeso ka aura!” Wani kalan tashi yayi dasauri yamike tsaye yana kallon Mamanshi da babu wasa akan fuskanta itama tabishi da kallo tazubamai idanu rass aka tace “kaine the most successful child acikin yaran sarki, you’ve archived alot Riyad at a very young age, ga ilimi kwali daban daban gareka, ga businesses da companies daka bude, ga natsuwa ga kamala ga kwarjini, naji kishen kishen dama mai Babban daki kaine zabinta sabida yanda mahaifinku ke sonka, Waziri shima nasan kodan yanda diyarshi ke sonka kuma yana mata kwadayinka kaizai dangwalamawa, to yaji maganan kuma kanason auren diyarshi komi yazo cikin sauki idan yana bangaren mu zai mana aikin yima sauran manyan fada maganan a zabeka, instead of su Kabir yan uwanka ko kannen babbanku dake neman kujeran sarautan, gwara kai dana kaikafi kowa chanchanta and bazan hutaba saina maidakai sarki, ai tsoron kada ka zama sarki yasa daga shigowanka garin suna neman halakamin kai amman Allah bai basu iko ba, kuma naji dadin abinda yafaru hakan yanunama jama’a cewa an tsaneka ana tsoron kada ka zama sarki saisa har anfara yunkurin kasheka, saisa saida na tabbatar kowa yasan abinda yasameka”.




💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 8️⃣


BAYAN 1YR!!


Cikeda natsuwa wasu manya manyan fadawa ke bude wani hamshakin kofa da girmanshi zaiyi girman wani karamin gate daidai karfe sha daya na safe, sannan dukansu suka fadi suka zube suna daga hannu irin yanda dai fadawa ke gaisuwa suka fara zuba kirari.

“Lafiya jakadan Baba Ali dan Baba Ali! Lafiya mai kiran gabas da yamma! Lafiya jinjirin wata sha kallo! Lafiya kwankwason jimina mai wuyar shafawa! Lafiya Garkami Wandon Karfe! Lafiya jijigen addini! Lafiya toya matsafa! Lafiya baya goya Marayu! Lafiya toron giwa! Lafiya tufaniyar gabas! Lafiya jinjirin wata shakallo! Taaaakawanka lafiya sarkin mu sarkin Riyad zakaran gwajin dafi mai hasken zuciya da hasken aura!, lafiya dan lellen Mai Babban daki…..”

Tunda suka fara kirarin nan kusan good 10min sai yanzu wani dogon mutum yafito yana sanye da wata milk kokuwar alkyabba dahar walkiya takeyi tsabagen kyanta ga rawani dawani white yadi mai kyau dake walkiya akamai, inda farare tarrr na idanunshi kake iya gani, hannunshi yarike wata sanda mai kyau, rabon da mutanen gari da yan fada suga fuskanshi shekara daya kenan, tun kafin yakaraso inda suke turarenshi yagama gauraye wajen da kamshin dadi dake dauke da yalwataccen ni’ima, ahankali yake tafiya kaman baiso yataka kasa, wani irin kwarjini shiganshi ke dauke dashi da bamaka iya kallonsa, har ya iso inda suke ya tsaya chak na kaman 5secs ya kallesu one by one to check idan kowa is healthy fine and present wanda hakan yana daga cikin abinda yasa jama’a ke sonshi, kaman baiso ya furta magana yace “kun tashi lpy”? Kaman jira suke. “Lapiyanmu kalau Sarkin mu mai adalaci, sannu sannu toron giwa tsintsiya madaurinki daya!” yanda jikinsu har rawa rawa yake sunamai kirari suna yabashi ya kalla sannan kawai yawuce duk suka biyoshi abaya, direct fada suka shige inda mutane suke cike makil wajen zama yayi ya zauna, batare daya hada ido da kowa ba this is mostly method dayayi adopting dayake samai natsuwa cus dazaran ya shigo fada he sees love hatred envy a idanun mutane da dama barinma yayanshi Kabeer, but koda wasa baitaba disrespecting yan uwanshi ba, and so far so good Kabeer din has been supportive bai bashi wani matsala ba haka ma yayyin babbanshi da Waziri ana koyamai komi everything is going smooth Alhamdulillah.


Munir sai kallonshi yake bayan yazauna, yadade baiga sarkin da mabiya keso kaman Riyad ba, anason Baban su but son da akema Riyad daban ne, har lakabi akamai da Sarki me farin jini, dudda akwai yan adawa but wlh ana sonshi barin yan cikin gari, cus kafin ma yazama sarki yana taimako sosai yasaka yara a school da dama, yanzu kawai dan he’s not happy about zama sarkin sai the whole abu yasa he hardly talks, yakara miskilanci da wulakanci fiye da da, he’s so angry sabida he’s feeling kawai responsibility akasamai akai da baya so, responsibility daya tsaya and funny enough he’s doing so good da leadership din saisa har yanzu an kasa fadin wani negative abu akanshi ko kokafadi babu wanda zai yarda ma though yasan alot of people na jiransa to just make a mistake ne and he pray dan uwanshi will not make that mistake dasukeso suke kuma jira yayi.


Almost 2hr yayi afadan sannan aka tashi yakoma side nashi, bayan an bude katon kofan nan kaman gate still akwai tafiya kafin asalin babban gininshi, baya mulki like others, he hardly let anyone a side nashi, daga Muneer sai Mom da Haleema.


Shida Muneer suka jera fadawa na binsu abaya ana kaiwa gate din kowa ya tsaya dan babu bafaden dake shiga ciki ko matarshi bata isa tashigo side dinba without izininshi, sake bude another door sukayi that will lead them to compound din da interlock ya cika ko’ina ga bishiyan mango dake wajen da flowers ko’ina sai wata arniyan jeep bulletproof dake compound din gawani secret gate dayake wajen any private outing tanan yake fita.

Shiga mainflat din sukayi WAN’ı irin crazy sitting room ne dakeda fadi na bala’in yasha funitures that are very beautiful, zama Muneer yayi yadauki laptop dake kan table yace “almost 2yrs bake leka hotel ba Riyad, its only right kaje mana” wucewa sama yayi dan yaje ya cire kayan nan dasuka isheshi.


Binshi da kallo kawai yayi kafin ya shiga replying mails, kai tsaye aka shigo falon dasauri Muneer yadago kanshi dan mamakin waye ya isa yayi hakan ganin Mom tana sanye da wani alkyabba da akayi da crystal yasa yadan taso yace “ina yini Mo….” Baima karasa gaidataba tawuce stairs tai sama fuuu.


Riyad yariga yasaka wandon wani yadi brown da farin singlet ajikinshi yana kokarin saka rigan aka bude kofan bedroom nashi, dago kanshi yayi suka hada ido da Mom data haderai kana ganinta kasan ranta abace, dan lumshe idanu yayi yakarasa saka rigan Mom takaraso ciki har zuwa gabanshi dab dashi ta tsaya cikin tsananin bacinrai tace “yau kwanan ka nawa rabonka da shiga turakan Haleema Riyad”? Hannu yamika ya dauki agogo daga saman bed yana kokarin sawa yace “Mom kinsan I’ve been busy dealing with lot of things, my business, this sarki thing, everything ma” “and so?” Mom tai maganan da fushi tana daga murya tace “sabida business da sauransu bazaka kula matanka ba kusan 1months da 1week baka shiga gidan ta ba, and baka bari ta shigo nan ba, sai gulma ake tell me menene banbancinka da su Muneer da basu da mata”? Dan yatsine fuska yayi still baice komiba yadauki links na hannun riganshi yana kokarin sawa Mom ta fizge links din cikeda masifa tace “Riyad wlh zan mugun sabamaka I hate this new attitude din naka, I’m talking to you baka kulani, ka shiga turakan Haleema koka kirata tazo nan your choice, people are watching and you know that, 1yr kenan kunyi aure ba ciki and it’s all thanks to you, ni bantaba ganin mai gudun mace har mace ba sai kai, badadan na tambaya tacemin kalau kake functioning ba dana fara tunanin kokai mace ce” sauke kanshi yayi kasa yayi shiru why will Mom be asking Haleema irin this kinds of question? Ahankali kanshi na kasa yace “kiyakuri Mom” cikin fushi tace “nayakuri nayakuri me? Get your wife pregnant nagayamaka dagayau nakaraji kun raba kwana” ta ijiye links din akan gado tajuya zata wuce hartakai wajen kofa zata fita ahankali yace “Mom” juyowa tayi tamai wani mugun kallo saikuma ahankali ta tako zuwa gabanshi ta tsaya tana kallon kwayan idanunshi, ahankali takai yatsanta tadaura kan kirjinshi cikin kakkausan murya tace “ni mahaifiyarka na umarceka dakai tarayya da matarka, make her pregnant within period na this sabon month da aka shiga, inba hakaba wlh saika gamu da fushina sosai Riyad” tajuya fuuuu tafice yadade tsaye ahaka idanunshi sunyi jaaa mode nashi ya chanza, he hates yanda Haleema tells Mom literally everything about marriage nasu, koma yace he hates yanda Mom ask everything akan aurensu, he hates both kawai, yana bala’in son sirri, he loves everything about shida matarshi nazama about them, anytime yakalli Haleema he doesn’t even feel like shine mijinta, he feel like Mom ne mijinta, kokarin saita muryanshi yayi yadauki wayanshi dake kan gadon, Munir yakira cikin muryanshi da bata fita sosai tsabagen bacin rai yace “ka aika akiramin Haleema pls” yana maganan ya katse wayan, tashi Munir kawai yayi yafice bayan yabada sakon yashiga mota yabar gidan cus yaji komi da Mom tafadi he just pity his brother, Mom is just over controlling Riyad, she’s in his matter, and baya iya cemata no, itakuma Haleema akanme zata dinga gayama Mamanshi komi gameda aurensu? Sabida taga baya iya tsallake maganan Mom ne, haba it’s annoying mana, Riyad dakeda kunya tagama fallasashi, it doesn’t matter koda Mamanshi ne some private mata barinma harkan auratayyan su baikamata Mom tama sani ba, the girl is sick wlh batasan menene boye sirrin mijinta ba, dashine matarshi tamai haka Allah he will deal with her, yayi tsaki aranshi.

Office yawuce abinshi inyaso yasameshi daga baya.

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 9️⃣


Zaune take a arnen falonta takara kiba yanzu ba kaman da datake so skinny ba, tayi bulbul taciko alamun Riyad ya iya kiwo tasami kwanciyan hankali, wasu bayi ke gyara mata farcen kafa jakadiya ta shigo zubewa tayi tace “Gimbiya Mai Martaba ya aiko akiraki chan bangaren sa” wani irin farin ciki daya lullubeta batasan sanda ta karbe kafanta ba ta mike da sauri tai sama bedroom nata ta shiga tana kiran wayan Mom awayanta kiran iPhone 15, ringing daya Mom ta daga Haleema tai wani ihu tace “Mom I love youuuu, you’re the best Mom, Mom wlh ina sonki sama da tawa Mamar ma, Mom dabanda ke da narasa gata, dana shiga uku, kinga Mom yanzun nan Mai Martaba ya aiko akirani kinmai magana ne?” Dan murmushi Mom tayi mai sauti kanta nawani swelling yanda Riyad baya tsallake dokanta, she just wish kowace uwa zatasami yaro mai taushin zuciya da jin maganan mahaifiyarshi irin Riyad kawai baya jure fushinta ko kadan ne, koyaya tace yayi abu kobayaso sai yayi, shi kawai baison commitment ne da nauyi akansa baison damuwa baison hayaniya but tace yayi kaza saiya yayine, murmushi tasakeyi tana wani ji da kanta tace “Madallah! sai a kimtsa aje, ki farantamai rai” gyadama Mom kai tayi cikin mugun farin cikin dan tana mahaukacin son Riyad tace “Mom banda kamarki me sharemin kukana, Mom thank you for making my husband to call me, bye Mom I love you” katse wayan tayi itakuma Haleeman cikeda jin dadi ta shiga shiryawa, tasha wasu magungunan da Jakadiya ke hada mata ta shiryata tsaf cikin wani hadadden atampa golden, ta daura Al kyabba akai ta feffesa turare sannan sauko kasa, Jakadiya da kuyanginta jaka biye da ita har zuwa side dinshi dayake da dan tazara tsakaninsu, tana zuwa dayake ansan da zuwanta aka barta ta shiga ciki Jakadiya da kuyangin kuma suka tsaya waje, shiga flat nashi tayi ko’ina na falon kamshin shi yake, murmushi tayi ta maida kofa tarufe sannan tacire Al Kyabban ta ijiye kan kujera tawuce sama tsayawa tayi gaban bedroom dinshi tai knocking.



Kusan 2min tayi wanda inda sabo ta saba jira haka duk sanda tai knocking, chan taji muryanshi ciki ciki cikeda isa yace “come…..in” bude kofan tayi gently ta maida kofan tarufe ta shiga dakin dakin tana tafiya ahankali sabida duhu gaske but tana iya ganinshi zaune bakin gado ya tsareta da idanu dake shinning even in the dark saida gabanta yafadi tadai daure ta maida takaraso zuwa gabanshi cikin yar kankanuwan murya dake cikeda yanga da iyayi tace “barka da warhaka Mai Martaba, kayi aike akirani gani” mikewa tsaye yayi yazuba mata ido, chan yace “how many times nagaya miki kidena kaima Mom maganata?” Faduwa gabanta yayi ta daure bata nunaba, cikeda makirci tace “ni kuma?akanme zankai karan mijina?” Wani kallo dayake mata yasa batasan lokaci da lips nata yashiga rawa ba, ganin yariga yagane ita tafadi tace “yes nagayama Mom baka zuwa wajena kuma ko nazo baka bari a barni na shigo? Kayakuri nayi kuskure bazan karaba, wlh bana iya bacci ne, narasa yanda zanyi dakaina” saikuma asanyaye tace “i need youu…”  wani kallo ya mata yace “and sabida hakan saki hadani da Mom”? Ahankali tace “magananta kadai kakeji saisa nagayamata amman kaya kur…” bata karasa maganan ba yawani kalan hankadata kan gado dasauri ta juyo ganin yana bude mazariyan wando wlh har cikin ranta taji kaman tai ihun dadi tadai daure tai shiru tana jiranshi, kafafunta yaja cikin fushi yace “you reported me sabida this I hope nabaki shikenan” ya kwashe skirt nata sama yadage rigan sama addu’a yayi  yashiga ciki, runtse idanu Haleematu tayi tanaji kaman zata shide, wata daya babu abinda ya shiga tsakaninsu sai yau.


Almost 1 good hour yayi cur akanta not because of kanshi but her, ya sauke hakkinta daga kanshi tunda harta fara kai karanshi, saida yaji ta bushe ya tabbatar idan yacigaba zafi kawai zataji sannan ya kyaleta sannan yatashi zaune kafin chan yamike tsaye yawuce bayi ya barta kan gadon wani mugun bacci na daukanta tana numfashi haryau takasa gane kan Riyad, zai iya 2month bai nemeta ba yawanci saitasa Mom a case nasu yake nemanta and he’s so damn good in bed Innalillahi! The way he’s this quiet bazaka taba tunanin zai iyacin mace ba, but en anytime yayi having wani abu da ita jitake kaman she’s the luckiest gurl on earth, Riyad is good on bed, she don’t even know how to explain, yana wasa da jikinta wani kalan dirty play fa, yauma haushin abinda tayine yasa bai tattabata yanda ya sababa, wlh haryau takasa gane yanajin dadin ta ko bayajin dadinta oho ko gurnani bayayi bai tabayiba, he’s just super wired guy data kasa fassara halinshi haryau, and wiredness dinshi ke kara mata sonshi sosai aranta wlh, ahaka tana lumlumshe idanu bacci yayi awon gaba da ita.

**



Around 5 Mama ta tadata daga bacci, da kyar ta tadunma Mama, Mama tace “ke yarinya sai nauyin bacci kaman wani kato, tashi kin manta yau zaku koma makaranta eh? Hope kin dauki permission wajen aiki an baki shift na yamma”? Gyadama Mama kai tayi cikin gajiyan bacci, hannu Mama tasa tadagota ta taro kafadanta hakan yasa Rashida tasauke kanta akan kafadar Mama tana kara lumshe idanu still cikin bacci, dan jijjigata Mama tayi tace “Rashida” ahankali tabude idahunta tass takalli Mama dasu Mama tace “I think drop most of ayyukanki tunda kin koma school kinga yanzu year 5 kike you need to study well, nakosa naga diyata tazama likita, saura 1yr yanzu, Allah ya aramin rai, ranan super wax zan saka amin combination da super lace” dan murmushi kadan Rashida tayi tanason taji Mama na maganganu haka it makes her happy, Mama tace “yanzu dai kinga kina bukatan lokacin hutawa da lokacin karatu bakiga yanda kike gajiya ba da kyar kike tashi, ki saki sauran ayyukan ki rike na hotel din nan kadai tunda anfi biya, su Maman Miwa da sauran wajajen nan ki sakesu” dan murmushi tayi sai kawai tahau yunkurin tashi ahankali dan muryanta baya fita sosai sabida daga bacci ta tashi tace “Mama so kike na bar aiki sabida mudinga karban abincin sadakan da yan anguwan nan suke kawo mana out of pity?” Tadanyi shiru daidai takarasa mikewa tsayen batare data kalli Mama ba tace “this year is clinicals, zamuyi aiki a pediatric da obstetrics&gynecology, I can manage everything Mama trust me, Alhamdulillah kome aka koyamin sau daya ya zauna akaina, sannan daga yanzu koda ranan Sunday ne zan dinga zuwa library duk sati sau daya nayi muraji’an duka abinda aka koya mana na that week, I can study Mama, I can do my duties na kula dake da siyamana kayan abinci da kudin magunguna, I can manage my work also” tana maganan tayaye labule tafita daga dakin tawuce waje saida tafara sa abinci awuta sannan tawuce bayi tayi wanka tafito lokacin har sanwan yayi tazuba taliya sannan takoma daki tashiga saka kaya Mama na zaune kan dadduma tana kallonta, tana kallon yanda taketa ciro kayan ghana masgon dasuke agoge daga gani kasan dan kaya mai kyau take nema na zuwa school abu Mama taji ya tsaya mata a wuya sai kuma ta daure kawai ta dauke kanta daga kallonta.

Wani doguwan rigan atampa maroon ta zaba ta maida gefe, taciro lab coat nata dayake a goge shima ta ijiye gefe sannan ta maida sauran kayan ta shirya tsaf tawuce tafita tasake juya taliyan sannan tadawo tasa hijabi ta kabbatar salla.


Tana idarwa bata tsaya yin azkar ba ta fita ta juyo taliyan a kula tasama Mama ruwan zafi na wanka sannan tadawo tasake zama kan dadduma tafara azkar tana gamawa ta kalli Mama dake kallonta tace “Good Morning Mama na nikadai, Mama naji dadi nikadai kika haifa nake moreki banda kanni dazaki dinga raba attention naki akanmu” most time tana maganan ne idan taga abu na damun Mama dan tasata tai murmushi, ganin Mama batai murmushi ba yasa takama hannunta tarike dasauri ahankali tace “Mamaaaaaaa” tai maganan ashagwabe tana lankwasa kai, ijiyan zuciya Mama ta sauke tace “babban burina arayuwa shine ki zama likita Rashida, banson wani abu dazai hanaki zama, kina bukatan lokacin dazaki karatu, banson ki fadi, banson ki sami carry over, nasan kinada kokari but dudda haka karatu yanada amfani, kina all this ayyuka bazaki sami lokacin yi ba, ki manta da kula dani Allah daya tsaga mana baki bazai hanamu abinda zamusa abakin ba, after this year next year zaki gama, please Rashida kibar ayyukan nan and focus a karatu” tunda Mama ke maganan take kallonta batason sata cikin damuwa hakan yasa tace “to naji Mama amman tunda kinga satın nan muka koma karatu da practicals bazasuyi serious ba kibari nayi aikin zuwa karshen wata abiyani kudina saina dena kinji, zancen night shift ai HOD mu tasan dani bata taba sani a night shift ba sabida ke Mama, so ko yanzu ma bazan bazanyi night shift ba, kinga na karbi albashina saimu ijiye, kuma Mama kidena damuwa yarki ta dauko brain dinki bazan fadiba In sha Allah bayan kinamin addu’a, to yanzu kin hakura na karasa zuwa karshen watan nan duk sai na saki aikin nabar na hotel din?” Shiru Mama tayi tana kallonta Rashida da taurin kai da kafiya hmm, ijiyan zuciya tasauke tace “okay! Yau sha uku ga wata, karshen wata zaki sallame kowa, next month banson ganinki kina zuwa ayyuka nan” gyadama Mama kai tayi tace “naji” tashi Mama tayi tace “ai shikenan” tawuce sip wani akwati zata dauko dasauri Rashida ta tashi tace “Mama stop ki kirani na dauko miki” dasauri tasa hannunta tadauki akwatin tasaukar dashi kasa Mama tazo wajen ta zauna itama Rashida ta zauna gaban box din tana jiran tadauki abinda zata dauka tasake daukan akwatin ta maida sama, wata yar jaka Mama tadauko acıkın box din tamika mata tace “gashi ungo” dasauri Rashida ta kalli jakan data bata tace “na menene Mama”? Tasa hannu tana karba, zage zip din box din Mama tashigayi tace “naki ne kibude” da sauri taciro bakin ledan data gani cikin jakan dayake a kulle tashiga budewa saiga crocs a ledansu pink color mai kyau ba asalin designers one dinba but irin normal wanda ake saidawa a market yan 5k-7k dakuma stethoscope pink shima mai kyau, da mamaki take kallon kayan dakuma murmushi akan fuskanta tama kasa cewa komi Mama ta kalleta tace “bakiso ne oya bani kayana, last month danaje clinic wata Hajiya tarabamana kudi a envelop naduba naga 20k ne shine na shiga kasuwa na siya miki crocs naga shi likitoshi kesawa a clinic dimu duka likitocin wajen shine akafansu shine na shiga kasuwa na sayomiki ashe haka takalmin keda tsada dubu takwas aka saidamin na hada miki da wannan abun gwajin nace nima y’ata tai kaman yan gayun likitocin danake gani a clinic dinmu” hawaye ne yacika idanun Rashida tana kallon Mama na bata labarin Mama takare da “nazo naboyesu nace bazan baki ba sai ranan dazakuyi resuming school” daidai lokacin hawaye ya sauko daga idanunta Mama tace “ke mehaka kuka kikemin”? Kawai rungume Mama tayi da gudu ta kankameta ahankali tace “thank you Mama thank you” shafa bayanta Mama tayi tace “gabaki dayan rayuwanki Rashida nine na cinye miki ita, bakida lokacin kanki, komi kika samu ni, kome kikeyi sabida nine, konace ki sayawa kanki abu bakiyi saisa na saya miki kema ki shiga sahun yan gayu aga y’ata fess fess akara kallonta sabida yanda tai kyau, Allah yakawo miji na gari” cikin shagwaba ta ture Mama tace “ni bazanyi aure ba Mama, bazan taba iya barinki ba” baki Mama ta kama tace “ke kodai zan kaiki gidan zumane amiki rukiya kaman me aljanu bazaki aure ba” gyadama Mama kai tayi tadauki takalminta tana budewa daga leda tace “inhar ban samu mijin dazai yarda na daukeki muje gidanshi tareba ina ganinki ina baki kulawa wlh gara na kare rayuwana ahaka” da sauri Mama tamata dakuwa tace “kinci mai garinku Rashida” dariya Rashida tayi sosai tace “wlh Mama da gaske nake bazan taba rabuwa dake ba Allah Mama” ganin Mama zatai magana yasa ta tashi da sauri tace “bari nasa takalmina” fararen kafanta ta zura cikin crocs din sun mata bala’in kyau Mama tace “Masha Allah Tubarkallah komi kema yarinyana kyau wlh, kinga kafanki aciki kuwa dudda kafan fara ba lalli amman yayi kyau” wani juyi tayi cikin takalmin tace “Mama inason takalmin thank you so much Mamaa, bari na tafi” tawuce tasa doguwan rigan data fito dashi yakamata ya nuna her flat tummy sosai da very full chest nata cus she has boobs kaman Mama, itama Mama harda rama yasa ba’a ganin nata yanzu, dan kwali ta daura tayafa gyalenta tai arranging lab coat nata a bag pack da books da stethoscope da Mama ta siyamata da komi ciki ta goya abaya tasa yar wayanta a aljihun riganta da earpiece tace “natafi Mama” Mama tace “dan Allah kici abinci kinji kada ki manta” dasauri tace “to Mama zanci, bye Mama” Mama tace “ubangiji Allah bada za’a Allah ya taimaka Allah ya tsareki Allah yakuma baki miji nagari”.


Shagon Maman Miwa taje ta gayamata ta koma school da safe zata dinga zuwa aiki, nan da nan tayi wanke wanke ta share ko’ina tai mopping after 8 tagama komi Maman Miwa tabata 2k saikuma ta bata 200 tace “kihau adaidaita kitafi makaranta baki takaba” murmushi kadan tayi tace “nagode Maman Miwa” sannan tawuce tafito MamanMiwa tabita da kallo tace yarinya ga kyau har kyau ba miji.


Adaidaita sahu ta tare ta shiga sai BUK direct department dinsu ta wuce staircase tahau tana tafiya daidai lokacin wani guy da wata young lady kaman mate na Rasheeda suna sanye da kayan gida lab coat a hannunsu na saukowa hada ido Rashida tayi da guy din da sauri ta dauke kai tacigaba da tafiya abinta tana hayowa su suna saukowa hade fuska yarinyar tayi tace “Bilal yaushe zaka fadamin inda kahadamin suprise birthday party”? Gabaki dayan hankalinshi nakan Rashida dake hayowa abinta batare data kara kallon inda suke ba, mintsilin shi yarinyar tayi abaya hakan yasa yakalleta da sauri yace “sorry Layla come again me kikace”? Abu taji ya tsaya mata awuya sai kawai tawuce da sauri tana sauka da sauri yabita da sauri yace “Layla wait common” tuni tafice dan tsayawa yayi daidai Rashida tahau staircase din dayake kai yabita da kallo sabida kyau datamai doguwan atampan riganta yamata kyau over, dudda ko man baki babu a lips nata balle hoda ko kwalli ahankali yace “we’re going to clinic you don’t need to go up kasa zamu” kaman bada ita yake magana ba kala bata cemai ba kawai ta juya tashiga sauka da sauri yabita yace “wai mesa bakimin magana Rashy?” Chak ta tsaya saikuma tajuyo ta kalleshi tace “kada ka sake kuskuren kirana da sunan nan only those that are dear to me ke kirana dashi not you” ta juya, dasauri yabita yace “I don’t understand why exactly you’re angry with me, I told you nace miki ina sonki ne banda knowledge na your mother’s illness, agidanmu baza’a taba barina na auri yar wacce takeda H…….” “Bilal!!!!” Rashida takirashi da karfi ta daga hannu zata kaimai mari ranta abala’in bace tace “the next time bakin nan naka zai ambato mahaifiyata wlh saina zubar da hakoranka! Nataba cemaka wani abu? Nace ka aureni dama? I don’t even know kana existing so go to hell!” Tana maganan tajuya fuuuu yabita da kallo kowa na department nasu yasan Rashida da masifa but shi he just said it badan rashin mutunci ba he was trying to tell her baza’a bari ya aureta agidansu ba knowing Mamanta nada HIV, baza’a taba bari ya auro diyar unholy mace ba, still he was trying to tell her su zama friends dan he was feeling guilty yanda yagama cewa yana sonta last year dan last year yayi joining nasu dan transfer ya karba daga former school dayake medicine a Sudan, sun fara soyayya sosai yan aji sukamai gulma Mamanta nada HiV bai yarda ba dan bata taba fadamai ba saida aka kirashi akace yazo ga Mamanta tazo clinic itama tana wajen Maman shine yaje ko yagani daga ranan yayi ghosting nata yaki kiranta yadaina daukan wayanda kotamai magana a class yayi banza da ita saima yazo yana kula yan matan class nasu sosai danya bakanta mata rai, saikuma during this 2weeks holiday saiyaji wani irin soyayya ta na tasomai yau daya ganta saiyaji tafi ko yaushe kyau sonyayyan yadawomai fresh azuciye kaman yahadiyeta dan wlh duk department nasu baiga me kyanta ba kawai dai no one can approach her ne sabida masifan ta da fitina.



Koda yafito yaga harta shige bus nasu ta zauna taciro yar wayanta ta makala earpiece tasa a kunne sabida yanda zuciya ta ke tafarfasa, ahankali yasauke ijiyan zuciya yawuce wajen motar shi inda Layla take a tsaye tana hararanshi yabude yana mata murmushi yace “wai ke lafiyanki common shiga mota muje” yashiga mota yatada yaja motan Rashida ta kalla sannan tasake sauke ijiyan zuciya taso Bilal last session nasu sabida she thought shine mutum na farko daya sota for who she is dan ta dauka yasan waye ita kowa na department nasu ai yasani so tadauka yasani, tun bata kulashi tafara kulashi sabida yanda yake shige mata, she really liked him suna waya but rana daya kawai yadaina kulata yadaina amsa wayanta yana kula yan matan ajinsu agabanta yana cemusu yana sonsu just to hurt her, abin yamata ciwo sabida tanada kishi but bata taba nunawa ba, bata taba nuna tadamu ba saima daina kallonshi datayi da kallon inda suke cus she’s even blaming herself data budemai zuciyanta bayan tasan duk wanda zatai soyayya dashi baya going anywhere,  idan ba lectures gareta ba earpiece zatasa a kunne tana karatu tanabin everything da aka musu, she’s a fast learner na ban mamaki, takoyama kanta rayuwan she’s enough for herself, she doesn’t need people cus gani take kowa yimata kallon yar mai HIV ake diyar fasuka, babu abinda ba’a kiran Mama dashi har anan ajinsu su ana cewa Mama karuwa ce cus gata kyakkyawa daman, batason wata ko wani yashigo space nata and hurt her saisa she’s always always protecting her space bawai batason tayi kawa bane ko kawance baya burgeta bane, no kawai she don’t wanna get hurt, kawayenta na layinsu duk iyayensu sun raba yaransu da ita saisa ta maida kanta and centered her life to be just she and her mom.


Yan ajin always sees her as mafadaciya ko magana kama Rashida zai iya koma muku fada saisa suna avoiding nata suma but during group work ko wani abu zatai participating that is idan bamata daukin nauyin yin aikin gabaki dayaba dan tanada bala’in kokari haka dai rayuwan ta yake.



Sunkai asibiti dudda sun saba da hospital din still saida akai orientation sannan aka nuna musu roaster gobe zasu fara taduba taba bata night, daga 8 ne shift nata zuwa 1 kullum banda asabar da lahadi all thanks to HOD nata! She’s so happy da roaster sukai few abu by 11 suka tafi direct hotel din ta wuce takai wajajen 1 tawuce wajen changing room nasu tabude locker dinta taciro uniform nata tashiga chanzawa daidai tagama chanza kayan tana kokarin saka karamin farin hijabinta aka turo door aka shigo changing room din wata cleaner na ce Joy tai murmushi tana kallon gashinta dasauri Rashida takarasa saka hijabin Joy tace “Hi kinzo muje Madam zata mana magana kafin mufara aiki a seminar room” maida locker Rashida tayi tarufe tadauki wayanta da earpiece tasaka a aljihun wando tawuce tafito Joy tabiyota abaya  wani babban hall sukaje da kujeru  ke cike su kusan 34 cleaners din na afternoon zama sukayi Madam dinsu dake tsaye gaban hall tace “I called for this meeting sabida na sanar daku Oga na gari he can come anytime, alot of you dakukai joining this hotel like 2yrs ago baku sanshi ba, he can come at any moment or day idan yaga dama, baya tolerating the slitest of dirt dan haka kuyi aiki dakyau, Rashida!” Dago kanta Rashida tayi takalleta Madam tace “since kina afternoon duty yanzu anytime kika shigo before ki goge anywhere ki tabbata kinzo wajena kin amshi key kin goge office din Oga, for afternoon kene mai gyara office din da safe kuma Kola, abubuwan mop na gyaran office dinshi is different dana general gyara after the meeting you will follow me ki karba” Gyadamata kai Rashida tayi tace “Yes Ma” tunda take aiki yau ne rana na farko dataji anyi maganan mai hotel dinma kusan shekara biyu kenan bai taba zuwa ba ko kuma yataba zuwa bata sani bane oho dai, addressing nasu tayi na kusan 20mins sannan tace “dismiss follow me Rashida” binta Rashida tayi abaya suka wuce office nata tamata handing over key card da sabon bucket mop su air freshener da sauransu a cleaning trolly tace “gashi maza maza 5th floor ai kinsan office din” Gyadamata kai Rashida tayi tafice daga office din tawuce elevator ta shiga zuwa 5th floor din, wani special corridor akebi aje office din da shi kadaine a hanyan corridor din, key wanda take kati ta manna a kofan kofan yabudu hakanan kawai gabanta yafadi batasan mesa ba hannunta tasa ta tura kofan ahankali ciki duhu dan an kashe wuta, hannu tasa tafara kunna wutan Babban office ne sosai daya hadu bana wasa ba, akwai dogon sofa banda table da chair ga babban tv ga desktop gawani mini library da akayishi design na tree kowani branch anyi naming nashi countey ga books na garin awajen saikuma wasu kofofi guda biyu daban daban ahankali tasa kafanta ta shiga ciki sannan ta maida kofan tarufe tana kallo dudda bawani datti, sauka idanunta yayı kan zanenta dake bangon office din dayayi wani irin mahaukacin kyau she can’t believe she drew this, daina kallo tayi tashigo ciro brush na cire cobweb.


💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 7️⃣

Zaune suke dukansu afada, dan kowa yanzu is at home babu wani maganan zuwa aiki ko wani abu zaman makoki suke, yawanci Kabir ke attending, Riyad na zaune inda yake hardly yake magana, wayanshi ne yahau ringing ganin Mom yasa yadauka yakai wayan kunne batare dayayi magana ba, Mom tace “come nayi arranging private outing dakai da Munir da 2 security personnel da Doddo (Baban Mom Attorney General na Nigeria) ya aiko maka dashi daga Abuja kuzo kuje kaga Haleema gobe zata wuce school” jiyayi kawai ranshi yabaci amman yadaure ahankali yace “okay” yazare wayan daga kunne, kallon yayinshi yayi yace “Mom nakirana bari naje” gyadamai kai sukayi banda Kabeer dako kallonshi baiyiba, tashi yayi a tsanake yana gyara zaman milk jumper rigan dake jikinshi nawani attajirin yadi, fadawa sukahaumai kirari. “Takawanka lafiya Babban mutum! Yariman dashi kadai aka haifa agarin Riyad mai martaba yabashi suna Riyad, dan kwalisan zakaran da ya riga yayi cha…..” wucewa yayi dasauri yafice dan baiso yawuce side na Mom a falo yasameta ita kadai tai murmushi ta taso dasauri tana gyaramai gaban wuyan riganshi tace “Masha Allah, yarona akwai kyau wlh, bama saika chanza kaya ba” ashagwabe kaman zaiyi kuka yace “Mommmm” dan hararanshi tayi tace “shagwabanka will not work nabiye maka u will never get married ko Doddo yayi na’am da decision din” ahankali yarike hannun Mom din kaman dan yaro yace “but Mom I don’t even know the girl balle na sota” dan shiru tayi tana kallon yanda yake mata wanda halinshi ne duk girmanshi idan bayason abu haka yake mata shagwaba at this point so take ta lallabashi dan batason tasake fada da yaronta datakeso sama da komi aduniya cikeda so tace “Son you are from royal family yawanci haka ake aure, first wife din Baban ka Maman su Kabeer da 2second wife dinsa Maman su Munir duk auren hadine baya sonsu, mai Babban daki ta zabamai su ya aura dan bayaja da maganan mahaifiyarsa, daga kan Maman su Shuibu dakuma ni last wife dinsa ne matan da marigayi yaso yakumayi soyayya damu is a normal thing haka abun yake, gidan sarauta kenan with time zakaso Haleematu she’s a good girl duk agaban mu nan ta taso and she really loves you kaman kamata asiri d’ana badai farin jini ba” Mom tai dan dariya dayasa kawai ya rungumeta tareda daura kanshi kan kafadanta wlh zaka dauka karamin yarone murya chan ciki yace “to Mom at least Baba yayi koda 7days ne kafin nafara zuwa neman wata, Mom I am still moaning my father I am not in the right state of mind to meet any girl ko talk to her” cikeda lalama Mom ta shafa kanshi tace “I know but do it for me kaji ko akwai abinda bazaka iyamin ba ni Maman ka?” Ahankali yace “babu” murmushi tayi tace “yauwa dan albarka, Oya tafi jeka shiga mota suna jiranka abaya” gyadama Mom kai yayi yasaketa ahankali wani kalan murmushi Mom take tabishi da kallo tana kara wani son yaron nata da alfahari dashi wucewa yayi yazaga baya budemai bayan wata mahaukaciyar tinted jeep akayi ya shige security yarufe kofa kallon yanayinshi Munir yayi ahankali yace “chill kawai being born from this family I guess comes with all this abubuwan” fuzar da iska Riyad yayi yakalli gefe baice komiba aka tada motan fita daga gidan sukayi tawani secret gate basu da nisa nan da nan sukakai gidan Waziri lafiyayyen kayattacen iso aka musu aka kaisu wani lafiyayen falo suka zauna wayanshi yaciro yana dannawa kawai, Maman Haleema ce tafito cikeda farinciki tace “sannunku da zuwa Yarima Riyad da Munir sannu sannunku” anatse Munir yace “ina yini Anty” anatse shima Riyad kanshi na kasa muryanshi baya fita sosai yace “ina yini Anty” washe baki tayi kaman ta yaga zuciyanta sabida farin ciki tace “aahhh Riyad call me Mama ai yanzu anzama daya sannunku da zuwa bari naje gatanan zuwa” tashi tayi tabar falon bata wani dade da fitaba Haleema tafito tana sanye dawani ubansu exclusive atampa an mata dinki Riga da skirt daya kamata dam ajiki, ta yano karamin gyale tayi makeup tai matukar kyau da black beauty ce abinta mai kyau tana kamshi, kallo daya tama Riyad zuciyanta yakusan tarwatse, gogan yayi masifan kyau yayi wani zama kaman shugaban kasa yana danna waya abinshi batare daya nuna alamun yamasan an shigo falon ba, zama tayi kujeran dake facing nasu cikin murya mai laushe da dadi tace “barka da zuwa Yarima Riyad ina yini” ganin Riyad wayanshi yake dannawa yasa da sauri cikin barkwanci kartaga kaman yamata wulakanci Munir yace “auu ni za’a watsama kasa a ido ni hoto ne a falon nan ko Riyad kadai kika gani”? Dan murmushi tayi tace “ai kaima zan gaidaka kawai nafara gaida wanda zai kasance mijinane kuma uban y’ay’ana nan bada jimawa ba” “uh uh uhmmmm” Munir yayi gyaran murya yana kama baki sai kawai yamike cikeda wasa yace “bari naje waje abuna tunda abun hakane, nima Allah yabani tawa uwar y’ayan” yataba Riyad ganin yaki dena taba waya yace “ina waje” gyadamai kai Riyad yayi yawuce yatafi zai cigaba da danna waya dasauri cikin murya mai sanyi Haleema tace “bismillah yallabai ga abinci da abunsha na ijiye maka a dinning” dan dago idanu yayi ya zubamata su dasauri tasauke nata idanun kasa dan bazata iya jure kallonshi ba, idanunshi kaman an wanke da madara, tana wani irin jin dadi aranta kaman an gama biya mata bukatunta na duniya, daga sama zuwa kasa ya kalleta yaune rana na farko dayake kallonta baiga wani makusa ba she’s fine, educated classy but shi baiji that feeling of love da akace anaji in his heart ba, his heart is not racing, daya ganta his heart didn’t flutter, infact zuciyanshi is beating normal, breathing nashi bai chanza ba, ya kalleta and he don’t feel like looking at her again, she’s fine but batai making heart nashi fine ba, he’s not having butterflies nor goosebumps acikinshi da jikinshi, he’s not finding her intriguing dudda tai makeup etc, nothing about her is enticing his aura, he read alot barinma lokacin PHd nashi, he knows the signs of love and baiji ko daya game da itaba, he sees her just the way he sees kowace diya mace aduniya nothing special nothing different, all this look and assessment yayishi ne in secs na kallonta kawai ya dauke kai yacigaba da danna wayanshi ayangance batare dayace mata uppan ba har lokacin.


Toshi yanzu mezai fadamata? He doesn’t even know what to say, watsapp yashiga yama Mom magana yace “Mom” nan da nan Mom saiga reply tace “ya akayi yaron Mom kunkai?” Da sauri yayi typing. “yes but I don’t know what to say to yarinyar Mom” reply Mom tamai da “start conversation ask her to tell you about herself” reply yamata da “Yaya zan fada?” Mom tace “Haleema tell me about yourself” kaman zai fashe da kuka yace “too long Mom” salati Mom tabuga a chatting din tace “zan bata maka raifa tell her now!!!” Da dago kanshi yayi yakalleta karaf suka hada idanu dan kallonshi take kaman tasami video dasauri yadauke kanshi murya ciki ciki ba yabo ba fallasa yace “tell me about yourself” wani irin murmushi tayi na jin dadi tace “okay but bari nakawo maka drinks tukunna tunda bakaso kaje dinning” batare data kalleta ba still yace “no banso” wani abu taji yanda yayi maganan bako kara amman tadaure takoma ta zauna tace “where do I even start, okay I am 24yrs, nayi sauka last 2yrs, ina karanta international relation a Oxford, ina final semester zan gama nan da 1month, ina business I have a cafe and na iya makeup but banama mutane kaina nakemawa, I love traveling too like you” tayi maganan tana kallonshi expecting reaction amman ko motsi baiyiba tace “I love having fun celebrations irin su biki, zuwa wedding dinner friends and I love shopping and I love reading novels mostly english ban iya karanta hausa books ba I think basically that’s all, ohh I have plenty friends” daga wayanshi yayi yama Mom typing tagama gayamin about herself Mom natafi ko? Dasauri Mom tace “common tell her about yourself too” ahankali yace “Mom I hate sharing u know ni nagaji i want to come back home I don’t like their house is making me feel sick” kawai yafito daga whatsapp din kafin Mom tace wani abu yamike zumbur yace “bye” kallonshi tayi kaman tahanashi tafiya tadai daure tace “tom nagode” so take yabata numbers shi koda shi bazai karbi nata ba amman bemayi maganan ba.



Yana fita yashiga mota Munir yabishi da kallo yanda yake cire boturan wuyan riganshi da sauri sauri sai kawai yahau dariya yace “banda business da yawo gari gari banga uban abinda ka iyaba Riyad wlh” wani juyowa Riyad yayi yamai mugun kallo baice komiba Munir ya kyalkyace da dariya zaiyi magana wayan Mom yashigo yakalli wayan kaman zaiyi kuka yadafe kanshi yace “ohhhh Mom nadamuna wlh” murmushi kawai Munir yayi baice komiba daga wayan yayi Mom tace “kana ina”? Ahankali yace “muna hanyan dawowa” katse wayan kawai tayi jin ana kiranta adayan wayan ganin batamata rai Riyad yakeson yi da ranan nan, ganin Waziri ne ke kiranta yasa tadauka cikin barkwanci yace “Inlaw Inlaw to Alhamdulillah, yanzun nan Maman Haleematu ke gayamin Yarima Riyad yaje yaga Haleematu da alamu akwai nasara” murmushi Mom tayi tace “eh haryama fara dawowa wai kunya, kasan fa Riyad akwai miskilanci da shegen kunya har yanzu abu yake kaman karamin yaro” dan dariya Waziri yayi yace “abinki da auta, yaro kwallin kwal, ai saisa yayi farin jini awajen kowa ina mai tabbatar miki yawanci yan kwamitin nada sarki idanunsu akanshi suke nadauka zanmasha wahalan convincing nasu amman bahaka ba wlh sunason Yarima Riyad sabida yacika sharuddan zama sarki, nafarko ga tsatso mai kyau jininshi gaba da baya asalin sarauta uwa da uba, banda haka baida any criminal record ko wani case da police ko wani abu, ga ilimi boko da islamiyya ga business daya bude dake kawoma Kano cigaba sosai dazun nan Gwamna ma yakirani kinsan Meyace mini?” Dasauri Mom tace “a’a meyace?” Dariya Waziri yayi yace “cewa yayi cikin yaran sarki waye mai manya manyan hotels din nan da gidajen mai din nan nacemai ai Riyad ne” dan dariya Mom tayi tace “ai Dodo ma nakirashi nasa yama Gwamna maganan” Waziri yace “ai ina mai tabbatar miki kaman Riyad yagama dawowa sarki dudda naga take taken Baffan su Mujitapha dakuma Kabeer amman Riyad yamusu fincikau dole ki tashi tsaye” dasauri Mom tace “tuni natashi kaga yanda ake sauka akanshi ne, duk nasamai magungunan tsari a abincin danake basa da kaikayi koma kan mashekiya” Waziri yace “yauwa hakan kinyi daidai, ranan da sarki yacika bakwai za’a sa ranar da za’a nada sabon sarki sai ayi bikin Sarautar da aurensu tare koyaya kuka gani”? Mom tace “kwarai ai duk inda zan shiga saina shiga na tabbatar Riyad yagaji sarautan nan yarona kadai ya chanchanci mulkin nan bayi yanda naga dama”.


BAYAN 1YR…..


SO WANNAN NE FIRST PART NA THIS LABARI NAKAWO SHİNE SABIDA KU GANE TUSHEN LABARIN BAN WANI SO NABATA LOKACI.


GOBE ZAMU CIGABA DA LABARIN BAYAN 1YEAR RIYAD YARIGA YAZAMA SARKI❤️


💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 🔟

Cobweb tafara ciccirewa kafin tafara shara da vacum cleaner sannan tafara goge goge tundaga kan su desktop din, frames na bango,  admiring design da komi na office din kowaye maishi really shows love nashi ma simplicity and art, gyara ko’ina tayi har labule saida tai dusting sannan tabude first kofan data gani ga mamakinta saitaga bedroom ne ga lafiyayyen gado awajen ga closet gyara komi tayi sharp sharp tai moping har bayin dake dakin sannan tafito tabude dayan kofan taga nan ma bayi ne ta gyara kusan 1hr tabata sannan tagama komi tafito takoma station nasu, kafin akira waya anason tazo room 456 ta gyara ta wuce taje ta gyara haka dai tai aiki had 5 sannan ta tashi.


Changing room takoma ta chanza kayan aikinta ta maida atampanta na safe tasaka pink crocs dinta na safe tana murmushin tuna Mama data siyamata sanan ta goya jakan nata tafito tana tafiya ahankali receptionist dinsu dake wajen tana ganinta cikeda fara’a tamata waving hannu tace “bye beautiful Rashy” dan kallonta Rashida tayi hatta daga hannu zata mata waving itama saikuma tasauke hannun like a weirdo, tadan kyafta ido sau biyu kafin tace “thanks” tawuce da sauri tafita dayan receptionist din tace “when will you stop throwing kanki on Rashida? Ko Madam dinmu tasan yarinyar is a weirdo” dan murmushi tayi tace “is because she’s like that nake sonta, I don’t want normal people irinmu as friends inason irinsu Rashida as friends, the girl is lovely” tabe baki dayan tayi tace “nidai nawuce asha night duty lafiya see you in the morning”.



Tana fitowa waje ta tsaya saikuma ta juyo jakanta da sauri zuwa baya tana kallon jakanta taja zip tashiga budewa tana kokarin ciro wayanta….


Ahankali yasauko da kafanshi dake sanye dawani Bottega veneta coffee color takalmi mai tsinannen kyau daga cikin motan, kumbunan shi farare kal kal agyare kaman an musu fenti tsabagen sheki dasuke, kafin gentle yakarasa saukowa yafito daga motan, dogone sosai yana sanye dawani coffee color soft yard na yan Malaysia mai bala’in taushi anmai simple aiki a wuyan, idanunshi sanye da bakin glasses na Cartier, glasses din yasa baka ganin idanunshi sai pink lips nashi dayayi so pinkish gawani irin lafiyayen bakin saje dayabi fuskanshi zuwa gemunshi da gashin baki daya karama fuskan shi kyau sosai da kwarjini da haiba kaman wani balarabe, hannunshi na daure da agogon Cartier shima latest collection dinsu, his entire body speaks luxury, he looks squeaky clean kaman ka lashesa,

daidai taciro wayan tana kokarin manna earpiece a kunnenta dan Mama takeso takira kawai taji sahun gudu gudu sauri sauri dasauri tajuyo dan taga meke faruwa, daidai lokacin itama Mirabel data fito daga cikin hotel din tazaro ido tace “Oga yazo OMG” tai parking space dagudu itama same with sauran ma’aikatan dake waje, kallon inda sukayi Rashida tayi har tana dage but still bama ta iya hango wanda ake kira da Oga sabida yanda ma’aikatan suka zagayeshi cikeda farinciki sunamai sannu da zuwa, dauke kanta kawai tayi takarasa makala earpiece din tafara tafiya abinta tana dialing number Mama….


Shifa he hates too much attention, the way suka zagayeshi ana gaidashi kaman wani celebrity yazo sai abin yakara batamai rai dan har yanzu abinda Mom tamai da Haleema na batamai rai, the way suka wani fito suna gaidashi abin kular dashi ma yayi wucewa kawai yayi batare daya kula ko mutum daya cikinsu ba yana tafiya a kasaitacce Munir shine ya tsaya amsasu daidai takai gate zata fita taji wani iska ya kadata kamshi mai dadi gaske wanda bata taba jin irin shi aduniya ba yadaki hancinta da saida ta lumshe idanu sabida dadin kamshin daidai an budemai kofa shima ya tsaya sabida sanyin dayaji yakai 10secs ahaka kafin yadaga kafa yashiga cikin lobby su dan security sun budemai glass door din, ya shiga ciki yana bin ko’ina da kallo sai kawai yawuce wajen elevator manager tafito dasaurin ta daga office dinta tana murmushi tace “welcome Sir” Gyadamata kai yayi yadauke kai yadaga hannunshi yana kallon agogon hannunshi daidai kofan na rufewa 5th floor yawuce direct office nashi yaje hannu yasa a aljihunshi yaciro wayanshi kawai ya manna a kofan kofan yabude yashiga ciki an kunna AC wajen sanyi, tsayawa yayi chak yana kallon frame na artwork dake bango dudda manager ta turama Munir hotunansu ta email shikuma ya nunamai but yanzu daya gansu in reality sai sukamai mugun kyau. Daga kafanshi yayi yataka zuwa wajen yasa hannunshi yasauko dashi yana kallo sai kawai yayi murmushi for the first time today yaji abu yasashi farin ciki. Zama yayi akan kujera tareda lumshe idanu yadaura hannunshi aka yayi shiruu he don’t like the way Mom kesashi yin abubuwan dabayaso yayi, she made him king dudda bayaso, she made him marry dudda bayaso, yanzu kuma she’s telling him how to handle family shi, bude kofan office din akayi aka shigo hakan yasa yabude ido kadan Munir ne yamaida kofan yarufe yashigo yaja kujera ya zauna kai tsaye tace “waikai meke damunka eh”? Kallonshi Riyad yayi saikuma yayi shiru tareda fuzar da iska, tashi Munir yayi yasan bazai gayamai ba yawuce wajen kofan bathroom haryasa hannu a kofan yajuyo yakalleshi yace “Riyad I hate seeing the slightest damuwa akan fuskan ka, banda you’re my brother, you are  also my best friend, kowani yanayi kake ciki affects me, life can be colorful idan you let it be that to you, be the Man of your life karka bari kowa yagaya maka ga yanda zakayi, you are loved, jama’a harda wayanda basu sanka ba na yabonka, kana adalci asarautan dakake yi kadena bari anything na damunka kaji”? Dan kallonshi Riyad yayi for the second time yayi murmushi yace “okay” bude kofan bathroom din Munir yayi harzai shiga ahankali Riyad yace “thanks” kallonshi Munir yayi sai kawai yayi murmushi yawuce yashiga bayin maganan Munir yasa yaji sanyi aranshi he will take things easy on kanshi and everyday he will try and do wat makes him happy he will live his life, daga yanzu kullum saiya fita zai chanza schedule nashi daga 4:00 har dare ya warema kanshi da  safiya kuma fada, he will leave 2 separate life dinshi privately and peacefully, tashi yayi ahankali shima yawuto yabude kofan dakin yashiga bathroom yawuce direct yadauro alwala yafito abu yataka dayaji ya chaki kafanshi dasauri ya tsaya yadaga kafar ya kalli kasan carpet din yaga karamin dankunne ne baki ya shiga kafanshi dudda bai shiga sosai ba, ahankali yakai hannunshi yacire daga kafanshi yakalli earring din murya chan kasa yace “who dropped this here?” Yayi shiru yanabin dan kunnen da kallo daidai Munir yace “kana alwala ne koka fito? Muje mosque” dasauri ya zura dan kunnen a aljihunshi absentmindedly gudun kar wani yataka, yataho yabude kofan yadauki glasses nashi da waya Munir yace “ba nan kasa zamuje salla mudawo muyi aikin ba” wucewa yayi yace “I thought kaikace i should always be happy, zanje na buga golf yau, tunda Mom tasamin aikin sarki ban buga golf ba” murmushi Munir yayi sai kawai yabiyoshi suka wuce suka fita.

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

  ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 1️⃣1️⃣

 


Salla sukayi a mosque nan ma anata gaidashi still few ya amsa dazasu wuce yasa Munir ya basu bandir na kudi dake pocket nashi, sannan yawuce mota ya shiga mazaunin direba Munir yana zuwa yazaro ido yace “mehaka rabon dakai driving da kanka about 1year kai tunda kazama sarki” murmushi yayi yamikamai hannu ya karbi key baice komi ba yatada mota suka wuce wani private waje dayake buga golf chanza kaya sukayi ga ma’aikatan shi yafara buga golf din yanayi yana murmushi, sosai Munir yaji dadi ganin he’s very happy today kullum ganinshi zakayi so moody. Anan sukai Isha’i sai wajajen 11 na dare sannan yagama yatafi office nashi na wajen yayi wanka ya maida kayanshi yana kallon yanda wayanshi ke ringing yakalli screen yaga Haleema a rubuce kaman bazai dauki wayan ba saikuma ya dauka yakai kunnenshi yayi shiru daga ta dayan bangaren tace “ina kajene yau Mai Martaba? 11 nadare yanzu fa” lumshe idanu kadan yayi bayabo ba fallasa yace “yanzu zan fara dawowa, make tea for me before i come” yana maganan yacire wayan daga kunnenshi ya katse ya ijiye ya karasa saka boturan riganshi shima Munir yashigo yace “mutafi” wucewa sukayi wannan karan Munir yayi tukin har gida, ta private gate dinshi as usual suka shigo parking sukayi yafito yana tafiya a natse har flat nashi, he’s very hungry but tea yakeso dan is late, waya yadaga yayi dailing number Haleema tana dagawa kafin tai magana yace “ina tea”? Dasauri tace “bari natashi na daura tunda kadawo” jiyayi ranshi yabaci but baiso ranshi yayta baci sabida ita hakan yasa yace “kibarshi banso” ya katse wayan yajuya yafito daga flat nashi, shi kawai bai iyajin yunwa ba ne, wajen kofan dazai sadashi da cikin gida yayi yabude fadawa na ganinshi suka zube zasu faramai kirarin rai abace yace “kuje kuyi bacci na sallameku” sauke kansu duka sukayi kasa yawuce fuuu direct flat din Ammi yawuce yana addu’a Allah sa Munir daya shiga bai rufe kofa ba kai tsaye yabude kofan, babu kowa a falo sai TV dake aiki tashar CNN, dinning ya kalla ganin kuloli akai ga flask na shayi yasa yawuce wajen sadaf sadaf kaman barawo yashiga bude warmers din sinasir yagani dake tururi kaman yanzu akayi abunka da kula mai kyau da miyan taushe dayasha cow tail dudda ba abinci yaso yaci ba dan dare yayi sosai saiyaji abun yabiyamai rai zama yayi ahankali yadauki plate ya ijiye yasa sinasir guda 3 da Miya yasa nama dayawa yadauki spoon yafara ci ahankali he loves abincin Ammi har ranshi, tafiya yaji a stairs hakan yasa yadago kanshi dasauri ganin Ammi tana sanye da lullubi ga carbi a hannunta yasa yasauke kanshi kasa da sauri murya chan kasa yace “ina yini Ammi” batace kala ba cigaba da saukowa tayi daga stairs din shikuma yakasa ci gaba da cin abinci sai ahankali ya yunkura zai tashi strictly tace “ina zaka?” Kanshi akasa still yace “uhmm dama nagama ci zan tafi ne” “sit down” tafadi babu wasa a muryanta, baiyi musu ba zama yakoma yayi har dinning din tazo tsayuwa tayi kusada shi rabon dayaji Ammi tsaye kusadashi haka harya manta he can’t even remember when, hannu tasa ahankali tadauki flask da cup mai kyau ta tsiyayamai ruwan shayi tadauki spoon da bottle na honey ta digamai aciki ta tura agabanshi kafin ahankali tace “idan kanaso katafi finish abincin daka faraci, nobody waste abincina in this house” kanshi na kasa har lokacin yakasa dago kanshi ya kalleta, juyawa tayi tawuce takoma falo tazauna tadauki remote ta chanza channel din zuwa Aljazeera ta maida idanunta wajen, adan hankali ya wiago ya kalleta sannan yajuyo da kanshi yacigaba da cin abincin kadan kadan tass ya cinye ya kora da ruwan shayin saiyaji hankalinshi ya kwanta, yanada cin abinci shi but only yasamu abinda yakeso, tashi yayi ahankali yajuyo yadan kalleta hada ido sukayi da sauri ya sauke kanshi kasa cikeda ladabi yace “good night Ammi” “Allah tashemu lafiya Riyad” tana maganan yawuce da sauri yabude kofa yafice tareda maido kofan yarufe ahankali karyayi kara, ahankali ta sauke ijiyan zuciya sannan ta lumshe ido kaman irin she’s hurt ko akwai wani abu azuciyanta, kafin ta tashi tawuce inda yatashi zama tayi wajen ta dauki cup din dayasha tea ta kalla tai shiru kaman wacce ke tunanin wani abu sai chan tadaga flask din ta tsiyaya tea dazun nan ta dafa shayin tawuce taje tai wankan dare, itama bata iya bacci idan batasha shayi da daddare ba, daukan cup din tayi takai bakinta ta kurba sannan ta taso tadawo falo ta zauna tana shan shayin.






Yana shiga side nashi yaga Haleema azaune ga tray shayin tasa wasu arnayen kayan bacci da sauri ta taso tace “ina kaje nakawo maka shayin baka nan babu masu gadinka ka koresu ne”? Rigan jikinshi yahau cirewa yace “yes, kidau shayin kitafi dashi I don’t want” Shiru tayi tana kallonshi tana bin jikinshi da kallo wucewa bayi kawai yayi bayan ya rataye rigan a hanger dake dakin mai kyau ijiyan zuciya tasauke tace “wash Allah na mutum kaman shi yayi kanshi” wucewa tayi ta dauke tray takai falo ta ijiye sannan tadawo dakin tai kwanciyarta akan gadonshi tana jiranshi yafito, yadan jima a bathroom din sannan yafito daure da towel a waist daya a hannunshi yana tsane kai, kallo daya yamata yadauke kai yashiga shafe shafenshi yana fesa turare kafin yawuce walk in closet room nashi yasaka wani dark blue pajamas sannan yafito ko kallon inda take baiyiba iPad nashi yadauka yawuce ya zauna kan sofa ya makala EarPod yayi playing video ranan da akaso kasheshi wanda yarinyar nan ta ceceshi ke ciki, ya kalli video nan yafi sau dubu he is just looking for the girl number datasa a file nata baya shiga, yatura anje address datasa a file nata ba’a ganta ba, yaje da kanshi shima bai ganta ba ance babu wata kamanta ma a layin he’s just greatful yarinyar saved his life, video always give him peace he don’t even know why he don’t care ko sata take koma wacece ita he just wants to reward her yabata better job for saving his life, and huge money to startup business or anything datakeso, gama kallon yayi sai ya zare EarPod din ya rufe iPad din ya ijiye yadan kalli gadon hada ido yayi da Haleema ba yabo ba fallasa yace “wat”? Dan murmushi tayi tace “let’s try having Baby, nakosa naga ina dauke da cikinka na haifo maka magaji” dan yatsine fuska yayi da ita da Mom baisan mesa duk suka damu da cikiba kaman auren yayi 10yrs this is just a year, Allah ke bada haihuwa not him, kaman bazai tashiba saikuma yatashi ya kashe wuta yawuce yahau gadon ya kwanta tareda juya mata baya da sauri ta mirgino ta kankameshi ta baya kaman zata fashe da kuka tace “let’s make Baby kaji My love” shiru yayi shi baisan kodan baida feelings for her kawai an auramai itane koko shine baida lafiyane amman kwata kwata bayajin sha’awan Haleematu ko zata tsaya gabanshi tsirara, everything he’s doing yanayi ne sabida matarshi ce dole ya kyautata mata yakuma sauke hakkin ta daga kanshi, before ya ankara hawa jikinshi tayi tana kokarin mai kiss yadauke kanshi haryau bai taba hada bakinshi da nata ba, jefar da ita gefenshi, hannunshi yakai yaja wandon pajamas dinshi kasa dasauri tashiga daga riganta sama itama, ahankali yakai hannunshi kan boobs nata ya shiga squeezing nasu sannan yayi addu’a yayi sliding in, nishinta ke tashi kawai daga dakin kaman zata shide, dakin yayi tsit, if there’s one thing she kind of understood about him yanada son wasa da boobs, anytime zaiyi abu da ita sunashan squeezing a hannunshi saisa bayan aurensu boobs nata suka kara girma sosai dudda baya sha but ya iya wasu dasu abin namata mugun dadi almost hour and half yayi duk tagama ficewa hayyacinta sannan ya rirriketa tasan he’s cumming cus that’s only time din dayake rirriketa and just be in her body itakuma she uses that opportunity to cuddle him, alokacin zai fara nishi da karfi kaman zai fashe mata da kuka like a baby, kankameta yayi sosai kanshi nakan kirjinta yafara nishi da karfi he just wants to cum yahuta baida kawowa dawuri, idan yakawo once idan he’s going for 2nd round zai iyakai 4hrs bai kawowa, rirrikeshi Haleema tayi tana shafamai kai kalan nishin dayake mata a kunne da fuska na kara tafiya da imaninta yana hitting wajen da kyau chan yayi karaaaa mai sauti wanda haka yake yajuye mata komi ciki, yakai almost 2min ahaka baitashiba yagama tsiyayewa ciki kotayi cikin shima yahuta da jaraban Mom sannan yasauka daga jikinta tareda maida wandonshi yajuya mata baya yana sauke ijiyan zuciya, dasauri tabiyoshi ta hugging nashi ta side, ko 1min baiyi da gamawa ba sai bacci jikinta yamata dadi, yakai kusan 1hr a kwance sannan yajanye jikinshi yatashi yawuce bayi yasake wanka ya chanza kaya yafito sai kawai yawuce dayan sakin yaje ya kwanta awajen.


***

Wuraren 6 takai gida da kafa takoma tana shiga taga Mama tareda Uwargida Baba Liman, Baba Liman shi kadai ke mutunci dasu a unguwan, yana tursasa matanshi suzo su duba Mama once in a while hakkin makotaka, anytime yayi noma ko wasu yan kudade suka shigomai he always send something to Mama dudda Rashida bataso dan shima bukatan taimakon yake, but tana girmamashi kodan mutunci da suke da Mama da yanda Mama ta daukeshi itama. Uwargidan tana shigowa once in a while tazo gaida Mama dudda ko ruwa batasha aka bata kujera ma saita share da dankwalinta take zama akai kaman irin idan ta zauna ko ta taba wani abu nasu zata kamu da HIV itama, Rashida bata sonta sabida Mama ne ma take gaidata dan da wannan zuwa tana kyama tana kaffa kaffa gwara tayi zamanta agidansu ai babu wanda yace dole saitazo, tana ganinta ta kirne rai ganin ta shimfida dan kwalinta saman kan tabarman da aka bata a tsakar gida ta zauna kai tsaye bayan tai sallama ta wuce wajen Mama dake zaune kan dakalin bakin kofansu ta rungumeta tace “Mama nadawo” murmushi Mama tayi tace “sannu da zuwa ga Indo baki gaidataba” kallon Matan tayi dake kallonta tana washe baki, mugun kallon da Rashida tama matan yasa da sauri Indo tamike tsaye tana dauke dankwalinta tace “bari naje Maryam Allah Kara sauki” Mama tace “nagode Indo saida safe a gaida yara” takalli Rashida tace “waike mesa fitinanniya ce”? Tashi tayi tace “Mama tunda ba dole akamata tadinga zuwa gidanmu ba ai sai tadena wannan kyama kyaman bazan dauka ba” shiru Mama tayi ta buga tagumi tana kallonta hakanma saiyasa tayi dariya tace “Mama mehaka kikai tagumi kina kallona kaman kinga hoto”? Cikeda damuwa Mama tace “tunani nake wakika biyo da temper nan naki Rashida? Kap dangina babu mai fada masifa, fushi, taurin kai da kafiya irin naki, to maybe sai dangin mahaifinki dan bangama saninasu ba abinki da yan Sarauta sunada yawa” tamau Rashida ta daure fuska sai kawai ta tashi tace “Mama inaga harda kallan son da mutumin nan yaga kinmai saisa ya wulakantaki, baki magana baki kawoshi ba after how many years Mama you still remember mutanen da mutumin that hurt and destroyed life dinki” kallonta Mama tayi tace “babanki yamin kirki abaya dudda ya wulakantanin amman hakan bazaisa na manta kirkinshi ba” ayanda fuskan Rashida yayi da ace zata iya dukan Mama datayi akufule tace “Allah karya dauramin son wani haka Mama cus inaaa! Mama you have no idea yanda na tsani mutumin nan and duk randa na sami opportunity wlh I will hurt him sama da yanda yayi hurting naki, bari nagama makaranta nazama wani abu saizan ya wulakantamini uwa!” Mama zata kara magana Rashida ta tashi da sauri kawai tashige ciki Mama tai murmushi kawai tareda sauke ijiyan zuciya.

***




Around 7 na safe yadawo daga masallaci wanda haka yakeyi daman before yayi bacci yatashi 10 ya shirya yaje fada by 11. Bacci yakoma adakin daya kwana ya kwanta, harya fara bacci yaji hayaniya sama sama da alamun kuka, dan bude idanunshi kadan yayi trying yaji da gaske anan side yaji kuka, knocking kofar dakin dayake ciki akayi saikuma yaji muryan Mom afadace tace “open this door Riyad nasan kana jina” tashi yayi ahankali ya kunna wutan dakin yana mamakin meya faru, yadauki jallabiya ya zura dan dagashi sai short yayi wajen kofan ahankali yabude kofan Mami yagani ranta abace saikuma ya hango Haleema duke tsakiyan corridor tana kuka sosai kaman an mata mutu har yanzu rigan baccin jiya ne ajikinta, yadai daure yace “good morning Mom…” hannu Mom tadagamai ranta amasifan bace tace “hold greeting naka I don’t want it Riyad” confusingly yake kallon Mom saikuma yakalli Haleema dake kuka sosai trying to ask meya sameta kawai yaga Mom ta mikamai hannunta da karamin dankunne ke kai tace “a ina kasamo wannan Riyad”? Kallon dan kunnen yayi harga Allah baigane dan kunnen bama hakan yasa yace “Mom wat is this”? Cikin fushi sosai Mom tarufeshi da fada tace “nikake tambaya wat is this? Matanka ta tsinci dan kunnen mace a aljihun rigan kayan dakasa jiya kadawo very late kusan to 12 nadare” sai alokacin yama gane dan kunnen nan dayatake ne akasa a office nashi dasauri yawani ma Haleema dake kuka kallo kai tsaye yace “kayana kika duba kika bincika is that abinda kikeyi anytime kikazo this side?”  Mami tace “look at me here nine nazo nike magana dakai not Haleema” authoritatively tace “tell me, me dan kunnen mata keyi a aljihun ka wanda bana matarka ba, mata kake bi yanzu Riyad? Me ka nema wajen Haleematu karasa? Dan kunnen waye tell me now”? Tunda yake baitaba jin Mom ta batamai rai irin na yau ba kanshi ya nuna yanama Mom wani irin kallo yace “Mom I’m your Son, kin sanni sama da kowa a duniyan nan, Mom yanzu akazo aka cemiki ina neman mata bazaki iya shedana ba? Do I look like ina neman Mata? Ni?” Harga Allah tun Riyad na yaro bai taso dason Mata ba, ko kallonsu bayayi hasalima kunya suke bashi amman dai cikeda kafiya dason nunama Haleema she own her Son tace “how do you want me to trust me bayan matarka taga dan kunne akayan dakasa jiya and kadawo very late eh? Look at the way the poor thing is crying” tanuna Haleematu dake wani irin mummunan kuka tace “ko kadan banso kayi hurting yarinyar nan cus she’s a good gurl, tadaukeni mahaifiyarta, Babanta yataka rawan gani sosai wajen zamanka sarki, he’s the one blocking all kulle kulle da akeyi yanzu daka zama sarki” “did I ask him to do anything for me?” Riyad yayi maganan da karfi da saida Mom tabude idanunta cikeda mamaki ta kalleshi, yau Riyad ya daga mata murya haka? Agaban matarshi, cikeda mamaki tace “Nikake dayama Murya Riyad?” Cikin fushi sosai yace “Mom abinda kikemin is totally wrong, sabida Haleema tace inabin mata saikizo ki yarda da maganan ta kinamin fada agabanta baki san danki ba? You’re not allowing me to be the man in my marriage, nagaji I can’t continue with this marriage because of Babanta kikasa ya nemamin sarki dagayau…….” da sauri Haleematu ta taso tana kuka sosai afirgice kawai ta zube agabanshi tarike kafanshi tace “dan Allah kayakuri wlh nasan bakabin mata bansan menakeyi ba danaga dan kunnen saisa nakira Mom” fizge kafanshi yayi yakalli Mom yace “dagayau tell her bata babu this side I forbid her from coming to my side, duk sanda nake bukatanta zan nemeta!” Rushewa da kuka sosai Haleematou tayi takama kafan Mom tace “Mom do something, dan Allah kimai magana ya yakuri, bazan karaba”

Yakalli yanda Haleema ke rokon Mom ya cije baki ya kalli Mom din dake kallonshi mamaki yagama kasheta yace “and for your question Mom” sai kawai yadaga mata kafanshi yanuna mata tafin kafan inda dan kunnen ya shiga yace “nataka dan kunnen nan akasa ya shigan min kafa, na cire zan yarda ganin ina cikin premises kar wani yaje yataka yasa nasa a pocket with the hope nafito i will trash it but I forgot” ya maida kafanshi ya ijiye yace “I don’t want the sarauta ki nemo wani kibashi, I need a break” yana maganan yabi ta gefensu yawuce dagashi sai jallabiyan jikinshi yanda ranshi yabaci ko waya bai daukaba Mom tajuya tabiyoshi dasauri ganin ahaka zai fita tace “Riyad, Riyad” hannu yasa yabude kofa azuciye yafito key motar compound nashi na wajen Munir hakan yasa yayi gate yafice fadawa zasumai kirari ya buga musu tsawa “leave me alone!” Kawai yawuce fuuuuuuuu shi kadai yana tafiya a bala’in zuciye kawai yawuce side din su Munir bude kofa yayi azuciye key daya hango akan table yawuce kaman zaki yadauka daidai Ammi na lekowa daga kitchen ganin shi yadau key dinta ranshi abace yasa tai shiru daidai yabude kofa yafice parking space nasu yaje yana danna key wani jeep yayi kara motar Ammi ce direct yawuce yabude ya shiga yanda ya danna horn zakasan ba lafiya aka budemai key yawuce yafita.


Kusan yaune rana na farko da Mom take ganin serious fushin Riyad haka, and for him to provoke like this that means abinda yafadi gaskiya ne babu matan dayake nema, hankalinta yatashi sosai, wayanta dake hannunta ta daga zata kirashi saitaga wayanshi akan gado kawai cike da takaici takalli Haleema dake kuka tace “you are not sure of something akan wani dalili da rashin hankali zaki tafka shirmen nan eh Halimatu? Jibi abinda kika jawo yanzu? Bakisan idan mai hakuri yayi fushi yafi zama worst ba? Jibi yanda yafita ko wanka baiyiba bai dauki wayanshi ba tsabagen bacinrai, sabida kinga dan kunne in this pocket mesa zaki assuming mata yakebi”? Cikin kuka Halimatu tace “Mami kishi ne yarufeni I can’t share mijina with anybody wlh, kiyakuri Mom kiyafemin dan Allah” dan tsukin takaici Mom tayi tace “naji is not your fault nima daban biyemiki ba nasan waye Riyad, yana tashen samartaka ma beyi neman mata ba sai yanzu, tashi kitafi side naki zansa azo agyara dakinshi lemme handle the situation” Kama hannun Mom Haleema tayi tace “Mom kinsan baya tsallake maganan ki, please kice yayi hakuri karyayi fushi dani koya chanzamin fuska” “naji tafi” Alkyabban tadauko tasaka tawuce tafita daga side din, Mom itama tafito ta tafi sauro da idanu takira babban bafaden gate din yataho da sauri ya zube yace “an gaida Mai Babban daki matan da darajanta yakai…..” Mom bata bari ya karasa maganan ba cikin whispering yace “inada aiki for you Sarki baida lafiya bazai iya fitowa ba shine abinda zaka sanar kaida yaranka bansan kowa yasan Sarki bayanan, zakaga babban sakon tukuici kai haka” Gyadamata Kai yayi yace “angama me Babban daki” juyawa Mom tayi takoma ciki takira Dr su kaman da gaske, kazo gida by 10 duba Riyad”.

**


1 dot tagama da hospital wanda a outpatient department group nasu yake tareda wani consultant na pediatrics, she’s happy sosai yanda itada Bilal da crew dinsa na yanmata basa group daya, salla tawuce tafarayi a masallaci sannan ta linke lab coat nata tasa a bagpack tawuce tafito daga mosque din tagoya jakan abaya tasa takalmi tafito Keke napep ta tare zuwa hotel, sauka tayi tabiyashi ta shiga ciki ko kallon receptionist wajen batayiba as usual changing room tawuce tashiga cire kayan jikinta tayi ta saka dark blue dogon wandon da light blue shirt mai botur tundaga kasan rigan har sama wajajen wuya, farin fatan jikinta ya haska kayan sosai kaman dan ita akai uniform din, clean baby hijab nata farı ta dauka ta saka wanda yarufe mata kirji sannan tasa takalminta, fitowa tayi  zuwa office din Madam tai knocking akace mata ta shigo, shiga tayi tace “good afternoon” “Afternoon Rashida oya ga card din jeki goge office din maza maza, ki dauko kayan gyaran office din a store” karban katin tayi tace “okay” fitowa tayi tawuce store tahada duka abubuwan dazatai amfani dashi sannan tawuce elevator zuwa 5th floor tayi corridor office din, manna katin tayi kofan yayi kara sannan ta tura kofan ahankali hakanan kawai taji gabanta yafadi ga office din yayi mahaukacin sanyi kaman kankara AC a kunne, ahankali ta shiga tareda maida kofan tarufe cikin yar muryanta tace “wayyoo sanyi” dasauri tawuce wajen kashe AC ta kashe tanabin office din da kallo alamun an shigo dama jiya ance Oga yazo lokacin da zata tafi saisa ya shigo office dinshi kenan, a aljihunta tasa hannu ta zaro yar wayanta ta makala earpiece din a kunnenta ta danna wakan Araina Grande mai suna Into You, sannan takoma wajen kofa tadauko kayan ayyukanta tawuce bayi ta tara ruwa tafara bin wakan tafito tadauki handglove black na aiki tazura a hannu tadauki brush din share kura tafara aikinta tana waka……


Ko manager shi batasan yana nan ba babu wanda yasani sabida yanda yazo da jallabiya he looks like normal guest yawuce direct elevator, tunda yazo yake kwance dazun nan ne ma ya iya tashi yayi zuhur yakoma ya kwanta though ba bacci yakeba but ya lumshe idanu kawai having moment of peace, tunda aka bude kofan office din aka shigo yaji, sai chan kuma yaji murya mai bala’in zaki tace wayyoo sanyi, saikuma ga same muryan tafara waka tana aikace aikace dake making sound, shi kadai yace “is she some sort of DJ ko wata Artist?” Cus muryanta dadi bata missing ko harafi daya, kaman tana performing a stage, chan kuma kawai saiya tashi zaune sabida ta kunna vacuum cleaner bayajin muryan nata da kyau kaman da, karan vacuum cleaner yafi muryanta kara, ahankali yataso yataka zuwa wajen kofan hannunshi yakai ahankali zai kama handle na kofan yabude kofan sai kawai yaji yafasa cus baimason aganshi amman kuma saiya tsaya chak awajen yanajin the way she’s singing din cus takashe machine din yanzu tana bin wakan Into your arms na Witty Lowry, God! Her voice is captivating kawai yaji yakasa matsawa.


Daukan bucket na mop din tayi a hannu tarike vacuum cleaner shima a dayan hannun ta tako zuwa gaban dakin sabida tagama da office sai uwardakan before wanke bayuka, juyar da fusknata tayi tana ijiye vacuum cleaner akasa still holding on to the bucket na mop takai free hand din tabude kofan ahankali fuskanta na kallon side din tana rera waka tadawo da hannun tana kokarin daukan vacuum cleaner back danta shigo tunda tabude kofan…

Tunda tabude kofan yayi setting eyes nashi chak akanta yana kallonta tundaga kan pink crocs din dake kafanta dayay finding nasu so funny, dogon dark blue wandonta dabai kamata ba at all kusan ma yaso yamata yawa ya kalla, zuwa navy blue rigan dashi ma bai kamata ba zuwa farin hijab din jikinta that looks extremely neat da side na face nata da he could see sajenta da dan gashinta baki sidik daya leko, daidai tadaga vacuum cleaner ta juyo da kanta kawai taga dogon farin mutum da farin jallabiya ajikinshi ya tsaya chak kaman gunki yazuba hannu a aljihun jallabiyan yana kallonta batada tsoro but saida ta tsorata tayi baya da sauri ganin namiji hakan yasa cord (wayan) vacuum cleaner ya kwasheta jikake timmm tafadi akasa ruwa mopping din hannunta ya kware mata daga ciki zuwa wando, zaro ido tayi atsorace tace “wayyoo Allah na” tai maza maza ta tashi tama rasa mezatayi arude tace “I am sorry” ganin kaman ba ghost bane maybe shine me hotel din takai hannu tana kakkabe jikinta da cinyanta da sauri chan ta lura da aljihuta ajike dasauri tace “Innalillahi wayana” hannu tasa a aljihun taciro wayanta ta cisge earpiece din tashiga tattaba wayan baya haske tace “innalillahi Innalillahi” bude wayan tayi da sauri taciro battery ta huhure wayan sannan tawuce table dagudu ta ijiye wayan awajen danya bushe sannan tajuyo tama kasa kallonshi taduka tana daukan mop tace “sorry i will clean everything yanzu” chak yake kallonta dan yana ganin full fuskanta ya ganeta the girl from the airport! The feisty gurl! Yarinyar daya dade yana nema to reward her for saving his life….

💫 SANYI DA ZAFI 💫

  ✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣2️⃣

Bucket na moping din tadauka da gudu tawuce bathroom na office din  ta tara wani ruwa ta taho da sauri jikinta duk rawa yake zata fara mopping ruwan kunfan kasan jikinta duk yana tsiyaya kaman daga sama taji sassanyar muryanshi yace “stop!” Dasauri tadago manyan fararen idanunta ta kalleshi, hada ido tasakeyi dashi for the second time da sauri ta dauke kai aranta tace “sai shegen kallon mata mtsww” fitowa daga dakin yayi ahankali, cikeda tsantsan kulawa yace “step aside” dasauri ta matsa gefe ga mamakinta sai kawai taga ya tsugunna yadauki bucket na mop din ya matsar gefe da vacuum cleaner, yashiga nannade carpet din na tsakiyan office din yadaga yadauka yawuce wajen kofa yabude yafitar dashi ya ijiye bakin kofan nan yashigo yasameta tana kokari fara mopping wajen cikin kwantacciyan murya yace “go and change” dan kallon daga kasan riganta har zuwa crocs na kafanta tayi  dake tsiyaya tace “karka damu I can do it banda wani uniform, zai bushe ai” yanda take kallon jikinta tana maganan yake kallo with her voice dake piercing kunnuwa sabida dadinsu, calmly yace “go take them off kisa kayan gida” kawai dan tasan office din mai hotel dinnan ne, sannan shita gani cikin offive din so dole tai assuming shine mai hotel din banda haka data gayamai me ruwanshi da yanda zatai aikinta yabarta tayi abinta tagama mana ha’a, sai gwadamata yanda zatayi yake, sai kawai tawuce kofa batare datace komiba tana zare handglove din, tabude kofa tafita yabita da kallo kafin kawai yazaga yazauna kan kujeranshi na office yayi shiru.

Changing room dinsu tawuce ta chanza kayan tasaka doguwan rigan atampanta brown ne da milk just straight gown babu wani ado ajiki, dan kwalin kayan ta daura aka sannan ta zari gyalenta brown ta yafa daya kara haskata hasken fatanta yayi bau aciki, ta kwashi kayan bayinsu na staff ta shiga ta dauraye kayan ta wanke cinyanta da kafanta da takalmin tama wanke fuskanta kawai gaba daya hakan yasa tai wani haske mai kyau dinnan na bayan ka wanke fuska, tawuce baya ta shanya kayan sannan tafito tana tafiya da sauri sauri sabida tasamu tai sauran ayyukanta tabar office dinshi, tashiga elevator zuwa 5th floor tawuce office din kofan office din ta bude ahankali tashigo tunda ta bude office din ya kafamata ido, the first time daya ganta uniform ne jikinta, yauma haka yanzu ne yafara ganinta da kayan gida, kasa dauke idanunshi yayi akanta, ta taho direct cikin office din batare data kalli wajen dayake bama, zubamata idanu yayi yana kara tantancewa itace dai wannan mara kunyan ta airport, bai cika manta face ba idan yasan mutum, hade fuska tayi batacemai komiba dan jikinta yabata kallonta ake, tadauki moping stick din tafara moping wajen ahankali tana gamawa tadan juyo ta kalleshi karaf suka dake hada ido dauke kai tayi tace “zan iya shiga dakin na gyara”? “Yes” ya amsa calmly hakan yasa kwai ta shiga ta sharo tai arranging bed din dataga ba’a gyare ba, ta wanke bathroom din, kusan 5min tayi sannan tafito tawuce bayin nan office ta gyara shi in 3min sannan tafito tai arranging abubuwan datai amfani dasu tafita dasu waje sannan tadawo tazo gaban table dinshi tasa hannunta tana kwasan wayanta na wajen yanabin white long fingers dinta da kallo that looks so feminine, ahankali yace “wat is your name?” Batare data kalleshi ba tace “Rashida Almustapha” tana maganan tajuya dasauri zata wuce kaman daga sama yace “is your back hurting you naga kin fadi tabaya”? “No it’s not” tabashi amsa atakaice tacigaba da tafiya da sauri bataso yayi wani maganan kuma, hartakai kofa tasa hannu zata bude yace “Rasheedahhh!” Wlh batasan meya faru ba hakanan gabanta yafadi chak ta tsaya takasa motsi sabida yanda yakira sunanta, kawai she felt something strange in her dayasa dasauri tajuyo ta kalleshi sake hada ido tayi dashi saikuma ta dauke kai tace “na’am” kusan 30secs yayi shiru saichan ahankali yace “Thank You” Da sauri ta kalleshi zatace thank you for wat saikuma ta tuna maybe na gyaran ne hakan yasa ta gyadamai kai kawai tama kasa magana sabida yanda heart nata yafara racing tajuya tafito dasauri ta kwashi komi tawuce kasa ta maida komi store tawuce taje dakunan dazata chanza duvet nasu takai washing machine takai sannan tahau gyara Allah yasota bata hadu da Madam ba balle ta tambayeta ya akayi tasa kayan gida ba.


Wuraren 6 tafito daga hotel din sai fama take da wayanta dayaki kunnuwa sai cire battery tana maidawa take sabida ya kunnu yaki kunnuwa, ga jakanta goye abayanta. “Hi Rashy” Aisha receptionist dake night zuwanta kenan tai waving nata tana murmushi awkwardly tadaga hannunta saikuma ta maida ta gyada mata kai kawai tawuce tafito waje tana hure huren waya, Munir da Riyad na tsaye awaje wannan karan ya chanza kaya zuwa jumper na milk yadi suna magan kaman daga sama ya hangota tafito tana hura wayanta, yanda hankalinshi da attention nashi yatafi wajenta saida Munir yajuya dasauri dan yaga meyake kallo haka ganin wacce yake kallo wacce kallo daya yamata she looks like worker nasu not guest yasa yace “who is she?” Batare daya dauke kanshi daga kallonta ba yace “my savior” dasauri Munir yadauke kanshi daga kallonta ya kalleshi dasauri yace “kaman ya your savior?” Yana kallonta yace “the girl that saved me from those goons a airport” dasauri Munir yajuya ya kalleta yace “wow the clearner damuka dade muna nema wat a small world ashe anan hotel namu take aiki, but did you tell her”? Girgixamai kai yayi daidai tasha kwanan layin yadauke kanshi yace “No bangayamata” Munir yace “why?” mota yashiga yace “bata ganeni ba” tada motan Munir yayi yace “ai da saika gayamata, How will you reward her yanzu?” Kai tsaye yace “I will ask her kome takeso arayuwa i will grant her any wish take da shi she’s part of the reason I’m alive today” murmushi Munir yayi yace “wat got you so angry today?” Yatsine fuska yayi yace “I don’t wanna talk about it” ahankali Munir yace “to mutafi gida? Mom tasa an sanar bakada lafiya just to manage situation din harda kiran Dr, tace na tabbatar mun dawo gida tare” hannunshi yasa yasauke glass na window ya lumshe idanu bai sake cewa komi ba, ganin baison magana yasa yace “azumi saura 7days fa bakai approving fund na kayan abincin daza’a rabama al umma da ma’aikatan ka ba” dan ijiyan zuciya yayi yace “i forgot bani file din da pen lemme sign” ahankali Munir yace “bari mukai i will 

💫 SANYI DA ZAFI 💫

   ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 1️⃣3️⃣


Gida tashiga around magrib agurguje tai alwala tashigo ciki Mama nakan dadduma hakan yasa ta tsaya kusada ita ta kabbatar sallan.


Tana idarwa cikeda damuwa tace “Mama ruwa yashiga wayana taki aiki wlh” tai maganan tana jawo jakanta taciro wayan cikeda damuwa itama Mama tace “garin yaya meya sameta?” Cikin damuwa tana kara huhhure wayan tace “faduwa nayi ruwa ya kwaromin shine ruwan yataba har wayan” dasauri Mama tasa hannu ta karbi wayan itama tana huhhura duk wani huji na wayan ta maida battery din kozata kunnu amman bata kunnu ba hakan yasa ta tashi tawuce chan wajen yan kayan abincinsu tabude ledan shinkafa tasa wayan ta zuba shinkafa akai tace “bari mugani kozata kunnu idan bata kunnu ba saina tattara kudin dake wajena kije ki sayo wata wayan dashi, kina bukatan waya kodan school, Allah kiyaye bakiji ciwo bako”? Gyadama Mama kai tayi tace “banji ciwo ba” Mama tace “to ai mun gode Allah tashi kiyo wanka kici abinci” dasauri tace “Mama girki kikayi”? Gyadamata kai tayi tace “eh nayi shinkafa da wake da mai sa yaji” murmushi tayi tace “Mama banace ki dena girki ba” ture mata hanci Mama tayi tace “to banji maganan ki ba Anty Rashida” kwashewa da dariya tayi hakan bakaramin dadi yama Mama ba ganinta duk cikin damuwa sabida wayan tasan lissafi take ta yanda zata taba kudin saving dinsu tasai waya dashi kafin takara samin wani kudin fa, rashin lafiyan Mama fa, abinci fa, kudin wuta fa, tasan duk abinda take tunani kenan ganin tayi dariya yasa hankali ta ya kwanta, cikin shagwaba tace “kai Mama nine Anty Rashida” Mama ta kama haba tace “yooo ai hakane, Mama karki kaza, karki kaza, kullum command kike bani yarnan kinga ai kinzama Anty Rashidan” sake bushewa da dariya tayi kawai saita kwanto jikin Mama tace “Mama stoppp wlh ni ba Anty Rashida bane, Mama ina hanaki ne fa sabida karki fadi, kinga kinada yawan ganin jiri, kınada migraine kuma, Mama I have to take care of you gwara namiki komi ko ruwan dazakisha na ijiye kusa dake sabida karki wahala wajen daukowa” tabe baki Mama tayi tadagata daga jikinta tace “jeki wanka kizo kici abinci” tashi tayi ba musu ta rage kayan jikinta tadaura zani ta kwashe kayan da lab coat da kayan Mama data cire yau dasafe tafito saida ta fara wankesu tsaf ta shanya sannan tawuce bayi tai wanka tadawo Mama tabata abincin ci tayi bawani sosai ba batawani cin abinci abin yabi jikinta sannan takai kwanon waje ta kuskure baki ta dawo tahau salla kusa da Mama tana idarwa ta kwanta awajen ko 2min ba’ayiba tafara minshari Mama tai shiru tana kallonta sai kawai tasa hannu tadauki feet dinta ta daura kan cinyanta dudda uban tafiya akasa datakeyi bata da kaushi kafanta still looks very fine ga nails dinta farare kal masu kyau, ahankali take massaging kafafun ayanda ta gyara kwanciya kasan tanajin dadin tausan Mama is just looking at her babu salloli biyar dazatayi arana da zatakai goshinta kasa dabazatama Rashida addu’a ba, banda kiyamun Layli datakeyi kullum, kullum addu’an ta shine Allah yakawo ma diyarta karshen wahalan nan Rashida ita ke ciyar da ita, itace cinta shanta suturanta magungunanta da komi na rayuwan su Rashida ke nema,  babu yanda zatayi ne dan batama da karfin aikin ne da itace zata fita ta nemawa diyarta abinci da komi ba diyarta tayi ba, kullum addu’an ta is Allah ya tsare yarinyar ya tsare imaninta kar wata rana tagaji da aikin wahalan nan tace zata shiga duniya tabi maza dan shine hanya mafi sauki da akebi asami kudi, addu’anta koda yaushe shine Allah yabata ikon kammala wannan karatun likitan, kowani shekara da hayya hayya take tara kudin school fees nata na last year bai musu wani wahala ba sabida tasami aikin hotel din nan ana biyan ta dubu 50k duk wata a nan ta tattara tabiya, fatanta shine Allah sa wannan shekaran na biyar kar kudin makarantan yayi yawa dubada yanda aka kakkara kudin makarantu, hawaye ta share ahankali daya zubo mata bata taba sanin dan Uwanta na jini zai iya juya mata bayaba sabida wannan cutan dudda da ranshi da lafiyanshi, bata da kowa sai Rashida, yau shekaru ashirin da uku kenan tana wannan wahalan tun Rashida na cikinta, ta haifo yarinya cikin wahala ta tashi cikin wahala sannan itama tana rayuwan wahala, batabama yarta komiba sai wahala, babu wanda ya yarda ya auri Rashida, ga yanda yar karaman yarinya ke aiki kaman namiji wata kalan uwace ita, hawaye ne suka kara zubo mata sai kawai ta jinginar da kanyon a bango takalli sama murya chan kasa that is very weak tace “Ya Allah idan mutuwata shine mafi alkhairi agareni dakuma y’ata, idan mutuwata zai cireta daga cikin wahalan nan datake ciki Allah ka kasheni, ka aurar da Rashida gidan dazata huta,  karufama Rashida asiri, ka lullubeta cikin nimarka Ya Allah.

Tadade ahaka yawanci tana boyema Rashida damuwanta da dama sabida kar yarinyar takasa karatu idan kanaso kaga Rashida ta birkice tarasa sukuni to Mama tace kaza namata ciwo tuni yarinyar zata rude, damuwa, tunani ga constant ciwon kai koda yaushe shiyafi damunta, saisa kullum tane asibiti BP ta is high, magungunan BP nema ke cinye musu kudi cus maganin HIV free ake bata a clinic dinsu.


Ganin yanda bacci ya shigeta yasa bata tadataba tabarta tai baccin anan kan dadduma.


Wuraren 5 Mama ta tadata da kyar ta tashi wanda hakan daman is daily battle nasu, gyaran gidan tayı tasa takai Mama tai wanka tai salla tazo ta dumama shinkafa da waken sannan tama Mama tuwo sunada miya daman kafin ta shirya cikin bakin abaya da stones nashi yagama fita tass but dudda haka ya mugun mata kyau abunka da fara tazo taje wajen wayanta taciro daga shinkafan tasa battery ta kunna amman still yaki kawowa Mama tace “bai kawo ba?” Gyadama Mama Kai tayi ahankali, dasauri Mama tazo karban wayan tayi tace “kodai ba chaji ne” tawuce wajen chazanta dake bango ta makala kusan 3min bai dauka ba, ahankali Mama ta tashi tace “bari nabaki dubu talatin din nan saiki sayo wata wayan kawai” dasauri tace “a’a Mama ki adana talatin din nan, bari zan kaita wajen yan waya a gyaramin zasu iya gyaramin” badan Mama taso ba dan wayan tariga tagama tsufa dukta farfashe tace “to shikenan bari na baki kudin gyaran” sip tabude taciro wani leda ta kirgo 5k tabata karba tayi sannan tayafa gyalenta tace “bye Mama” har zaure Mama tarakota tace “adawo lpy” dayake 9 ake fara clinic dinsu hakan yasa taje shagon Maman kuwa tayi aiki ta karbi 2k dinta sannan tawuce shan wajen gyara takai wayan ganin zai dauki lokaci tace “zata dawo da yamma” tashiga keke sai hospital nasu.


she’s not really doing much a consulting room take zama attached to consultant din da aka assigning nata to him yana duba yara marasa lafiya yana tambayanta me aganinta take tunanin is diagnosis din tafadi, kokuma yace wani investigation yakamata ayima yaron tafado sunayen series of test da za’ayi ganin how brilliant d girl is tsohon likitan yace “i will comfortably leave the office for you tommorow” gyadamai kai tayi dan she hardly smile outside, haka dai tagama by 1  tawuce mosque tai salla ta linke labcoat tasa a bag sannan tafito tashiga keke sai hotel.



Yau tadanyi latti sabida traffic sai around 2:30 tashigo hotel din ko kallon mutanen dake reception da lobby gabaki daya batayi ba da sauri sauri tawuce changing room nasu kofa tabude ahankali, ma’aikatan su tagani gudu uku a lobby suna chanza kaya da kallo suka bita batace musu kala ba tawuce locker dinta tasa password dinta tabude, daya daga cikinsu ne taja tsaki tace “mutum sai fadin dai, nagadai da mutum dan wani ne dabaizo hotel neman aikin shara da wanke bayi ba, tundadai duk ansan juna menene na jijji dakai kaman diyar wasu” ? Sauran biyun ne suka kwashe da dariya daya tace “dadine dake Hussy baki hadiye abu aciki” parking gashinta tashiga yi da ribbon tace “eh mana kullum fuskan mutum amurtuke ana fadin rai ana daga shoulder kaman yar shugaban kasa amman shine akazo aikin wanke bayi a hotel” wani irin buga marfin locker Rashida tayi saida yayi kara pammm!Tajuyo tai facing Hussy direct cikin zafin rai tace “dani kike maganganun nan?” Wani banzan shakiyin kallo Hussy tamata dan tadade tanajin haushin Rashida wai ace ma’aikata nawa a hotel din nan yarinya bata kula kowa, kuma kai kasauke kanka ka kulata taki kulaka back, bama wannan yafi bata mata rai ba yanda take nuna bamatasan anyi hallita irinsu a wajen ba ko ka kulata ita bazata kulakaba sai bakin taurin kai, jibidai yanzu datazo tasamesu ko Hi bazata iya gayamusu ba? Amman basu isheta kallo ba, cikeda tsana tace “naga dai ban kira suna ba, amman duk wanda ya tsargu dashi nake” wani irin kallo Rashida tamata kaman taci ubanta saikuma ta tuna nan wajen aikin tane, da kudin aikin wajen nan zata biya school fees and other things bari kawai ta barta today is her lucky day, sai kawai tajuya tasa hannu zata dauki uniform nata batare data kara magana ba, cikeda neman fada Hussy tai wani shewa tace “jakan ta tsorata” juyowa Rashida tayi da mugun zafin rai batai wata wata ba ta fizgo gaban rigan Hussy ta kifa mata mari a fuska ihu jikake tasss! Hussy tayi ihu ta chakume gaban rigan Rashida tace ni kika mara”?  Sai dambe, dukanta Rashida take bana wasaba har gyalenta na fadi kasa bakin gashinta datai parking donut mai bala’in kyau ya bayyana, sauran yammatan biyu na kallo sunajin dadi ganin suna dakan juna dudda Rashida nacin uban Hussy amman kallon fada da dadi yake sukaki rabasu, ganin jini Rashida tafasa bakin Hussy yasa daya cikinsu ta tsorata tace “baruwana kar ayi kisan kai agabana” dasauri tabude kofa tafita da gudu dayan ma tabiyota hango Madam sukayi a lobby tana magana da receptionist kafin sukai wajen ma sukai ihu. “Madam ana fada” daidai lokacin Munir da Riyad na shigowa yana shaye da brown jumper yasa brown shade a idanunshi na CK dayamai kyau sosai, arude dayan tace “Ma come oo harda blood everywhere!” ganin Riyad yasa Madam tace “Sir welcome wai ana fada I don’t even know with who lemme handle it” tawuce jin yasa Munir yace “let’s intervene” Munir yayi gaba Riyad yabiyosu abaya yana tafiya one one a kasaitance, da gudu Madam ta shiga dakin tai ihu “what is this”? Ganin blood har wuyan Hussy, Rashida bama tasan an shigo bama Munir yashigo dakin daidai Riyad na isowa chak ya tsaya wajen kofan batare daya shigo ciki ba yana kallon su, jan Rashida Madam ta shigayi da karfi gaske ganin yanda take dukan Hussy, sauran yan aikin suna banbare hannunta daga jikin Hussy sunajan Hussy da bakinta yayi jina jina da jini harda hanci baya suka kwasheta da kyar daga hannun Rashida, Madam data rike Rashida cikin tsananin bacin rai tace “fighting awajen aiki are you too Mad? Rashida wat is this why did you beat her up like this?” Itafa idan tana fushi bata gane kowa, kabar da hannun Madam tayi daga jikinta a haukace kaman ba Rashida ba cus ranta yabaci tace “dalla sakeni kekuma Malama” tajuya zata closet nata cikeda taurin kai duka ma’aikatan har Munir saida yakalli Rashida yasake kara kallonta jin abinda ta gayama Madam, Hussy dake haki an riketa tace “Ma kinga halinta ko saisa all worker ke cemata psycho, kolomental ce wlh, mahaukaciya ce very weird girl, shegiya yar shaye shaye, an gayamiki bamusan asalinki bane, uwarta nada HIV!” Chak Rashida dake tafiya ta tsaya kaman kankara, ihu Hussy tayi ganin ta tsaya chak da tafiyan datakeyi that means maganan ya shigeta tace “ai duk munsan sirrin ta Ma, harnan akazo tundaga layinsu aka gayamana we should be careful with her tanada HIV Mamanta ma nadashi, bamu gayamiki ba Madam sabida karki koreta cus munsan she needs this job for her virus drugs da Mamanta, amman shine zata kama dukana ba ban mata komiba bayan tanada wacce tafi chanchanta adaka islamically agida, diyar fasika kawai!” Wani irin juyowa da Rashida tayi zaka dauka zakanya ce ta taho da gudu tareta Madam tayi tace “where do you think you’re going” wani irin hankada Madam Rashida tayi saida Munir yatare Madan da sauri dan inda tafadi wlh saita karye, Hussy na ganin haka ta wuce da gudu tabi gefen Riyad ta gudu tafice da gudu Rashida ta taho itama tsabagen fushi ko ganin gabanta batayi ahankali Riyad yadaga kafanshi yashigo ya tare kofan yayi blocking nata, hakan yasa ta dago jajayen idanunta takalleshi adake cikin tsananin fushi da zuciya tace “ka tashin mini daga hanya” Madam da Munir ya daga kyar tace “it seems da gaske yarinyar nan is mad, call security namu and call the police” yana kallonta ta glass batare daya dauke idanunshi daga kallonta ba yace “don’t call anybody” cikin kumfan zuciya kaman zata fashe tai wani irin ihu tace “nace ka tashinmini daga hanya” strictly yace “you’re not going anywhere!” Wlh ayanda zuciya ke daukanta kaman ta dagashi ta yar takeji kawai tasan batada karfin ne, yanda hannayenta ke rawa da jikinta yasa kawai ta juya fuuuu tawuce dan bence din dake wajen ta zauna tai folding hands dinta akirji duk yan dakin kallonta suke she’s shaking, sai alokacin yakalli Munir yace “get first aid box go and attend to that girl, yakalli Madam da sauran yar aikin dake kallon Rashida da mamaki kaman yau suka fara ganinta yace “ku wuce kutafi” cikeda mamaki Madam tana kallonta tace “this is your last day here” duk wucewa sukayi suka fita yarage Riyad kadai dake tsaye awajen kofan dan kwalinta dake kasan dakin ya kalla ahankali ya shigo ya duka gently yadauka dusting nashi yayi sannan yataho inda take zaune kanta akasa tayi folding hands a kirji ahankali ya yafa gyalen akanta.


Dago kanta tayi tazubamai jajayen rinannun idanunta yanda yara masu taurin kan nan sukeyi tace “ina ruwanka dani? Wayace katabamin gyale na? Wat is your business with me? Nabar aikin naku dagayau nima, bazan kara aiki inda wata ta kira Mamana…….” Saita kasa karasa maganan sabida yanda abin ya tsayamata awuya saikawai tajuya mai baya da sauri takai hannunta ta sharce hawayen daya soma zubomata, data sharce da wani yasake zubowa sunki tsayawa yakai almost 1min yana kallonta sannan yajuya ahankali yafice tareda maida kofan yarufe kaman jira take fashewa tayi da kuka haryafara tafiya yajuyo sautin kukanta chak ya tsaya har shesheka takeyi yakai kusan 1min ahaka sannan yabar wajen, kusan 5min tayi tana kuka sannan ta goge fuskanta tass ta tashi tawuce drawer ta ta shiga kwashe yan small small tarakacen datake dashi awajen uniform nasu tabar musu sannan ta goya jakan abaya ta tsaya takara goge fuskanta tass bazaka gane tai kuka ba unless u look into her eyes tafito sai kallonta ake a reception amman ko kallonsu batayiba ta wuce tafita ta tafiyanta gida.



💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣5️⃣


Da gangan Munir yabar wayanshi awajen yadauke car key yafice, tashi Riyad yayi yawuce yasaka pajamas yadawo ya kishingida tareda lumshe idanu, wayan Muneer ne yahau ringing hakan yasa yabude idanu kadan yakalli screen din ganin Mom R yasa yayi shiru yana kallo wayan na dab da katse wa yasa hannu ya dauka yakai kunnenshi yaki magana daga ta dayan bangaren Mom tace “Son” ahankali yace “Mom ina yini” ijiyan zuciya Mom ta sauke she really miss him chan tace “sabida I questioned you zakai zuciya kabar gidan? Riyad when did you grow dahar zakabar min gida sabida namaka fada? Riyad I still see you as my little baby boy da I have to guide every step of the way, your are my purpose, you are the reason I become a Mom, did you really leave house yau kwana biyu sabida na tambayeka game da abu Riyad”? Mom tai maganan muryanta na tsinkewa kaman zatai kuka, Riyad yayi shiru Mom abin ya matukar bata mata rai tace “ko kakai 100yrs of being a man I will always see you as my little child, I will always tell you do this and that, I agree raina abace yake ranan datamin maganan dan kunnen nan and I wasn’t thinking clearly, but still inada right nai fada, Babanka yayi aure aure but tell me menene fa’idan hakan yanzu? Kullum gidanshi cikin rikici makirci da fada ake, kalli Baffan ka tunda yama Amaryanshi koran kare bai sake marmarin kara aure ba sabida yaga implications din gashinan shida Jummai are living peacefully and happily, wat I’m saying is mata dayawa masifa ne, bazan taba bari ka auro wata wacce ban sani ba ko ban aminta da ita kaman Haleematu ba kafin azo arabani da d’ana that is the reason namaka fada and asked you ranan, and gashi nakosa naga Haleematu tai ciki amman shiru, dakaina nakai yarinyar taga gynecologist ance she’s fine kaine dai baka cika nemanta ba, kuma ita Haleematun tagayamin yawanci koka nemeta ba rannan ovulation dinta bane saisa har yanzu batai ciki ba, mesa kakemin haka Riyad? Kai ba dan gidan nan bane bakaga yanda matan yayyinka ke haihuwa shekara shekara ba? Duk shirin da Babanku yakema yaranshi maza tun suna yara kaima an maka amman narasa mesa kakeda sanyi a harkan raya sunna” da sauri Riyad yacire wayan daga kunnenshi yanajin wani irin kunya da nauyi idan Mom namai irin maganganun nan, danna wayan kawai yayi a speaker ya ijiye agefense yana jinta. “Kap yaran family nan wlh basama matansu wasa kai har rama matan suke sabida yanda yaran Mai Martaba Baba Ali fire for fire ne akan matansu” wannan karan Riyad baisan sanda ya dafe kanshi yace “Mom can we change the topic please” cikeda bacin rai Mom tace “Kaci gidanku da change of topic Riyad, nabaka gobe come back home and continue kaga yanzu kayi skipping 2days babu abinda ya shiga tsakaninka da Haleema, kubani grandson nagaya maka saida safe” ta kashe wayan, ijiyan zuciya ya sauke yakoma ya kwanta tareda lumshe idanunshi.


Har Muneer yadawo a kwance yasameshi yace “ina tuki natuna wani abu daya faru dazu yanda dayar ma’aikaciyar yarinyar tace ma Masifaffiyar mamanta nada HIV” dagokai Riyad yayi yamai wani shegen kallo yace “and so”? Dan sosa kai Muneer yayi yace “bakomi kawai natuna abin ne” juyar da kansa yayi sai chan yace “HIV is just like any other ciwo, having it doesn’t mean you are bad ko karshenka yazo, stop with the stigmatization” dasauri Muneer yace “haba noo bana stigmatization sai kace Baffan mu da akace ya kori matarshi mai ciki da akace tanada shi, ko tana ina oho”? Tashi Riyad yayi yace “let’s eat” abinci suka shiga ci he ate alot kam yana gamawa yadauki laptop yafara aiki daman yunwa yahanashi yi.

Cikin bacci taji ana tabamata kai sabida tsabagen yanda bacci yau bai shigeta ba taba cikin tashin hankali firgigit ta farka.

Cikin dare sau biyu cikin dare Dr da Nurses sukazo duba Mama duk tana zaune bata runtsa ba harsaida Dr yace “kihau gado ki kwanta kusada ita mana ko ga babban sofa kihau” girgizamai kai tayi tana zaune kan yar kujeran dake gaban gadon, cikin sanyin murya tace “zan zauna anan” gyadamata kan Dr yayi yawuce harzai fita tace “ina bill dinmu?” Dan juyowa yayi yace “your bill has been cleared receipt duk suna cikin ledan drip dinta” yana maganan yabude kofa yafice from yanayin mutanen kawai yasan Mai Martaba taimakonsu yake.

Tashi tayi dasauri tawuce wajen ledan drip din da duk za’a sama Mama tabude taciro takardun receipt wanda na farkon na meal tagani 2 person breakfast 2person lunch dinner da snacks na 3days taga 270k, abincinta itada Mama kullum 30k for 3days 270k zaro idanu tayi takai hannunta tana dafa kirjinta, tadauki dayan receipt din single room dasuke dakeda gado sofa fridge da bayi is 25k per day kwana uku 75000, sai magungunan Mama gabaki daya da drip da allurai taga 497,250 wannan karan saida ta fada kujera ta zauna, duka kudin 842,250naira, kusan miliyan daya ta ina zata fara neman kudaded nan? No gobe zatasa a sallamesu, but ko an sallamesu sunyi kwana daya which is 25k daki, sai kudin magunguna 497,250 dole saita biya ta ina zata fara, hawaye taji sun zubomata sai kawai ta gogesu da sauri tahada duka receipt din ta linke tasa a jakanta tadauko kudinsu ta kara kirgawa duka savings dinsu kenan 150k tadade ahaka saita maida jaka ta kama hannun Mama ta rike har aka kira asubahi idanunta biyu tashi tayi tawuce bayi tayo alwala tafito tabude jaka ta ciro dadduma anyi alamun gabas aşaman dakin hakan yasa ta kabbarta salla ta idar tai azkar tana zaune kan dadduma Dr yakara shigowa dasauri ta tashi ta linke dadduma Dr yaduba Mama yajuyo yakalli Rashida datai zuru zuru yace “Alhamdulillah BP yasoma sauka, maganin zai saketa soon zata farka bada jimawa ba” gyadamai kai tayi, murmushi Dr yayi yace “Maman ki will be fine kinji” gyadamai kai tayi ahankali tace “thank you” wucewa yayi  yafita


Zama tayi har bakwai da rabi kallon Mama take sai alokacin tafara hamma sai kawai ta kifa kanta anan bakin gado ko 1min batayiba bacci yayi awon gaba da ita.


Wajajen 10 na safiya Mama ke bude idanunta ahankali bakinta dauke da kiran sunan Allah, saman dakin ta kalla sannan ta sauko da idanuwanta ta kalli drip da ake samata kafin ta sauke idanun kan Rashida dake zaune kan kujera ta kwantar da kanta bakin gadon kusada hannunta tana bacci, ijiyan zuciya ta sauke ahankali komi daya faru jiya na dawo mata, ta tuna yanda tagama magana da bawan Allah nan mai kirki tafara tafiya tafadi tabbas taga bawan Allahn hankali tashe yazo yana kiranta Mama Mama dishi dishi take gani bama ta iya magana dağa baya kuma taga shida security sun kaita mota daganan kuma bata sake sannin inda kanta yake ba, ahankali cikeda karfin hali irin nata ta cire drip din ta sauka tana tafiya da kyar tawuce kofan data gani ta bude ta shiga bayi ta dauro Alwala tafito ta sanya hijabi taje ta sauna kan dadduman data gani tai salla dağa zaunen datake tun magrib da isha’i tahada dana safiya sannan ta dawo ta lallabo ta zauna agadon jin jiri na neman yakara dibanta motsin da gadon yayi yasa firgigit Rashida ta bude idanunta ganin Mama zaune da hijab dinta yasa da sauri ta tashi tace “Mama kincire drip din” takama hannun Mama dasauri tashiga maida mata drip din tace “mesa baki tasheni ba har yanzu BP ki is high Mama, you can fall at any moment”


Yanda take maganan Mama take kallo kaman ba Rashida ba duk ta tsure harta rame idanunta sun fada ciki sosai, hannunta Mama takai ahankali ta kama habarta hakan yasa gently tadago fuskanta ta kalli Mama duk yanda taso taboye damuwanta takasa da duka zuciyanta tafashe da kuka sosai atsaye hawayen na sauka kan hannun Mama, cikin kuka tace “Mama dan Allah kiyakuri I keep causing you pain koda yaushe, Mama I know how sick you are but kullum kara miki damuwa nake Mama, akan mene bazanyi hakuri na dinga danne komi ba, komine sainayi fada akai, is because of me BP ki yatashi, Mama kiyakuri kiyafemin dan Allah” har sheshekan kuka take, zuwanshi kenan yakai hannu kenan zai knocking kofan yaji sautin kuka da maganan datake hakan yasa ya tsaya chak.


Ahankali Mama ta girgiza mata kai tace “shiiiiii don’t ever blame kanki for ciwo ba cus ba laifinki bane ko daya, stop crying to bagani nan naji sauki ba, gashi nan duk kin bata fuskanki jibi yanda idanuwanki sukai ja sabida kuka bari kiga” Mama sai kawai takama bakin hijabinta takai kan fuskanta tashiga sharemata ta shafa kumatunta tasake murmushi tace “I have the most beautiful yarinya wlh idan tai kuka sainaga idanun nata ma sunfi kyau” dan murmushi kadan tayi wasu hawayen na taruwa, Mama tace “ai kaga abin karki kukan ya isa nace, yanzu dai tafi gida ki shirya kitafi school idan zaki dawo saiki biya wajen gyaran wayanki” baki Rashida tabude zatai magana akai knocking kofar just once kallon kofan sukayi dukansu, Mama tace “jeki bude kofan muga ko likita ne natafi gida” but Dr direct yake bude kofan tai maganan aranta tasa hannu ta goge fuskanta tass sannan tawuce wajen kofan tasa hannu ta bude ido da ido tayi da Riyad dake sanye cikin wata shadda yau sky blue jumper kanshi ba hula tashin Kansa ya kwanta sidik tunda take bata tabajin kamshin turare mai dadin nashi ba, da sauri ta dauke kanta dağa kallonshi Mama hangoshi yasa tace “bismillah bawan Allah” anatse akamilance yashigo har gaban gadon yaje yaduka dasauri Mama tace “tashi tashi haba zauna ga waje” tabashi kujera ijiye ledan dake hannunshi yayına gefen gadon yace “ya karfin jiki Mama ina kwana” murmushi Mama tayi tace “jiki Alhamdulillah naji sauki, nagode da kulawa ka kawoni asibiti banda bakin maka godiya Allah maka Albarka” takalli Rashida dake tsaye wajen kofan tai folding hannu tace “baki iya gaisuwa bane ko akwai abu abakinki ne” dan juyawa tayi da kyar tace “ina kwana” baki Mama tasaki tana kallonta ganin baka yasa da kyar tace “mungode” dasauri Mama takalleshi tace “Ya sunanka ne?” Ahankali yace “Riyad sunana” daidai lokacin akai knocking tareda shigowa dakin wata ce tana sanye da uniform na ma’aikata tace “good morning Ma dazu nazo nakawo muku breakfast naga kuna bacci natafi dashi dan karyayi sanyi yanzu zanje nakawo muku” tawuce tafita daga wajen kofan akunbure Rashida tace “Mama kicemai yasa a sallamemu mutafi asibitin mu” dan juyowa yayi daga inda


Yake yazuba mata ido dauke kai tayi strictly yace “Dr yace 3days Mama zatayi anan and hakan ne zai faru” dasauri Mama tace “Riyad kaga ai dawainiyan zaiyi yawa ta ina zamu sami kudin biyanka? Dan Allah kasa asallamemu naje general dana saba zuwa kaji, Allah yamaka Albarka Allah yakara daukaka” daidai lokacin aka kawo abincin breakfast ne omlete da bread toast sausage tea dakuma bowl na fruits yarinyar ta saukar dama da Mama wajen ijiye abinci kan gado sannan takai dayan abincin kan table sannan takalli Riyad tace “Sir do you need anything”? “No thanks” yafadi atakaice, Mama ta kalli Rashida dake tsaye kikam har lokacin awajen kaman mai gadi tace “zokiyi kari kitafi school don’t even tell me bazaki ba” kaman zatai kuka tace “Mama ni banso naje wazai zauna dake natafi” “I will be here with Mama” dağa Mama har Rashida dukansu kallon Riyad sukayi, hakanan Mama kawai taji tanason natsuwan yaron, abin yana mata ma kaman tasanshi batason tai rubbing in his face hakan yasa tai murmushi tace “to kinji Riyad zai zauna yatayani hira zoki ci abinci kitafi school kinyi katti already banson kina fashi a school kije gida ki shirya kitafi” bataso taje school ba but abinda yafima damunta is wannan mutumin dayakeyi kaman irin ya sansu din nan ko su yan uwa ne saiwani shishigi yaje musu mutumin da shekaran jiya ta sanshi, batason tai gardama sabida Mama batada lafiya hakan yasa ta taho wajen gadon gefen Riyad ta ballama jakan abubuwan dayakawo harara karaf akan idanunshi sannan tadauki jakanta dake wajen ta taso tajuyo hada ido sukayi tadauke kanta tajuya Mama tace “abincin fa” akufule tace “ni bazan ci ba” tawuce wajen wardrobe na dakin taciro kayan jakan an Mama daya kawo ta maidasu ciki kudin taboye karkashin kayan sannan tawuce tai hanyar kofa  tace “natafi” tabude kofan tafice ijiyan zuciya Mama tasauke tasa cokali ta a abinci tace “I have a very stubborn yarinya Riyad” dan murmushi kadan Riyad yayi baice komiba, Mama tai shiru kaman mai tunani tace “she’s all abinda na mallaka aduniyan nan” saita dauki fruits takai bakinta tafara taunawa sai kawai tafashe da kuka as if she’s holding on to something ahankali Riyad yace “Mama stop crying she will stop being stubborn soon duk yarinta ne, zata dena nan gaba, stop crying kinji Mama is not good for you zai hanaki warkewa” ijiye spoon din tayi takai bakin hijabinta ta goge fuskanta tace “ciwo na bana warkewa bane, HIV gareni Riyad” tadanyi murmushi tace “I don’t even know why nake fadamaka nasan kariga kasani Rashida tacemin agabanku abokiyar aikinta tace inada shi” tai shiru sai kuma ta zufar da iska dağa bakinta tace “I’ve caused Rashida pain tun tana ciki na, yarinyar nan tayi girma cikin bullying din society yar fasika yar mazinaciya yar me HIV so sometimes I don’t even blame masifa da fadan da stubbornness nata society shaped her to be that way dole tai finding means na yanda zatai surviving.


Mama takara shiru saikuma tasa hannu tadauki bowl din fruit din tarike tadauki spoon tadau lemu zatakai baki is as if akwai so many things acikin zuciyanta dake damunta tace “wlh, wlh tunda nake arayuwana bantaba fasikanci ba, inada cikin 6months ina laulayi sosai aka kaini hospital akamin gwaje gwaje the next thing inada HIV, aka gwada Mijina baida shi, kishiyata ma baidashi babu wanda ya yarda da magana ta, Mijina ya koreni, yamin koran kare, nakoma garinmu dayake dagani sai yayana iyayenmu suka haifa shima ya koreni wai bazan jamai abun kunya ba yana babban mutun a kauye karnazo naraba ma kauyensu kanjamau, haka nai garari aduniya da ciki ajikina” Tasakeyin shiruuu tana kallon bowl na fruits din tace “har yau har yau bansan tayaya nakamu da HIV ba Riyad, haryau bansani ba” saikawai tafashe da kuka dayasa idanun Riyad sukai ja yasauke kanshi kasa Mama tabashi tausayi and wlh he believed her cus you can see honestly a maganan ta, her body language, maida bowl din tayi ta ijiye tace “cikin garari na haifi Rashida, komi nawa saida na saida just to sustained bata madara dan ban bata nono ba haka likitoci suka gayamin, ina zuwa clinic lokacin da karfina nafara aikace aikace ina goyata ahaka nasata school ta taso tanada ilimi  har yar baiwa ake kiranta lokacin, cikin wahala sosai Rashida ta tashi, ba gatan uba ba gatan yan uwa, just ni kadai takedashi, tun batasan menene HIV be sabida yanda jama’an unguwa ke constantly singing dinshi akanta tazo tasan menene shi, tana wajajen JSS1 karfina yasoma gasawa as small as that girl sai ita tasoma zuwa gidajen danake aikatau tanayi amadadina nina zauna agida sabida rashin lafiya tundaga lokacin kawowa yau Rashida dakake gani itace ci na, sha na, suturata, wajen zamana, magunguna na, kudin makarantan ta da komi, anywhere da zata samu aiki tayi she wants to go sabida batason taje taroki kowa yamana abu, ko an kawo mana taimako bata amsa, she’s 23 but she works like a 45yrs old man” Mama tai shiru tasa hannu ta share fuskanta chan tace “Riyad I’ve become a burden arayuwan y’ata, I’ve become a curse in her life, I believe idan na mutu she will enjoy life better….” “Mama!” Riyad yakirata da sauri, fashewa dawani irin kuka Mama tayi takalli Riyad tana bubbuga zuciyanta ta saman riga tace “I am hurt sabida I have the best daughter a duniya dabana iyama komi kawai nasata a wahala ne, I am selfish Riyad dan dana haifeta dazan iya kaita gidan marayu amman nace nizan raineta ta taso suffering, yara yammata irin ta suna gidan iyayensu akillace nawa na garari aduniya from morning to night bata airport, bata shagon abinci, bata hotel tana shara da wanke wanke da wanke bayi just to make ends meet, so I am selfish Riyad”  Mama tafara sheshekan kuka da kawai kasan matan nan ta tara abu dayawa azuciyanta ne tace “na zaman ma Rashida alakakai arayuwa, na zaman mata annoba, sabida ni kullum aiki take, kowace yar budurwa na gidan iyayenta na jin dadi iya yen na nemo abinci su bata taci ni tawa ke gararin duniya ta nemo tabani naci, I’ve burden my poor daughter, I don’t deserve to be her Mother wlh I do not!!” Tashi Riyad yayi ahankali yazauna bakin gadon dan kukan da Mama take is getting too much, calmly yace “Mama don’t say that, you are wrong Mama!” Ahankali yace “kinsan yanda yarki ke sonki kuwa?” Saikuma yasa hannu a aljihunshi ya ciro handky yamika mata yace “goge fuskanki Mama nabaki labari” da kyar Mama tasa hannu ta karba ta share fuskanta tass takalli Riyad da jajayen idanunta, dan murmushi yayi just to calm her down but jiyake kaman yamata kuka shima yace “Mama all abubuwan dakike tunani akan yarki is totally wrong cus I see complete opposite of abinda kika fada” dan shiru yayi kaman mai tunani chan yace “all I see a idanun yarki is you are her motivation, her inspiration, her strength, her confident, Mama kece dalilin dayasa yarka is strong! Fearless and resilient, bold, I witness how she fought with her soul sabida ke Mama!” Dan murmushi Mama tayi ganin haka yasa Riyad yace “Mama ke kinga yanda tayi ne ai harni namiji saida na tsorata kartazo ta hada dani” daidai lokacin Mama ta kwashe da dariya yanda yayi maganan was sooo funny, ganin tai dariya yasa cikedason kwantar mata da hankali yace “Mama karki taba tunanin ke burden ce arayuwan ta ko curse all I see is kece the whole entire reason na existence nata, Mama yarki na sonki fiyeda tunaninki and duk yaran dake son iyayenshi bata taba daukansu koya kallesu a matsayin wahala kowani abu trust me Mama” murmushi Mama tayi tana kallonshi har cikin ranta taji sanyi da maganganunshi yace “idan you want her to keep being her ki warke kiji sauki sabida hankalinta ya kwanta Mama inba hakaba rashin lafiyanki will shatter her tiny little heart I’m sure ko’ina take yanzu hankalinta rabi da kwata na kanki she might not concentrate ko a school right”? Gyadamai kai Mama tayi ahankali saikuma chan tace “nagode Riyad, you made me feel good” murmushi yamata yace “kici abincin ko zakisha yoghurt”? Gyadamai kai Mama tayi freely kaman ta sanshi da dadewa kawai saiya sauka daga gadon yabude ledan daya kawo yaciro komi yakawo ajuwa dates, ruwan Zamzam babban gora dakuma yoghurt, cup ya dauka na tea da aka kawoma Mama yaje ya zubar Mama sai binshi da kallo take ta natsu da yaron kaman tasanshi da chan, yataho da cup din ya tsiyaya mata yoghurt din aciki yabata karba tayi ahankali tace “bani dabinon” dasauri yabude daya yabata ta karba yadawo ya zauna tashiga sha tanacin dabinon wlh haka ya zauna da ita sai hira suke kaman sun san juna har Dr yashigo yadubata yadan shiga hiran shima na 5min kafin yawuce yatafi wajajen zuhur yafito yatafi masallaci ana idarwa yadawo yazauna Mama tace “bakaci komi ba” cikinshi yataba yace “kuma yunwa nakeji sosai Mama tea kawai nasha dazan fito” dasauri Mama tace “tashi kaje gida kaci abinci dan Allah” zaiyi magana aka bude kofan dakin da sallama Rashida ce tana sanye dawani material ja dogon riga ne har kasa ta yafa gyale baki kayan sun mata kyau sosai ta goya jakan school abaya da pink crocs din nan akafanta sai wayanta dake hannunta tana gumi a goshi dan da kafa tazo gashin gaban kanta duk sun kwanta, ko kadan batasan zata ganshi ba ganinshi yasa ta hade rai sai kawai ta shigo ta ijiye jakanta kan kujera tazo ta gefenshi takai hannunta da sauri ta taba goshin Mama tace “Mama ya jikin meke miki ciwo yanzu”? Dauke kanshi yayi daga kallonta Mama tace “lafiya na kalau” da idanu ta nuna mata Riyad hakan yasa ba yabo ba fallasa tace “sannu” wayanshi yaciro yashiga dannawa Mama tamata dakuwa da hannu hakan yasa ahankali tace “ina yini” shiru yayi chan yace “fyn” sai shegen jiji dakai sabida yaga yanada hotel halama na babanshine ba nashi ba tafadi aranta, maida wayan yayi a aljihu yamike tsaye yace “Mama bari naje”dasauri Mama tace “nagode nagode Riyad Allah maka Albarka nagode kaji saika dawo agida Mama” “zasuji” yayi maganan yana juyawa yawuce yafita wucewa wajen wardrobe na dakin Rashida tayi taciro kudin tarike a hannu tace “ina zuwa Mama” kafin Mama takirata harta bude kofa tafita daga dakin dagudu tabishi abaya ita bama tasan sunanshi ba hakan yasa ta kasa kiranshi gashi wayanshi na kunne har parking space yabude mota ya shiga mota yana kokarin tadawa tai knocking glass din hakan yasa yasauke glass din kasa ya zubamata mayun idanunshi haka nan taji gabanta yafadi kawai saitaji muryanta ya makale, dan gyaran murya tayi kadan duk yana kallonta sannan tadago hannunta dake dauke da kudin ta mikamai yabi kudin da kallo da aka daure da lobari sannan yajaye idanunshi dagakan kudin yazuba mata manyan idanunshi still baice komiba aranta tace “amman anyi dan wulakanci anan” saikuma ta daure ganin kallon kudin me yake mata tace “150k ne nan, sauran kudin daka kashe I will pay you back small small” dauke kanshi yayi daga kallonta ya kunna motan kaman wanda akace dole yayi magana yace “keep your money ban bukatanshi” jitayi ranta yafara tafarfasa sabida yanda yayi maganan a wulakance ta kalleshi tace “nikuma ban bukatar taimakon ka ko angayamaka i need your help to take care of my mother ne”? Da kokarin yin reverse yake but jin maganan ta yasa ya dan dakata yakalleta yace “you need all the help Rashidahhh!” Faduwa gabanta yayi yanda yakira sunanta saikuma amsan daya maida mata yadawo mata wani irin sparking taji tanayi zatai magana taga yayi reverse abinshi yana kallonta yana saka wani bakin glass a idanu sannan yajuyar da kan motan yafice abinshi kaman ta kurma ihu takeji.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣4️⃣


Wuraren 3 Mama na zaune tsakar gida tana gyaran shinkafa ta kunna radio ta ijiye gefenta saman tabarma tana sauraro taji an turo kofa an shigo hakan yasa ta kafa ido taga wazai shigo bakuwa tayine saitaga Rashida sosai gabanta yafadi ganinta cus bata taba ganin Rashida ta shigo gida around this time ba, kallo daya ta mata tagane tai kuka dawuya ne Rashida tama wani abu tai kuka, ita kadai ke iyasa yarta kuka dasauri ta ijiye tray shinkafan tace “lafiya menene kika dawo dawuri haka?” Murmushi ta kakalo tace “Mama kaina ke ciwo sosai saisa nadawo” tai maganan tana zama kusada Mama kanta Mama ta taba tace “bari na kawo miki vitamin C kisha tashi ki cire jallabiyan kisha iska” tashi tayi tawuce ciki Mama tabi jakanta dayay strange girma da kallo sai kawai ta jawo tabude ganin karikitan ta ne ciki yasa da sauri ta tashi tabita daki tana tsugunne  gaban ganamasgo tana neman kaya Mama tace “an koreki wajen aiki ne”? Dago kanta tayi ta kalli Mama zatai magana Mama tace “karki kuskura kimin karya an koreki daga wajen aiki ne?” Ahankali tace “Madam dina tace yau ne last day na aiki na a hotel dinsu” waje Mama tasamu dasauri ta zauna jin jiri zai dibeta tace “Meya faru tell me everything” Mama tariga ta ganota hakan yasa tafadima Mama komi ba karya, ba karamin baci ran Mama yayi ba tace “sau nawa zan gayamiki ki dinga hakuri arayuwa Rashida eh? Zagi na kari ne? Koko zagi na nunawa ajiki ne? Dan an zageni sai mene” dasauri Rashida ta kalli Mama, Mama tace “yes dan wata ta zageni and so wat dazaki hau fada awajen aikin ki kina hankade Madam dinki har sau biyu mai hotel din gabaki dayama shima kinmai rashin kunya” ahankali takai hannu ta goge hawaye tace “Mama bazan iya daurewa azageki agabana ba ko ace wani abu mara kyau wlh” saikuma tarushe da kuka tace “narasa me nayima yan layin nan duk inda nake aiki sai sunsan yanda sukayi sukaje suka batani su fallasani, wlh kowaye meyi ban yafemai ba” tabama Mama tausayi amman kawai saita wuce tabude drawer tadauko hijabinta har kasa ta saka da sauri Rashida ta mike tace “Mama ina zaki?” Cikin dan masifa tace “ina zani? Ina kuwa zani inba wajen aikin naki ba naje nabada hakuri itama yarinyar a nunamin gidansu naje nabada hakuri, idan babu aikin nan tayaya zaki gama makarantan ki eh? Me zamuci? Dame zaki sami kudin siyan tufafi? Ga wayanki ta lalace baki dawo da itabama that means bata gyaruba duk ina zamu samu kudin nan kafin kisami aikin nan kin manta kalan wahalan dakikayi eh? To zuwa zanyi nabada hakuri” dasauri ta taho takama bakin hijabinta tace “Mama dan Allah dan Allah karkije kinji Mama” fizge hijabinta Mama tayi tace “inda bakiso kisani naje nabada hakuri ai da bakiyi abinda zai tursasani inje ba, yau ko basu karbeki ba dolena naje na bada hakurin abinda kikayi kinma mutanen dake gaba dake reni sannan kin fasama yar mutane hanci da baki” baki Rashida tabude zatai magana Mama ta nunata da hannu tace “kimin shiru anan” ta fiziğe hijabinta tajuya tafita fuu Rashida nada zuciya so tasan yarinyar didn’t even realize how important this work is to them most especially towards karatun ta she will do everything ta tabbatar Rashida tagama karatun ta lafiya.


Kafa Mama tasa ahanya tana tafiya ahankali kanta na sarawa amman ta daure cus she knows what school din Rasheeda means to her, she will not allow her to sabotage mean na school fees payment nata ba, she just hopes darajanta zaisa sumata afuwa.

Tanakai junction ta tare keke da taso taje da kafa ne, amman taji jiri na dibanta bazata iyaba, har hotel din aka kaita ta sauko tabiya kudin tajuya ta kalli tamkeken hotel din almost duka inda Rashida take aiki ta sani musamman take binta dan tasan inda diyarta ke aiki incase wani abu yafaru she knows inda zataje neman diyarta amman bata taba shiga wajajen aikinta ba, ijiyan zuciya ta sauke jin yanda heart nata ke beating saita dan natsu kafin ta shiga building din motoci cike anyi parking, hotel din yahadu bana wasaba, karasawa tayi zuwa entrance door din zata shiga from yanda take looking security guard dake gadon kofan shiga reception din yace “Hajiya wakike nema? Idan zancen taimakone Oga yace jibi ranan juma’a za’ayi rabon abincin azumi you can come by 10AM” ahankali Mama tanuna kanta tace “nine Maman Rashida sannunku da aiki, Rashida na aiki anan maybe kasanta, to tayi laifi ne shine nace bari nazo nabawa Oganta hakuri dan Allah akomar da ita sannan nabama yarinyar hakuri” kallon Mama sukayi sannan suka kalli juna kafin daya ya nuna mata kujera dake chan gefe wani plastic chair yace “guest da ma’aikata kadai ke shiga ciki jeki zauna achan Oga nada baki amman zai fito anjima kadan sai a gayamai” Mama batai musu ba tace “toh” wucewa tayi zuwa kujeran dasuka nuna mata ta zauna tabuga tagumi tai shiru burinta kawai karsu kori Rashida addu’anta kenan, gabanta sai faduwa yake cikeda fargaba.






Tunda yaje office nashi yayi shiru bakin dasukayi ma yawanci Munir ke kulasu, agogon hannunshi kiran Rolex ya kalla 5 tayi na yamma kaman an tsikaresh ya mike duk kallonshi sukayi “excuse me” yafadi tareda wucewa wajen kofa yafice Munir yabishi da kallo kafin yacigaba da abinda yake samin kanshi yayida shiga elevator ya sauka kasa, he doesn’t even know why he’s doing this but samun kanshi yayi da zuwa hanyar changing room din ganin kofan wangale abude yasa yadan leka ciki babu kowa wajen fuzar da iska yayi yajuyo yafito daidai Madam zata shigo hanyar chak ta tsaya ganinshi surprisingly tace “Yallabai wani abu kake bukata”? Kaman bazaiyi magana ba saikuma yace “where is she”? Kallon hanyan Madam tayi tace “wa she? Oh mahaukaciyan nan”? Dan lumshe idanu kadan yayi hakanan yaji kalman azuciyanshi yadai daure bai nuna wani abuba ya kalleta, dasauri tace “ta tatare kayanta ta kwashe komi na locker ta tatafi tabar aikin da kanta kafin mu mata official kora”  yanda taga yahade fuska yasa dasauri tace “sorr….” Ahankali yace “sack the other gurl Hus….” Cikeda Mamaki Madam tace “Hussyn Yallabai”? Babu wasa akan fuskarshi yace “I don’t want her working for my company, just compensate for the injury, give the other gurl a call tadawo aiki” yana maganan yawuce baki Madam yakasa kulluwa tana kallonshi, yarinyar data barar da ita yake cewa akirata back, wacce aka jibga yayi sacking, dan ijiyan zuciya tasauke aranta tace “his company his rule!” Tawuce ta tafi office nata.

Wucewa kawai yayi yabar wajen yafito, security daya budema wani guest kofa dazai shigo ne ya hango yallabai hakan yasa yashigo ciki da gudu daidai zai shiga elevator yace “Yallabai barka da hutawa dama wata mata ke nemanka awaje” wani kallo Riyad yamai irin wata wa? Shi kuwa? Dasauri security yace “tace wai itace Maman yarinyar da aka kora tazo tabada hakuri tana waje, she’s Rashida’s Mom Sir” hakanan Riyad kawai yaji gabanshi yafadi but yadaure yace “why is she sitting outside?” Dan sauke kanshi kasa Security yayi yace “uhmm Yallabai cewa akayi cutan kanj……” fuuu Riyad yawuce zuwa entrance door din kafinma abudemai kofan dayake glass door ne yana iya hangota yanda tazauna kan kujera tayi tagumi tana kallon waje daya cikeda tsananin damuwa and kana kallon matan kasan she’s really sick she looks so skinny and pale jiyayi zuciyanshi yamai ba dadi sosai yanda security sukai trashing nata awaje haka, dasauri yafice bayan an budemai kofan yayi wajenta direct yana zuwa kawai saiya duka cus bemasan mezaiyi ba, she’s the mother of the girl that save his life kome yayi bai biyataba, cikeda girmamawa yace “Mama” firgigit Mama tadawo daga dogon tunani datake tajuyo ta kalleshi, dasauri tace “Naam Bawan Allah kaina mai wajen nan nazo nabada hak…..” kafin takarasa maganan dasauri yace “Mama” hakanan Mama taji yanda yakirata yataba zuciyanta, yanda yakira sunnan just touched so many things a zuciyanta kawai sai hawaye, life and sickness nata have made her so emotional, muryanta na rawa tace “dan Allah dan Allah kuya kuri nasan Rashida da zafin zuciya ga fada ga taurin kai, kome akace tama yarnyar nan nasan tayi dan Allah kuyakuri kurufamin asiri kada ku koreta daga aikin nan dan Allah ku taimakeni” tai maganan tana jan kujeran baya zata duka dasauri Riyad yakama knees nata ahankali yace “Mama dan Allah karki rokeni, ban koreta ba zata iya cigaba da zuwa aiki” da sauri Mama ta kalli fuskanshi tace “da gaske?” Gyadamata kai yayi yace “eh” ijiyan zuciya Mama ta sauke tace “to inane gidansu yarinyar naje na bada hakuri” ahankali yana sakin knees nata yace “basai kin bada ba lafiyanta kalau Mama, is just normal misunderstanding da kananun maganan yara yajawo fadan kada ki damu kinji” gyadamai kai tayi tace “Allah maka albarka” murmushi yamata kadan baice komiba, Mama tace “bari natafi gida to Alhamdulillah nagode nagode nagode kaji” daga yanda take maganan kasan hankalinta ya kwanta gyadamata kai yayi, Mama tace “to sai an jima” “saida safe Mama” yafadi ahankali, Mama ta wuce cike da farin ciki tafara tafiya kadan kadan sabida yanda kanta ke sarawa, tayi tafiya daya biyu uku ana hudu kawai ta yanke jiki tafadi, Riyad na tsaye yanama security magana sukaji karan fadin abu juyowa sukayi ganin Mama yasa dawani irin gudu Riyad yayi wajenta suma security din haka dago kanta yayi yana tapping hannunta yana kiranta. “Mama Mama Mama” amman shiru dasauri yace “help me” daukanta sukayi yabude bayan motanshi yasata yakoma yashiga gaba yatada motar sai wani babban private hospital dayake zuwa anytime yake Kano yana zuwa aka karbi Mama sai emergency yawuce office na Dr dinshi ya shiga Dr ya sallami patient dayake tareda shi yace “Ranka shi dade mai Martaba” dan yatsine fuska yayi yace “don’t call me that I have a patient tana Emergency I want you to be on her case fast” tashi Dr yayi suka fito tare ya shiga emergency din, shi ya tsaya agaban wajen yarasa yanda zaiyi sai kuma yakoma office na Dr ya zauna, yana nan zaune yana jiranshi har aka kira magrib saiya tashi yafito yawuce mosque yana gani Munir na kiranshi yaki dauka salla yayi yafito yawuce ciki yakoma office na Dr yazauna sai gashi Dr yashigo dasauri Riyad yatashi yace “how is she ta farfado?” Gyadamai kai Dr yayi yace “da kyar muka samu ta farfado amman tana bacci” saikuma ya zauna ya kalli Riyad yace “kasan wacce ka kawo? Who is she to you?” Batare daya amsashi ba yace “does that matter? Meke damunta? How can I help?” Gyara zama Dr yayi yace “she’s HIV patient!” Yayi maganan yana kallon fuskan Riyad dayaga bai chanza ba saima yace “me da me take bukata yanzu”? Ahankali Dr yace “is like she’s on medication so bahsine abinda ke damunta ba bashine kuma dalilin yankewan jikinta tafadi ba, abinda yafi komi damunta is BP, BP ta yayi raising sama sosai I don’t think zan sallameta yau ko gobe ko jibi ma sef, sai ya sauko sannan zan sallameta, just get wanda zai zauna da ita and then drugs” yashiga rubuce rubuce duk Riyad na kallonshi saida yagama komi sannan yanunamai takardan, tashi Riyad yayi yazaro wallet dinshi ya ijiye akan table din cikeda izza yace “take any amount kake bukata for drugs, bills, pin is 6648” yana maganan yawuce yafita akasaitance yasauka kasa dakin dayaga an shiga da ita yawuce shiga yayi ahankali ya tsaya bakin gadon an cire hijabinta daga ita sai riga da zani da hulan dake kanta an samata drip, shiru yayi yana kallonta sannan yajuya yafice daga dakin  yawuce yaje motanshi yashiga yadau wayanshi yana shirin kiran Munir wayanshi yashiga ringing Munir dinne yana dagawa kafin yayi magana yace “Munir open file na employees dina a desktop get info na Rashida I need address nata ASAP” kafin yayi magana ya katse wayan yayi shiru chan saiga Munir din yakira yace “suna Ranji, wajen tudun Murtala” baimasan inane wajen ba but haka ya katse wayan ya kunna google map yashiga driving….


Tunda tai magrib ta zauna tai shiru tana mamakin ina mama taje harta dau hijabi kota bita hotel dinne ko wani case dinne akeyi achan but karta kara bata ran Mama taje wajen hakan yasa ta daure ta hakura, kuma zai iya yuwa tadawo takai karanta wajen  Baba liman ne dantana haka wani zubin hakan yasa ta zauna adaki zugum kaman wata marainiya idan aka kira isha’i bata dawo ba zatasa Hijabi taje ta nemeta….


Shigowa layin yayi ga majalissar maza gaban shaguna ana zance rage wutan motan yayi karya haskosu yana karasowa yakashe motan kawai ya bude ya sauko yazo wajen yamika musu hannu yace “Assalamu Alaykum” atare duk suka amsashi suna karban hannunshi ganin arniyan motan dayake ja, yace “dan Allah tambaya nake” dasauri sukace “Allah sa mun sani” anatse yace “gidansu Rashida nake nema” tsit wajen sukayi kaman ba su ba saikuma daya daga cikin samarin yatashi yace “bismillah yallabai zomu kebe mana” binshi Riyad yayi sujkaje wajen mota kaman mutumin arziki yace “nasan ba laifinka bane Rashida kam nada kyau Masha Allah yarinya kaman Balarabiya amma dai kyan dan maciji ne, yanda muke gayamaka dinnan haka muke gayama duk wani saurayi dazaice zaizo nemanta hakkinmu ne na yan unguwa, hakkin makotaka tunda su basu fadin gaskiya” tunda yafara magana Riyad yaji ranshi na baci amman ya daure dan he wants the address, mutumin yace “kagadai uwar yarinyar nan fasika ce garin kwashe kasheta ta kwaso kanjamau Rashidan ma muna kyautata zato tanada shi tun acikinta tasam….” “Zaka fadamin adreshin ko bazaka fadi ba”? Riyad tafadi sounding bitter and angry baki mutumin yabude zaiyi magana Adamu mai chemist da tun zuwan Riyad ya hangoshi daga chemist yace “kaje chan kasan layi zakaga gida mai jan kofa nan ne gidansu Rashida” kallonshi Riyad yayi yace “thank you” yawuce yakoma mota yatada mota yabar wajen, gaban gida mai red door yayi parking ya sauka ya tsaya gaban kofan yakai hannu yayi knocking, Rashida na zaune kan dadduma taji ana knocking hakan yasa ta tashi dasauri batare data cire pink hijab dinta ba tafito silipas ta zura gabanta sai faduwa yake ta taho zaure tana mamaki Mama ta kulle kofan ne dazu dan idan aka rufe yana shiga jam, ganin kofan abude ga wani arnen black car parked agaban gidansu wani mutumi a tsaye yajuyama kofan baya so bata ganin fuskanshi yasa ta fito kai tsaye cikin muryanta mai bala’in dadi tace tace “kaine kai knocking wa kake nema?” Har cikin zuciyanshi yaji sanyin muryanta hakanan, cikeda wani irin kwarjini yajuyo yana zuba hannun cikin aljihun rigan dake jikinshi, hada ido sukayi ta kalleshi ido cikin ido dan akwai wuta a kofar gidansu mamaki da tunani yacika kanta, ba mutumin nan bane mai hotel dinda take aiki ba? Ko idanunta gizo yake mata? How is he agidan su? Ganin ya tsaya yana kallonta bayako kyafta ido yasa tadan dauke kai tattare bakin hijabinta tashigayi tana tabawa saikuma takai hijabin bakinta, saichan tacire, saikuma chan ciki ciki kaman an sata dole ahankali tace “ina yini” he’s looking at her mostly sabida baisan mezai fada mata ba, chan yace “Mama wants to see you” hakanan gabanta yayi bala’in fadi dasauri ta kalleshi baki tabude zatai magana saita kasa sabida yanda kirjinta ke bugawa da gudu da sauri sai kawai ta tsugunna, wani irin tausayi yaji tabashi yakasa cemata komi, da kyar kusan 30sec sannna ta mike jin tadawo daidai cikeda karfin hali tace “ina Mama wat happened to her? Nace mata kartazo tabada hakuri but taki jina, normal Mama da tuni tadawo, tana ina yanzu? Just tell me wat happened to my mother mekuka mata? Me kuka gaya mata? My Mom is very sick, tell me tana ina yanzu?” Tai maganan hawaye na cika idanunta harwani kyalli suke adake still kallonta yake yace “she’s fine now but tana hospital” hannuwanta biyu ta daura a fuska saikuma ta juya takai hijabinta ta goge fuskanta tass tajuyo ta kalleshi da jajayen idanun hijabinta daya jike da kuka ya kalla sannan yakalleta, cikeda dauriya da karfin hali tace “inane asibitin bani address din natafi” batare dayay magana ba yajuya yace “get few things da Mama zata bukata lock the house I will take you there is late bazakije da kanki ba” yayi maganan authoritatively yawuce yabude motan ya shiga gaba, kallonshi tayi sai hawaye sai kawai tajuya takoma cikin gida, drawer tabude takwaso simple t-shirt tasa ajaka tadaga kayansu ta dauko ledan duka kudin dasuke ijiya 139k, tadauki dadduma da zanin gado wankakke tasa ajakan bayanta takashe wuta tafito sai goge hawayenta take tarufo kofan waje tasa key sannan tajuyo ta kalli motan, bata taba shiga mota babba haka ba, ahankali yakawo hannunshi yabude kofan ganin yanda take kallon motan kaman matsoraciya, daurewa tayi ta matso ta shigo ta zauna agaban ta maida kofan tarufe wani sanyi da kamshi na dukanta ta rungume jakan a hannunta gam.


Tada motan yayi ahankali sannan yafara tafiya bini bini tajuyar da kanta takalli gefen window tana goge fuska, sunyi tafiya na kusan 30min sannan sukakai asibitin da saida ta firgita ganin kyanshi dan tasan zaiyi tsada tayaya zata biya kudin?

Parking motan yayi yafito, kokarin bude kofanta tashigayi tafito takasa, cus ba irin normal kofan mota data saba dashi bane, abinma yana nema yakarasata kuka ta daure ganinshi ya zagayo ta inda take yana kallonta ta glass dan wannan motan ba tinted bane, bude mata kofan tayi da sauri ta sauko batare data kalleshi ba ta tsaya gefenshi dan nesa dashi maida kofan yayi yarufe sannan yafara tafiya tabiyoshi abaya da saurinta suka shigo cikin hospital din har zuwa dakin da Mama take kwance kafinma yasa hannu yabude kofan da sauri tasha gabanshi ta rigashi tura kofan tashiga ta tsaya chak tana kallon Mama dake bacci an samata ruwa an makala mata wasu abubuwa a hannu yarda jakan dake hannunta tayi awajen tawuce dakin da gudu taje inda Mama take kawai ta kwanta jikin Mama ta manna fuskanta akan wuyanta tana kuka sosai wanda babu kara idanba ka kalli kakkarwan da jikinta keyiba bazaka gane kuka takeyiba, ahankali yaduka yadauki jakanta yashigo dakin yakawo gefen gadon ya ijiye saikuma ya zuba hannayenshi a aljihu yana kallonsu, takai 3min ahaka sannan ta taso da sauri ta dauki Dr note dake saman table na gadon ta shiga karance karance magungunan da alluran dake wajen ta shiga duddubawa tana karantawa har drip din da aka samata sannan ta sauke ijiyan zuciya tasake zama bakin gadon takama hannun Mama tarike gam tana kallonta,  kawai kana ganin Rashida kasan yanda takeson Mamanta, ta dade ahaka tana kankame da hannun Mama sannan tasaki hannun takai hannayenta ta share fuskanta tajuyo tareda tashi tsaye ta kalleshi hada ido sukayi da sauri ta dauke kai cikin muryanta dahar ya chanza sauti sabida kuka tace “nawa ka kashe nabiyaka inaso akira Dr ya sallameta na nemo keke napep nakaita chan asibitin datake amfani dashi” yana kallonta right in the eye yace “which hospital”? Ahankali tace “teaching hospital” kai tsaye cikeda izza da iko kaman Mamarsa yace “kibarta anan” da sauri ta kalleshi sake hada ido sukayi cikin konewan idanu Rashida tace “wannan kuma nice next of kin nata i decide and make decision for my Mom not you, nawa nidai ka kashe” yadade yana kallonta baitaba ganin feisty mara kunyan yarinya irin this girl ba, yana kallonta yace “idan Dr yazo ki tambayeshi” yajuya zai wuce tace “eh zan tambaya and i will pay you back cus banson any favor ko taimako from anybody zan kawoma kudinka” dan jimm yayi sai kawai yabude kofan yafita, mota yawuce yashiga yatada yayi dialing number Dr yana dagawa yace “Dr on no condition zakai releasing that patient without letting me know, don’t let the Daughter take her to another hospital, sign them up for abinci” cikeda girmamawa yace “to Ranka shi dade” dan yatsine fuska yayi ahankali yace “and about that!” Yadanyi shiru chan yace “don’t disclose my identity to anyone nor address me ahaka in front of anybody” Dr yace “shikenan Riy….” Harya katse wayan ya bala’in gaji hotel yakoma ya kashe mota ya sauke ya shiga ciki ana gaidashi ko amsasu baiyiba yawuce office nashi straight yana budewa ya shige ganin desktop a kunne yasan Munir na ciki, hakan yasa yawuce ciki Munir na kwance yana buga game a tv dagashi sai singlet da 3quater ganinshi yasa ya ijiye remote yataso yace “ance Maman yarinyar tazo and she fainted kasata a mota hospital ka kaita” yana cire riga yace “eh” tsayawa Munir yayi yana kallonshi yace “I know the girl itace wacce saved you but are you sure zaka barta tacigaba da aiki kai the girl have quiet a temper” batare daya amsashi ba kawai yawuce yafada bayi wanka yayo yafito daure da towel a waist turaruka ya tsaya ya fesa sannan yazo yazauna, Munir tace “Mom takirani yafi sau goma nace mata we are not together tace she will call back in the next 5mins idan ban hadata dakai ba zata kai karana wajen Ammi” Shiru yasakeyi hakan yasa Munir yadafa kafadanshi yace “common mana fushin ya isa haka before kasa karyan vakada lafiya da Mami tayi azo asani please go back home” yatsine fuska yayi yace “I’m hungry Muneer, please kaje gida ka kawomin abincin Ammi” tashi Muneer yayi yace “okay”.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣6️⃣


Rashida tadade awajen tsaye ranta na kunan wulakancin daya mata sannan takoma ciki Mama tace “ina kikaje”? Kudinsu ta nunama Mama tace “naje rage kudin daya kashe mana ne amman yaki kulani” yanda take maganan kasan ranta abace yake Mama bata cemata komiba idan sabone tasaba da halin Rashidan nan na batason ataimakesu, itafa kawai bataso ne sabida gori da wani abu dazaije yadawo. 

Har dare duba Mama ake akai akai ana zuwa auna BP da sai sauka yake ahankali ahankali, kawai Mama is at stage da batason damuwa da wani abu dazai tsoratata ko tadamata da hankali ko kadan, tare suka sauko sukai isha’i suna idarwa tazare hijabinta ta ijiye nan kan dadduman yanda kanta kemata nauyi sabida jiya batai bacci ba jiya batasan lokacin data wuce tahau kan gadon ta shige cikin chan bango danta barma Mama dake azkar space nata, taja bargo ta rufa ko 1min bata karaba sai bacci tafara jan munshari juyowa Mama tayi dagakan dadduma ta kalleta sai kawai ta cigaba da jan charbinta tana zikiri,  knocking akayi tareda budo kofan Mama tace “bismillah” ahankali ya shigo rikeda basket na kayan abinci wannan karan yana sanye da jean da riga dasukamai kyau, dasauri Mama tace “Riyad kaine sannu da zuwa” zata yunkura dasauri yace “No Mama karki tashi” yataho inda take ya duka basket din ya ijiye yace “abinci nakawo miki Mama na gida, nasan abincin asibiti ba dadi” murmushi Mama tayi tace “sannu da dawainiya Riyad, sannu Allah saka da alkhairi, ni bandama bakin maka godiya again” dan satan kallon Rashida yayi daya hango a gado tarufa da bargon gadon sabida AC amman kana ganin fuskanta karaf a kan idon Mama dauke kai yayi dasauri daga kallonta yamike tsaye yace “Mama bari naje” dasauri Mama tace “nagode Riyad saida safe ayi tuki ahankali” “Toh Mama” yafadi yajuya hakanan yasami kanshi da sake kallonta yana tafiya harsaida ya bude kofa sannan yajuyar da kanshi ya kalli kofan yafice Mama tadanyi murmushi kadan tareda bude kulan, she just feel wani irin strong trust for Riyad connection that she feels towards the boy yawuce misali, bude kulan tayi taga tuwo da miyan kuka ga man shanu da yaji a gefe da namomi sai kuma 3rd kulan pepper soup ne, shiru tayi tana kallon abincin tana tuna rayuwan datayi abaya ire iren abincin nan sune cimarta dan abincin da Baban Rashida yafici kenan, he always complements abincinta especially pepper soup yace baitabacin pepper soup mai dadin nataba, spoon tadauka ta debo naman takai baki wato duk kalan dadin rayuwa da mulkin dakake ciki idan Allah yaso kwacewa it takes seconds yayi hakan, alokacin bata taba sanin zatai rayuwan da abinci zai gagaresu ba! Ijiyan zuciya ta sauke sai kawai ta ture tunanin kafin kanta yafara ciwo.


Mota Riyad yawuce da Munir keciki yana jiranshi yabude gaba yashiga Munir yatada mota yace “hope she’s feeling better tunda you don’t want me to go with you” yatsine fuska yayi yace “thanks for the food daka karbomin daga wajen Ammi”baicemai komiba suka wuce gida, ta side nashi suka shiga as usual, parking Munir yayi yawuce yafita dan yaje side nasu shikuma yawuce flat dinshi, zaune yaga Mom afalo tana ganinshi ta taso da saurinta tazo wajen kawai ta rungumeshi saikuma ta dago tahau taba fuskanshi tace “you have not been eating Son, look at you, duk ka rame” ahankali yace “I’m fine Mom” waje yasamu ya zauna Mom ma tazauna tace “kayakuri kayafema Haleematu is not her fault banson kayi fushi da ita over petty mistake, she’s just 25 yanzu so kagani she’s still a small girl, kishi take batason ka kula mata which nayi supporting hakan” kaman bazaiyi magana ha saikuma yace “Mom she needs to learn to respect my privacy, tadena bincikamin kaya and tadena…..” yadanyi shiru Mom tace “tadena me?” Baki yabude saikuma yayi shiru sai chan kuma yace “tadena sharing my private affairs with my Mom” dakuwa Mom tamai tace “she shared private affairs naka dani da duniya tai sharing? Zanje nagayama duniya baka iya kwanciya da matanka kullum ne”? Lumshe idanu yayi sai kawai ya kalli gefe duk Mom na kallonshi sai kawai ta mike tsaye tace “if you don’t want that then kaima do the needful, kama yarinyar nan ciki kagani, I just need heir to the king, gabaki dayan masarautan nan jira ake aga matarka ta haihu so kake ace ita juya ce? Yanzu gashi kayi fushi kabar gida 2 nema ko 3days yanzu bakuyiba, I will tell her to come now kuma wlh kamata maganan fadan nan saina sabamaka umarni na baka, tarayya nace kuyi kui bacci good night” tai maganan tawuce tana fita daga daki yabita da kallo wondering wat happened? Mom bata damunshi ada tana duk abinda yaga dama yanzu ko she dictate everything. Tashi yayi ahankali kawai yafada bayi yashiga wanka fitowa yayi ya shirya cikin pajamas yadan gaji so he just wanna sleep kwanciya yayi yana kashe wuta yana ji akai iso Sarauniya zata shigo ta telecom ana neman izininshi dan barinta danna boturin yayi alamun a barta, da saurinta Haleematu ta shigo taci gayu tasaka gold alkyabba wucewa ciki tayi da sallama ta shiga bedroom nashi dayayi sanyi sosai ga duhu hannu tamika zata kunna wutan strictly yace “karki kunnamin wuta” da sauri ta tsaya saikuma ahankali tashiga cire Alkyabban wasu arnan kayan bacci tasaka tataho ahankali ta hayo gadon kawai ta rungumeshi tana manna boobs dinta awuyanshi tace “I’m sorry Ranka shi dadi bazan kara maimaita kallan laifin dana maka ba dan Allah ka gafarce ni kaji”.


Kasa magana yayi yay shiru dago kanta tayi takai hannunta kan gefen fuskanshi ta shafa tace “amin afuwa akulani” tashiga shafa fuskanshi ahankali zuwa kirjinshi zuwa kasa daidai zata kai hannun wandonshi kawai ya jefata gadon yabita yanajan wandonshi kasa he don’t know so many things na zuciyanshi harda mara kunyan yarinyar nan he just needs natsuwa kawai ya shigeta tareda sakin ijiyan zuciya sannan yafara ita kanta takasa gane yanason sex ne bayaso ne oho shifa yafi karfin ya nemeki saidai ke kizo, kuma kikazo ya rikeki kaman mayunwaci wani zubin, saida tafara kabar da hannayenshi akan boobs dinta sabida yanda suke mata shegen zafi yau dan he’s handling her very rough but yaki yau yabata wahala saida tafara tureshi amman cinta yake chan ya kankameta yafara numfashi da karfin gaske ahhhh! Uhmmmmm! Assshhhh! Ya feso ciki sannan yasaketa dasauri yatashi yawuce yafada bayi wanka yayo kawai yafito feeling calm ya kwanta sai bacci.

Wuraren 7 Mama ta tursasata dole taje gida ta shirya ta sanar da Baba Liman batada lafiya sannan ta tafi school karta kara latti bataso tabar Mama ita kadaiba amman tawuce ta tafi, yau in patient pediatric ward tayi aiki the kids loves her, she’s so gently and sweet with them har sauran yan group dinta ma were jealous hakadai tai aiki har 1  tai salla ta tafi tadawo hospital har dare Riyad baizo ba suna zaune kan dadduma Mama tace “yau Riyad shiru” tabe baki Rashida tayi tace “sai kace daman kin sanshi daga wani waje ne ni wlh bakiga yanda nakejin haushin sa ba na tsanes……” wani kallo da Mama tamata yasa ta hadiye maganan kawai ta tashi tawuce ta zauna akan kujera tahau duba log book nata tana yan karance karance, tadauki book tana karatun everything datayi takuma koya tunda bata samu taje library ba sabida Mama, anan kan kujeran tai bacci.


Yau dadi takeji za’a sallamesu Mama tace “wai bazaki school bane” dasauri tace “Mama Dr yazo ya sallame mu zan kaiki gida saina tafi ai nadauki permission a hospital” Shiru Mama tamata wajajen 9 Dr yazo yakalli Mama dayaga har hijabi da kaya ta chanza sun gama arranging komi yace “Mama yanzu kin gaji damu zaki tafi ki barni”? Dan dariya Mama tayi tace “ai asibiti ba abun so bane likita dan haka zan tafi in barka fa” dariya yayi sosai yaduduba Mama duk Rashida na kallon abinda yake da manyan idanunta kaman za’a Mamanta wani mugunta yace “Alhamdulillah Mama BP ki yasauko Mama, dan Allah ki rage tunani kinji” yajuyo ya kalli Rashida yace “makesure baki barin Maman ki na yawan tunani, da shiga damuwa da stress da tashin hankali none of abinda na lissafo is good for her, she needs to be happy all the time, Mama take your drugs akai akai kinji Mama” gyadamai kai tayi sannan yabama Rashida takardan sallama yaced “you can go now, mun sallameta everything has been cleared by Riyad, ga magungunan ta nan bari namiki bayanin yanda zatasha” yashiga yima Rashida bayani gyadamai kai tayi tace “thank you” murmushi yayi yace “Mama yarki kaman Balarabiya akwai wani akasa ne idan babu kowa ina kam…..” kasa karasa maganan yayi sabida turo kofan da akayi babu ko knocking duk suka juyo Riyad ne, yasaka wani ash color shadda mai haske yana wani irin kamshi mai dadi dake banbanta shi da mutane da dama, dasauri Rashida tadauke kai daga kallonshi mugun haushinsa takeji, takalli Mama tace “Mama tunda na hada komi bari naje na nemo mana keke napep” kafin Mama tabata amsa ma tajuya ko kallon Riyad batayiba tabi ta gefenshi tafice, Dr yace “ahh Riyad kaine barka da zuwa” adikile yace “yauwa” dan kallonshi Mama tayi bata tabajin irin muryan nan tattare dashi ba, kin kallon Dr yayi yawuce wajen Mama yace “Mama ina kwana nazo nakaiki gida” yakalli kayan dasuka hahhada yaduka ya kwasa duka da kulolin yafice Dr yabishi da kallon Mamaki, aranshi yace “who are this people to Riyad cus this is just more than help akwai wani abu akasa, look at the way he’s serving them” saikuma yakalli Mama yace “Mama Allah kiyaye hanya” yawuce yafita shima, shiru Mama tayi kaman mai tunanin wani abu sai chan tai murmusa kawai, shigowa yayi yazo har wajen gadon yace “Mama can you walk? Ko in dauko kujera”? Dan murmushi tayi tace “haba zan iya tafiya Riyad” saukowa tayi daga gadon ahankali tafara tafiya yana kaffa kaffa da ita dudda bawai riketa yayi ba Mama ta rame sosai kaman iska zai kadata tafadi sunyi tafiya sun fito cikeda kulawa yace “zaki huta Mama?” Wlh har cikin zuciyanta tajejin Riyad yanzu, he’s caring and just too protective da sauri tace “a’a bangajiba da karfina fa muje kagani” murmushi yayi suka fito har wajen mota baya yabude mata dayake jeep ne sai alokacin ya taimaka mata ta shiga ta hanyar dan dukawa ya nuna mata shoulder shi yace “dafani ki shiga” kallon shaddan jikinshi kalkal Mama tayi saikuma ta kalli hannunta dudda bawai datti bane a hannunta amman saitace “kai haba karna bata maka kaya” ahankali yakai hannunshi yakama nata yadaura akan shouldershi yana rage tsayi yace “Mama kibata duk albarkanki ne” ahankali Mama tai murmushi kafin ta dafashi da kyau ta daga kafanta ta taka step din ta shiga motar yana kallonta yace “are you comfortable Mama” gyadamai kai tayi tace “yes Riyad thank you” daidai lokacin Rashida na shigowa hospital din tana cikin wani empty keke napep ta hangosu, azuciye ta sauko ta taho wajen daidai yajuyo, chak ya tsaya yayi folding hannunshi a kirji tundaga kan kafafunta yake kallo dake cikin wani bakin flat shoe daya gama mutuwa but dudda haka kafanta ya haska flat shoe din, zuwa skirt dake jikinta na atampa da pink hijabin data saka mai hula ya tasya mata a guiwa, tana zuwa ta tsaya agabanshi cikeda masifa tace “bakai zaka kaimu gida ba nariga na kira keke” wani banzan kallon raini yamata yace “then saikije ki sallameshi” yanda yamata maganan kaman ta kurma ihu mutumin nan dan bala’in rainin wayo ne sabida yaga yanada kudi da hotel shine zai dinga ma mutane magana yanda yaga dama, wai ina ruwanshi dasu? Cikin fushi tace “nace maka kafito mini da Mamana daga motan ka, wayasani ma ko dan yankan kaine kai tunda sai shegemana kake” wani kallo yamata sai kawai yawuce yabude mazaunin direba ya shiga ya zauna itakuma ta shiga kiciniyan bude kofan back sit, da hannu Riyad yakira  mai keken da sauri ya sauko yazo wajen yace “gani yallabai” kudi dayawa yazaro daga aljihu ya mikamai yace “gashi kaje” karba yayi yahau godiya Mama tai murmushi ciki ciki dan duk tana kallon draman tai kaman batasan sunayi ba making sick and tired face, danna glass na window tayi takalli Rashida dake tsaye tana kallon Riyad kaman zata iya fada dashi akace tayi, Mama tace “shigo muje kina batama Riyad lokaci zaije aiki fa Rashida” kallon Mama tayi har idanunta sunyi ja akufule tace “kuje ni bazan shiga motan ba” Mama na kallonta tace “zan saba miki fa wlh, zoki shiga mota muwuce” kallon Mama tayi bataso ta batama Mama rai yasa ta danne zuciyanta da kyar ta zagayo harta bude kofan baya Mama tace “tunda ga direba kin samu ko dole ki shigo baya” wani sweet smile Riyad yasaki ya gyara fuskanshi da sauri yana kallon waje kaman baisan anayi ba, kaman tayi ihu Rashida ta maida kofan tarufe takoma gaba tabude kofan ahankali tadan kalleshi ganin waje yake kallo abinshi yasa da kyar tashiga ta zauna ta jawo kofan tarufe tana harare harare, murmushi yayi yatada yajuyo yadan kallo Mama da tausassan murya yace “Mama are you comfortable? Natada motan” wani irin murmushin dadi Mama tasaki tace “I’m comfortable d’ana muje” wani irin zafi Rashida taji aranta yanda Mama takira Riyad danta kawai saita ciro wayanta ta manna earpiece tasa a kunne, tada motan Riyad yayi suka tafi baya wani gudu sosai, Mama sai hira takemai kaman tasanshi hakan yakara tunzura Rashida dudda batajin mesuke fadi but tana ganin bakin Mama na motsi, har anguwansu hira suke sai kallon motan ake a kofar gidansu yayi parking ya bude kofa ya sauko yabude baya Mama ta sauko ahankali yabude booth ya kwaso bags nasu Mama tace “key na bakin jakan” takai hannu tasa blavk jakan aljihun taciromai tabashi yana sane yasan bata iya bude kofan motanshi ba ya shareta shiga da Mama ciki yayi sai kallon gidansu yake koina a gyare tsaf zaunawa Mama tayi yace “bari naje Mama Allah kara sauki” Mama tace “nagode nagode Allah maka Albarka, wai ina Rashida ne hala ta wuce wani waje” baice komiba yawuce Mama tabishi dagodiya dayake motan tinted ne baya iya ganota but yaga yanda motan ke motsin ana bubbugata yayi kaman bai saniba yawuce yabude kofa yashiga ya zauna batare daya kalleta ba yace “wat are you still doing in my car”? Akufule tace “inba dole ba mema zai kawoni cikin your so called car”? Still yaki kallonta yace “get out!” Kaman yana magana dawata dabba kirjinta tafarfasa yake tace “ka budemin kaga idan nakara wani numfashi a motan naka” dan kallonta yayi strictly yace “who are you to make Riyad work for you”? Mamaki ne yakashe Rashida irin what exactly guy din nan thinks of himself ne, tadai daure ta danne zuciyanta da kyar tace “to ai ban iya bude kofan bane ni” dan juyowa yayi yayi facing nata yace “then learn to soften muryanki and ask for help politely miss” ido cikin ido take kallonshi ya zubamata mayun idanunshi dayasa kawai taji jikinta namata wani iri, duk yanda taso ta daure tacigaba da kallonshi itama saita kasa tadauke idanunta dan kasa jure kwayar idanunshi tayi, ta hadiye wani abu da kyar dataji yaa tsayamata a wuya tadan runtse idanu kai kasan she’s about to say komene zatace ne out of compulsion tace “kadan budemin kofan motan nafita” sosai yake kallonta sabida yanda kawai yaji muryanta pierce his heart, this is the first time tunda ya santa takemai magana softly but da gangan dan ya kureta yakaita bango yace “soften your voice more and add please cus no one command Riyad!” Da sauri ta kalleshi wani kallo yamata na idan baki fadi ba zanja motata nayi gaba abuna, kaman tayi ihu takeji shine namiji na farko so far so good tunda ta girman nan ya iya tankwarata yakuma juyata haka, batasan mesa ba batakaimai duka ko kokawa ba the normal ita datuni takaimai duka suyi dambe but shi takasa, agogon hannunshi yakala kirar TAG Heuer yace “you have 5secs left ko i will go wherever zani u will be here is none of my business” yayi maganan yana kunna motan ma abinshi, wani ijiyan zuciya ta sauke ta sauke muryanta kasa kaman ba ita ba sounding like a Baby tace “kadan budemin kofan motan” dan juyo da kanshi yayi ya kalleta muryanta is the best muryan mace daya tabaji in his entire life, yanda yake mata wani irin kallon yasa ahankali kaman ba itaba lips nata na rawa rawa tace “p……..p….lease…..please!” sannan ta dauke kai da sauri kaman tai abin kunya din nan, sabida son yakaita bango gabaki daya shikuma annoyingly and authoritatively yace “good gurl!” kaman wata damusa ta kalleshi for the first time Riyad yasakin mata wani kalan murmushi dayasa taji zuciyabta yabuga rasss! Yana beating dum! Dum! Dum!! Da sauri ta dauke kai trying to control yanda zuciyanta ke beating takasa, dan tasowa yayi daga sit din dayake ta gefen ido taga ya nufota da sauri ta juyo da kanta ta kalleshi dan kaman zai hugging nata, hada ido sukayi gashi yaki daina kallonta kaman akwai wani abu dayake son gani game da ita sai kawai lips dinta yahau rawa tawani koma baya da sauri ta manne jikin kujeran kaman zata nitse ciki har hannunta rawa yake barin yanda kamshin turarenshi ke shiga hancinta jinshi dab da ita infact yadin kayan jikinshi ke tabata ta she was scared, lost, shaking, it was just a freaking reaction jikinta keyi dabatasan na me ba, he could feel heartbeat dinta, he could clearly see kwayan idanunta, this whole fadan nata is just an act! A mask! Hannunshi yakai ahankali kaman baiso yabude kofan still looking at her ya bude kofan tareda komawa seat nashi ya zauna bude idanunta tayi da sauri he was expecting tamai rashin kunya but saiyaga duk ta dimauce ta sauka da sauri kawai ta maida kofan tawuce ta shiga gidansu da sauri sai kawai ya girgiza kai yatada motan yawuce yabar anguwan.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

 ✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣7️⃣

Tana shiga gıda Mamag tace “ke kuma an ina kika tsaya?” Ahankali tace “waje” kawai tashiga ciki zata kwaso kayan abinci dan daura girki Mama tace “kibar girki inada abincin da Riyad yakawomin har yanzu da zafinsu a kula shi zanci, kizo kije school daganan ki wuce aiki, Riyad yace kidawo” dasauri tafito daga dakin ta kalli Mama tace “Mama nifa yau na dauki permission bazanje school ba” saikuma ta taho ta zauna wajen Mama tace “Mama wai kinsan mutumin chan ne”? Mama na kallon kwayar idanunta tace “wani mutumin”? Cikeda mugun hali tace “shi wannan mutumin daya kawomu naga kunatayi kaman daman kunsan juna ne tun chan” dan murmushi kadan Mama tayi tace “a’a amman kawai zuciyata ya natsu dashi kaman na sanshi daga wani wuri, kema kinsan dawuya nake natsuwa da mutane amman shi kawai yayi fuce araina, mutumin arziki ne mutunci da dattaku, yanada halaye da dama nagari, bantaba gani a idanunshi yamin kallon mai wata cuta ba, gakuma yanda yabiya kudin asibiti akamin komi, wanda yamaka Akhairi kasoshi” ranta adan bace tace “Mama ni na tsaneshi” baki Mama tasaki tana kallonta ganin da gaske take, yunkurawa tayi tace “kuma konawa ya kashe miki a asibiti saina biyashi alkawari ne ko zanyi shekara dari ina neman kudin” dan dariya Mama tayi tace “zo ki juye abinciccikan ki wanke kulolin nidai fitina’u” wucewa tayi ta kwasa batai musu ba haka dai tai aikin komi Baba Liman ma yashigo gaida Mama wuraren 1 ta shirya ta tafi aikin sabida yanda Mama tace “saitaje” ga mamakinta ko kallon banza Madam bata mata ba hakama sauran ma’aikatan dudda bataga Hussy ba, kin zuwa office na Riyad tayi tadaiyi duka ayyukanta idan tana gaban desk aka kira ana neman cleaner a so so room ta taje, harta tashi by 6 bata ganshi ba bakaramin dadi tajiba ta tafi gida.


Washegari da sassafe ta tafi hospital nasu yau pediatric surgery departmant zasu to watch not to do itada team dinta zasu, direct tawuce inda suke ijiye bags nasu ta ijiye aka dan musu lectures kadan sannan tawuce tashiga shirye shiryen shiga surgery tsayawa tayi tana wanke hannunta wata tazo itama ta tsaya kusada ita tai murmushi tace “Hi” saikuma ta kalli Labcoat nata tace “Rashida I’m Maimuna but Maimoon ake cemin, tun ranan monday nake noticing naki, can we be friends pls”? Dan tsayawa Rashida tayi tana kallonta like a weirdo dasauri Maimoon tace “please” dan lumshe ido Rashida tayi yarinyar seems very cool and calm ahankali tace “I don’t know yanda ake friendship gaskiya” murmushi sosai Maimoon tamata tace “I know and I will teach you, let’s go” shiga cikin operation room din sukayi duk hannayensu a sama aka sassaka musu handglove ga yaron da za’ama operation din da baifi shekara biyar ba anyi sedating nashi shigowa surgeon din yayi wanda Babba ne bawai yaro ba aka samai nashi handglove din yawuce surgical table din student Doctors din dasuke su bakwai duk suka tsaya a gefe, Dr yace “yaron nan dake kan table din nan nada hydrocele wazai gayamin procedure da zanbi in this surgery, and ya sunan surgery din”? Maimoon ce tafara daga hannu tabata amsa yace “wrong” almost dukansu saida suka bada amsa yace “wrong” yakalli Rashida dabatai magana ba dan ita bata show off ko a aji, yace “make attempt miss” dan ijiyan zuciya ta sauke Rashida confidently cikin turencinta that is good muryanta kuma makes it sweet a kunne tace “zamuyi Hydrocelectomy surgery to remove the hydrocele daga scrotum din, zamuyi making incision anan…..” tafara bayanin procedure din da sai kawai Dr ya tsaya yana kallonta exactly abinda zaiyi tafadi kaman ta tabayi, hannu yamikama head nurse yace “scalpel” samai wuka akayi a hannu yarike yadauki marker yamikama Rashida yace “come close” ahankali ta matso kusada surgeon din gabanta nadan faduwa yabata marker yace “draw the line” karba tayi ahankali taja, to her biggest shock yace “make the cut” dasauri ta kalleshi, confidently yace “I’m here you won’t make a mistake so go ahead” dan tsayawa tayi Dr yace “we all start ahaka, go for it, I’m right here ina kallonki” bismillah tayi ahankali ta karba tana kokarin kallon fuskan yaron yace “don’t look at his face” ijiyan zuciya ta sauke tareda rufe ido what is her biggest motivation da inspiration na son zama likita? Ahankali tace “Mama! I want to become the best Doctor for Mama! I want to make research nagano yanda ake curing HIV for Mama! I want to make Mama better, I want to be the best Dr in Nigeria da kewaye da al umma zasuyi alfahari dasun samu” daidainan tabude idanunta kawai tashiga cutting Dr na tsaye kusa da ita yace “suction” aka kwashe jinin, wasa wasa da shi da Rashida sukai surgery din nan tass yasake barinta tai stitching yaron up, her stitching style kadai saida ya kalleta almost 10yrs yana aiki in this surgery student Doctors daban daban interns but baitaba ganin skilled yar baiwan Dr like this girl ba ita kanta for now bama tasan wacece itaba imagine abinda take iyayi in year5, sallaman su yayi yakalli Rashida yace “makesure you become a surgeon Doctor R” dan sunnar da kanta tayi batare datai murnushi ba cus she hardly smile outside tawuce tafita Maimoon tabiyota tace “wowwww you are amazing Rash kai! I can never do that” ahankali tace “thanks” dasauri Maimoon tace “let’s go grab some drinks” wayanta Rash taciro daga jaka taga 2:30 tace “ohh no I have to go to work” taciro log book dinta da sauri tawuce taje aka mata signing tajuyo takalli Maimoon tace “gobe” bata jira amsanta ba tajuya dasauri Maimoon ta tsaya awajen tai shiru tana kallonta, tace “she’s unique, Bilal you loose a rare gem”.  Wajajen 3 takai hotel din dan saida ta tsaya tai salla tana shiga tawuce changing room tafito kenan saiga Madam tace “yanzu ne lokacin zuwa aiki i will deduct 5k from salary naki” sauke kanta tayi kasa tawuce tashiga aiki thank God yau Friday gobe ba aikin, tass tagama aikace aikacen ta wuraren 5 Madam ta kirasu hall duk suka wuce, abinci tagani an kakkasa buhun shinkafa, jarkan mai, indomie, madara da milo sugar sai gero da taliya tace “kowa ya tafi da abincin azuminshi gida courtesy of  Oga” sai murna ake, tunda tafara aiki dasu da Ramadan ana basu abinci last year an bata is not new thing amman saitakeji yanzu kaman karta dauka sabida Riyad but kuma idan bata dauka ba za’ayita surutu daman ance tanada girman kai, Madam tace “zansa security su taya kowa fita da nashi sai kuje ku kira keke, Happy Ramadan to everyone” ihu duk sukayi ana shouting thank you Ma sannan ta sallamesu wucewa tayi ta chanza kaya ta goya jakanta tafito taje ta taho da keke tana zuwa security suka tayata lodawa abayan keken ta tafi.


Yau sunday tana so taje kasuwa tadan yo musu yan kananun cefenen azumi tunda batada aiki yau, atampa tasaka green shima ya kwana biyu tadau wani black hijabi ta daura asama mai hula ya tsaya mata a knee aiko yamata kyau tafito falo inda Mama ke zaune tana kirga kudinsu, zuwa tayi kusada Mama ta zauna Mama tace “yauwa kin shirya”? Gyadama Mama kai tayi, kudin da Mama takasa agabanta kashi biyu ta dauki me yawan tabata tace “ga wannan kudin dubu talatin ne nakine kisai dan atampa da takalmi da yan kayan kwalliya da turare kema kiyi kyau da salla kuka dawo sai akai dinki ko” dasauri ta maidama Mama kudin tace “Mama bana bukatan kayan salla, kayan danake dasu zan iya sawa da salla, Mama we have important things to do, drugs dinki, abinci, school fees dina dakuma kudin da mutumin chan ya kashe na asibiti ni sai na biyashi” kallonta Mama take tace “shiyace miki kibiyashi “? Girgizama Mama kai tayi tace “Mama you’re my responsibility ni kadai don’t others, banson wani ya taimakeni wajen kula da mahaifiyata, inda bekaiki asibitin masu kudin nan nasu ba dana iya biya amman yakama kaman an sashi ya kaiki asibitin kudi” tai maganan tana batarai tsayawa kawai Mama tayi tana kallonta tun Rashida na yarinya tanada wani irin kishi dasai ka san halinta ne zakasan kishine itafa batason kowa na raban Maman ta, yana daga cikin abinda yasa takejin haushin Riyad dakuma so tabiyashi kudinshi sabida yanda taga yana nan nan da ita bataso taga Mama na kula wasu with a smile, maida kudin kawai Mama tayi hannunta ta danne tace “listen to me umarni nabaki kisai kayan salla inaso nima naga yarinyana tayi kyau takuma fito da salla kinji” shiru tayi tana kallon Mama taki magana hade fuska Mama tayi tace “bazaki amsaba?” Ahankali tace “naji toh” dan murmushi tayi tabata 20k tace “wannan sai kiyo su cefene su maggi da nama da kayan miya tunda mun sami kayan abinci” gyadama Mama kai tayi ahankali ta tashi Mama tace “adawo lpy ki duba titi kafin ki tsallaka kinji” toh ta amsa tawuce tasa takalminta tafita abinta Mama tai murmushi.


Kusan 3hrs tabata a kasuwa, tasayo atampa mai kyau da gyale da takalmi tadansai bra da pant guda biyu sai pad dan tanaji cikinta na ciwo sannan tayo cefene tashigo keke tabar kasuwan.

Abakin titi aka saukesu hakan yasa ta dandaro cikin anguwansu da kafa, tun kafin takai gidansu ta hango wata arniyan karaman mota baka pake a kofar gidansu motan waye wannan? Hakan yasa ta kara sauri tana zuwa tabude kofar gidansu da sauri ta shiga saura kadan tayi karo da Riyad azaure yadan koma baya kadan tsayawa itama tayi gabanta kawai yafadi ta zubamai ido, yana sanye da wani milk soft yard dake kyalli yabi jikinshi kaman magic, kafanshi kafanshi sanye da Jordaan leather loafers brown, hannunshi daure da agogon Audemars Piguet, dayan hannunshi rike da waya samsung galaxy fold, ba hula gashin kanshi ya kwanta yana sheki sai kamshi yake zubawa, dauke kai tayi da sauri daga kallonshi dan he’s so clean wlh ko datti ko stain ko tabo guda daya babu ajikin kayanshi, haka kayan a goge babu squeezing ko daya, shima tundaga kan kafafunta dake sanye dawani black takalmi flat da duk an dinke ya kalla dudda fararen kafanta are shinning ga long fararen nails na kafanta da babu lalli ko daya akai zuwa ataman dake jikinta da hijabin da ledoji biyun dake hannunta bakake data rike sannan yazubama fuskanta idanu she looks tired, she’s even sweating a goshi dan duk gashi ya kwanta a goshin nata, ga lips dinta sun bushe kaman she’s a bit sick. “Kallon fa”? Tai maganan cikeda rashin kunya dayasa ya daidaita kwayar idanunshi cikin nata dasauri ta janye idanunta hakanan taji takasa kallonshi but tsabagen karfin hali tace “kadena zuwa gidanmu banso” cikeda isa kaman anyi forcing nashi yayi maganan awulakance yace “are you angry ba wajenki nake zuwa ba”? Wani dum! Taji saukan maganan da sauri ta kalleshi tsaf shima yake kallonta mene mutumin nan yace? Mema ya dauketa? Taji haushi dan ba wajenta yake zuwa ba on wat ground? Kokarin hado martanin dazata bashi take dan she was a bit speechless but yarigata wani kallon raini yamata calmly yace “bakida matsayin dazan zo nemanki” yana maganan yabi ta gefenta yafice wlh takai 1 good minute fassara maganan shi take akanta taji ranta na kumfa dasauri tajuyo tafito kofar gida daidai yaja motanshi tabishi da kallo yana wani saka bakin glass a idanunshi ko inda take bai kallo ba yawuce abinshi kaman zata hadiye zuciya tamutu tace “nima ka isa kazo wajena ne aka gayamaka? Sai ji dakai kaman wani dan shugaban kasa sabida yana takama da dan hotel din dayake dashi I will leave your company soon zan nemi wani hotel din wlh kuwa” tana maganan tajuya tana saisaita bacin ranta takoma cikin gidan kaya tagani cikin gidansu harda su indomie da kwalin kwai kudan 5 crete gasu manta manyan roban madara Milo oat, wlh shopping data gani zube a compound yakai na 300k ga bandir na kudi kuma ijiye kasa na yan 1k guda biyu dasauri ta shiga ta tsaya gaban kayan ranta abace tace “Mama waya kawo mana abubuwan nan”?


Ahankali Mama tace “Riyad yakawo” kaman zata fashe sabida bacin rai tace “Mama shine zaki karba?” Kallonta Mama tayi tace “babu yanda banyi dashi ba amman yaki yarda wai ni mahaifiyar sa ce kodan darajan azumi na amsa, kinga uban kudin daya ijiye dane naki amsa da kyar na zari yasake daura daya, haka ya ijiye komi anan dan ni naki karba” cikeda bakin ciki harda abinda yamata a zaure tace “Mama shine baki kira yara kinsa sun maidamai da kayan mota ba”? Kaman wacce aka daka kawai saita fashe da kuka sosai ta ijiye kayan data shigo dasu daga kasuwa nan kasa ta tsallaka tashiga daki kawai tahau kuka idanunta sunyi jajir tashi Mama tayi tabiyota ciki cikeda damuwa tace “Rashida mekuma haka da kuka? Duk mai imani yadaga ido yaga rayuwanmu dole yaji tausayinmu, na karba badan komi ba saidai naga yaron kirki ne hakanan zuciyana ya natsu dashi kuma bawai saurayi bane ya gayamin yanada mata so mutum ne mai hankali ba yaro ba, saikuma dalili nabiyu shine karbansu zai saukaka miki kema at least daganan zuwa 2month zamu manta da siyan Kayan abinci albashin dazaki samu saimu hada da wayan nan kudin ki biya kudin school fees ragowan mu rike na asibiti, you think I’m happy da rayuwan wahalan dakikeyi? Understand me it’s Ramadan kyaututuka haka is normal ko na yan anguwan man sabida baki karba ne da yanzu an kawo mana, it’s okay ya isa stop crying” Mama tajawota cikeda lallashi rabon datai kuka haka tun ranan da aka kwantar da ita a asibiti cikin kuka tace “Mama stop collecting abu daga hannun kowa, I’m enough for you, Mama bazan taba bari ki kwana da yunwa ba, I will never” hawaye taji yaciko idanunta saikuma tai murmushi ta danne takai hannunta ta share mata fuska tace “I know y’ata will never allow me to go hungry, natuba to bazan kara karban komi daga hannun kowa ba, Rashida na is enough for me, the best daughter aduk duniyan nan, come here” Mama kawai ta rungumeta tana murmushi she’s lucky Allah ya azurtata da y’a dake sonta haka, sun dade ahaka sannan Mama ta dagota takai hannu ta yaye hijabin jikinta ta tana taba wuyanta tace “jikinki da zafi baki da lafiya ne”? Ahankali tace “cikina ke ciwo kadan gobe naje asibiti zan karbi magani” cikeda so Mama tace “sannu kinji, zauna kihuta ni zan miki girki” dasauri tace “zanyi Mama” tashi zatayi Mama takama hannunta bawasa kan fuskanta tace “zauna kihuta” zama tayi Mama ta tashi atampanta tafara dubawa ta yaba sannan tashiga daura musu abinci itakuma anan bacci yayi awon gaba da ita.


Da kyar Mama ta tadata around 4 na asuba sabida suyi sahur, tariga tasan bata azumi wucewa tayi tama Mama abincin sahur sannan tawuce bayi yau da hot water tai wanka dan zazzabi takeji da ciwon mara but she feels she can manage dan is not that serious tana dawowa takaima Mama itama nata ruwan zafin tashigo daki tace “muje Mama” idanunta Mama ta kalla tace “dan Allah kina zuwa clinic kisha magana kar zazzabin nan yarufeki da kyau kinji” gyadamata kai tayi Mama tace “barshi zan iya zuwa bayin da kaina jeki kimtsa” batai musu ba ciki tawuce tashiga kimtsawa tasa black abaya tahada jakanta na baya saikuma ta kara kwanciya yawanci a rashin karfi ne kafi gane Rashida is sick dan baka ganewa a baki da fuska sabida masifa da fada, shigowa Mama tayi ganinta a kwance yasa Mama tace “namiki shayi”? Girgizama Mama kai tace “idan naje school zanci abinci Mama karki damu” da dan damuwa Mama tadauko mai tana shafawa hartai salla tana kwance wajen saima lumshe ido data farayi sai kawai Mama ta barta zuwa 7 ta tabata tace “tashi kitafi school” tashi tayi ganin Mama tafara damuwa yasa tace “laaaa Mama kinga najini garau maybe dama baccin danake ji yakara karamin zazzabi” 200k na jiya Mama takawo da 100k nasu tasa asama tabata tace “gashi ki biya kudin makaranta kisai yan littafan da baza’a rasa ba” kallon kudin tayi zatai magana Mama tace “ni Maman ki aka bama kudin nan, nikuma nabaki, kaman yanda Hajiyan nan taraba mana 20k a clinic naje na siyamiki crocs consider wannan kudin haka, go and pay school fees naki and buy textbooks dakike bukata” ayanda fuskanta kadai yayi kasan bataso ba but ganin yanda Mama tayi yasa tasa hannu ta karba kawai tasa kudin ajaka ta goya, taja black gyale tashiga rolling tai kyau kaman balarabiya dudda bakomi akan fuskanta sannan tace “Mama natafi” 5k takara cirowa cikin kudinsu dabaifi 50k ba Mama tabata tace “dan Allah kihau keke yau, kici abinci mai kyau a school kinji” gyadama Mama kai tayi tace “natafi Mama thank you” “adawo lpy Allah bada sa’a” fita tayi tana kaiwa junction ta shiga cafe tai printing ramita, sannan tafito tashiga keke sai bank taje tafara biyan school fees nata sannan tafito tashiga keke again sai asibitin su, sauka tayi wuraren 9:30 taga student nasu Maimoon na hangota ta taho wajenta dagudu tace “anyi releasing namu yau, kaman za’ayi manyan baki ne dai ance mu student mutafi wlh” ahankali tace “really, bari na karbi magani to natafi” dasauri Maimoon tace “meke damunki”? Dan yatsine fuska tayi tana tafiya tace “I think I’m coming down with Maleria saikuma cramps” Maimoon tace “oh no sorry” office nasu tashiga tabude locker ana ijiye musu magani haka tadauki na Maleria da cramps suka fito yawance Maimoon ke hiran, ahankali tace “I want to buy food da water dazansha magani dashi” dasauri Maimoon tace “muje cafeteria” Jellof rice tasaya da beef 800, tasai ruwa daya ganin tana bude jaka yasa Maimoon tace “mu zauna anan kici mana” girgiza kai tayi tace “kema kawai na gayamiki ne only Mama na ke sani idan bana azumi I don’t want people knowing kunya yake sani” dan murmushi Maimoon tayi tana kallonta yanda take arranging abincin ajaka tana maganan she looks so cute and adorable maida jakan bayanta tayi ta goya tace “bari naje to sai gobe” Gyadamata Kai Maimoon tayi suka fito tana kaiwa titi tashiga keke, is just around 10 yanzu gwara ta tafi hotel tamusu aiki saita sami free evening har gaban hotel din aka kaita ta sauka tabiya kudi tashiga ciki, direct changing room nasu taje, saida tafara chanza kaya sannan tadan fito ganin kowa na aikinshi yan morning sun riga sunzo tun dazu so kafin wani yadawo dakin nan cikinsu kuma probably sai idan yan afternoon sunzo kuma, hakan yasa tadawo ta maida kofan tarufe batare data saka sakata ba takoma ta zauna taciro rice daga bag da water dakuma maganinta ta ijiye kan long bench dake wajen itama ta sauna ahankali sannan ta dauki abincin tabude tasa spoon tafara ci ahankali bayamata dadi ma abincin sabida zazzabi.


Ahankali yake tafiya da shi da Munir dawasu ma’aikata guda biyu dake biyedashi abaya, akwai some changes dayakeso ayi abinda ma yakawo shi hotel din kenan this morning, duk ya gama nuna musu saura changing room na ma’aikatan shi corridor suka shigo suna biyeda shi yasa hannu yabude kofan yasakai ciki yana magana yace “the lockers nakes…….” Shiru yayi ganin yanda Rashida tawani yarda takeaway jellof rice din da ruwan yashiga tittila akasa ta tashi tsaye da sauri daidai su Munir zasu biyoshi su shigo ciki yace “wait!” Duk kallonshi sukayi suna tsaye bakin kofan batare da sun shigo ba strictly yace “kuje lobby” yanayinshi kawai yasa Munir yace “okay” yajuya ma’aikatan ma suka bishi yajuyo yazuba mata ido tana kallonshi cikeda fada baki tabude zatai magana dan akwai abinci abakinta sai kawai tai wani wawan kwarewa sai tari, maida kofan yayi yarufe ya kalleta ganin yanda take tari kaman zata mutu yasa gently yaduka yadauki bottle water nata daya fadi yadan zube yamike tsaye yasake kallonta tsabagen tarin datakeyi tama kasa tsayuwa ta tsugunna idanunta sunyi jajir ga rice guda daya fito daga hancinta alamun ba karamin kwarewa tayi ba, dasauri yataka zuwa inda take ahankali ya tsugunna yamika mata bottle water batare dayayi magana ba yana kallon fuskanta, tsabagen azaba sabida ga yaji a abinci ga kearewa mai kyau batasan lokacin data daura duka hannayenta biyu saman kan nashi ba takama both hannunshi da goran takai bakinta hakanan jiyayi jinin jikinshi ya tsaya chak jin saukan hannayenta biyu kan nashi, ahankali yadaura idanunshi kan hannunta dake saman nashi sannan yakai idanunshi kan fuskanta da yanda takeshan ruwan kaman yaki, tass ta shanye ruwan sannan tacire bakinta daga goran har lokacin tana rikeda hannunshi dabatasan tayiba tana sauke ijiyan zuciya kaman wacce tagudo daga hanyan mutuwa idanunta sunyi jaa, kusan 1min tayi tana sauke ijiyan zuciya sannan ahankali kaman mara gaskiya tadan dago kanta tadaura idanunta akan nashi yanda yake duke dab da ita kamshin turarenshi ya bade wajen da sauri ta maida idanunta kasa still bata sakeshi ba, yana kallon fuskanta baya ko kyafta ido yace “can you let go off my hand now”? Dawani irin sauri ta kalleshi saikuma ta kalli goran ruwan data rike ganin yanda ta kama hannunshi da duka hannuwanta biyu saida taji kaman ta kurma ihu sabida kunya dawani irin sauri tasakeshi hakan yasa ya mike tsaye ya kalli magungunan ta dake kan bench na wajen sannan yawuce kofa haryasa hannu yabude kofan ya tsaya batare daya juyoba yace “kifito amaidaki gida, kafin ki mutu in my building” dasauri ta kalleshi kaman wata damusa dan juyo da kanshi yayi but bai kalleta ba yace “take days off when you feel better you can resume” yasa kafa yafita saikuma ya tsaya yace “someone will clean the place you don’t have to, kifito akaiki gida!” Yana maganan yawuce yafita takai almost 2min aduke a inda yabarta saikuma ta daga hannuwanta ta kalla yanda tarikeshi saikawai taji kunya da haushin kanta sai abin yasa taji mugun zazzabi ya rufeta tanama jin sanyi, ahankali ta lallaba ta mike tadauki jakanta ta goya abaya batare data chanza uniform nata ta maida abayanta ba kafin wani ya sake shigowa yaganta tana chanza kaya she will not take the risk, tadauki magungunanta tarike a hannu tafito tana tafiya ahankali hakanan kawai sanyi taji tanaji barinma a hannuwanta dasuke abude dan uniform nasu short hands ne, gashi small farin baby hijab ne jikinta that covers her chest only, ahankali take tafiya is as if every step datai taking yana kara mata zazzabi harta fito lobby kadan kadan take tafita tana jin sanyi kaman akwai kankara awajen, hakan yasa bakinta yahau kakkarwa irin na me jin sanyi din nan kaman an sata a cold room, idanunta na rawa rawa suna kukkullewa kadan kadan take bude idanunta tasan ta hango mutane zazzaune da suit a lobby daganan kuma batasan meya sake faruwa ba dipp kaman an dauke wuta ta zube awajen.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 1️⃣8️⃣


Ahankali take bude idanunta dataji sun mata nauyi sosai kafin tagama budesu da kyar tazubasu asaman dakin sake lumshe idanun tayi tabudesu taga drip na ruwa hakan yasa tabi dakin da kallo da kyau, idanunta ne suka sauka kan Riyad dake zaune kan wata kujera mai kyau one seater, wannan karan babu jacket na suit ajikinshi just white shirt da trouser hannunshi rike da wani file yabude yana karantawa ga pen a hannunshi, faduwa gabanta yafarayi kadan kadan hannunta daya ta daga taga anyi fixing drip hakan yasa ta daga dayan hannun takai saman fuskanta sabida iska dataji yana shiganta da kyau jitayi babu hijabinta kan fusnanta babu dan kwali asaman kanta, hannunta takai saman wuyanta zuwa saman riganta taji an bude boturan saman riganta har zuwa wajen bra Allah yasa tasaka singlet sauke hannun tayi kasa tacikin bargo taji an daga riganta da vex din sama cikinta abude ga hook na wandonta an bude ahaukace ta tashi zaune tawani fincike drip din da aka samata taja bargon sama tana kare kirjinta tai wani irin ihuuu tace “mekamini”? Sauke file din dayake rikedashi yana karantawa yayi kan coffee table dake gabanshi yakalleta tareda sauke soft boyayyen ijiyan zuciya, yazuba mata mayun idanunshi daidai lokacin tufkin gashinta ya warware black silky hair nata yawani irin zubo half ta face nata ragowan ta baya abun just grip his attention dayasa yawani zuba mata idanu kaman tsohon maye kaman akwai wani abu dayake kallo ajikinta, ihu Rashida tayi sosai taja bargon tarufe har wuyanta tace “you pervert Allah ya isa ban yafemaka ba wlh mugu azzalumi kaci amanata ta, wat have you done to me? Dame kai drugging dina? Wani substance kasa aruwan daka bani, sabida kaga kanada kudi idan kasaba yima yan mata haka ana kyaleka wlh akaina you’ve messed with the wrong person bazan taba kyale wanda ya batamin rayuwana ba” gashi takasa tashi sabida yanda aka kwance hook na wandonta daidai lokacin taji an bude kofa dasauri tajuyo idanunta sunyi jazur wata mata tagani very elderly zatakai 45 tafito daga bathroom na dakin rikeda bowl a hannunta tace “young Lady calm down” ta taho wajen da sauri tana ijiye bowl din da Rashida tabi da kallo taga ruwa ne da karamin towel aciki tace “calm down no one did anything you’re sick, your fainted and Mr Riyad called, my name is Dr Amara Kennedy, I’m this hotel’s Doctor, incase of any emergency or anything ni ake kira” tadan sauke ijiyan zuciya tazauna bakin gadon tace “calm down, I came in immediately an kirani, you were running serious temperature dayasa kikai passing out kina convulsing this is the result of your blood test” tai maganan tana mika hannu ta dauki wata paper dake saman drawer gadon hakan yasa itama Rashida da gabanta ke faduwa sosai ta kalli wajen, taga allurai da magunguna daukan takardan tayi tamika mata tace “take a look” matse bargon tayi da wuyanta tasa hannunta dake rawa har lokacin ta karbi takardan tashiga dubawa Dr tace “kinada high typhoid da Maleria, namiki allurai so I got water ina shafa miki ajiki just to get temperature nata to cool down and for Mr Riyad dakika gani he just came in not less than a minute ago yadubaki saina tashi nima after I cover you up naje bathroom dan na zubar da ruwan and get another one” ji tayi hankalinta ya wani irin kwanta saikuma taji kunyan abubuwan data gama fadi, gashi ta gama zage zage kasa kallon wajen dayake tayi ta kalli Dr ahankali tace “I want to go home” Dr tace “I think Mr Riyad arrange driver that will take you home, but I think you need to change sabida” tanuna mata kafanta da idanu tashi Riyad yayi yajuya yafita daga dakin yace “ku sameni awaje” lumshe idanu tayi jin muryanshi tana kara mugun jin kunyan wat she just did.

 Da taimakon Dr ta tashi bayi ta kaita bayan ta dauki gown nata dake jaka she change, kayan kuma ta kulla a Leda tasa ajaka takai gida ta wanke she is feeling better yanzu tareda Dr suka fito waje yana tsaye jikin mota shida Munir suna magana yayi shiru hangosu dayayi har saida Munir yajuyo dan ganin meyake kallo kin karasawa wajen motan tayi tace “I will take keke” kafin Dr tayi magana tayi gate da saurinta tafice duk yana tsaye awajen yana kallonta ta tare keke ta shiga sai kawai yabude bayan motan ya shiga ya zauna Munir kuma yadanyi magana da Dr ya sallameta sannan yadawo ya shiga yaja motan sundanyi nisa kadan Munir yace “in tambayeka mana Riyad?” Dago kanshi Riyad yayi ya kalleshi batare daya bashi amsaba alamun yana jinshi, Munir yace “why do you give that girl special attention?” Shiru yayi yadauke kanshi ya maida kofa yana kallo sai chan yace “do i?” Munir yace “yes on different occasion” wayanshi yaciro daga aljihun gaban riganshi ya shiga dannawa yace “I had no idea” shiru Munir yayi yace “before you hardly come to the hotel cus I always handle it, office kafi zuwa but tun randa ka ganta anan hotel yazama shine latest head office namu, look at dazu when she fainted you took off jacket naka ka rufamata and just picked her up ka kaita sama kahau kiran Dr without assigning me to do that, not to mention dat day datama yarinya duka normal you dakayi sacking nata but bakayiba, saikai sacking wacce akama duka, are you perhaps interested in her? Cus this is beyond she saved my life” Chak ya tsayan da danna wayan dayakeyi ya tsare screen din da ido kawai that moment na dazu na gashinta na zubowa nadawo mishi rabon dayaga breath taking view haka harya manta sai yau, dan fuzar da iska yayi yasa hannu yasauke glass na motan kasa ahankali yace “I’m not interested in her I just find the girl fascinating! She’s a topic!” dan murmushi kadan Munir yasaki yace “okay oo, but wat do you mean by she’s a topic”? Wannan karan shiru Riyad yayi yafi nada chan yace “she’s a topic in my heart that I just feel obligated to study” Riyad ma dan rainin wayone Munir yafadi a zuciya jin yanda yake using english yana sugarcoating the word affection dayake developing for the girl but woo idan tai tsami za’aji ai hakan yasa yace “uhmm topic indeed!”.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

 ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 1️⃣9️⃣


Har kofar gidansu me keke yasauketa tasauka tabiya kudi ta shiga gida, anriga anyi magrib Mama na ganinta tabar kunun datakesha ta taso dasauri tace “yaya jikin ne?” Kin fadama Mama ta suma tayi sabida karta tsorata tace “Mama naji sauki wlh har allura an mini, kinsha ruwa lpy” zaunar da ita Mama tayi tasamata kunu karba tayi tashiga sha still bata da karfi Mama bata wani bari tai aiki ba wanka kawai tabarta tayi tana shiga daki ta kwanta ko kaya bata saka ba sai bacci  washe garin ranan ma ko school bata iya taje ba, bini bini taita tuna abinda tayi tanajin kunya.

Sai jibi ta tashi garau taje school tadawo dayake tagayama Mama a bata off a aiki bataje ba.

Azumi biyar tasha arana na 6 ranan day 7 taje hotel din sai addu’a take karsu hadu cikin ikon Allah bata ganshi ba har azumi yayi nisa basu kara haduwa ba taji sosai dataji wasu ma’aikatansu na cewa Oga umara yaje saisa tunda aka fara azumi baya zuwa itadai ko ajikinta.


Yau saturday morning taje aiki around 2 ta tashi ta shirya ta goya jakanta abaya yau daman hijabi tasaka tunda aka fara ramadan hijabi take sawa hakanan kawai taji kirjinta nata bugawa tana tuna Mama hakan yasa tana shiga keke taciro yar vivo nata ajaka tai dailing number Mama amman harta katse bata dagaba that is so unlike Mama, sake kira tayi shima shiru hakan yasa ta shiga damuwa ko zazzabin Mama yatashi ne?

Abakin junction ta sauka tashigo layin su da kafa tun kafin takai gida ta hango manya manyan motoci guda biyu agaban gidan saikuma taga yaran layi an taru a kofar gidansu some nata fitowa da biscuit da taliya guda guda a hannunsu yanda taji zuciyanta na tafarfasa har sarkakewa numfashinta yake da sauri ta kutsa cikin yaran ta shiga cikin gidan wata babban mace ce tsaye tsakar gidan taci uban lace da duwatsun lace din har kashe ido suke tarike wani arnen jaka a hannunta akalla zatai 45-48yrs gawasu mata haka wanda kana gani ma’aikatan ta ne sun rike kwalin taliya a hannu datake rabama yara ga wani buhun local rice akasan tsakar gidan an yatsar da karamin man gyada a jarka, Mama takalla dake zaune kan tabarma sanye da hijabi abinta duk yanayinta yayi wani irin alamun she’s not happy ganin Rashida yasa tai maza ta gyara fuskanta tace “kin dawo yarinya na”? Daidai lokacin matan ta dago kanta ta zubama Rashida wani kallo, da sauri Rashida tai wajen Mamanta cikeda tsananin so takai hannunta ta taba fuskan Mama tace “Mama did you cry? Sun miki wani abune? Mesa baki kirani ba”? Tai maganan tana daga hijabin Mama tana duba jikinta da hannayenta cikeda so.

Matar dake tsaye tana kallonsu, tawani bushe da dariya tace “akanme zan daki me kanjamau banda yarinta irin naki”? Dasauri Rashida tajuyo da kanta ta kalli matar zatai magana Mama tajuyo da ita yace “tashi mushiga ciki tunda kindawo abincin zakka takawo mana nace mata karta damu mun gode, muje ciki idan tagama rabo saita tafi” Rashida zatai magana matan tace “ke har kinyi darajan korana daga gidanki wulakantacciya irinki me bin maza da aurenta nasunna” zabura Rashida tayi ta tashi Mama ta taso dasauri takama hannunta tace “ke zonan muje daki” wani irin dariya matan tayi tace “naga alama baki bata tarbiya ba saki hannunta dan Allah zan bata tarbiya ni” kama Rashida Mama tayi takomar da ita bayanta tahade hannayenta tace “Hajiya Jummai na rokeki da girman Allah kifitan mini daga gidana stop provoking my daughter, banson hayaniya dan girman Allah kitafi” kallon idanun Rashida tayi yanda take kallonta kaman zata kasheta da idanu to be honest sabida Rashida tazo, Mama batada karfin bala’i kuma banda haka tasan babu abinda Zainab keso aduniya irin yarta Rashida saiso yanzu burinta shine ta nakasa diyar tata itama ta lalata mata rayuwa, da gangan matan ta kalli yaran dasuka cika gidan tace “ku nuna matar nan kuce ke tsohuwar banza me HIV” aiko yaran suka kalli Mama sukace “ke tsohuwar ban…….” Wani fincike kanta da Rashida tayi daga hannun Mama ta taho wlh watsewa yaran nan sukayi dan ansan halinta suka fice daga gidan dagudu, kaman zakanya tawani tsaya agaban matan tanuna mata hanyar zaure tace “ke Jummai fita daga gidan nan tunda bana mijinki bane before I loose my temper” dasauri Mama tazo takama hannun Rashida tace “ke muje” cikeda masifa Rashida tace “Mama ki banni lemme put this useless woman in her place babban banza kawai yar wahala” fizgota ama tayi cikin fushi tace “stop insulting elders” itama Rashida cikin fushi tace “Mama she’s not an elder, waye ita dazata shigo gidanmu ta zageki enough! Yanzu ba da bane, I will protect you Mama, Madam ki fita daga gidan nan and take this trash dakika kawo away we have morethan enough” tafarfasa zuciyan Jummai yake kaman ta chakamata wuka takeji ta nuna kanta tace “ni kika zaga”? Rashida tace “akwai wata kalanki anan ne?” Kallon yan matan dake tare da ita tayi tace “kuma ita da uwarta duka” kambu! Rashida jitayi jikinta yakama da wuta rike ta Mama tayi tasan halinta tace “muje ciki mu rufe kofa Rashida don’t fight them” ganin yan matan biyu sunyo kansu yasa tawani kama Mama ta maida bayanda daidai sunzo suka kakkawo mata duka dunkule hannu tayi ta zubamusu nushi aciki duk sukai ihu kafin tafara dambe dasu sai kawai Mama ta shiga kuka ganin yanda su biyu suka tarunma yarta dudda Rashida nacin ubansu cikin kuka Mama tai gaban Hajiya Jummai tahada hannunta tace “Hajiya Jummai na rokeki da Allah kiyakuri kifita daga rayuwan mu shekaru ashrin da uku munyi zaman kishiyoyi narabu da mijinki tun kafin na haiho Rashida, narabu ashi ko amafarki kinsan bazai kara aurena ba takuran nan ne menene eh?” Daidai lokacin jikake kum kum kum Rashida ta barar dasu duk sun daki bango sun zuzxube kasa a sume goshinsu na jini daga Mama har Hajiya Jumai ihu sukayi Mama tace “Innalillahi wa innailaihi raji’un Rashida me kikeyi”?Mama tai wajen da gudu hankalinta atashe tana tattabasu itakuma Haj Jumai tashiga ciro waya daga jaka tace “shikenan ta kashemin bayi, yarki is a killer she’s a murderer wayyooo jama’a ku taimakeni sun kashemi yan aiki daga mun kawo musu abincin taimako” Jumai tafice waje da gudu tana ihu tana making call before you know it yara da manya an shigo gidansu maza sukai kan matan ana dagosu amman ko motsi basuyi Jumai tashiga nuna Rashida dake tsaye a gefe tace “wlh yau idan Police basu rabamu ba sai nasa kema an kasheki kokuma nakashe uwarki” takama Mama zata kai mari wani irin damke hannunta da Rashida tayi ta murda saida tahau ihuuu bana wasaba mazan duk sun kasa tabata sabida tsoron Rashida itakuma tana ihu Mama najan Rashida amman bataji zuciya yakaimata wuya idanunta sunyi jaaa tace “you keep hurting my Mom tun kafin a haifeni I’m ready to kill you today to die Mama na tahuta” kawai takai hannunta dayan takama wuyanta ta matse gam daidai lokacin saita yar sanda macen dake tare da yan sandan tawani rapkama Rashida kulki a baya hakan yasa tasaketa Mama tafashe da kuka ganin yanda aka rafkama yarta kulku itakuma Jumai da gangan tazube tana haki tace “officer she’s a murderer daga zuwa basu abinci munga mabukata ne shikenan, macen police din tashiga sama hannun Rashidan ankwa tace “you’re under arrest for attempt murder na Hajiya Jummai” sauran yan sandan suka shiga duba sauran sukace sunada rai but they need hospital, kutafi da me laifin” fashewa da kuka sosai Mama tayi tai kneeling tace “dan Allah kuyakuri laifinane niku tafi dani not my daughter she’s a small girl ko aure batayiba dan Allah karku kullemini diya dan Allah” cikin zuciya Rashida tace “Mama stop begging kowa babu Allah cikinsu kitashi Mama, babu wanda ya isa yamin wani abu anan Mama kitashi” macen police din tace “au haka kikace? Kinyi laifi still kina rashin kunya kina taurin kai”? Cikeda dakewa Rashida tace “laifin me nayi kin tambayeni mesukayi min su? Ko nima bakiga jikina da ciwo ba ne it was self defense, kuma garau suke sabida Ogan su tace karsu farfado ne sukai kaman suma I’m a doctor I know idan mutum is unconscious, dukanku are corrupt officers working for this evil woman!” Tassss!! Yar sandan ta dauke Rashida da mari da saida tai tangal tangal zata fadi Mama ta tashi da gudu tai ihuuuu tana tare Rashida, Jumai tai wani murmushi kaman an mata busharan aljanna, tarota da Mama tayi yasa bata fadi ba ta kalli yar sandan da idanunta dasukai jazur kaman zata daketa babu ko alamun hawaye, yar sandan tace “ke me taurin kaiko? Zan gyaramiki zama muje police station wlh saikinyi dana sanin abinda kikayi dahar yasa na kaiki police station” kallon Rank dinta Rashida tayi tace “yar wahala saisa har yau bakikai any matakiba, corrupt evil woman” zata kara kaimata mari dayan dan sandan yace “stop let’s go to police station tarubuta statement, let’s go” wani irin finciketa yar sandan tayi daga hannun Mama sukai gaba da ita Mama tabisu da gudu, yanda suka wurgata bayan motan kaman wacce aka kama da bomb suka ja motan Mama na gudu tana binsu harsaida ta fadi akasa duk Rashida na kallo idanunta sunyi kamar jini ganin yanda mahaifiyarta ke wahala all because of this family gidan Sarautan nan, she hates that house da kowa naciki, duk randa tazama wani abu she will ruin them, they will pay for abinda sukama mahaifiyarta, this woman tazo har gidansu ta wulakanta mata mahaifiya duk all because of kishin jakin mijinta Alhaji Mujitapa Baba Ali! Give Rashida few years! I will come for dukanku! I will ruin all of you and gabaki dayan gidan sarautan saina tarwatsashi!!!.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣0️⃣


Mama na duke a tsakiyan anguwa tana kuka sosai ana kallonta an taru Hajiya Jummai tazo inda take tsugunnawa tayi takai bakinta saitin kunnen Mama tace “mission accomplished! Now watch how I will ruin rayuwar yarki this is just the 1st step, watch and see how zanyi feeding yarki to those hungry police officers, I will make sure sunyi kacha kacha da duk wani abu daya maidata diya mace, barima kiji Amarya na aikamusu yau akwai biki” tawani kwashe da dariya, juyo da kanta Mama tayi ta kalleta irin kallon nan na bakomi akwai Allah sannan tace “nabaki raina ki dauka Jummai, yau kidauki wuka ki sakamin aciki na mutu na yarda, kome kikeso kiyi dani kiyi amman spare yarinya na, she’s a small girl, meta miki? Mijinki dama tun tana ciki yace ba tasa bace haryau ko fuskanta baitaba ganiba to meta miki? She’s not a threat, she’s a small child kulleta a police station will ruin her life, Hajiya Jummai banda kowa sai ita, kiyafema Rashida ni kisa a kulleni” murmushi tayi tace “kinga I hate you with every blood na jikina saisa I want to end you using abinda kikafi komi so, wlh wlh ko kudina zasu kare yau saina tabbatar an yaga yarki a cell, wlh sainasa sun maidata nama, saina tabbatar sun halakar da rayuwanta tass, maybe then na hakura nasa afito da ita kokuma na aikata prison she need to be taught a lesson, ke I will cook her up bazata fito daga cell anytime soon ba, this is for auren Mijina dakikayi!” Tana maganan ta tashi tawuce wajen mota ahankali Mama tajuyo da rinannun idanunta ta kalleta ga mamakin Mama saitaga yan matan sun taso fess da kafansu sun fito sun shiga mota direba sun yatada motan sun tafi, Ahankali Mama ta tashi wani kalan bubbugawa zuciyanta keyi dabai taba mata arayuwanta ba, yan layin sai kallonta suke mata an lalleko daga gida tanaji ana kananun magana ana dama maraji makomarsa kenan anzo baku abinci mu makota mun shaida but yarki tazo tana dukan mutanen arziki ai gashinan tahadu da daidai da ita, gida Mama ta shiga ta tattaro duka kudin dasuke dashi tasan belin mutum da kudi akeyi sunada 80k agida a account din Rashida kuma akwai 100k da aka mata salary na hotel just jiya 50k ake biyanta but sallan nan sai aka basu 100k, sakawa tayi a lalita tasa takalmi tafito ta kulle gidan ta shiga tafiya bama tasan wani police station aka kaita ba, tafiya take a anguwa wasu nacemata Allah kiyaye gaba wasu na Binta da kallo Adamu me chemist ne yafito hangota dayayi dan shi yana mutunci dasu yace “Mama Allah kiyaye gaba ina zaki yanzu”? Bama ta iya magana sai hawaye bakin hijabinta tasa tace “bansani ba duk police station dana gani zan shiga” dasauri yace “ina ganin kije head quarter dan naga babban police car suka zo dashi sabida local street police post ba’a ijiye musu manyan motoci haka, Allah kiyaye gaba”  gyadamai kai tayi ta wuce ta tare keke ta shiga 500 aka kaita headquarters.

Sauka tayi tashiga ciki ta tafi chan gaban kanta yan sanda dake wajen sukace “lafiya Hajiya” baki Mama tabude zatai magana sai kuka matar tace “Hajiya dan Allah kifita ki gama kukan saiki dawo” dasauri dayan dan sandan yace “mehaka Grace? Mama lafiya calm down meya faru fadamana”? Da kyar ta tsagaita kukan tace “y’ata wasu yan sanda suka kama kusan minti talatin kenan bansan inda aka kaitaba yan anguwan mu since nazo nan headquarter” mutumin yace “ya sunan diyar taki”? Ahankali tace “Rashida Almustapha” log book dake gabansu yaduba yaga sunanta kafin yayi magana Grace tace “banan aka kawota ba kije wani police station din” kallon Matan Mama tayi saikuma ta kalli wanda ke attending to her ahankali yace “Mama je waje ki zauna ina zuwa” fita waje Mama tayi tasami waje ta zauna, kirjinta bugawa yake like never before ga azumi abakinta wlh kusan 2hrs tai spending awajen dan har 5 tayi sannan yafito yazo wajenta yace “zo gefe Mama” Dasauri Mama tabishi ahankali yace “Mama bansanki ba amman kin bani tausayi wlh tuntuni sai bin office daban daban nake ama barki kiga diyarki sunki, wai yaran data daka suna ICU, sannan she attacked officer mu wata and abuse her” cikeda tashin hankali Mama tace “wlh wlh karyane sherine agabana yaran suna shiga mota da kafansu basa ICU, kuma wlh Rashida bata taba police dinba” ahankali yace “to yanzu dai  bani dubu goma zan taimakeki da kyau koda yarki zata kwana zansa ido akanta kar acutar da ita” fashewa da kuka Mama tayi tana tura hannu alalita ta kirgo 10k tabashi ya karba yace “bari kiji Mama the truth is powerful mutane sukasa aka kulle miki yarinya dan haka yanzu dai idan kinada wani babba haka kije kitaho dashi ko za’a miki alfarma abaki belinta inba hakaba wlh bazama kisan yarki na nan ba ninedai nafada miki” yanda Mama ke kuka sai yataba zuciyanka tace “wanake dashi? Banda kowa sai Allah ni” dan sandan yace “nidai nayi miki iya nawa kije ko waye kisamo, suna ganin kalan kudi ajikinsa zasu badata, bari nakoma ciki kada anemeni” wucewa yayi yakoma ciki yabar Mama wajen tsaye shiru Mama tayi saikuma ta daga idanunta takalli sama irin kallon Ya Allah kana ganin komeke faruwa sannan tasa bakin hijabinta tashiga tafiya tawuce gate kafanta yayi butu butu da hijabinta ma sabida zaman kasa datayi sai tunani take ina zata shagon Mama miwa tane tunda tanada kudi but tace baruwanta da police station bata zuwa, Rashida tafada mata tace taji ance Riyad na Umara saisa batai tunaninsa ba.


Bari taje ta gwada yima manager magana kozata taimaketa gashi Baba Liman yaje kauyensu shima duba gona, adaidaita tasake shiga ta tafi hotel din hanyar shiga taje yauma wasu security daban ne dana ranan suna ganinta sukace “ina zaki”? Arude Mama tace “manager zan gani” wani kallo suka mata daga sama har kasa sannan sukace jira anan daya yashiga ciki yama manager magana tafito daga office nata hango Mama tayi daga glass door tace “I don’t know her, please send her away yau banda lokacin all this beggars I’m very busy” takoma office security yafita yaje inda Mama take tsaye yace “batanan” tsayawa Mama tayi tana kallonshi yanda taji kaman jiri na neman dibanta batasan sanda ta duka ba saitahau kiran sunan Allah. “Allahumma ajirni fi musibati……Innalillahi wa innailaihi raji’un, Ya Allah kadubi yarinyana dake cikin cell kar awani abu yasameta please karsu cimma burinsu” tashi tayi tana taba bango kawai kaman kanta ya kwance takeji cus batada hope kuma yanzu sai magana take ita kadai. “Rashida na is scared, yarinyana bata taba zuwa police station bama, yanzu tanachan locked up a cell an ciremata slippers, an karbe komi nata, hala ana azabtar da itama, idan suka batama mata rayuwa fa, wat if they rape her? My poor baby must be so scared yanzu, yarinyana batada kowa aduniya sai ni, wat are they doing to my child right now……….” Diiiiiiiiiiiiii! Taji karan ana daddanna mata car horn dayasa kawai ta birkice hannunuwanta tadaura saman kunne ta kulle idanunta kawai tahau juwajuwa akan titi go slow kawai yahadu bama tasan meke faruwa ba,  “Mamaa!” Taji an kira sunanta da karfi dasauri tabude idanunta dasukai jazur, Riyad tagani tsaye agabanta yana sanye da farin shadda datasha aiki kanshi da kula ganinshi kawai saita fashe da kuka sosai ahankali yasa hannunshi yasauke hannayenta daga saman kunne ganin she’s not herself yakama hannuwanta duka biyun sukabar tsakiyan titi zuwa motanshi yabude baya yasata shima yashiga bayan wani bodyguard dake tukanshi yaja motan suka gangara gefen hanya yayi parking, Riyad dake kallonta yace “Mama menene? Why are you in the middle of road”? Bakinta rawa yake ta birkice kawai tace “Riyad…….Riyad…….Riyad” hannunta yakama ahankali yace “get me water” fita direban yayi anatse Riyad yace “Mama calm down I’m here now, calm down everything will be fine, calm down Mama kinji” bakinta is still calling name nashi, ahankali yace kice “Innalillahi Wa Innailaihi Raji’un” ahankali Mama tace “Innalillahi wa innailaihi raji’un” dan natsuwa tasamu kadan daidai lokacin an kawo ruwan budewa yayi yabata tasha kadan sannan yace “wat happen Mama”? Fashewa da kuka tayi tace “tasa an kamamin yarinya an kulle a police station” anatse yace “wace”? “Kishiyata wacce mukai zaman aure tare kafin mijinmu ya koreni”? “Wat happened Mama”? Labari Mama tabashi tundaga time datazo gidan da time da Rashida ta shigo, da all abinda yafaru da duka abinda tagayama Mama na zatai feeding Rashida to yan sanda” jiyayi ranshi yayi tsananin baci, “drive” yafadi ahankali yama Munir text dan daga gidansu zuwa head quarter is even closer than daga nan hotel zuwa wajen.


Wajajen magrib sukakai police headquarter ya kalli Mama yace “Mama ki zauna anan zan fito da ita kinji” gyadamai kai Mama tayi ya kalli security yace “make sure she stays in the car she’s not feeling well” “yes sir” ya amsa yana fita yaga Munir yafito daga tashi motar ga sauran bodyguard nashi yayi gaba kawai Munir da guards nashi na binshi abaya, all eyes yadawo on them ko kallon yan sandan wajen baiyiba yawuce sama direct zuwa office  na inspector cus yasanshi sosai yana kawo gaisuwa fada dudda bai sanshi babu rawani ba, kai tsaye yabude kofan ba knocking babu komi Inspector na zaune yana dube duba, da zafi sosai an anger kan muryan Riyad yace “I will sue you and I will sue the entire police headquarters for rashin adalci for tauye hakkin talaka, for rashin yin investigation, I will make sure anyi sacking all of you anyi replacing naku with better and eloquent officers dasuka shirya yin aikinsu yanda yakamata” from yanda yake magana kadai yasa gaban Inspector yashiga faduwa yama kasa magana, Munir yace “you must be confuse kana magana da Mai Martaba SARKI RIYAD! Sarki mai adalci, sarkin talakawa” wani kalan tashi inspector yace “an gaida Mai Martaba Allah huci zuciya ka, tub……” hannu Riyad yadagamai yace “release Miss Rashida Almustapha, and nabaka 24hrs kuyi realeasing evidence cewa yaran data daka suna ICU with Doctors report and everything, and again inaso kuyi proving cewa she’s really a killer, banda haka I want to know wat right that officer takedashi to slap and hit Miss Rashida, and again wanda aka bishi har gida shine akaje neman tsokana, prove all this ba set up bane inba hakaba” Munir yace “zaku hadu da bacin ran Mai Martaba” baki Inspector yabude zaiyi magana Riyad yadagamai hannu for the second time yadakamai tsawa sabida yanda ranshi yake abace yace “release her now!!!!” Shi kanshi Munir saida ya kalli Riyad rabon dayaga dan uwanshi yayi fushi haka harya manta, da wuya Riyad yayi fushi, jikinshi har rawa Inspector yake yafita dasauri shi baimasan case din ba duk suka bishi yawuce kasa Riyad na biyedashi yadauki key na kofan da ake budewa a shiga bangaren cell nasu yabude kofan da sauri ya shiga saikuma ya juyo yace “Allah taimaki ranka shi dade ban santa ba ita yarinyar” wuceshi Riyad yayi kawai yashiga ciki mutumin ya bishi abaya cell cell ne daban daban, na mata daban na maza daban but duka ajere suke, ga mutane kukkule amman baiga Rashida ba in any of cell na mata dasuka wuce ba,  zagawa dashi Inspector yayi zuwa cell masu kama dana kaji ana kiran dakunan NO SS CELL wato no sitting no standing cell, wanda shi na punishment ne bazaka iya tsayuwa ba bazaka iya zama ba kana duke kawai idan anaso a azabtar dakai ake kaika wajen, hangota Riyad yayi ita kadai an rufeta a cell dayakenan kaman cell din dan buri alalo alalo gwanin ban tausayi she looks very very miserable and terrible ko kadan bata kallo inda suke ba danta dauka matarce tadawo, ahankali Inspector da gabanshi ke faduwa ganin ita kadai ce abarayin NO SS yace “itace naga kana kallonta”? Juyo da kanta Rasheeda tayi jin datayi anyi magana tunda ta shigo wajen sai yanzu taga haske hasken Riyad dake tsaye yana kallonta idanunshi sun chanza launi kallo yake mata dabazaka iya tantance na menene ba, ahankali yake kallonta even though she’s not crying but kasan she’s very very scared, she’s terrified, she’s lonely, she’s afraid, dauke kanta tayi daga kallonshi da sauri tashiga wasa da fingers nata, bude kofan Inspector yayi yace “fito” kokarin motsi tayi da kafa amman takasa sabida yanda kafafunta suka sankare suka rike sai kawai Riyad yaji zuciyanshi ta tsinke awani irin hankali yafara tafiya dudda bata kallonshi but every step nashi tana jinshi har a bangon zuciyanta, ahankali azo gaban cell din ya tsaya chak still taki dago da kanta, yakai wajen 10secs yana kallonta kafin awani irin hankali yaciro hannunshi daga aljihu yamika mata cikin wani irin murya mai masifan taushi yace “Rasheedah!” Har kasan zuciyanta taji yanda yakirata hakan yasa tadago kanta takalleshi sannan takalli hannunshi dayake mika mata batare data karbi hannunba, ahankali yace “come Mama is waiting” dasauri ta kalli fuskanshi kafin awani irin hankali takai hannunta tadaura gently kaman mai tsoro cikin nashi, atare dukansu sukaji shock amman yadaure yakamata sannan ya fizgota tashi daya tafado kirjinshi making deep sound mara kara sosai dazai nuna how hurt she’s, kafafun na mata ciwo sosai amman sabida dauriya da taurin rai taki nunawa but takasa motsi tana kirjinshi, dan sauke kai Inspector yayi aranshi yace “budurwan mai martaba muka kulle dama? Suwaye keson sani a bala’i” takai one minute a kirjinshi batare daya taba bayanta ba banda hannunta daya rike but ita takasa motsa kafan tafita daga kirjinshi, in a very caring tone dabama tasan yanada shi ba yace “can you walk now”? Duk yanda taso karta kalleshi kasawa tayi tana kirjinshi tadaga fuskanta takalleshi hada idanu sukayi cikeda tsananin kulawa yace “can you walk yanzu?” Very soft itama ta gyadamai kai tana yunkurin fita daga kirjinshi, saitai baya zata fadi dasauri yakai hannunshi daya yakama waist nata sai kawai adake yakama hannunta daya yakai ta bayan kanshi ya ijiye yayi supporting nata dakyau kafin yace “let’s go” she’s scared internally, she’s shaking bamata da karfin wani abu so she just followed him tana dan dingishi suka fito ahaka.


Hannu yasa yabude kofa mutanen data gani awajan da yawa gasu police gawasu kaman bodyguard ga Munir datake gani a hotel nasu ga yan sanda maza biyu na dazu bataga macen ba yasa tadan yunkura cikeda karfin hali zata fita daga jikinshi kaman daga sama taji saukan hannunshi akan waist nata yamaidata side nashi da kyau dawani irin sauri tadan juyo da kanta ta kalleshi but fuskanshi is looking straight bayako kallonta yacigaba da tafiya da ita hakan yasa ahankali ta maida kanta kasa daidai sunzo kofan fita saiga yar sandan dazu tana shigowa itama suka hada ido wani abu Rashida taji yazo mata wuya ya tsaya duk kalan ciwon da kafanta ke mata amman saida taji tasami karfin daga kafan kawai takai ta kwasheta within a blink of an eye jikake tippptipp! Officer tai wani mummunan faduwa danko ita bata lura da kafan da Rashida tasamata ba dan fuskan Rashidan take kallo dana Riyad datagani tareda ita, da all the people dake wajen,  yan sandan sukai kanta ganin kalan faduwan datayi ana “lafiya kika fadi haka sannu me kike kallo haka” dan babu wanda ya lura da abinda Rashida tayi dagowa officer tayi hancinta na jini ta kallo kofan hada ido tayi da Rashida dake mata kallon munyi settling score dake, tsayawa shima Riyad yayi yana kallon Rashidan cus he saw wat she did saikuma kawai yacigaba da tafiya da ita suka fice har wajen motan shi su Munir suka biyosu baya yabude baya Mama idanunta harsun kumbura na zaune taganshi da Rashida dataga har yar rama tayi, sai kawai Mama tafashe da kuka jikin Rashida yayi mugun sanyi da taimakonshi ta shiga bayan motan sai kawai ta rungume Mama dan jim yayi yana kallonsu kafin ya maida kofan bayan yarufe yajuyo yadan taka zuwa wajensu Munir dake kallonshi kallon what is going on, anatse yace “I will see you at home bari na kaisu gida” bai jira amsan Munir ba yajuya yawuce saiya shiga gaba direban yatada motan yaja har lokacin Mama kuka take wlh takasa magana ma, hakuri take ta bama Mama amman yana shigowa tayi shiru kawai dai ta rungumeta agaban wani pharmacy yasa aka tsaya yafita yashiga yakai kusan 10min aciki yafito rikeda leda yadawo ciki ya zauna aka tada motan har zuwa anguwan su parking yayi yabude gaban motan yafito yabude bangaren Mama ahankali Rashida tasaketa goge fuskanta tayi ta sauko sannan ta mikama Rashidan hannu tace “taho muje” cike da karfin hali ganin yana wajen yasa tace “ni zan iya fita dakaina” tsayawa Mama tayi tana kallonta irin kallon wani irin taurin kai da karfin hali Rashida kedashi ne, shima Riyad folding hannunshi yayi a kirji ya tsaya kawai suna kallonta jan jiki tayi har tazo bakin kofan ahankali ta daga kafa daya tafito hakama dayan sannan ta yunkura ta tashi dudda she’s not showing the pain a fuskanta but wlh kasan da kyar take komi takawa tashigayi ahankali sai kawai tawuce tai zaure da dafa bango ta shige cikin gida, Mama tabiyota abaya tana shiga rabin buhun shinkafar taci karo dashi a tsakar gidan nasu jitayi zuciyanta kawai yarikice ranta yabaci tama manta tanada ciwo kawai tai wajen shinkafan azuciye ta daga shinkafan zata mike kafanta yayi wani irin kara da duk dauriyanta saida tai ihu daidai lokacin Riyad ya shigo gidan azuciye yayi wajen yasa hannu ya fizge buhun shinkafan yayi ihu yace “what is your problem?” Kallonshi tayi ido cikin ido tace “mezamuyi da shinkafarsu? Zubarwa zany…….” “Quiet!” Riyad ya daka mata tsawa da saida taji jikinta yayi rawa, cikin tsananin fushi ya nuna Mama datake rabe a bangon zaure kawai ta tsaya chak tana kallon yarinyar tata gwanin ban tausayi, irin kallon yaya zanyi da wannan yarinyar ya Allah, yace “can you give your Mom just a minute of peace?” Kallon Mama tayi saikuma ta kalleshi zata bude baki authoritatively Riyad yace “I said quiet!” Cikin kwayar idanunshi ta kalla the anger datake gani da fushi kawai saitaji takasa magana wani bai taba shutting nata up in her life ba sai yau, cikeda tsananin bacin rai yace “kina tunanin komi arayuwan nan you settle it da fada da duka you think is by fighting?” Yasake shiru saikuma ya lumshe idanu tareda fuzar da iska yasake kallonta yace “every action have consequences do you for once sit down kiyi tunanin waye ke suffering consequences na action naki?” Yadan mata ihu kadan still kallonshi take da manyan idanun nan nata, saiya sake nuna Mama dake tsaye looking at them tana goge hawaye da bayan hijabi yace “do you have slight idea of abinda Mamanki went through today? Did you even know an ina naganta?” Yasakeyin shiru saikuma a sanyaye yet da tsaurin harshe yace “do you even love your mother?” Wani kallo datamai har saida idanunta sukahau sparking sabida anger kaman zata rufeshi da duka, cikin fushi tace “kai waye dazaka tambayeni ko inason mahaifiyata, waye kai”? Cikin tsatsauran murya Mama tace “tamaka rashin kunya ka yanka mata mari Riyad!”.


RASHIDA IS STUBBORN CUS WATT🔥

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣1️⃣


Kallon Mama Rashida tayi zuciyanta yafara tsinkewa ganin shi Mama take supporting tabude baki zatai magana saitaji kuka na son subuce mata hakan yasa tarike maganan da kyar ta danne kukan tace “to sai in tsaya ina kallo ana zagin Mamana”? Rai abace Riyad yasa hannu a lips nashi yace “shush” abu taji yazo mata wuya wayeshi dahar zai dinga mata fada agidansu kuma Mama na supporting nashi sai kace wani Yayanta, dauke kai tayi daga kallonshi tana huci kaman damusa yace “zagi baya kari, zagi baya chanza fatan mutum, you are a very selfish girl that care about feelings nata not her mother” wannan karan juyo da kanta tayi ta kalleshi idanunta sun ciko da hawaye amman tahanasu zubowa shima yana kallonta kyar yace “duk yaron daya gwammace yabi zuciyanshi dayabi maganan Mamanshi is selfish! Your mother is sick! Anything daya shafeki affects her greatly, akanme bazakiyi hakuri ba just for her safety and wellbeing huhh? And kince kinason Maman ki? Your are just a terrible selfish daughter wacce ta damu da ego nata not her mother” shima yayi maganan idanunsa na ja Mama kawai kallonsu take bata tabajin tanason Riyad kaman yanda taji tana sonshi ba yau, cikin fushi yace “your Mom nada BP very high BP, kwanciyan hankali takeso but kullum cikin tashin hankali take sabida ke! Kullum fitinan ta kike da fitinu daban daban do you want to kill her?” Daidainan hawaye ya zubo sharr daga idanunta da sauri ta dauke kanta tasa bayan hannu ta share, cikeda fada yace “I saw your Mom at the middle of titi bamatasan metakeyi ba she was panicking calling your name, yarinyana! Y’ata, da kinfito daga police station kinga ta mutu fa?” Takawa yayi zuwa inda take facing ya tsaya chak agabanta adake hakan yasa ta kalleshi da rinannun idanunta ya nuna mata yatsu cikeda wulakanci 👉🏻 yace “take this as your last and final warning, idan kika kara troubling Mama zanzo I will take her away from you na kaita inda za’ayi cherishing nata forever, sannan abata peace of mind data rasa daga wajenki, I dare you ki kara trying wani nonsense hali dazai tadama Maman ki hankali saina sabamiki you selfish egotistic girl!!” Yana maganan yajuya zuwa inda Mama take a zaure cikeda so yace “muje Mama” juyo da kanta tayi ta kallesu abunda taji tuntuni yana wuyanta kawai taji yazo mata baki da sauri tajuya tashiga daki tawuce uwardaka sai kuka taji kawai ta tsani Riyad, kishi yakamata yanda Mama kaman tafisonshi sama da ita, he’s making her look like a bad daughter.


Zaunar da Mama yayi akan tabarma sai ya zauna a gefenta yace “Mama kidena damuwa kinji she’s fine babu abinda yasameta, itakuma Matan zansa anemota she will pay for abinda ta muku” dasauri Mama ta girgizamai kai tace “Riyad tunda ka karbomin Rashida kabar mutanen nan da halinsu duk inda kake tunani sun wuce haka I don’t want to involve you a matsalanmu this people are terrible and very powerful banso sumaka wani abu, kamin alkawari bazakasa anemota ba, kabarta da halinta, karma ka koma police station din, bawai koda yaushe take damunmu ba, rabonta da gidan nan kusan 5yrs ago sai yau datazo maybe sai nan da another 5yrs kuma zata kara zuwa, banson wani tashin hankalin banson damuwa, banda ma karfin zuwa police station bada statement, haka kuma banso Rashida taje police station wazai aureta? It will ruin her life? Cell din nan kadai yanzu ma yayi ruining life nata yan anguwan nan babu inda bazasukai labarin ba, I’m tired of all this, I keep causing pain arayuwanta, nice darkness na rayuwanta, nasan Rashida bataji she’s stubborn but she became like this sabida ni, no body wants to be friends da ita, no body wants to marry her, koyaya wani yazo nemanta Sheri da gaskiya sai yan layin nan sun tara sun fada akanta yanzu kuma dataje cell we are ruin gabaki daya” Mama ta share kwallan daya zubomata saikuma tadaga kai ta kalli Riyad da fuskanshi yayi kaman zaiyi kuka tace “Riyad kamin komi arayuwan nan wanda har dan uwana na jini bemin ba, thank you for everything, thank you for saving my daughter’s life, nagode Riyad kaji, but don’t involve kanka in our personal family issues is not worth it, babu amfanin shiga 23yrs of matsala kana shiga zata dawo sabuwa I hope you understand”? Shiru yayi sai chan ya gyadama Mama kai yace “I understand Mama nabar case din but duk randa tasake zuwa I won’t spare her” murmushi Mama tamai tace “tashi kaje gida kaima ka huta gobe salla, kasha ruwa Allah maka Albarka” wlh har cikin ranshi he’s feeling very attached to Mama kaman karya barta ahaka amman yadaure ledan Pharmacy dake aljihunshi yaciro yabata yace “gashi Mama na kafanta ne” yayi maganan yana tashi yace “saida safe Mama” kallonshi kawai Mama take cikeda kauna tace “saida safe Riyad ayi salla lafiya” sannan takalli ledan pharmacy din tana tuna yanda yama Rashida fada yanzun nan saikuma tai murmushi.



Gyara zama Mama tayi tai shiru ita kadai awajen Allah kadai yasan tunani tunanin metake bini bini tasa hannu ta share hawayenta dayake zubomata, ruwan dabatasha kenan ba, har wajen 12 na dare ita kadai, sannan ta tashi da kyar tawuce tayo alwala kanta kaman zai cire tashiga daki tadauki pure water tasha sannan tahau dadduma azaune tai sallan tana idarwa tashiga uwardaka akasa taga Rashida na bacci ko hijabi bata cireba tsabagen fitina, zama tayi wajen ta yaye skirt na jikinta tadauki ledan ta ciro man shafawan daya siyo Mama tai shiru tana kallo saikuma ta kalli fuskan Rashidan ahankali tace “stop this madness and see Riyad Rashida, is because you’re hurt abin yakara batamai rai yake miki fada not just sabida ni kadai” dan murmushi kadan Mama tayi tace “he’s romantic” saikuma takai hannunta saman bakinta kaman mainin kunya tace “ke Zainabu” budewa tayi ta lakato ta shafa mata maganin a kafafunta sannan ta ijiye maganin saikuma tai tagumi tana kallonta addu’a kawai take Allah yarage mata zafin zuciya da yawan fushi din nan kar watarana fushi yasa tai kisan kai yanda ta watsar da matan nan biyu dazu ga jini a goshinsu Mama ta girgiza ainun batasan Rashida tayi nisa hakaba. 


Har asuba tayi Mama bata kulle idanu da sunan bacci ba.


Ahankali tabude idanunta jin an tabata ganin Mama sanye da hijabi tai alwala yasa ta tashi zaune da sauri ahankali tace “Mama” kallonta Mama tayi saitai shiru bata amsaba kaman irin da abin ta kwana hakan yasa tafashe da kuka mai karfi tace “Mama dan Allah kiyakuri ki yafemin bazan kara miki rashin ji ba, kome kikace nayi zanyi, Mama everything is my fault, danaji maganan ki dakikace nabari nabarsu munshiga dakin da duk haka bai faru ba, Mama da mota ya kadeki dame zan gayama Allah”? Yanda take kuka wlh saita baka tausayi Mama taso yau ta shareta Amman saitaji bazata iyaba saita zauna tace “kimin shiru” tsagaita kukan tayi tana kallon Mama da rinannun idanunta, ahankali Mama tace “yawan fushi nasa kai abu da dama dazakai nadama Doctor” cikin raunin murya tace “Mama u hate that woman, I hate mijinta, I hate entire family nasu, those people made you suffer all your life har yanzu kuma basu barkıba” Mama na kallonta tace “idan zaki bimin hakki na ne then kiyi focusing a school, ki gama school ki zama wani abu, ki nuna musu cewa Mamanki dasuka wulakanta ta haifoki diya me albarka me goshi, ki zama Dr tukunna and cure me kinji kidena fada da mutane akaina focus on goal naki nan gaba na warke no body can troll me right”? Gyadama Mama kai tayi Mama tace “bansan ko zamuyi rayuwa tare har karshe ba babu wanda yasan gobe ke babu wanda yasan anjima ma, idan bana raye kikai wani abu who will protect you and stand by you? Ayau dudda banda wani abu but at least I use strength dina na shiga gari ina neman wanda zai taimakeni ya tsayama diyata but randa bananan fa? Who will fight for you and stand by you? Lokaci yayi dazaki bar halin nan, ke kadai gareni kene komi nawa if something happens to you I die, jiya I was so scared…..” saikuma tafashe da kuka dayasa Rashida ta rungume Mamanta da gudu tace “Mama it’s okay bazan kara ba kinji, I’m here now I’m fine kinga kafan ma naji ya warke tass” ta shilla kafan sama Mama tace “maganin da Riyad ya siyamiki ne” haderai tayi da sauri tace “Mama wlh na tsaneshi baida kirki niyake gayama zai rabaki dani yana kirana selfish daughter” ahankali Mama tace “he did the right thing, kuma kika dameni zan bishi dagaske, Allah yamai albarka daya miki fada, naji dadi da akwai wanda zai iya miki fada haka kiyi shiru dan gani kike kaman kinfi karfin kowa” tashi tayi sabida bataso tace wani abu tasake batama Mama rai kawai tawuce tafita.


Alwala tayo sai yanzu ma ta Tuna ki ruwa batasha ba jiya to waka yasha? Har Mama ma batasha ba Tana salla tafita tea tahada musu sukasha sannan takaima Mama ruwan wanka tadawo tadawo ta gyara gidan ciki da waje tsaf Mama tace “zoki wanka karmu rasa sallan idi idan muka dawo mayi girki”.

Wanka awuce tayo tadawo atampanta na salla data karbo fara wajen dinki ta warware skirt da riga ne blue pink atampa ne tasaka da sabon bra da pant tayi kyau sosai dudda batai lalle ba daman jiya sukace zasuyi but Allah bai nufa ba, ta daura dan kwali Mama tace “zauna kisa kwalli ki shafa jan baki kodan darajan yau salla” batai musu ba tazauna tajawo basket na kayan kwalliya tadauki kwalli tasaka tadau wani pink tsohon jan bakinta ta shafa ta gyara gashinta wanda shi ta wanke abayi yanzu da safen nan ta shafa mai ta taje tai parking sannan ta daura dan kwali ta fesa turare ta tashi sai Mama dake kokarin sa hijabi tabita da kallo batasan lokacin datace “tubarkallah Allah ubangiji ya nunamin aurenki haka kici gayu kısa kayan amare” turo baki tayi taki amsawa tadauki pink hijabin data dinko na salla tasaka ta dauki dadduman su da yar wayanta suka fito rufe gidan sukayi da kafa sukaje masallacin ana salla ana kaiwa sujud Mama tashiga rokon Allah yabama Rashida mijin dazai sota ya tsaya mata yakuma kula da ita, sallamewa akayi suka wuce kasuwa kaji guda biyu suka sayo da kayan Miya da fulawa dasu butter sannan suka shigo keke suka tafi gida suna dawowa ta shiga kiciniyar hada gawayi dan daura abinci ganin gawayinsu saura kadan gashi tasa abinci a wuta yasa tarike kudi a hannu tawuce zaure dan neman yaro ta aika makotansu yakawo mata gawayi, tana sakai awaje karaf suka hada ido da Riyad daya bude kofa yafito daga cikin mota yana sanye da manyan kaya da babban riga da hula bugawa kirjinta yayi sabida yanda yayi kyau na bala’i, sai kawai ta tsaya chak ita takasa komawa ciki ita takasa motsi ita takasa daina kallonshi, har saida shi yadauke kanshi daga kallonta akufule yace “kifito yan duniya suga kwalliyan sallan da kyau!” Runtse idanu yayi dan baisan ya akayi maganan tafito daga bakinshi ba, saikuma yahade giran sama da kasa yajuyo yamata wani irin kallon da kawai taji tajuya da sauri takoma cikin gida kirjinta na bugawa dim dim dim chan sai ga sallaman yaro yashigo da kwalin kaji yace “gashi wai inji Riyad aba Mama” afadace Rashida tace “Kai maidamai kace batanan” yaron yace “ai yashiga mota yatafi” ranta taji yabaci daga daki Mama tace “ijiye zo ga tukuici” dasauri yaron ya nuna new 1k note dake hannunshi yace “ai yabani dubu daya” yajuya yafita abinshi, hijabi Rashida ta dauka tasaka tafita ganin bayanan yasa ta shiga makota tasayo gawayi tana dawowa taga Mama tacire just 3 acikin kajin da an gyara but ba’a yayyanka ba tace “dauka sauran kikai gidan Baba Liman kice kawo mana akayi karsuki karba” batai musu ba ta dauka tawuce takai a zaure tahadu da Liman yace “jiya naje kauye saida nadawo naji abinda yafaru Allah kiyaye gaba ki gayama Mamanki zan shigo anjima da yamma” gyadamai kai tayi tawuce ta koma gida lafiyayyen girki tayi tai dambun naman kaza ta soya some tai pepper chicken da some, tai jellof rice tai cincin around 4 tagama komi ta shiga daki ganin Mama duk bata wani cicciba yasa tace “Mama baki ciba” ahankali Mama tace “kaina kedan ciwo anjima ya sauka zan sha” kallon Mama tayi saikuma ta zauna kusada ita tace “Mama kedai sabida ina chan ina aiki ne yasa bakiciba, bude bakinki kiga” ta deba rice din takai bakinta dan murmushi Mama tayi tabude ta karba just to make her smile ta yarda taci amman ko taste bataji na abincin ba.

Har isha’i hira sukeyi around 9 tai bacci awajen Mama tabita da kallo sannan ta lallaba ta mike tana dafa bango kujera ta dauka da buta tawuce chan bakin makwarara amai ta kwara sai ijiyan zuciya takeyi ta wanke fuska tadawo daki kafafunta ta kalla da tun dazu da rana sai zugi suke mata gashi ta lura sunata kumbura, yanzu ma sun karu sai kawai ta zauna tai tagumi tana kallon Rashida damuwa da fargabanta data shigane yasa kawai taji jikinta yanaso  ya rikice haryakai ga abinci ma bataso, tunani take, takasa manta maganan Jummai, dudda tahana Riyad karyay involving kansa a case din tasan yanda aka ciro Rasheedan nan that woman will find a way ta cutar da Rashida Alkawari ne wannan! She’s just scared for yarta, idan tafita school aka dauketa fa? Idan aka halakata fa? Idan tasa akama Rashida wani abu fa? Wat if she set Rashida up yanzu ta yanda zata tura mata yarinya prison inda ko Riyad bazai iya cirota ba, abinda ke kara firgitata is zuciyan Rashida just like yanda tazo jiya ta takali Rashida and she fell for it still haka zata karayi Rashida kuma ba hakuri taje tai wani abu shikenan akamata akai prison with concrete evidence. Yaya zatai protecting Rashida? Kodai su saida gidan su koma kauyensu dudda Kawu ya koreta ada dasuka je? But makarantan Rashida fa, itafa asibiti fa, auren Rashida fa? Riyad fa? Batama Rashida kwadayi tai auren kauye, tanaso diyarta tazama wata babba aduniya, but idan matan nan ta turo maza suka dauke Rashida sukai amfani da itafa suka lalata mata rayuwa tunda dai burinta na police station bai yuwuba, tayaya zata kare yarta? Dudda Rashida akwai karfi akwai zuciya but maza maza ne! Idan akai kidanapping Rashida yanzu yaya zatayi? Tunani daban daban take sai kawai jikinta yasake rikicewa har aka kira asuba yau takasa tashi tana wajen zaune tana kallon yarta,har Rashida ta farka da kanta tabude ido taga Mama murmushi tayi tai mika ta tashi tace “Mama baki tadani ba sabida ba aiki ko” gari yawaye Mama banyi salla ba”.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣2️⃣


Dasauri ta tashi tafice alwala tayo tashigo agurguje tasa hijabi ta tada salla tana sallamewa daganan kan daduman ta hango kafan Mama yanda suka kumbura suntum dawani irin sauri ta taso tazo wajen tace “innalillahi” dan yatsa tasa ya nitse akafan yanda jikin Rashida yahau rawa saida ta tsorata tace “Ma…..m” tama kasa magana tsabagen yanda zuciyanta ke bugawa saikuma ta juya a haukace zata fita daga dakin hijabin dake jikinta Mama takama hakan yasa da sauri tajuyo saikuma ta duka, ahankali Mama da bakinta baya motsi sosai tace “kaini nai fitsari nai alwala nai salla” gyadamata kai Rashida tayi da sauri tace “to Mama” tawuce tafita takai ruwa bayinsu sannan tadawo daukan Mama tayi ta dagata Mama ta tashi kafan natama nitsewa yake dasauri Rashida ta zaunar da ita tace “Mama  tsaya nakawo po kiyi fitsarin adaki namiki alwala” ta zaunar da ita tacire hijabin ta ijiye tafice taje chan hanyan bayi ta dauko po ta wanke tadawo dakin da taimakonta Mama tayi tai tsarki tadauko tafito tadawo ta goge wajen tass sannan tamata alwala ta daura ta kan dadduma dantai salla hannunta Mama takama tamata murmushi tace “relax babu abinda zai sameni daga hannunki inajin yanda zuciyanki ke bugawa” kallonta Rashida tayi idanunta sun cika da hawaye baki tabude zatai magana saita kasa tafashe da kuka tace “Mama wlh ina sonki Mama, Mama kene rayuwana gabaki daya Mama kiyakuri kiji sauki I know damuwana yasa BP ki yatashi bare naje nakira Musa yaron Baba Liman ya kaimu asibiti, Mama kiyafemin wlh wlh wlh bazan kara saki magana ba, Mama kina cewa nabari nabari kinji Mama wlh na rantse da Allah” dayan hannunta Mama takai saman fuskanta ta goge hawayen dasuka zubo ahankali Mama tace “come” matso da fuskanta tayi kiss Mama tamata a goshi muryanta chan kasa tace “I love you Rashida remember this always konai fushi dake bahar zuciyata bane kinji, stop crying I will be fine muje asibitin jeki kira Musa” tai maganan tana kara goge mata fuskan tass tashi Rashida tayi tadauki hijabinta tafice daga gidan, gidan Baba Liman tawuce a kofar gidama taganshi ganinta yasa kafin tamayi magana yace “lafiya?” Ahankali tace “Musa nazo kira yakaimu asibiti jikin Mama yatashi” ahankali Baba Liman yace “Subhanallahi Allah yabata lpy jeki kimtsa zan biyoshi muzo” juyawa tayi takoma gidan Mama nakan dadduma kallonta tayi da kafafun dasuke amike kaman kara kumbura suke every minute, wata yar jakarsu ta dauka ta shiga debama Mama su t-shirt da zani she’s a student doctor she know case din Mama is not something daza’a sallamesu gobe, tadau zanin gado wankakke da hijabi itama tasa yan kayanta dan daga wajen zata dinga zuwa department dinsu ta kwaso duka kudin dasuke dashi tashiga kirgawa gashi sun kashe kudi akasuwa ranan salla, Mama sai kallonta take yanda jikinta ke rawa kaman tamata kuka tadai daure bataso ma tanuna mata kalan azaban datakeji saisa take daurewa sunayen Allah akwai take kira abakinta, 85k sukedashi tadauki wayanta tanada about 51k a account, jakan makarantan da da komi keciki tagoya ta gungura jakan takawo tsakar gida daidai lokacin an buga gate dasauri ta gungura box din waje su kasa a keke ahankali tace “Musa zoka tayani mu dauketa bazata iya tafiya ba” daga Musa har Baba Liman biyota sukai ciki, Baba yakalli Mama da idanunta ke a kulle sabida tsananin ciwo yace “sannu da jikin Maman Rashida sannu” gyadamai kai tayi batare data bude idanubta ba, Baba Liman yace “kawomin ruwa Rashida namata addu’a” dan yana ganin Mama yasan ita kadai tasan metakeji, kawomai ruwa tayi da sauri karba yayi yayi addu’o’i ciki yabata yace “bata tasha ki shafa mata sauran akafa” karba tayi cike da tsantsan so tace “Mama sha Baba Liman yamiki addu’a” ahankali Mama tabude idanunta dasukai jazur tadaurasu kan Rashida tadan bude bakinta kadan samata ruwan Rashida tayi tasha kadan sannan ta tsiyaya a hannunta ta shafa mata a kafafun sannan ta ijiye a gefe tace “Musa zoka tayani” zuwa yayi atare suka daga Mama tsaye sannan suka dauketa chak suka fita da ita a keke suka sata dawowa ciki tayi tadan gyara ko’ina agurguje sannan tadauko key tafito ta kulle gidan da kofansu tazo tashiga keke tazauna Musa yatada keken Baba Liman yace “duk yanda ake ciki kinkirani, Allah baki lpy Maman Rashida” Ameen Rashida ta amsa Musa yaja keken itakuma tashiga kiran HOD nata wacce suke kira da Mrs Bugaje wacce take Doctor Mama, kusan a kira nabiyu ta daga sabida girkin salla yau yawon salla, tana dagawa tace “Rashida how are you sorry ina kitchen ne I missed call naki is everything fine”? Ahankali tace “Ma jikin Mama ne kafafunta sun kumbura sosai she’s in pain muna hanyan tafiya hospital” Dasauri Dr Bugaje tace “take her to A & E, she must be treated as emergency, bari I will call Dr Usama yau ina off but I will come once na gama girki for my family, don’t worry okay Maman ki will be fine” gyadamata kai Rashida tayi tana sharce hawayen dakeson zubomata daga idanu sannan ta katse wayan, suna kaiwa asibiti A & E tawuce ba’asa sun jira anything ba sabida Rashida is a Dr aka sa Mama agado akai ciki da ita Dr Usaman yazo Rashida takasa komi, all ciwon Mama tadamata da hankali yake but hakanan she’s getting a special vibe daga wannan kaman zaifi kowannne worst duba da kafafunta tana tsaye inda yagama dubata, sannan yajuyo yakalli Rashida Dr Usama yazo yace “follow me” binshi tayi ahankali har zuwa office nashi saikuma yajuyo ya kalleta dan murmushi kadan yamata cikeda hikima na manya yace “calm down Dr Rashida sit” tana tsaye tace “tell me meke damun Mamana Dr” Dr Bugaje warned him about telling her anything yabari saitazo hakan yasa yace “is just blood pressure ta yatashi” tana kallon kwayan idanunshi tace “tell me I can handle anything I know People living with HIV (PLHIV) dakuma HBP (High blood pressure) Hypertension sunada significantly high risk of cardiovascular events abubuwan daya danganci matsalan ciwon zuciya da mutuwa, which is thought to be due to a complex interplay of various factors including immune dysfunction, endothelial dysfunction, and inflammatory changes, nasan Mama na is at risk of coming down da stroke, heart attack, heart failure, kumburin jijiyoyin daukan jini na jikinta, taushewan vessels dake daukan jini daga zuciya zuwa jiki, kidney issues, high cholesterol, dakuma matsalolin iya numfashi” hijabinta takama tadaura daura kan fuskanta tana matse idanunta sosai dakeson suyi kuka tace “just tell me wanne daga ciki ke damun Mamana?” Wlh ayanda yaga Rashida shi kanshi saiyaji bazai iya gayamata ba gwara Mrs Bugaje tazo tagaya mata, dan murmushi yace “I actually called you nagaya miki yanayinki din nan zai saka Maman ki cikin tashin hankali, calm down Mrs Bugaje is coming wuce kitafi” wani irin kallo tama Dr saikuma ta tashi tawuce takoma A&E din tazauna kan kujeran dake gaban gadanso takalli Mama da idanunta ke kulle sai bakinta daketa motsi na la’ilaha illallah tanashan azaba takai hannunta takama tarike gam, kawai she’s just looking at Mamanta feeling pains she wish itane akan gadon kwance ta dauke ciwon instead of Mamanta, tana zaune awajen wayan jakanta yashiga kara na Mama cirowa tayi taga Liman dauka tayi takai kunne yace “Yaya jikin nata me akace Rashida?” Ahankali tace “Dr Bugaje nake jira tazo gatanan a hanya” anatse yace “kome ake ciki ki kirani Allah bata lpy” ahankali tace “Ameen ta katse wayan” ta ijiye.


Around 12 Mrs Bugaje tashigo office nata tafara zuwa ta ijiye bag nata da komi ta sanya lab coat tafito Babban mace ce dazata kai 50yrs haka office na Dr Usama taje tadan jima kafin sutaho ward din tare Rashida na zaune rikeda hannun Mama taji muryan Mrs Bugaje cikeda wasa irin na professional Doctors din nan tace “Mama yaya mukayi ni da ke?


Wat was our agreement? Dasauri Rashida ta juyo ta kalleta, handglove tashiga sawa tana murmushi tana kallon Mama kaman irin nothing serious din nan sannan tataho gaban gadon tace “open your eyes for me Mama kar Rashida tafashemin da kuka anan dukta damu” ahankali Mama tashiga bude idanunta da kyar tabude kadan sunyi jazur takalli Rashida dake tsaye gefen Mrs Bugaje tai zuru zuru bakaramin dadin hakan Mrs Bugaje tajiba tace “good job Mama, tell me meke damunki? Meya tadamiki da hankali haka dahar kika bata agreement namu na bazaki dinga tunani be?” Mrs Bugaje tai maganan tana duba kafafun Mama tana dubawa kumhurin yanzu ya wuce guiwowinta ma, cikin wani irin murya da baya fita Mama tace “Jummai, Jummai zata halakamin rayuwan yarinyana, Jummai nason halakamin yarinya” dasauri Rashida tai wajen takama hannunta da sauri tace “Mama dama abinda kiketa tunani kenan babu wacce zata iyamin komi I can defend myself kinji kidena tunanin” girgizakai Mama tayi hankalinta nawani irin tashi takalli Dr tace “Mrs Bugaje hide…….hide my daughter…..banson ta cutarmini da yarinya, nasan Jummai nasan bazata  kyaleta ba, Jummai Jummai, yarinyana, Rashi……Rashi….Rash….” Kawai sai Mama tafara yunkurowa tana wani irin nishi kaman zata mutu numfashi kaman yana gagaranta ma, Mrs Bugaje tai maza takama kafadarta tana maidata gado tace “Mama calm down calm down Mama I will hide Rashida babu abinda za’a ma yarinyarki” inaaa kaman ma Mama batasan inda kanta yakeba wani irin gasping breath Mama keyi dayasa Rashida kawai tadaura hannunwanta kan baki tana wani irin kuka tana kallon Mama dataga Mrs Bugaje da Dr Usama are trying to save at all cost Mama tasha ciwo but not irin wannan bata tabajinta this scared arayuwanta ba Mama is her biggest strength for the first time arayuwanta taji karfinta jarumtarta ma gaxawa she don’t even know ina kanta yake tadaiji an jijigata ance “Rashida!” Firgigit tadawo daidai Mrs Bugaje ne tace “come with me” dasauri takalli Mama dataga an sama oxygen a hanci wasu ma’aikata na gungurata zuwa wani wajen dabama tasani ba har office na Mrs Bugaje taje zaunar da ita Mrs Bugaje tayi akan kujera itama tazauna ganin yanda take kuma saita kara tashi tabude fridge na office din taciro cold water tamika mata tace “sha” ahankali Rashida tabude tadan kurbi kadan daidai lokacin Dr Usama na shigowa dawasu papers kusan guda 5, Mrs Bugaje ta karba tace “thank you Dr” gyadamata kai yayi yace “bari nakoma” yajuya yafice papers din Mrs Bugaje tasaka glass tana dubawa kusan 20min sannan ta ijiye tareda sauke glasses din takalli Rashida daketa kallonta she doesn’t even know what this small girl will do, ahankali tace “Rashida tun kina 100 level nasan how strong you are, bantaba ganin strong resilient student arayuwana like you ba wacce at a very young age shoulder responsibilities Mamanta da school da komi na rayuwansu, I supported you all through pull some strings na tabbatar kina gamawa da clinic dinki by 1PM wanda ba’a taba dagama student kafa haka ba, but I made it happen sabida I see you I see rayuwan dakikeyi a daughter like you deserve standing ovation, dan haka banson ki karaya this time fight this also kaman yanda you fought komi na baya kuka cigaba da rayuwa kinji Rashida” gyadamata kai Rashida tayi tana kallonta tana rike duka abubuwan datakeji azuciyanta, Dr Bugaje tace “BP Mama yakai level din da ko makiyina bazanmai fatan yakaiba, legs nata are starting to have stroke sabida blood vassel nata na zuwa wato Artherties nata are blocked jini baya fita da kyau, now dole mu mata procedure call……” ahankali Rashida tace “arherectomy!” Ijiyan zuciya Mrs Bugaje tasauke tace “yes, minimal invasive procedure ne dazamuyi dan muyi flushing buildup din daya cika vessel din sabida jini yasamu yawuce wajen freely, that is one” tadan sauke ijiyan zuciya tadauki paper gabanta tamika mata tace “ga result na express ECG da Dr Usama yasa aka mata can you read ECG da kyau?” Gyadamata kai Rashida tayi da sauri takarba tana karanta rhythm din, cikin wata kalan sassanyar murya Mrs Bugaje tace “I think zuciyan Mamanki is failing!” Wannan karan ijiye paper Rashida tayi agabanta tadaura hannunta saman idanunta ta matse hawaye still yana diddiga from side, wlh kawai dan ita Dr ne but she wants to cry for the girl, ahankali tace “matsalan HIV is yanacin kwayoyin garkuwan jiki, dazaran cuta tashigeka HIV yana cinye wayan nan garkuwan na jikinka da naturally suke fighting cuta kowace iri, it’s a long shot but banso kiyi loosing hope we can still save your Mom” har lokacin Rashida batasaki idanunta ba hancinta kawai yake motsi tip na hancin yayi jazur wani tsinkakkiyar majina na lekowa daga hancin, ahankali Mrs Bugaje tace “Rashida” dago kanta tayi tana sakin idanunta cikin muryanta dahar yakoma kaman na me mura tace “naam” wani paper again Mrs Bugaje tabata tace “idan kinaso muyi treatment nata ayi procedure sannan ai connecting Mama da machine dazai taimaki heart dinta dake failing sannan ayi tackling BP da stroke din, to this is just a rough estimate na kudin dakike bugata rough estimate dan zaifi haka anything heart magungunan shi da treatment nashi is expensive, plus oxygen da yanzu muka sata akai dazai dinga tayata breathing you need about 2.5M!” Kallon list din take kawai, ta ina zata sami kalan kudin nan? Wani aiki zatayi tasami kudin nan just today sabida afarama Mama treatment sai alokacin kawai taji kuka yazomata kawai tafashe da kuka da karfin gaske tawani zube kasa daga jikin kujera ta dunkule paper a hannunta tana kuka sosai tashi Mrs Bugaje tayi ta zagayo ta duka ahankali agabanta idanunta sunyi jaaa tadafata tace “I know bakida this kind of money bakida hanyan samunsu Rashida it’s okay ya isa kukan we will not let Mama die” wani irin kallon Mrs Bugaje take tana kuka, Mrs Bugaje tace “Rashida I’m a family woman kwanan nan nama yarana dake UK registration na school wlh banda kudi but I will give you 200k sauran kudin kuma akwai this student loan da student ke iya applying idan kafara internship duk albashinka za’a dinga karba as payment for the loan, but matsalan shine CMD kadai ke signing and approving but baya gari dole mujira yadawo which bamuda lokacin the next option is student doctors and other people’s help seek for donation for Maman ki yawanci an sanki ansan situation na Mamanki they will help you hopefully zamu iya tashi da something, in the meantime kudin nan dazan baki dayan chanjin dake hannunki jeki sayi necessary magani dasu drip da ake bukata sabida afara ma Mama treatment kinji and pay for oxygen also dan na this hour kawai zasu bata idan baku biyaba bazasu bata again ba, Stop crying, remember na gayamiki you have to be strong ke kadai Mamanki keda shi, kene kadai zaki iya kula da ita, stand up dagata Mrs Bugaje tayi tace “Allah baya hada bawa da abinda yafi karfinshi kinji” gyadamata kai Rashida tayi takama hijabinta ta goge fuskanta tass, jakanta Mrs Bugaje tadauka ta bude taciro bandır na 100k guda biyu wanda sabida ita ta taho dashi tabata tasan basu dashi cus tun awaya Dr Usama yagaya mata komi tace “take” tsayawa tayi tana kallon kudin Allahu Akbar tunda tafara girma tafara aiki bata taba accepting wani kudi daza’a bata sabida Mama ba saidai Mama ta amsa yau gashi ita ake bama kudin taimako zata karba hannunta tamika dahar rawa suke ta amsa tama kasa godiya sabida shock Mrs Bugaje ta dauki precribtion sheet dawasu papers tabata tace “jeki sayo magungunan sannan kibiya kudin ECG da aka mata ki kowamin a ICU” gyadama Mrs Bugaje kai tayi tafito tafiya kawai take taje ta bibbiya kudin ECG tasayo magunguna dasu drip tabiya kudin oxygen na kwana uku dan per hour ake biya shi, da kudin da Mrs bugaje taba tada kudin account dinta da na hannunta duka sun kare sai naira dari biyar daya rage mata this is duka kudinta gaba da baya, dawowa tayi ta tsaya gaban ICU mrs bugaje tafito ta amsa tace “now go round ask for help from this Doctors kinji” gyadamata kai tayi tajuya batamasan taya zata faraba stufent Dr dinsu duk sunje hutun salla public holiday wayanta ta dauka tasami waje ta zauna tai shiru yau ne rana na farko datai realizing good human relation ma wani abu ne arayuwa mu’amala me kyau yanada ranan sa, duk yanda kakaiga you don’t need anybody las las you still need everybody saidai in Allah bai jarabceka dawani abu ba, yanzu kotai magana a group ma yan class dinsu zasu taimaketa? Yawanci tayi fada dasu, yawanci bata kulasu kosun kulata, daurewa tayi tashiga typing komi na neman taimako Mamanta na critical condition tana neman 2.5M ta tura group din da acct details nata bini bini tana duba info kusun gani taga duk sun gani Layla ma fitowa tayi tafara hira a group din babu ko Allah sawake few friends nata suka shigo suka biyemata suna hira suna turo emojis na dariya.


💫 SANYI DA ZAFI 💫

 ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣3️⃣


Kawai saita fito daga watsapp din da sauri tama kashe data ta ijiye wayan tasakeyin shiruu batada kowa Baffa yakori Mama takirashi? Yadena daukan number Mama banda haka ta tsani duk wanda ya wulakanta mahaifiyarta tashi tayi tana numfashi ahankali tashigo A&E ward din ta tsaya tana kallon yanda Doctors ke aiki trying to save lives duka duka nawane salary su babu wanda baida matsala tayaya zata fara binsu one by one tana neman taimako? Da kyar taja kafanta tawuce wajen wata Macen Dr datake tsaye gaban nursing station tana magana dasu ahankali Rashida tace “sannu” dasauri likitan tajuyo ta kalleta tace “yauwa sannu” kasa magana Rashida tayi batasan ta yanda zata fara rokon ba Dr tace “lafiya?” Ahankali Rashida tace “taimako nake nema, uhmmm” tahadiye abu awuyanta tace “Mama na needs 2.5M” kallonta Dr tayi saikuma chan tace “sorry about your Mom but kinsan this is the 2nd month da government basu biyamu ba? Metron fadamata” Dasauri katuwar Metron na wajen tace “wlh da na iya roko nima I’m bold enough like you danabi kowa na nema tsabagen rashin kudi this Tinubu Tenure no good for us kawai, ba’a biyamuba everyone is broke” gyadamusu kai Rashida tayi tawuce kawai taje wani lungu ta duka tana maida numfashi tana ahaka wayanta yahau ringing fitoda wayan tayi ganin Mrs Bugaje yasa ta tashi tama kasa daga wayan ta taho da gudu danta dauka wani abu yasami Mama agaban ICU taga Mrs Bugaje, tana kallon Dr Usama dake kokarin helping Mama machine din da aka samata sai kuka yake arude tace “Dr what is happening to Mama”? Dasauri Dr tace “she needs atherectomy now vessels dinta sun kara blocking, you need to pay I think 800k ne or so kudin amata before we loose your Mom go” Mrs Bugaje na maganan ta juya takoma ciki Rashida tajuya itama bamatasan mezatayi ba Baba Liman tashiga kira tana tafiya kaman mahaukaciya ahanya tace “Baba Liman wazaisai gidanmu Mama na bukatan 2.5M yanzu kuma ana neman 800k ayi flushing zuciyanta” Baba Liman yace “Subhanallahi ta ina zamu samo wanda zaisai gidanku yanzu yanzu Rashida ai kusan is impossible amman bari natara jama’a naji” ya katse wayan batasan ma ina xatasa kanta ba Riyad! Kawai taji zuciyanta ya ambato, Riyad ne yafado mata arai, he helped them before, and yana shiri da Mama taje ta nemi rance ne kafin a saida gidansu? Tunanin yasa tashiga keke tawuce hotel last 500 naira tabiya keke dashi, ta sauka saikuma ta tsaya tai shiru tayaya zatai facing nashi? Mutumin dabata tabamai godiyan abubuwan dayama Mama ba saima rashin kunya datakemai accusing him of lalata mata? Yau Allah yana nunamata abubuwa da dama datayi abaya that were wrong gashi yanzu she needs his help desperately dudda tagama mai rashin kunya da kurin cewa she alone can take care of Mamanta bata taba sanin a day like this will come ba, takai kusan 5min tsaye take awaje cikin rana tana lissafin yanda zatai confronting Riyad kafin tadai daure tadaga kafa tashigo building din tawuce ciki direct elevator ta tafi tana addu’a Allah yasa yana nan, har office nashi taje ta tsaya gaban kofan tana kallo kafin ahankali tadaga hannunta tai knocking, jin shiru yasa takara knocking, harta fara tunanin kobezo bane dan yau ranan yawon salla ne nabiyu sai chan taji daga ciki ance “come in” cikeda isa, ahankali ta murza kofan ta shige yana zaune gaban desk nashi yana sanye dawani milk yadi shidai yanason kaya masu haske, rubuce rubuce yake da pen da sauri he seems busy batare daya dagokai ba yace “yes” ijiyan zuciya tadan sauke saikuma maganan ya makale a wuyanta batasan ta yanda zata fara maganan ba, chan dai tadaure cikin muryanta me rauni tace “aron kudi nake nema 2.5million kafin asaida gidanmu nadawo maka da kudin” tunda tafara maganan chak ya dena rubutun dayake batare daya dago kanshi ba saida takai karshen maganan sannan yadago kanshi ya kalleta tundaga kafafunta dayaga slippers tasaka dawani maroon hijabi har kasa da ko’ina dabbare dabbaren ruwan hawaye, kanta akasa takasa dago idanunta ta kalleshi but tip din dogon nose dinta dayagani that looks reddish and runny nose yagane she cried, ahankali yataso yazagayo ya tsaya agabanta yana kallonta but taki dago kanta awani irin hankali akuma taushashe yace “wat happened to Mama?” Kaman yatabo mata wani gyambon ciwo a kirji dago fuskanta tayi tazubamai jajayen idanunta shima kallonta yake baki tabude zatai magana sai kawai tafashe da kuka jikinta and everything is just shaking, tunda ya santa today is the first day yake ganin hawayen ta eye to eye, today is the first time yake ganinta this weak, wani irin sheshekan kuka kawai take agabanshi dayasa yakai hannunshi cikin aljihu yazaro handky yabata cikin wani irin soft tone yace “nothing will happen to Mama kinji” gyadamai kai tayi kaman baby tasa hannu ta karbi handkerchief din takai fuskanta tana gogewa still wasu hawayen na zubowa shikuma yajuya yadauke car key nashi da wayanshi yakalleta yace “stop crying let’s go”tsayar da kukan tayi da kyar sannan tabishi yayi gaba fitowa sukayi atare suka shiga elevator tana gefenshi suka sauka kasa yan reception dake lobby sai kallonsu suka dasuka fito but ko’ajikinshi hanyar mota yayi da kanshi yaje wajen yabude mata kofa yana kallonta ahankali tazo ta shiga ta zauna ya maida kofan yarufe yazaga ya shiga dayan yatada motan suna tafiya sai kiranshi ake yaki dauka daga Mama takira sai Munir yakira yau hawa ana bukatanshi da sassafe yafito because of wani important work nashi da US sunce yatura musu wani abu abun yake tashigo yabarshi yanzu ma.

Dayake yasan kwanaki sunce general hospital suke using hakan yasa hanyar ya dauka motan yayi tsit sai ijiyan zuciyan datake saukewa na wayanda sukasha kuka, suna shiga asibitin yace “ina zamu” cikin muryanta da baya fita sosai tace “A&E” nan sukayi yasami waje yayi parking yafito praying babu wanda zaiyi recognizing nashi yadauki black glass nashi yasaka yafito yazagayo yabude mata, ahankali tasauko suka jera ciki har zuwa ICU daidai lokacin Dr Bugaje natahowa wajen ganin Rashida tareda wani hadadden guy yasa glass yasa takarasa shima ya zare glass nashi, yana zuwa yabama Dr Usama hannu yace “sannunku” yakalli ciki ICU dayaga Mama da oxygen unconscious yace “me ake bukata yanzu”? Anatse Dr bugaje da dudda batasan wayeshi ba but he looks responsible tace “follow me” office dinta suka bishi Dr Bugaje da Usama explained everything to him yana fahimtan komi with so much care and affection yace “idan akayi Atherectomy din zaiyi aiki bazai koma ya taushe ba or do you think nafita da ita UK within the week”? Ahankali Rashida tadago kanta takalli Riyad dayayi maganan da hankalinshi nakan su Dr sunamai bayanai, Dr Bugaje tace “kozaka kaita UK dole muyi flushing na pipe din nan inba hakaba she won’t make it” gyadamusu kai yayi yace “okay a ina zan biya kudin komi”? Dr Usama yace “account building yana nan opposite MOPD idan kafita daga this building” gyadamusu kai yayi yace “thank you” yatashi rikeda takardun biyan kudin itama Rashida ta tashi tabiyoshi ahankali yajuyo yakalleta hada ido sukayi saikuma yadauke kai yacigaba da tafiya tana biyeda shi har saida sukazo wajen ICU din da kujeru ke gaban wajen, da hannu yanuna mata kujeran gently yace “sit” kallonshi tayi da rinannun idanunta saikuma ta gyadamai kai like an obedient girl ta zauna ahankali shikuma yawuce yatafi, almost 20minutes shiru hakan yasa ta tashi tun kafin takai account building din taganshi tsaye a layin biyan kudi jitayi zuciyanta yamata wani iri game dashi, no one tunda ta taso has ever done something like this for them, saikuma tajuyo tadawo tazauna wajen tana kallon Mama ta glass almost 15minutes sai gashi yadawo ga papers a hannunshi gawata yar leda a hannunshi, yana zuwa daidai inda take zaune saiya tsaya agabanta ya bude ledan yaciro wani iced coffee yakalleta yana mikamata yace “have this” ahankali take kallonshi yanda yazuba mata ido yasa gently tasa hannu ta karba hawaye na kara cikowa a idanunta, sai kawai taji she’s feeling bad sai kuma taji tabama kanta tausayi sai kawai tafashe da kuka kaman an daketa tarike cup din gam a hannunta gwanin ban tausayi, softly yace “it’s okay, stop crying kinji” yanda yayi maganan sai taji zuciyanta yamata wani irin sanyi ta gyadamaikai tareda kai cup din bakinta saida yaga ta kurba kadan sannan yawuce.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

 ✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣4️⃣


Yadan jima acikin office din Dr Bugaje kafin su fito dukansu atare daidai lokacin kuma Baba Liman da danshi Musa na zuwa asibitin sun shigo cikin A&E din hango Rashida yasa suka taho wajen suma su Dr nazuwa wajen tareda su Riyad Baba Liman yace “ya jikin nata mai siyan gidaje wai baya gari saiya dawo ga abinda nahado dai daga masallaci” yaciro wasu kudi dabasukai 30k ba zai bata Riyad yace “kabarshi an sami kudin Baba” Dasauri Baba ya kalleshi daidai lokacin kuma an fito da Mama za’a wuce da ita operation room Rashida ta tashi dasauri zata kama hannun Mama that is unconscious Dr Bugaje ta hanata tace “wait here nan da 1hr zamu gama, sit and rest okay” komawa tayi tazauna tasake daura hannayenta kan idanunta Baba Liman yace “sai hakuri Allah yabama Zainabu lpy, Allah yabata lafiya, Allah yabata lpy” duk zama sukayi banda Riyad dake tsaye awajen, kusan 20min Baba Liman yayi sannan yatashi yace “bari naje Rashida, lokacin salla na gabatowa” ko dago kanta batayiba anatse Riyad yace “mungode” hannu Baba yabashi suka gaisa yawuce Musa biyedashi suka tafi ahankali Riyad ya zauna kan kujeran gefenta ya kalleta zaiyi magana kuma saiyayi shiru tabashi tausayi, it’s just she and her Mom. “Your Mom is going to be fine stop crying kaman this is the end” dago jajayen idanunta tayi ta kalleshi, ahankali yace “okay”? Gyadamai kai tayi.

After 2hrs aka fito da Mama but ba’a barsu sunje wajenta ma aka sake shigar da ita ICU aka connecting nata da machine again.

Har dare Riyad na hospital din nan, Rashida looks so miserable, mutane ma rahama ne, batada kowa, she’s just alone, kawai yaji he can’t leave her, koda bazai dinga mata wani magana ba but at least presence nashi is something, gashi batada karfi to handle anything, wasa wasa har 4 na asuba suna zaune wajen nan ita Rashidan ma bacci yadan kwasheta shiko idanunshi biyu, yana zaune awajen yana kallon yanda take bacci azaune idanunta sun kumbura suntum, he’s feeling just too many things towards her acikin zuciyansa.


Ahankali Mama ke bude idanunta, glass ne dakin ICU, na waje can see naciki, and naciki can see waje, ahankali idanunta suka sauka kan Riyad dake zaune kan kujeran dake facing room nata na zaman wayanda keda patient a ICU, kallon Rashida dake bacci awahale kawai yake, kallo ne da duka abinda Mama tagani a idanunshi is so much care, love, tausayi, concern da affection daidai lokacin Dr Mumina tashigo, ganin Mama idanunta biyu yasa tace “how are you feeling Ma”? Oxygen din Mama tai yunkurin cirewa tana kokarin magana dasauri Dr Mumina tace “mekikeso tell me?” Waje Mama tanuna cikin muryan dabata fita sosai tace “I want to talk to My son” juyawa Dr tayi takalli Riyad da Mama ke nunama ta ta gyadamata kai tajuyo tafito hakan yasa Riyad yajuyo jin an bude kofa, da hannu tamai alamu yazo tashi yayi dasauri yana kallon ciki ganin Mama ta farka finally, scrub Dr Munina abashi yasaka da takalmi da hula da handglove sannan yabi Dr ciki Dr taduba komi kafin tadan zarema Mama oxygen mask din tace “kimai magana  ahankali, don’t stress too much, I will be back to put it for you nan bada jimawa ba” tajuya tafita zama Riyad yayi kan kujeran gaban gadon cikeda so dakuma tausayi yakalli Mama da ko idanunta bata iya budewa da kyau yace “Mama ya jikinki”? Hannunta Mama ta mikamai alamun yabata nashi, bata hannunshi yayi da sauri Mama takama tarike gam tasake shiru tana numfashi ahankali kaman magana wahala yake mata, cikin muryan tsananin rashin lafiya dake fita da kyar tace “Riyad” ahankali Riyad yace “na’am Mama please stop talking, Mama it looks painful I’m here bazanje ko’inaba kinji”



Ahankali Mama takara cewa Riyad, kankame hannunta Riyad yayi sosai he’s just feeling Mama’s pain yace “Mama dan Allah stop talking” girgixamai kai tayi tace “Riyad lokacina yayi aduniya lokutan da Allah yadeba mini” Dasauri Riyad yace “Mama kidena magana haka zaki sami lafiya bagashi yanzu kin farfado ba eh Mama”? Dan murmushi tayi ta kankame hannunshi tana numfashi wani kala wani kala, chan tace “Riyad duk duniya dakai kadai na yarda! Kanada hankali, kanada amana ga taimako kaiba yaro bane sannan kanada iyali, ka taimakeni so da dama, thanks to you Rashida bata kwana a police cell ba” tayi shiru kuma tana sake kankame hannunshi tace “banso na rasu ban damkawa kowa amanar y’ata ba banda wanda zan bamawa, Riyad Yayana na jini ya koreni! Mijina ya koreni! Baba Liman matanshi basa sona, tsorona da tsoron ciwona kowa yake! Kaine mutum na farko daya shigo rayuwanmu baka kyamace muba baka tsorata damu ba” tasake shiru saikuma tace “kishiyata data kulle yarinyana a police station ka fito da ita nasan saita bata ma Rashida rayuwa, nasan saitayi wani abun, yanzu haka rayuwan Rashida nacikin hadari zata cutarmin da diya” hawaye ne suka gangaro daga gefen idanun Mama saikuma tafashe da kuka sosai tana kankame hannun Riyad tace “Riyad dan Allah dan Allah na rokeka da girman Allah ka auri Rashida! Sabida na samu na mutu in peace nasan na damka maka ita, wlh Rashida batada HIV kaman ni batada wani cuta ajikinta, Riyad ka taimaki yarinyana, kayi jahadi akanta, ka aureta kahadata da matarka su zauna lafiya, inaso na mutu bayan nadan tana under care naka da kukanwanka amatsayin matarka zaka karemin ita” Kai! Yanda Mama ke kuka sai yasa Riyad yaji kaman zaiyi kuka, Mama na son Rashida beyond words, she’s on sick bed but still damuwan Rasheeda ne aranta, ahankali yakai hannunshi dayan that is free ya sharemata fuska muryanshi sounding so weak yace “stop begging me! And kidena damuwa, stop worrying Mama, Mama zan auri Rashida! And namiki alkawari zan kula da ita amana! Bazan taba cutar da ita ba! Zan tsayamata! I will be her shield! I will be her shade! Mama I will stand by her and with her, and zan so yarki and stay her husband till my last breath” wani irin murmushin kuka Mama tayi tace “bayan narasu nasan she will be shattered be there for her Riyad and make sure tayi completing karatunta na zama kwararriyan likita!” Gyadamata kai yayi yakasa magana, Mama tace “Rashida is a good sweet person wata rana you will see her other side, rayuwa ya maidata me taurin kan nan but my daughter is an Angel!” Gyadamata kai Riyad yayi yace “Mama stop talking ya isa” girgixamai kai Mama tayi tace “kaje kazo da yan uwanka zan kira Baba Liman inaso na aurar da Rashida dakaina anan kafin na rasu! Inaso naga yarinyana tai aure” “Mama bazaki rasu ba” Riyad yafadi da karfi jijiyan kanshi na fitowa daidai Dr na zuwa ganin Mama na kuka yasa tace “ohh noo, BP ta will shoot again, she needs to stay happy” ahankali Riyad yajuya yafita.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR



EPISODE 2️⃣5️⃣

Yana fitowa tsayawa yayi yakalli Rashida dake bacci kafin yawuce yafita yatafi parking space ya shiga motanshi yatada gida yawuce yana zuwa remote dake motanshi ya dauka ya danna gate yabudu ya shigo yayi parking motan ya sauko yana tafiya ahankali yawuce ciki yana bude kofa yaga Mom zaune kan kujera saida gabanshi yafadi ganinta tashi tayi tace “daga ina kake?” Rasa abinda zai fadi yayi cus ya tsani karya and ya tsani yinta da bakinshi Mom tace “did you know how important yesterday was for Royal Family kuwa? Kasan mekayi Riyad? An nemeka an rasa, Baffan ka Mai babban daki, su Kabeeru duk ansan baka gida narasa mezance? Wani dalili yasa mukaje Umara da wuri dan mudawo kayi salla da mutanenka ayi hawan salla dakai right? Kasan kalan tijaran da abin kunyan daka jamin kuwa”? Runtse idanu yayi yama rasa mezaice ahankali yace “I will handle it Mom wani important work ne yatasomin, I can create another event at my leasure time kiyakuri, its work” “important work da ake fita da sassafe adawo by 5 na asuba are you out of your mind Riyad!” Mom takirashi azafafe dayasa yasauke kanshi kasa tace “banso na zargeka the first time da matan ka tai accusing naka fushin dakayi yasa ban yarda ba but bari kaji idanma wata kake nema wlh wlh dukda kana sarki baka isa ka karomin aure ba!” Ahankali Riyad ya kalleta Mom tace “yes! Haleema is the only daughter Inlaw dana yarda da ita cus yarinyar nan worship me sama da uwarta data kawoni duniya, ban yarda da karo aure ba azo arabani da d’ana ba! Aurenka is just a year now na auramaka yarinya datake da komi kyawun sura, good tsatso, oxford graduate, full package ce Haleema har yau ka kasa mata ciki ragon banza ragon hofi kaman ba jinin Baba Ali ba, nagaya maka idan baka dena all this abubuwan ba wlh zan mugun saba maka, yau Haleema na period still ka kasa mata ciki this month again yawo kake a duniya don’t allow me to face you fa Riyad nafara bin lamarinka ina binciken ka, look at me nakasa bacci all because of you gadin dawowanka nake eh why are you doing this Riyad yaushe kadawo mara jin maganata”? Wani iri dayaji yasa ahankali yace “Mom kiyakuri” mugun kallo ta watsamai tawuce tafice daga flat din, shikuma ahankali yawuce bedroom dinshi wanka yayi yayi salla sannan yadan kwanta bawani bacci yayi ba around 8 yatashi yadauki wayanshi yakira Munir sannan yashiga wanka yafito yaji Munir a falo yana waya shiryawa yayi cikin wani mahaukacin farin gizna yasa hula ya Allah hula yamai kyau, yasaka wani bakin takalmin Berluti, ya daura agogon Vacheron Constantin a writs nashi, ya manna wani Carrera black glasses a idanunshi Ya Allah kaga Riyad saika kara kallonshi saukowa yashigayi Munir ya tsare shi da ido yace “wannan gayun ina zamu haka!?”


Kin magana Riyad yayi yana karasa zuwa falon ya jefamai car keys Munir ya chabe yana mikewa tsaye suka fito tare mota sukayi suka shiga Munir yatada motan yace “ina zamu”? Ahankali Riyad ya sauke ijiyan zuciya he’s just torn between Mom dinshi and Mama, yana tausayin Mama and he feels obligated to help them, Rashida batada kowa, and he promised kanshi kafinma ya gano Rashida cewa he will helped the girl, he’s doing this for the girl that saved life nashi, murya chan kasa yace “I’m sorry Mom” kallonshi Munir yayi jin abinda yafadi hakan yasa ahankali yace “wajen Baba Buba zamu” dasauri Munir ya kalleshi yace “Baba Buba? You mean Baban Ammi”? Dauke kai Riyad yayi ahankali yace “yes Kakana!” Tada motan Munir yashigayi mamaki yagama kasheshi yace “Riyad as far as I know I can’t even remember the last time kaje ka gaidashi, ni banmasan kasan yana existing ba” wani iri fuskanshi yayi saikuma ahankali yace “i will change from now” fita sukayi saikuma chan Munir yace “mezai maka? You’re sounding kaman you need something from him?” Shiru Riyad yayi na kusan 5minutes chan yace “aure nakeso ya karbanmin! I want to Marry Rashida!” Wani burki da Munir yaci kan titi saida yakusan creating hatsari yaja motan da gudu yana gangara wa gefe yakalli Riyad daya ciro wayanshi yana dubawa jin karan text message daya shigo wanda yaga na Haleema ne.

“Baby marana na ciwo? A ina ka kwana jiya?”.


Ahankali Munir yace “Riyad looked at me! Zaka auri Rasheeda? Waya sani agida? Mom tasani? Gwaggo tasani? Baffan mu yasani? Waya sani?” Batare daya kalleshi ba yace “no one knows! Will tell when I feel like it” yasake shiru chan yadanna mata “Kisha magani, Allah kara sauki” ya maida wayan aljihu sannan yadago ya kalleshi yace “I feel obligated to help them Munir, the girl is young, she’s a child, the Mom is very sick a ICU lets go” tada motan Munir yayi harsukakai wani kauye nan Outskirts na Kano bai kara magana ba gaban wani babban gida sukai parking ga rumfa da dalibai suka cika gawani tsoho kan kujera dake da haske kaman Riyad yaci manyan kaya na sauraransu yana hangosu ya tsare Riyad da idanu wanda ya manta rabon daya ganshi saikuma ya dauke kai sannan ya sallami yaran yama Munir alamu da hannu dasuzo.

Shiga rumfar sukayi suka zauna atare suka gaidashi ya amsa sannan yakalli Riyad da kansa ke kasa yace “yau katuna dani? Meya kawoka gidana”? Wani iri Riyad yaji amman ya daure yace “kayakuri Buba” ijiyan zuciya Buba yayi yakalli Munir yace “nasan wani abu yakawoku so tell me” kallon Riyad Munir yayi sannan yace “Buba Riyad keso ka bishi ka karbamai aure” kallon Riyad yayi yace “mesa baka nemi yan uwan mahaifinka ba kazo nan? Ko yan uwan wacce itace mahaifiyar ka yanzu?” Munir zai bude baki Buba yace “kamin shiru” yakalli Riyad yace “kamin magana koka tashi ka bar nan wajen” murya chan kasa Riyad yace “bazasu barni na aureta bane na gaya musu Buba sabida ciwon Mahaifiyarta” Buba na kallonshi yace “wani irin ciwo”? Ahankali Riyad yace “HIV” shiru Buba yayi chan yace “kanason yarinyar tsakaninka da Allah?” Shiru yayi chan yace “inaso na aureta, banso ta auri wani karya wulakantata” saikuma ahankali yace  “ita ce ta ceci rayuwana lokacin da za’a kasheni” Buba yadan jima yana kallonshi sai chan yace “kutashi muje” Dasauri Riyad yadago kanshi ya kalli Buban yana dan murmushi daya karamai kyau Buba yace “saina chanza ra’ayina tunda ka tsaya kana kallona kaman yauka fara ganina a doron kasa” tashi da sauri Riyad yayi yana murmushi yawuce Munir ya bishi Buba yabisu da kallo Allah yasani yanason jikanshi sama da duk yanda zai kwatanta abin aduniya, tunda har yatuna dashi a lokacin dayakeda serious bukata haka he will support jikanshi, Babban Aminunshi yakira suka shiga bayan motan Munir da Riyad suka shiga gaba suka wuce.


💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 2️⃣6️⃣


As usual wajajen 6 Rashida tabude idanunta da kyar sabida tsabagen gajiya da kuka, kaman ba itane tuntuni ake hayaniyan asibiti ana shiga da fice ba ko bude idanu batayi ba sabida nauyin baccinta, dasauri tamike tsaye ta tafi wajen glass door din ta jingina kanta tana leka Mama trying to see ko tana numfashi, taganta tana bacci and tana breathing, dan ijiyan zuciya tasauke takalli inda ta tashi tasan har tai bacci Riyad na nan koda yaushe yatafi oho wucewa tayi bayi tayo alwala bayan taciro brush ajakanta tayi ta tafi masallaci tai salla tama Mama addu’a sosai tadauki Qur’ani yau ta karanta tasake ma Mama addu’a bayan tagama, tana dawowa Dr Mumina tace “Your Mom wants to see you” jikinta har rawa yake ta gyada matakai abubuwa aka bata tasaka sannan tashiga dakin idanun Mama abude kadan take kallonta dasauri taje gaban gadon ta duka takai fuskanta saitin na Mama tace “Mama ya jiki? Are you fine Mama? Kinji sauki? Sannu Mama na, sannu kinji Mama, Mama ina sonki kinji, mezakici”? Girgiza mata kai tayi bakinta nadan motsi hakan yasa dasauri takai kunnenta saitin bakin Mama, murya chan kasa Mama tace “inaso namiki aure yau!” Dasauri Rashida tajuyo takalli fuskan Mama kodai bata hayyacinta ne kodai she’s hellucinating ne? Ganin bakin Mama yacigaba da motsi yasa tasake kai kunnenta saitin bakinta ahankali Mama tace “I want someone that will take care of you koda zan mutu I want to die in peace, I told Riyad ya aureki!” Dawani irin sauri ta kalli Mama gabanta nawani irin faduwa naban tsoro murya chan kasa Mama tace “I trust Riyad! Yanada hankali zai hadaku ku biyu yarike amana! Rashida I need to hand you over to wani tun yanzu da raina kafin na rasu!” Hawaye ne yazubo daga idanun Rashida cikeda damuwa tace “Mama nace bazaki rasuba! Mama nothing will happen to you In sha Allah, Mama yaya zanyi idan kika tafi kika barni”? Kallonta Mama take saikuma tai yunkurin dago hannuwanta biyu dasauri Rashida takama hannuwanta takai fuskanta, hawaye na gangarowa daga idanunta cikin muryan Mama da baya fita da kyau tace “Rashida ina sonki, inasonki sosai my little Rauda, ina matukar kaunarki My Doctor my Rish Rish, my only baby, yarinya na kyakkyawa I love you” wani irin kama hannuwan Mama Rashida tayi saita fasheda kuka sosai, Mama itama hawaye gangarowa yayı daga gefen idanunta tace “I’m scared na mutu banyi handing naki over to anybody ba, Riyad is the only mutum da xuciyana ya yardashi aduniya! Riyad zabina ne Rashida! Riyad is my choice! Riyad is the only man dana kalla namiki sha’awansa as miji will you marry Riyad for me? For my sake? For my happiness”? Kankame hannun Mama Rashida tayi sosai tana kallon kwayan idanun Mama tana kuka itama Mama kuka take, cikin wani kalan murya Mama tace “wat if na mutum? Wakike dashi? I want to hand you over to Riyad kinji, zaki aureshi sabida inaso”? Gyadamata kai Rashida tayi at this point the only burin datake dashi aduniya is taga magaifiyarta ta warke jin kanta take idan Mama tacemata tai kisan kai zata iyayi tsabagen yanda takeso ta faranta mata rai and make her happy, cikin kuka tace “Mama I will marry Riyad sabida kince nayi! Nariga namiki alkawari bazan kara saki a damuwa ba, kome kikeso Mama shixan dingayi I will always keep you happy, Mama dan Allah karki mutu kinji, kinji Mama karki mutu ki banni kinji Mama? Kin tuna namiki alkawari zan zama likita and develop a cure for you? Mama you have to stay alive and wait for me! Mama kinga inaso kixama hope for mutanen dakeda HIV dudda already you’re, kinyi rayuwa da HIV for 23yrs, you fought Mama ba dare ba rana, kika haifeni, you protected me Mama look at me yau na girma but banda shi, Mama karki banni kitafi kinji help me fulfill this legacy nawa after all this battle yarki likita Dr Rashida found a cure and Mama is HIV FREE!!! Kimin alkawari you will live for me and zaki jirani har lokacin Mama”? Murmushi sosai Mama tayi kawai tajawo kan Rashida tadaura akan fuskanta ta kankameta sosai tama kasa magana, sun dade ahaka sannan Mama tace “stop crying babu inda zani, I will stay for you, ranan graduation naki na saka exclusive super wax na kafa gwargwaro akai harda glass” dan murmushin kuka Rashida tayi tama kasa magana Mama tace “kiramin Baba Liman” gyadamata kai tayi tadauki wayan takirashi, yace “gashinan zuwa” around 8 Dr Bugaje tashigo duba Mama ahankali Mama tace “inaso nama diyata aure” shiru Mrs Bugaje tayi tana kallon Mama wanda somehow she understand Mama, she knows daga inda decision na Mama is coming from, gyadama Mama kai tayi tace “shine mutumin nan”? Gyadamata kai Mama tayi, Dr Bugaje tace “ba’a bari mutane su shigo ICU sukazo zansa akawoki office dina sai ayi awajen” gyadamata kai Mama tayi Mrs Bugaje zata tashi Mama tace “Mrs Bugaje” dasauri tajuyo takalli Mama, ahankali Mama tace “kina ganin zan warke?” Tambayan yazoma Mrs Bugaje wani iri amman ta daure tai murmushi tadawo tasake zama tace “Mama mutane na mutuwa amusu wanka akusan binnesu ma su farfado balle ciwo, the point is shi cuta da mutuwa duka suna hannun Allah Mama kuma Allah sai warkar dake in sha Allah kinji” daidai lokacin ta hango Riyad ya shigo tareda wani tsoho dakuma wani matashi,  Mrs Bugaje tace “Ina Rashida”? Ahankali Mama tace “taje siyomin abinci dudda na ce mata banson cin komi” dasauri Mrs Bugaje tace “you need to eat Mama, bari na musu magana” fitowa tayi cikeda fara’a ta gaisa dasu tace “bismillahan ku a office dina za’ayi komi” ahankali Riyad yakalli Munir da Buba yace “kuje ina zuwa i need to get something in the car” yayi maganan yana juyawa sukuma sukabi Dr Bugaje.


Samin kanshi yayi da fitowa waje yana kalle kalle just to look for her lura da yayi batanan.

Daga cafeteria take, swallow tasai ma Mama da miyan kubewa sai bottle water ahankali take tafiya dukta rame batada karfi kawai gatanan ne, idanunta har yanzu basu washe ba sunyi ja sun kumbura, gashin idanunta sun tattare, tip na nose dinta is still looking very reddish sabida kuka, lips nata sun kara yin pinkish sosai sabida kuka, she’s is looking tiredly beautiful, daidai tazo ta wajajen A&E din taji an kwala mata kira. “Rashy” dasauri tajuyo Bilal ta hango yafito daga parking space yana tahowa wajen da dan gudu gudu sauri sauri yana sanye da riga da wando na jean da riga yazo daidai gabanta ya tsaya cikeda damuwa yace “tun jiya bana online ina jirgi coming back from Dubai ina dawowa kuma nahau baccin gajiya da asuban nan naga message dinki a group ya jikin Mama”? Yayi maganan cikeda so dakuma damuwa soyayyanta nawani dawomai fresh arai, ahankali dan batada karfin hayaniya yanzu ko fada tace “Alhamdulillah da sauki” dasauri yashiga tura hannu a aljihunshi yaciro wraps na kudi yan 500 guda biyu that’s 100k yana mata wani irin kallon soyayya smiling and feeling kanshi yamika mata yace “nazo nabaki this and to assure you cewa you’re not alone I’m here for you, Dad na UK but he will send his accountant to take care of all the bills kinji Rashy ko miliyan hundred ne Daddy will pay I got yo…….” Kasa karasa maganan yayi ganin wani hadadden guy yazo wajen ya tsaya dab da Rashida ga bakin shade a idanunshi yazuba hannu a aljihu kaman military, ko kadan Rashida bataji alamun tafiyanshi ba kawai taji tsayuwan mutum kusada ita dakuma kamshin turarenshi daya cika mata hanci hakan yasa ta dago kanta ahankali ta kalleshi daidai shima yana kallonta batare daya kalli Bilal ba, cikin warm yet controlling voice yace “daga ina kike?” Ya Allah! Wani irin kyau Riyad yamata dayasa takasa daina kallonshi like a little girl innocently tace “abinci naje siyoma Mama” yana kallonta still batare daya dauke idanu daga kanta ba yace “and who is this?” asanyaye tace “dan ajinmu ne” bayabo ba fallasa Riyad yace “let’s go” ko musu batayiba tajuya tafara tafiya yama Bilal wani banzan kallo da hannunshi har yanzu yake position na bada komi sannan shima yajuya.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR

EPISODE 2️⃣7️⃣


Dawani irin full confidence Bilal yazo wajen ta yau but ganin wani lafiyayyen guy me kirarran jiki tareda ita and from the way he’s doing kaman saurayinta ne yasa yaji zuciyanshi na kumfa, daman Rashy nada saurayi ne? Who is he? Waye atare da ita? Waye dan wulakancin nan? Well yasan koma waye da wuya idan yakaishi kudi he will wait she will come begging for the money yana gama tunanin yajuya azuciye yayi motanshi ya shiga yabar hospital din.

Tare suka shigo ward din daidai lokacin shima Baba Liman na zuwa da ladanin masallaci su biyu, gaisawa suka tsaya yi da Riyad ita kuma Rashida ta wuce, shiga cikin ICU Nurse din da Mrs Bugaje ta turo tayi akasa Mama akan wani wheelchair aka gungurota har zuwa office din Mrs Bugaje Rashida na biyeda ita saikuma su Riyad da Baba liman da Ladanin is duk suka shiga ciki.


Already Mrs Bugaje tasa an saka kujeru duk aka zazzauna gawasu sababbin syringe agabanta guda biyu, anatse tace “welcome to my office” sannan tace “before muyi proceeding muyi asalin abinda yakawomu nan office din, as a medical Doctor i want do something for both Riyad and Rashida” ta taso dagakan kujeranta da kanta tazo gaban desk ta kalli Riyad ahankali tace “bani hannunka” bata hannunshi yayi ta kulle igiyan tajajininsa tasa a specimen box tarubuta suna sannan tama Rashida ma haka, sannan tabama wani Nurse dake wajen data kira musamman tace “Abbakar take it to the Lab I need Asap results on this two sample kan genotype blood group HIV, hepatitis da sauransu important blood test na aure” gyadamata kai yayi yace “Yes Ma” yawuce yafita takoma tazauna takalli Riyad tace “inaso kasan wakake aure ba kokanto ba zargi a zuciyanka ko na yan uwanka dake nan wajen” Baba Liman yace “kwarai” Rashida dai na wajen Mama kanta akasa takasa kallon kowa na dakin, almost 20min akayi aka kawo result din Mrs Bugaje ta karba tarike na Riyad a hannunta tamikama Riyad na Rashida tace “take open it” karba yayi ya warware takardan ahankali, Mrs Bugaje tace “read it kowa yaji” dan shiru Riyad yayi chan yace  “genotyp AA, blood group O+, HIV negative, HEP B Negative, HEP C Negative komima negative” yayi maganan ahankali,  Mrs Bugaje ta bude na Riyad tana saka glass na idanunta like a professional tace “Genoyype na Riyad is AS Rashida is AA so you guys are compactable zaku iya aure, Blood group O+ shima, HIV, HepB and HepC da sauran komi negative, Masha Allah” tai maganan tana bama Baba Liman wanda kaman shine zai tsayama Rashida as uba, sannan tace “Alhamdulillah nayi part dina sai daura aure yanzu” faduwa gaban Rashida ya shigayi sosai, cikeda hikima na manya Buba yace “Alhamdulillah Masha Allah, muna addu’a muna kuma rokon Allah daya bawa mahaifiyarki lafiya Rashida Ameen Ameen, Mahaifin jikana ya rasu nine zan tsaya mishi a matsayin uba, sannan sunna ne atambayi yarinya nawa takeso amatsayin sadakinta, dan haka Riyad tambayi your wife to be nawa takeso a matsayin sadaki”.   Dan murmushi Mama dake cikin ciwo tayi ahankali Riyad yakalli Rashida da kanta ke kasa ki fuskanta baka iya gani da kyau sabida yanda kan nata ke kasa cikin murya mai taushi yace “nawa kikeso na biyaki sadaki?” Kasa magana tayi kai ko motsi bata iyayi itama Mama batace komiba, Mrs Bugaje tai murmushi itama tai shiru, Baba Liman yace “tunda nine zan tsaya amatsayin waliyin Amarya bari na ari bakinsu” yakalli Rashida yana murmushi yace “yarmu me kyau ce! Ga ilimi boko da islamiyya ga hazaka gakuma son iyaye dan haka bazanmuma Riyad karamin kudi ba ko Zainabu”? Duk ciwon Mama saida tai murmushi sosai hakan ba karamin dadi yama kowa na dakin ba, Baba Liman yasake murmushi yace “dubu dari biyu mukeso akudin sadaki” harga Allah yafadi haka sabida yasan basuda kudi kuma dole amata Kayan daki dazaran Mama taji sauki an sallameta saisa yasa kudi haka, hannu Buba yasa acikin babban rigan dake jikinsa yaciro wrapper na 1k guda biyu yasa akan jikin Riyad yace “tashi kaje kabata sadakinta” kallon Buba yayi cikeda so sannan yatashi ahankali har zuwa inda Rashida ke zaune yamika mata kudin cikin wani kalan murya mai taushi yace “ga sadakin ki” hannu dasauri takai ta kulle fuskanta tana rike kukan datakeji gawani irin kunya Mrs Bugaje tace “ayiriri Amarya na kunya ijiye akan cinyanta” ijiyewa Riyad yayi yajuya yakoma ya zauna sannan aka fara daura aure agaban Buba da Aminin sa, Liman da Ladani, Munir da Riyad, Dr Bugaje da Dr Usama, Mama dakuma Rashida, agaban su aka daura aure tsakanin Riyad Baba Ali da Rashida Almustapha akan sadaki naira dubu dari biyu!.



Mama na ganin an shafe Fatihan daura aure sai kawai tajawo Rashida ta rungumeta tana wani irin emotional kuka bata taba sanin Allah zai nuna mata auren yarta Rashida haka ba, itama Rashida kuka take she can’t believe ita aka daurama aure just now, wai yanzu tazama matar Riyad? Dreaming takeyi ne, tasowa Buba yayi yazo wajen su yace “kidena kuka shi ciwo na Allah ne, hakama waraka ta Allah ce, komi yayi zafi maganinsa Allah, Allah zai baki lpy kinji” gyadamai kai tayi ahankali Mama tana sakin Rashida tace “Riyad” zuwa wajen yayi yadan saci kallon yanda Rashida ke sharce hawaye Mama tace “nagode Riyad!” lumshe idanu yayi, Buba ya juyo ya kalli Rashida dake kuka sosai sai kawai yaduka agabanta hannunshi yakai yakama kuncinta hakan yasa Rashida takalleshi da jajayen idanunta, cikeda wani irin tausayin yarinyar da kaunarta dayaji Allah yasamai hakanan yace “dena kuka Allah zai bawa Mahaifiyarki lafiya kinji” gyadamai kai tayi ahankali cikeda kunya ganin tsoho dashi ya duka agabanta,  murmushi yayi mata yasa yadauki byro daya gani akan table na Dr Bugaje yace “dan tsammini takarda Docta” paper Dr Bugaje tabashi rubuta number shi yayi yabama Rashida yace “duk randa Riyad yamiki wani laifi, koya bata miki rai, call me zanzo har gidanku na sabamishi, saina ciwa mijin naki mutunci” akunyace ta sunnar dakai Mama tai murmushi sosai Buba yace “karba” ahankali Rashida tasa hannu ta amsa sannan yatashi yakalli Munir yace “muje ka maidamu gida” dasauri Riyad yace “zan maidaku Buba” kallonshi Buba yayi yace “stay da iyalanka kabar Munir ya kaini” wani iri Rashida taji jin ance iyalanka shikuma Riyad saiya gyadamai kai suka wuce suka fita nurses sukazo suka wuce da Mama aka fita da ita, ganin Riyad har lokacin tsaye a office din itakuma Rashida takasa mikewa sai hawaye take gogewa yasa Dr Bugaje ta tashi itama tace “bari na bisu” gyadamata kai yayi tawuce tafice ganin haka yasa itama Rashida ta tashi da sauri tazo zata fice kawai taji yakama hannunta, mugun faduwa gabanta yayi da saida ya lura dasauri ta kalleshi hada idanu sukayi yamata wani irin kallo kaman baimasan yarike hannunta ba gently yace “who is that guy”? Yanda yamata maganan yana kallon kwayan idanunta dasuke ajike yasa takasa jure kallonshi takasa magana, dan jawota yayi sabida yanda take so light this days kawai ta taho dab dashi gabanta nafaduwa sosai mehaka yake mata, cikin whispering voice yace “me tsakaninku”? Heart dinta na racing sosai tace “bakomi classmate dina ne” “mesa yakawo miki kudi?” Dan kallonshi tayi yanda yau yake kallonta saitaga kaman ya banbanta da yanda yasaba kallonta ada, sake sauke kanta kasa tayi tace “nayi seeking help a group namu for Mama” hannunshi dake free ya mikamata yace “your phone” dan kallonshi tayi saikuma ba musu tasamai wayanta a hannunshi ya karba a aljihu taga yasaka wayan nata ahankali yace “the next time he approaches you tell him someone owns you now! And that person is Me!” dago kanta Rashida tayi da sauri ta kalleshi yanda yake maganan kaman yaci wani competition saikuma ta gyadamai kai yace “zanje and get you food and clothes you need to shower and change” sake gyadamai kai tayi takosa yasaki hannunta dataji yana mata kaman shock, ahankali yasaki hannun yace “let’s go” tare suka fito har zuwa ICU Mama da Mrs Bugaje dake tare duk suka kallesu murmushi Mama tayi Dr Bugaje tace “congratulations Mama, Allah ya sanya albarka, Mama yanzu saiki kwantar da hankalinki ayanda nake ganin yaron nan Riyad he will protect Rashida no matter what so dan Allah kiji sauki BP ki ya sauko” gyadamata kai Mama tayi tanajin wani karfi da lafiya na shiganta.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣8️⃣


Gyadamata kai Mama tayi cikeda farin ciki dudda maganan ta baya fitowa da kyau tace “Alhamdulillah Mrs Bugaje wlh ina cikin wani irin farin ciki da bazan iya misalta miki shi ba” murmushi tayi.

Wucewa Riyad yayi yatafi yabar Rasheeda awajen, fitowa Mrs Bugaje tayi takalli Rasheeda tace “scrub in kije wajen Mamanki” da sauri ta taso tayi cikin ICU din bayan tasaka abubuwan Mama na ganinta cikeda karfin hali tasa hannunta asaman hanci tace “ayiri…..” saikuma tahau tari da sauri Rashida tazo wajen tace “Mama stoppp” ijiyan zuciya ta sauke tace “Rashida kinsan yanda nake murna kuwa naga aurenki Alhamdulillah kinga na warke tass kalli kafafuna harsun soma sakewa” kafafun Rashida takalla saikuma takalli Mama yanda taketa murmushi is not like tanason auren nan, infact ita bamata taso da burin tai aure ba sannan one single feeling batada shi for Riyad kawai dai daga jiya saita fara kallonshi ta fuska daban compare to before data tsaneshi, jiya ta gane Riyad shi mai sonsu ne ba kyamatan su ba, yana kula da Mama, shine the first person that genuinely know them kuma yasosu ahaka sannan ya tsaya musu, kallonta Mama tayi tace “me mijin naki yace? Ina yaje”? Dasauri ta kalli Mama jin kalman mijin yamata wani banbaran, murya chan kasa tace “wai zaije yakawomin kaya da abinci nai wanka” wani irin blushing da Mama keyi saida Rashida kawai ta maida Mama tv tana kallo is this aure of a thing yakesa Mama farin ciki haka ko wani abun ne dabata sani ba to wani abuma? Is just auren nan, sai murna Mama keyi. Wajajen 4 Riyad yadawo tareda Munir dake rike da basket na abinci shikuma yana rikeda wani paper bag dan babba Mrs Bugaje ta kallesu tace “yauwa I was waiting for you to come inaso na maida Mama wani daki kodan this big occasion she seems very happy, her biggest fear and worry is yartane yanzu data damka maka ita kaman 90% of matsalanta sun tafi” anatse Riyad yace “I prefer private single room” gyadamai kai Dr Bugaje tayi tasa Nurse ta gunguro Mama daga dakin tana fadamusu dakin da za’a kaita, dan satan kallon Rashida Riyad yayi dayaga idanunta sundan soma sabewa, first floor aka kaisu wani single room mai kyau da komi ciki akai connecting Mama da machine na zuciyan still sannan Nurses din suka fita ijiye abincin Munir yayi shikuma Riyad ya kalli Rashida tareda bata bag din, dan kallonshi tayi saikuma tasa hannu asanyaye ta karba murya chan kasa ta yanda dagashi sai ita zasuji maganan yace “shower before I come back, zanje mosque” gyadamai kai tayi suka wuce mosque Mama tawani yunkuro ta tashi kaman maison gulma tace “zonan mugani meya kawo miki? Imaza jeki wankan ke to karya dawo ya ganki daka daka” kallon Mama kawai Rashida take with a huge suprise kaman ba Mama ba, farin cikinta yaki boyuwa, bag din tamikama Mama, Mama ta zazzage tana fito da abin ciki tana washe baki sosai abaya ne kala uku acikin jakan duka black black amman sun hadu duba tsayinsu tayi taga 58 wlh tsayin yarta, sai cream dakuma wasu lafiyayyun turare guda biyu, daya cikin abayan Mama tazaba tadauka tabata tace “ungo wannan zakisa jeki wankan, ki chanza breziya da wando kuma, akara wanke baki ba kyau miji yaji wari” sokoko Rashida ke kallon Mama wai ba Mama ce mara lafiya ba take maganan wani miji? Ita Mama tadauka ta Riyad take she’s just after her taji sauki kawai shine burinta, just to make her happy ta karbi wanda ta zaba mata tawuce, akwatinsu tabude tadauki bra da pant tashiga bayin dakin that is very neat tai wanka ta shirya tai alwala tabude turarukan ta fesa wow saida ta lumshe idanu sunada wani irin feminine scent mai dadi, yafa gyalen tayi akai tafito Mama ta bita da kallo sabida yanda yarinyarta takoma tsaf kalan yar masu kudi tai murmushi itakuma ta shimfida dadduma tai salla Mama tace “zoki zubamin abincin bikin ki” dasauri ta juyo ta kalli Mama dake murmushi sai kawai ta tashi tawuce tadauki plate tana bude warners din ta debama Mama tuwo tazauna gaban gadon tana feeding Mama ahankali tace “Mama ai kin warke ko?” Gyadamata kai Mama tayi tace “na warke tass bakiga inacin abinci ba” murmushi tayi tace “thank you Mama dakika warke” tana cikin bata abincin suka shigo dakin duk yanda Riyad yaso ya daure karya kalleta kasawa yayi baitaba ganin abaya yama wata kyau kaman yanda yaga wannan yama Rashida kyau ba, dudda Mama bata cinye tuwon ba but taci rabi, sai satan kallon yanda Riyad ke kallon yarta take kaman tace yadauketa su tafi kawai dai dan rashin lafiya ne, Mama tace “deba kici kema” girgizama Mama kai tayi alamun bazata ci ba, Mama tace “Riyad kaga yarinyar nan batason cin abinci fa wlh sai kayi da gaske” murmushi Munir yayi duk suka zazzauna tareda Mama har magrib sannan suna tafi.


Yau kwanan Mama 3 a hospital she’s recovering like magic tun jiya sukai resuming amman kiri kiri taki zuwa taki maganan ma sabida kar Mama tace ta wuce tatafi, tana zaune tareda Mama around 8 na safe Mrs Bugaje tashigo dakin ganinta tareda Mama yasa tace “ba some of yan class naku naga a A&E ana wardround dasu ba? Wani department kike this week?” Ahankali Rashida tace “Gynae” hararanta Mrs Bugaje tayi tace “my friend stand up and go” Mama tace “wai dama sun koma?” Mrs Bugaje tace “tun jiya ma taki zuwa” dakanta Mama tayi abaya bada zafi sosai ba tace “wuce kafin na saba miki” tashi tayi tawuce wajen drawer daki tadauki jakanta taciro gogaggen lab coat dinta, daya daga cikin abayan da Riyad yasaimata ne ajikinta hakan yasa ta warware gyalen tai rolling aka sannan ta warware lab coat din tasaka tadauki stethoscope nata pink ta makala a wuya tadauki pink crocs nata tasa sannan ta dauki turaren ta fesa, tunda tana asibiti yasa bazata  dauki jaka ba, pen ta dauka ta makala a pocket nata sannan tadau wani dan jotter tasa a aljihu, earpiece nata ta dauka zatasa a pocket ta tuna haryau Riyad bai bata wayanta ba kuma takasamai magana ahankali ta maida ear piece din jaka ta rufe, ta rufe wardrobe din sannan tajuyo takalli Mama da Dr Bugaje ke dubawa tace “natafi” “adawo lafiya Amarya” dan turo baki tayi tana kallon Mama sannan tabude kofan tafito tafara tafiya tawuce staircase daidai ta sauka kasa Riyad na zuwa wajen hada ido sukayi yana sanye da wani jumper dark brown daya haska fatanshi yasa bakin glasses a ido, ranan nan Mama tagayamai tanaso ya tsaya akanta tagama karatunta na likita hakan yasa yasan yes she’s doing medicine but today is the first time yake ganinta cikin kayan dake nuna ita likita ce, ahankali yakai hannunshi ya zare glasses daga idanunshi yazuba mata mayun idanunshi, da sauri tasauke kanta kasa gabanta na faduwa azuciyanta tace bantaba ganin wanda baya kunyan kallon mace irinsa ba, murya chan kasa tace “ina kwana” batare daya amsaba koya dauke ido akanta ba yace “ina zaki?” Ahankali tace “department namu munyi resuming” yana kallonta still yace “which department” da dan kankanuwan murya kaman ba Rashida ba tace “this week ina outpatient department a gynae” gyadamata kai yayi yace “let’s go” dasauri ta kalleshi but haryayi gaba hakan yasa tabishi suka jera har ward dinsu yabita sannan ya tsaya yace “go” agabanshi tawuce tashiga consulting room 2 yadan jima tsaye saikuma yajuyo.


Mama na zaune ita kadai tai shiru tana tunani though good tunani yau take akai knocking kofan tareda sallama daga ciki tai murmushi jin Riyad ne tashigo “shigo d’ana” bude kofa yayi yashiga yana murmushi yawuce wajen gadon yaja kujera yana zama yace “you look good Mama, ya karfin jikin?” Murmushi tamai tace “Alhamdulillah ya iyalinka?” Ahankali yace “Alhamdulillah Mama” murmushi tamai tace “ka kwatanta adalci kaji, mata munada kishi dan haka ka lallashi matarka da kyau kaji Riyad” gyadamata kai yayi yace “toh Mama” cikin farin ciki tace “kaga nasoma samin sauki sosai ana sallamana muka koma gida sai afara shirye shiryen bikinku ko sabida Rashida ta tare gidan ka” gyadamata kai yayi feeling happy ganin how excited she’s with the whole wedding yace “Mama kome kikeso haka za’ayi” wani irin murmushi tayi harda dan kyalkyala dariya kadan tace “inaso ama Rashida lalle a hannu amata kwalliya saikuyi hoto kubani amaidashi frame nasaka a falona ina kallonku kullum” dan murmushi Riyad yayi yace “to Mama haka za’ayi” murmushi tayi sosai saikuma tace “tayani daga gadon na zauna” tashi yayi ya taba botur din dake dago gado gadon yataso Mama tai kwanciyan zama ya gyara mata bargo sannan yakoma ya zauna ganin tai shiru tana tunani yasa yace “tunanin me kike kuma Mama?” Ahankali tajuyo takalleshi cikin dan damuwa kadan tace “kana gani nakira mahaifinta na sanarda shi an daurama yarshi aure?” Shiru Riyad yayi, dan murmushi Mama tayi ganin baice komiba tace “I put you in a tight spot ko? Kona kirashi ma bazan sameshi ba yayi blocking dina tun lokacin amman nakan turamishi sakon waya duk ranan birthday Rashida na gayamai yarshi ta shiga shekara kaza kaza dakuma lokacin dataci jamb taci UTME aka bata admission medicine na aikamai sako amman haryau bansan ko yana ganin sakona ba ko baya gani ba” ijiyan zuciya ta sauke takalli Riyad tace “bari nabaka labari na yau Riyad”.

💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 2️⃣9️⃣


Ahankali Mama tace “ni yar jigawa ce, anan kauyenmu yake ance kakan kakana daga Morocco yake wai saisa mukeda haske, iyayenmu dani da Yayana Sama’ila suka haifa, iyayena nada gonaki da dama a kauyen mu, Babana is a very very big farmer har su CNN sunyimai interview, banda nashi gonakin yanama mutane managing gonaki kaman gonakin sarkin kano nan marigayi Baba Ali naji yarasu, Allah ya jikanshi da rahama” Ahankali Riyad yace “Ameen” yana kallon Mama jin she just mentioned Babanshi, Mama tace “dudda a kauye muke Babana yasani makaranta yace yanaso na zama yar jarida nima namai interview wata rana, yayana Sama’ila shi baiyi boko ba tare suke komi na gona da Babana, kauyenmu ba school wani next village yakesa yayana Samaila na kaini makaranta kullum a machine dinsa saina dawo da dakaina” tai shiru tace “ina JSS 3 akwai wata rana nazo gida naga wasu maza guda biyu sunzo gidanmu na gaidasu natafi dakin Mamana, so daga bayane Baba kecemin ai sarkin kano ne da kaninsa Al Mustapha sunzo wajen Baba, nace Baba ina doki bangansu da kayan sarakuna ba, to alokacin nasan ashe sarakuna na private outing suyi normal shiga kaman kowa, gasu basu wani girma sosai ba Babana ya girmesu duka dan yadan manyanta, bayan kwana biyu Baba yacemin Kanin sarki na sona” Mama tadanyi murmushi tana kallon wani zoben dake hannunta tace “kafin kace me haka akamana aure anan kauye aka tafi dani gidan Sarautan Kano”.

Wani irin kallon Mama Riyad keyi to be honest besan Mama ba, dudda yasan labarin lokacin auren anata cewa Baffa yakaro aure daga kauye and Baba supported him shiyamai auren, shida baison shiga mutane, banda hakama yawancin idan zakaga matayensu da Alkyabba zaka gansu unless you’re very close to them ko kana zuwa bangarensu you hardly knows fuskansu, ko first wife na Baffan su is because tana zuwa wajen Mom akai akai yasa yasan ta daba hakaba dabai santa ba. Ahankali Mama tace “Riyad even though Mujitappa Baban Rashida yayi hurting dina deeply bazan taba iya ignoring the fact cewa that Man loves me and care for me kaman ba gobe ba, bai bar kowa ya hantareni ba, dakanshi yake koyamin etiquette na gidan Sarauta da sauransu, yasa aka cigaba da koyamin karatu a gıda, ya kuladani Riyad bai bar kowa yayi hurting dina ba hatta Jummai kishiyata” tadanyi murmushi tace “ance tana kishi dani alokacin sabida bata haihuba then nikuma bayan bayan 1yr da aurenmu saiga ciki watan cikin daya ajikina nafara ciwo sosai da saida aka kaini asibiti lokacin anmin all test but banda HIV banda komi nadawo gida yacigaba da kuladani yana nan nan dani itama Jummai surprisingly tana kula dani, tadena min kallon kishiya, she was so happy then zan haifa musu Baby” Mama tadanyi shiru kafin ahankali tace “ina around 5month Baba na da Mama na sukai hatsari a motan dazai kawosu Kano dubani, kawai abin yakara birkita jikina ina shiga 6month nai landing hospital ciwona was serious dahar ICU aka sani cus banajin magani, banci bansha na rame kaman tsinke, akamin test dayawa the next thing was inada HIV!” Mama tai shiru tareda fuzar da iska idanunta yayi ja tace “imagine ina around 1-2 months da ciki anmin all test ba’aga HIV ba ina 6 months da ciki ace inada shi dole Muji ya yarda maza nakebi da cikina da aka fadamai inada HIV, an sashi yazo yayi test din shima da matarshi Jummai sukayi su negative abinda yasa yasake yarda da zargin inada HIV sabida laulayin ciki yasa babu abinda ya shiga tsakanina dashi tundaga watan farko harna 6 din nan cus bana iya komi Riyad mugun laulayi nayi” Mama tai shiru tace “haka nadanji sauki aka sallameni yatafi dani gida naje na samu an kira yayana Sama’ila an tara jama’a a fada dan Muji bai iya fushi ba” ta share fuskanta chan tace “koran cin mutunci, koran toxarci, koran tijara akamin agaban kowa ana nunani ana shiga barayina bayi na watso kayana waje wai sabida cikin nema ba’amin duka ba aka korani no one! No one Riyad, Babu wanda a masarautan nan ya tsayamin ba mai Martaba Baba Ali ba! Ba mai Babban daki ba! Ba sauran matan sarki ba! Babu ne kawai aka koramu ni da Sama’ila ana tunkudani” runtse idanu Riyad yayi Mama tace “munafita daga fada Sama’ila yahau zubamin Allah ya isa bai yafemin ba wannan tijaran dana jamai da cikina ina fasikanci karna sake na bishi, Riyad haka yatafi ya barni dan uwana na jini biyar babu a hannuna ni da aka sallameni daga asibiti da safen ranan, nahau tafiya a hanya yunwa menene menene naje wani gidan abinci na wanke kwanuka na kusan kwana goma sannan natara kudi natafi kauyenmu nan ma Samaila yace ban isa na zauna ba, bashi bani nace to araba gado abani yace yaji haka yaraba yabani miliyan biyu nadawo nazo ina neman gida ahaka na sami gidanmu dakake gani nasaya akan miliyan daya agine ahaka nasai yar katifa nadan natsu nafara tunanin rayuwan to me yafaru? HIV Taya zan samu? Banda Mujitapa babu namijin daya taba rikemin hannu aduniya sai Babana da Yayana.


Nai tunani nai tunani narasa tayaya nasamu, nama kaina fada natashi natafi general asibiti, na hadu da Mrs Bugaje tun tana matsayin resident Doctor ta taimakeni da shawarwari da abubuwa da dama, dakuma ilimi kan yanda ake rayuwa da HIV, duk yanda zanbi nabi dan na samu Muji ya saurareni yaki bansan ya akayiba ko bibiyata Jummai take haka ta gano gidan nan ita tazo ta fallasama kowa na anguwan mu inada HIV nice Matar kanin sarki aka koroni menene menene, dabadan nina sayi gidan ba da sun koreni tuni, ahaka cikin wahala na haifo Rashida duniya ta CS, ban bata nono ba gudun karna bata cutan, duka kudadena na gado suka kare a siyamata madara da sauransu hakan yasa na dage nafara aikatau still ina zuwa asibiti ina karban maganin HIV da ake bamu free sabida y’ata banso na mutu inaso nataso da ita inaso na rayu nayi accepting ni mutum me HiV ce,  nacigaba da renonta harna soma gazawa ta karba aiki awajena tun tana primary school sabida Rashida nada kwazo” hannu Mama tasa ta share fuskanta tace “Gidan Sarauta wani irin gidane da bada kowa ya dace ba kaman ni yanzu I’m one, haryau bansan yanda na sami ciwon nan ba but nasan it’s connected to gidan, banason wani alaka da gidan nan har abada!”.

 💫 SANYI DA ZAFI 💫

✍🏻M SHAKUR


EPISODE 3️⃣0️⃣



Faduwa gaban Riyad yayi sosai jin abinda Mama tace, ahankali Mama tace “gidan nan gave my life tabo dabazai taba goguwa ba, gidan nan yasa y’ata is like this, ranan nan i told you karka shiga maganan nan sabida Jummai can hurt you Riyad basu da imani, look at yanda suka maida rayuwana yau, look at how far they’re willing to go tana kulle innocent yarinya a police cell” Mama tafashe da kuka tace “jibeni kaman tsinke nida keda kiba and Riyad nobody stood for me yayi defending dina, tsoro ne, menene oho but kowa stood there and watch me being humiliated, Riyad those people hurt me! An min sheri anmin kazafi, na wahala sannan poor child dina ta wahala look at Rashida, all her life washing plate da washing bayuka daban daban in different organizations takeyi just to feed me and sponsor school nata” Mama tai maganan tana fashewa da kuka dayasa Riyad yatashi daga kan kujera soyake yama cema Mama sorry yakasa saikawai yajuya yafita da sauri ya shiga sauka kasa yana karasa sauka beben yana cin karo da Munir dake kokarin hayowa rikeda Basket na abinci da sauri yakama hannun Munir yashiga tafiya da sauri da sauri Munir yabishi hankali tashe yace “Riyad what happened you’re scaring me, Meya faru?” Saida sukaje jikin mota Riyad ya tsaya tareda dafa kanshi Munir dasauri yace “Riyad menene wai”? Fuzar da iska Riyad yayi ahankali saikuma yakalli Munir yace “Rashida is our cousin! Yarinyar Baffa ce!” Dawani irin sauri Munir yace “wait wait, wat”? Ya ijiye basket na hannunshi yana kokarin connecting dot din yace “Mama ce daman matar Baffa daya kora me ciki?” Gyadamai kai Riyad yayi dasauri Munir yace “but ai ni nataba ganinta sau daya tazo gaida Ammi tanada kiba could it be sabida pregnancy ko maybe lokacin ban wani yin wayau nayi ba sosai ba I think ina around 10yrs lokacin saisa ban gane ta ba?” Lumshe idanu Riyad yayi yadafa mota yana sauke ijiyan zuciya sannan yadago yakalli Munir yace “Munir Mama don’t want anything to do with our family and I’m here na auri Rashida without knowing su waye su? I want to tell Mama wayeni!” Da sauri Munir yace “idan tace ka saki Rashida fa?” Dasauri yakalli Munir saikuma yakasa magana yadan duka ahankali awajen yayi shiru even though wani bangare na cemai karya fadama Mama yanzu yabari a sallameta but another part na zuciyanshi na cemai gwara yafada mata here and now she deserves to know waye ke auren yarta, tashi yayi yakalli Munir dake kallonshi yace “let’s go” Munir baicemai komiba yabi bayanshi suka tafi ahankali yabude dakin ya shiga yaga Mama na bacci peacefully.

Ijiye abincin Munir yayi yace “she’s sleeping zomuje muyi salla” fita sukai salla by 2:00PM Rashida ta dawo ganin Mama na bacci yasa ta duddubata tai murmushi tazauna tana kallon kulan abincin tadauki plate tabude kulan jellof rice tadeba kadan cikinta harya saba bata iyacin abinci she’s really missing her phone hakan yasa ta faraci tana cikin ci aka bude kofan Riyad ne hada ido sukayi da sauri ta dauke kanta ya kalli abincin dake plate din datakeci saikuma yakaraso ya ijiye wani waya wanda ga dukkan alamu sabo ne but bai bata kwalin ba ya ijiye gefen gadon ahankali yace “be using this ur sim is inside” kallon wayan tayi iPhone ne dudda batasan iPhone nawa bane dan bata saba dasu ba bataso ta karba but kuma batasan yanda zatai rejecting wayan ba, abu tahadiye a wuyanta murya chan kasa tace “thank you” juyawa yayi haryakai kofa yace “bari naje if anything comes up call me my number is inside” gyadamai kai tayi ahankali sannan yabude kofa yafice itakuma ta tsaya tana kallon wayan kafin chan tasa hannu tadauka tana taba screen din yabude gallery tafara shiga taga all pictures nata na yar vivo nata na wajen wanda yawanci hotunan pages na textbooks datake karatu dasu a library ne sai few pictures nata da lab coat da picture nata da Mama saikuma tashiga wajen waka taga songs dinta duka akwai murmushi tasakeyi sai kawai ta ijiye plate na abincin da duka baifi 3spoons tayiba ta kwanta jikin Mama tana kallon hotuna ahaka har akai magrib Mama tadan tashi taci abinci saikuma tasake komawa bacci magungunan ta da alluran dama suna sata bacci sabida abun ka da mai BP.


Zaune suke cikin mota wuraren 8 nadare gaban A&E, bude bayan motan akayi aka shigo Jummai dataci lafiyayyen shadda tadago kai takalli officer data shigo tana murmushi tace “thanks for coming Grace” Grace tace “you’re welcome Hajiya but wat is so urgent dakika kirani asibiti” bandage dake saman hancin Grace Jummai ta kalla tace “I want to end this mutanen da yarsu tamiki this but I want to confirm something are you sure Sarkin Kano ne yazo yayi bailing yarinyar Grace?” Dasauri Garce tace “100%, Oga yafadi mana haka fa kinga yanda jikinshi ke rawa ne daya budeta” mamaki yakara kashe Hajiya Jummai tace “how did Riyad know Zainab? Lokaci da aka kori Zainab Riyad was maybe around 13 yrs, yanzu duka dukanshi he’s 36, Riyad da baya zama gida how ya sansu haryake ma’amala dasu?” Saikuma ta kalli Grace tace “yasa kayan sarki dayazo?” Dasauri tace “no Ma, nothing shows he’s a king banda bodyguard dake binshi” shiru Hajiya Jummai takarayi saikuma tadauki wayanta cus takasa yarda Riyad ne taciro hoton Riyad ta nunama Grace tace “shine?” Shiru Grace tayi bata wani kalli fuskanshi ba lokacin dazata shiga Rashida take kallo but kaman shi hakan yasa tace “eh kaman shi but I’m not sure kinsan da daddare yazo and bana officer dasuke fitowa ne nikuma nake shiga” gyadakai tayi tace “okay” sannan tadauki wata bakar ViVa leather tabata tace “use this hold body I will look for you soon when it’s time to cook the girl up” murmushi Grace tayi tana hango how thick ledan looks da kudi ta karba tace “Hajiya I will remain loyal forever and ever thank you Ma saida safe” tabude motan tafice ta maida ta rufe Hajiya Jummai takalli wata mata dake gaban motan bakakirin da ita fuskanta sai uban muni ga kujera tace “kin shirya aikin ki Yar Mussa?” Da sauri matan tace “kwarai Hajiya! Rayuwata taki ce” Hajiya Jummai tai murmushi tana kada kafa tace “sauka kije ki tabbatar kin zuba ko a abinsha ko a abin ci, saikinzo gida” Dasauri tace “toh” sauka tayi anan parking space tawuce tana gyara hijabin jikinta sannan tawuce ta shiga cikin A&E tana sunnar da kai kasa, dakin cleaners tawuce dinsu tawuce anan ta dauki roban mop ta cire hijabi tasaka wani green riga da wando uniform sannan tafito ward tashiga gogewa tass kafin tawuce sama first floor lokacin 9:00 knocking gaban kofan 211 tayi but shiru hakan yasa tabude tashiga ciki Mama na bacci ga drip ga komi na aiki, Rashida itama tana zaune kan kujera but ta kifa kanta kan gadon takama hannun Mama tana bacci tana minshari kadan kadan dan bata gaji sosai yau ba, maida kofan Yar Mussa tayi tarufe tace “laaa nazo goge goge suna bacci” ta tsaya takalli dakin tass babu CCtV, bude idanu Mama tayi kadan dan ta dade tana bacci da sauri Yar Mussa ta juya taciro mop tashiga goge gogenta, dan tari Mama tayi jin wuyanta ya bushe sosai murya chan kasa tana kallon mai moping tace “dan taimakamin da ruwa” ijiye mop din Yar Mussa tayi ta juyo da sauri ta taho tace “to” dukawa tayi tadauki bottle water guda daya daga jakan bottle water dake wajen tanajin dadi azuciyanta tace “perfect opportunity” tabude goran tana tura hannu a aljihunta da sauri taciro wani syringe dake dauke dawani substance ta matsa da sauri aruwan tana jijjigawa, ahankali Mama dataji shiru tace “bakiga ruwan bane ko Rashida ta chanza musu wuri ne? Bude fridge kika dan Allah” Da sauri ta taso tana murmushi tace “a’a nagani” tamikama Mama goran tana ijiye marfin goran saman gadon sannan tajuya tacigaba da moping din da sauri da sauri, sosai Mama tasha ruwan thirsty kusan rabin goran tasha sannan tadauki marfin ta rufe, Yar Mussa  tagama moping tazo gaban gadon takalli ruwan da Mama tarage tace “dan Allah dan bani Insha nima kishin nakeji” Mama tace “kidauka karkisha ragowana” dasauri matan tasa hannu ta fizge ruwan har saida gaban Mama yafadi hakanan hakan Yar Mussa tace “nadau sabo bazan shanye ba wannan ya isa karmuyi asara bari naje kiyi bacci abinki” tana maganan tayi kofa bayan tadauki mop da bucket tabude kofan tafita tashiga next room tacigaba da aikacenta.


Mama tabita da kallo saikuma tace “hala batasan inada HiV ba” saikuma takalli Rashida da yau bata minshari sosai sabida batai aikin wahala sosai ba tashafa kanta tana murmushi tace “Amaryan Riyad” knocking akayi aka shigo office din Dr Bugaje ce sanye da scrub tana kallon Mama tace “kinga sai yanzu nafito daga surgery nan dana gayamiki wlh nace nadubaki kafin natafi, akwai wani abu dake miki ciwo?” Tayi maganan tana makala stethoscope dan duba heartbeat na Mama, Mama tace “lafiyana kalau wlh kaman ki sallame ni gobe ma naje nafara shirye shiryen bikin Rashida” dan dariya Mrs Bugaje tayi tace “mother Inlaw of the year Mama” kafafun Mama ta kalla da sun sabe kusan rabi tace “Alhamdulillah Mama kin sami lafiya sosai Welldone Mama, you’re a superwoman, wannan hartai bacci” tanuna Rashida, Mama tace “ai Rashida gatada nauyin bacci kamanme” Mrs Bugaje tace “tom bari naje Mama saida safe, banda tunani kinji ko” murmushi Mama tayi tace “to nagode, a gaida yara” juyawa Mrs Bugaje tayi hartakai kofa Mama tace “Doctor” juyowa Mrs Bugaje tayi Mama tace “ina alfahari na sanki, nasan ko bani Rashida nada wata uwa da mentor, thank you for everything” dan blushing tayi tace “Mama stop thanking me ki warke sabida ki koma gida nan da jibi ko gata” Mama tace “shikenan a kiyi tuki ahankali dare yayi” “toh” tafadi tana fita Mama kuma tashiga shafa fuskan Rashida har bacci yasoma kwasheta kafin chan bacci yayi nasaran dauketa.


Jijjiga da bed keyi up and down yasa cikin nauyayyen bacci Rashida tadan bude idanunta sabida yanda motsin ke mugun damun kanta, kafin chan motsin yayi yawa tabude idanun gabaki daya tana tashi zaune, Mama tagani tana wani bankarewa tana kama cikinta tana. “Hasbunaallahu wa ni’imal wakeel, Lailaha illallah wayyooo cikina wayyooo cikina” dawani irin sauri Rashida tai ihu. “Mama” daidai Mama tawani irin mirgino zata fado daga gado Rashida ta tareta takamata ajikinta tama rasa mezatayi, bata taba ganin Mama in this pain and agony ba cus tanada dauriya na ban mamaki, kankame Mama tayi datake abu kaman zata tashi ga kafafunta basa motsi tsabagen azaba tace “Rashida cikina wayyooo Rashida cikina, Rashida cikina” “somebody help me Doctorsssss!” Rashida tai wani irin ihu daya dauka ako’ina daidai lokacin kawai hancin Mama yafara fitowa da jini dayasa tasake buga wani uban ihu. “Doctors” daidai nan Dr Mumina dawasu nurses suka shigo ganin Rashida da Mama akasa yasa tace “meya sameta”? Jikin Rashida kawai rawa take bamata iya magana ba, kankame Mama tayi a hannunta Dr Mumina tashiga saka handglove hakama Nurses din wasu Drs ma na shigowa aka daga Mama daga jikinta aka daura akan gado Rashida na wani irin kuka tace “wat happened to her? Why is she bleeding daga hanci” Dr Mumina tama Nurse alamu tafita da Rashida wayanta Rashida ta dauka Nurse tafita da ita, rawa jikinta yake tana tsaye awajen Doctors sai zuwa suke ana shiga dakin da Mama ke, tanajin wayyyoo Allah cikina, cikina abinda Mama ke fadi kenan, tunda ta taso bata taba ganin Mama tai ihu tana kururuwa for ciwo ba sai yau, chan Rashida taji ana call Professor call him fast, taga nurses sun fito da gudun gaske sai kawai taji kafafunta na lankwashewa ta zube akasan wajen flat hannunta ya shiga rawa tabude wayan nata tashiga contact taga Riyad hakan yasa tai dialing number.


Yau sabida damuwa yamai yawa koda yagama abinda zaiyi da Haleema anan kan gadon ya kwanta bayan yayo wanka, wayanshi yahau kara hakan yasa yabude ido is so odd akirashi da night wayan yatashi yadauka Rashida tafito jikin screen din dayasa kawai yaji gabanshi yafadi fita yayi daga dakin yasauko kasa daidai wayan na katsewa yayi dialing number back yana ringing ya daga. Anatse yace “meke faruwa?”Nunfashinta kawai yakeji bata iya magana da kyar tace “zan…..zan mutu” katse wayan kawai yayi yakoma sama yashiga saka kaya Haleema na tashi dan tun ringing na wayan ta tashi tace “ina zaka Baby”? Ahankali yace “sleep fita zanyi” zatai magana yadauki car key yafita da sauri yashiga motanshi yana danna remote gate yabudu yaja motan aguje  dayake dare ne wlh cikin 5 good minutes ya iso asibitin sama yahayo aguje, tana zaune a inda take akasa ta hangoshi yana tahowa yana kallonta she felt as if her strength is coming towards her, dawani irin gudu cikin kuka ta tashi tai wajenshi batai wata wata ba tawani irin fada cikin kirjinshi ta kankameshi gamgam kaman wani zai rabata dashi tana wani irin kuka tama kasa magana, ahankali yasa hannunshi on her back yariketa yama kasa magana sai breathing fast, suna ahaka saiga Mrs Bugaje da hijabi tana gudu sosai tawuce su tai dakin kawai his mind tell him something hakan yasa yayi hugging nata so tight tareda manna mata peck a wuya, cikin wani irin murya na lallashi yace “stop crying Jewel, come” yadagota hannu yasa ya sharemata fuska yace “I’m here now Mama will be fine kinji”? Gyadamai kai tayi yakama hannunta saiya sauka kasa da ita yayi wajajen wasu kujeru ya zaunar da ita yaduka agabanta yace “stay here bari naje sama naga meke faruwa” gyadamai kai tayi yatashi yajuya yakoma sama gabanshi faduwa kawai yake non stop, direct yabude kofan dakin daidai lokacin da babban professor kecewa ke daga hannunshi yana kallon wristwatch dinsa yace “Time of death 4:57AM” chak Riyad ya tsaya kanshi na wani irin making bell sound yashigabin kowa na dakin da kallo tundaga kan Mrs Bugaje datai mutuwan tsaye tanama Mama wani irin kallo da idanunta ke kallon sama ga jini a hancinta da bakinta na gangara har lokacin, kafin ahankali Professor yakai hannunshi dake sanye da glove ya rufemata idanu sannan yaja farin zanin gadon yarufeta.



EPISODE 3️⃣1️⃣

Sarawa kawai kan Riyad keyi, Mama dasuka gama hira jiya, he left this hospital shida Munir jiya around 7 Mama was absolutely fine tana bacci, Mama was out of danger, kafafunta kumburin sun soma sauka, now tarasu? Yakasa anything tunanin, ahankali Mrs Bugaje tasa hannu tadauki wayan Mama data gani saman fridge tajuyo takalli Riyad that looks terrible tabashi wayan anatse tace “call Baba Liman!” Saikuma muryanta na rawa tace “how do I face Rashida?” Hannu yasa ya karbi wayan cikeda taurin zuciya na maza yadanna wayan yaga Baba Liman a dial calls yakira asuba tayi so wayan na ringing yadaga da sallama me sanyi ganin lokacin da ake kiranshi da wayan Zainab, ahankali Riyad yace “Baba Riyad ne Allah yayima Mama cikawa!” “Innalillahi wa Innailaihi raji’un! Allah ya gafartama Zainab! Zainab Allah yasa karshen wahalan kenan! Nazo ne ko zaku taho da ita? Ahankali Riyad yace “zamu taho da ita” Baba Liman yace “toh! Allahu Akbar akwai lokacin da Zainab ta taba bani number dan uwanta Sama’ila tace duk randa ta mutu nakirashi nagayamai shi kadai ne jininta daya rage aduniya, hakkine agari ni nayi hakan bari nakirashi” ahankali Riyad tace “toh” yadaga wayanshi yakira Buba yakira Munir duk sukace gasunan zuwa, yakalli Dr Bugaje yace “lemme get Rashida” gyadamai kai tayi tana hawaye maganan da Mama tamata dazu na dawomata sabo azuciya.

Rashida na zaune inda ya ijiye ta gabanta sai faduwa yake none stop bini bini tana goge hawaye, kamshinshi kadai taji hakan yasa tadago takalleshi wani irin tsawaa kirjinta yayi sabida yanda taga idanunshi sunyi jaaa, amman ta daure tana dafa kujera tamike tsaye ta tako zuwa gabanshi ta tsaya tahau bude baki tanaso tai wani specific tambaya but tambayan yaki fitowa daga bakinta, Riyad jiyayi zai fashe da kuka ganin reaction na Rashida, runtse idanunshi yayi dayasa Rashida tawani irin kurma ihu a inda suke tace “nooooooooooo!” Saikuma tabi ta gefenshi ta kwasa da gudu tai sama yabita shima, ahankali tabude kofan Mrs Bugaje tafara gani tsaye idanunta sunyi jaaaaa hakan yasa tafara kokarin daga kanta tanaso takalli gadon dakin amman tana tsoron kallo kafin ta daure ta kalla taga Mama kwance an lullubeta da farin zani, wani kalan lankwasewa kafafun Rashida sukayi nan daidai Riyad na shigowa yazo gabanta ya duka gadon tamai pointing tana nunawa da hannu still takasa magana sai kuma tafara wani irin jiniya tace “Ma………Ma……..Mama na……..ni……” kaman ta zare ta nuna kanta tace “ni……Mama…..Mamana……Maman Rashida…..ni….ni…..Mama na ni, nawa My Mama achan”? Kai! Wani irin fadowa hawaye sukayi daga idanun Riyad yanda kalaman ke fita daga bakinta adaburce, akuma hargitse, ya gyadamata kai gently yace “Mama ta ras……….” “Noooooooo!” Rashida tai wani irin ihu tafashe da wani irin kuka da majina yafeso daga hancinta har zuwa baki tana wani irin babbaka kuka tana dukan kirjin Riyad da babu karfi a hannunwanta, daidai Munir ya iso shima yaci birki ya tsaya yana kallon yanda Rashida ke kuka beating Riyad chest, kuka Rashida take dake tsumarai daidai nan shima Buba ya iso da manyan abokanenshi mota guda sukayo dawata mota doguwa cikeda hikima da dabara yace “Munir kayi procedures kabiya komi abamu gawanta mutafi dashi” yakalli Riyad yace “Riyad take her to the car kujiramu tunda bamusan gidansu ba” ahankali Mrs Bugaje tace “I will go with you Riyad nima bansan gidan ba” daga Rashida dake kuka yayi kawai ta sheme a suma daukan ta yayi chak yawuce mota ya ijiyeta abaya.



*SANYI DA ZAFI*


*EPISODE 32*

Cikin minutes Buba yayiarranging canopy ganin ranayasoma fitowa ga jama'a atsaye, aka kawo taburmaitundaga makarantan sa akashimfida awaje, Munir daRiyad suka kawo likafani dahandglove da turare dasuaudugu Matan anguwa dukababu wacce tai attempting yimaMama wanka da Mrs Bugaje ketambaya duk sunki karsu samiHIV, wai tsoro, hakan yasa MrsBugaje ta karbi komi tashiga kairuwa ciki ita zatayi.

Ahankali Rashida ke budeidanunta takalli Mrs Bugajedake kanta anatse tace"Rashida!" Tashi tayi zaune dagudu tana kallon matan layinsuda hijabai da suka cika falonwasu na kuka suna kallontawasu na mata kallon tausayisai kawai ta tashi kamanwacce bata hayyacinta tayiuwardaka tana daga labule MrsBugaje taje wajen tace "zanmaMamanki wanka Rashida come"


sannan tawuce ciki Rashidatabita tazauna tana kallonMama kuri, handglove MrsBugaje tasaka sannan tafaraRashida sai kallon Mama take,zata kuskurema Mama bakitaga bakin Mama yayi greenda abin saida yasa tabudebakin Mama da kyau har throatdin Mama was green dasauritakalli Rashida but from the wayyarinyar ke kallon Mama kasanbata hayyacinta saita fasamaganan takarasa yima Mamawan

Wuraren 8:10 wani dan dattijonmutum dake kama da Mamayasauka daga machine danBaba Liman yamai kwatance,hannunshi rikeda da yar jaka,fuskanshi ba yabo ba fallasayashiga yima jama'a sallamaBaba Liman na ganinshi yace"Sama'ila ya hakuri"? Ahankaliyace "hakuri sai ma'aiki" butaaka bashi yazauna yafara alwalaRiyad sai kallonshi yake irinhope you're happy yanzu tamutu? Yana gamawa da Riyadda Munir da Baba Liman daBuba dashi Samailan sukaicikin gida har zuwa uwardakanda makara Rashida na zaunetana kallon Mama da anriga anshiryata tsaff tagansu Riyad saikallonta yake yanda take kallonMama ganin zasu dauketa yasatarushe da kuka tahau kabar da

mutu? Yana gamawa da Riyadda Munir da Baba Liman daBuba dashi Samailan sukaicikin gida har zuwa uwardakanda makara Rashida na zaunetana kallon Mama da anriga anshiryata tsaff tagansu Riyad saikallonta yake yanda take kallonMama ganin zasu dauketa yasatarushe da kuka tahau kabar dahannunsu tace "wallahi Mamana da rai wlh kubarmin ita, zatatashi" zata kama makaran Riyadyariketa kuka take da haki ganinan dauketa ansa aciki an dagamakaran saita kara sumewaajikinshi karbanta Mrs Bugajetayi yatashi suka fice aka sallaciMama aka kaita makwancintaRashida bata tashi ba.


Wuraren 1 suka dawo dagamakabarta akai sallan zuhursannan aka kawo abinci wandaRiyad yasa Munir yakira hotelkitchen nashi aka dafa akakawo abinci a big big kulaakakai cikin gida bangarenmata sauran kulan waje,abunka da anguwan yaku bayi

mata sauran Kuan waje,abunka da anguwan yaku bayisai jama'a suka fara tururuwakaman gidan biki ana zuwa cinabinci anama Mama addu'a.

Riyad dinma gashi nan ne kawaitunanin Rashida yake kuma bahalin ya shiga cikin gidan danmata sun cika gidan, yaki kulauncle din Rashida Sama'ila,yadaiga Baba Liman namaiexplaining komi chan yakiraRiyad din yace "bismillah Riyad"bayabo ba fallasa yazo wajenyabashi hannu Sama'ila yakarba yace "Allah sanya alheri,Allah baku zaman Ipy" AmeenRiyad ya amsa ahankali sannanyatashi daga wajen.

Wuraren 2 Rashida tabudeidanunta dake mata nauyikaman duwatsu Mrs Bugajedake kusada ita ta kalleta dasauri tace "kin tashi" fuskanMrs Bugaje take kallo chankuma cikin yar muryanta dabata fita sosai bakinta nawaniirin rawa tace "da gaske Mamana tarasu"? Yanayin sigan dayanayin da maganan yafito

yanayin da maganan yafitodaga bakin Rashida sai kawaiyasa hawaye ya sauko dagafuskanta ta gyadamata kai kafinahankali tace "yes RashidaMama tarasu har an kaita, prayfor Mamanki, yar aljanna ceMama in sha Allah wani irinnumfashi Rashida keyi kamanzuciyanta zai bare yarabebiyu sai kuma ahankali tanadaga kwance awajen kawaitajuyama Mrs Bugaje baya tamanna fuskanta a bango tanawani irin kankame jikinta isas if ma batasan metakeyi ba,ahankali Mrs Bugaje tadaurahannu kan jikinta ta dagotatana kallon fuskanta yanda yayijajir gabaki daya tace "Rashidacry Mama tarasu" sarawakanta yayi takulle idanuntatace "Mama na, Mama?" MrsBugaje tace "eh Maman ki" tanama Mrs Bugaje kallon asalinwacce bata hayyacinta tace"to menene amfanin rayuwanayanzu? Banda kowa Mama tatafi, Rashida batada kowa!"Fashewa da kuka sosai MrsBugaje tayi sabida tausayinRashida dayasa matan falon

Rashida dayasa matan talonsuka taso suna shigowauwardakan jin sautin kuka sosaikawai Mrs Bugaje ta kankameRashida gangan ajikinta tace"Rashidaaaaaa l'm so sorryabout your Mom, wayyoooAllah kirjina Rashida yau kinbani tausayi kaico! Naso aceAllah yana barin wani dan wanidanasan definitely zai barmikiMama, Rashida kiyakuri karkicebakida kowa wlh kinada mu,gani ga mijinki Riyad ga BabaLiman, Rashida you are notalone" duka yan dakin kallonRashida suke da aka rungumeidanunta sunyi jajir da fuskantaamman bata kuka idanuntama kaman sun juyane batasanmetakeyi ba gata nan ne kawai.


Mrs Bugaje saida tai kuka tagodema Allah sannan tasakiRashidan tace "muje kiyi salla"kallonta Rashida tayi tace"salla an kirako bari nafara kaiMama tai alwala saini nayi"tafita daga jikin Mrs Bugajeda sauri tana mikewa tsayetayi falo da sauri, Mrs Bugaje


tama banamataaIai Motn

tayi falo da sauri, Mrs Bugajetama kasa motsawa sai MatanBaba Liman ne ta tashi da sauritabita tace "Rashida' tsayawatayi tajuyo takalleta tace "laaaanatuna kayan Mama nazodauka" tawuce uwardaka dasauri tabude sip tadauki wanikaramin jaka tashiga sakarigunan Mama awajen tace"bari nai sauri" tamaida sipdin tarufe tajuyo kowa yakasacemata komi tayi falo kotakalmi bata sakaba tarike jakangam tana tafiya Matar Limantabiyota da gudu tanajan wanihijabi data gani kan igiya tana"Rashida Rashida" ganin batajitafiya kawai take yasa tafarakwalama mijinta kira. "MalamMalam" amman har Rashidatafito tayi gaba Riyad na zauneyaga fitowanta dasauri yatashidaidai Matan Liman na fitowaitama tace "Malam Rashidatahada kaya wai zata kaimaMamanta a asibiti" tareta Riyadyayi takalleshi da sauri tananunamai jakan tace "Mamazan kaima kaya jirana take"kallonta yayi daga sama harkasa ba takalmi akafanta da


Ronta yayi daga sama harkasa ba takalmi akafanta dagaita sai abayan daya siyamata dadankwali daure akanta fuskantais looking reddish.



*SANYI DA ZAFI*

*EPISODE 33*


Hannunshi daya yasa yarike mata hannu yamikamamatan Liman dayan hannunshi alamun tabashihijabinta bashi tayi yajuyo yakalleta ya warwarehijabin yana kokarin samata ahankali yace "to sakahijabi kafin kitafi" yayi maganan yana samata hijabiya kalli jakan data rike gangan yace "babu safaajakan Mama tace ki kawo mata safa muje ciki kidauka saimuje" wani irin murmushi ta sakinmai dayabayyana fararen hakoranta tajuya da sauri tai cikingidan batare data kalli su Buba dasuka tattashisuna kallonta ba anatse Liman yayi sallama cikingidan mata suka amsa Buba ma yabishi ciki yanamaSama'ila magana yace "muna bukatan ka muje"tashi yayi yabisu sai Riyad shima yabisu falon sukashiga Matan Liman tace "tana ciki tana zazzago dakayan durowas su" ciki suka shiga hakan yasasauran matan dake dakin suka fito banda MrsBugaje dahar lokacin take inda take, jikin kofanuwardakan Riyad ya tsaya yana kallonta dawani irintausayi aka zazzauna Baba Liman yaje gabandrawer ahankali yace "Rashida" batare data kalleshiba tace "sauri nake safa nake nemawa Mama"hannunta yarike chak dayasa tajuyo takalleshi cikinihu yace "Rashida! Ki natsu! Maman ki tarasu!"Tarasu! Tarasu!! Tarasu!! Haka kalman ke singing abrain nata dayasa tai wani irin ihu tana taushekunnenta tawani zube awajen tace "nooo" ahankaliBuba yace "yanadaga cikin shikashikan musuluncishine imani da kaddara mai kyau da mara kyau,Allah yama Mama cikawa, ga dan uwan Mamankiyazo daga kauyensu" yanuna Sama'ila dake kallontayace "mutuwa ba dadi Rashida amman kiyakuri, kidaure, ki cije ki hadiye, kima Mamanki addu'a,agabank12:08


Maman Rashida...ni...ni....Mama na ni, nawa MyMama achan"? Kai! Wani irin fadowa hawaye sukayidaga idanun Riyad yanda kalaman ke fita dagabakinta adaburce, akuma hargitse, ya gyadamatakai gently yace "Mama ta ras......" "Noooo000o!"Rashida tai wani irin ihu tafashe da wani irin kukada majina yafeso daga hancinta har zuwa baki tanawani irin babbaka kuka tana dukan kirjin Riyad dababu karfi a hannunwanta, daidai Munir ya isoshima yaci birki ya tsaya yana kallon yanda Rashidake kuka beating Riyad chest, kuka Rashida takedake tsumarai daidai nan shima Buba ya iso damanyan abokanenshi mota guda sukayo dawatamota doguwa cikeda hikima da dabara yace "Munirkayi procedures kabiya komi abamu gawanta mutafidashi" yakalli Riyad yace "Riyad take her to the carkujiramu tunda bamusan gidansu ba" ahankali MrsBugaje tace "I will go with you Riyad nima bansangidan ba" daga Rashida dake kuka yayi kawai tasheme a suma daukan ta yayi chak yawuce mota yaijiyeta abaya.


Within 1Omin Munir yagama komi aka basu Mamasuka sata abayan luxurious hadaden bus dasukazodashi akaja motocin lokacin 6 yawuce na safe akatafi Riyad na gaba har anguwan su da alreadymutane sun taru a layi da masallaci, parking akayi,aka fasa key dake kofar gidansu sannan aka shigagidan da Mama Matan anguwa suka faffara zuwaana shiga cikin gidan, Riyad yadauki Rashida daharlokacin take a sume itama yayi ciki da ita MrsBugaje ta karbeta Baba Liman ya sanar za'ai sallaby 9 danuwanta zai iso anything 8:00dagakauyensu.



*EPISODE 34*

Shiru Riyad yayi saikuma yace "just ka kawominkayan sawa gobe, I can't leave her alone like this,she has no one, babu anybody a anguwan dayayimaking attempt yama kwana da ita" gyadamai kaiMunir yayi yawuce yatafi shikuma yakoma cikingidan batare daya kalli Sama'ila dake zaune a kofargidan ba, falo yashiga yawuce uwardakan tanakwance inda ya barta tana bacci lips nata yagasuna motsi ahankali yaduka awajen yakai hannunshisaman goshinta yaji jikinta kaman wuta wayanshiyasake cirowa yayi dialing number Mrs Bugaje dayakarba ringing daya tadaga ahankali yace "she'srunning temperature Ma" ijiyan zuciya Mrs Bugajetasauke tace "she must! Ko ruwa batasha ba tunsafe, if you can get her to eat something kafin nankabata paracetamol idan temperature yaki kwanciyaget water and towel kadan goga mata ajiki" ahankaliyace "okay" katse wayan yayi yatashi yafitacompound kulolin abincin da aka kawo daga hotelnashi yaje yaduba babu komi ciki an cinye tass,makota ma sun wanke a ijiye wucewa yayi wajeganin yanda Sama'ila ke kallonshi yasa yace "barina sayo mata magani bata da lafiya" gyadamai kaiyayi yace "toh Allah sawake" mota yashiga yabarwajen, shikuma Sama'ilan yashigo ciki uwardakanyaje yakalli Rashida dake sambatu cikin baccinzazzabin Mama kawai take kira, girgiza kai yayikawai yatashi yafito tsakar gida ya shimfida tabarmaya ijiye pilow daya dauko a uwardakan su damanyariga yasa gidan akasuwa yana saidawa yabamayar gadonta Alhamdulilah ta aurar da ita batabarmai kaya akaiba yaji bala'in dadın hakan mijintava tattarata sutaur can kauyan su agayara kwanciya



*EPISODE 35*

Zufa yaji yana keto mata sai nishi take, ahankaliyadagota yakalli jikinta dasauri yadauke kai whitesinglet ne acikin dogon rigan da white inner skirtperky huge boobs nata daya gani yasa yadauke kaidasauri dan da abayan zai ciremata saiyaji yakasasai kawai ya rungumeta yana shafa bayanta itakumatafara lumlimshe idanu ahaka yana shafa matabayan genuine bacci yadauketa ajikinshi shimaahaka yayi baccin rikeda ita thank god yasawayanshi a silent dan kiran Mom dana Halima saidaya kashemai batir.


Yadanyi nisa kadan a bacci yaji tana rawa dakafafunta cikin bacci bude idanunshi yayi yakalletafrom the way she's doing yasan fitsari takeji baijintayi fitsari jiya all through ba dasauri yatashi yanadagata bude idanu tayi kadan takalleshi hannunshiyasa yakamata suka fice Sama'ila na tsakar gidankan tabarma yanajan minshari hanyar daya ganiyake kyautata nan ne bayinsu yayi da ita kafin sukaifitsarin yazubo mata tsayawa tayi chak ta kalli kasahakan yasa shima ya kalli kasan sai kawai tafashedawani irin kuka mara sauti dayasa ta bashi tausayiahankali yace "shiga bayi lemme get you water andanother clothes" Wajen wasu robobi daya gani yajega karamin basket na sponge da soap kawaiyadauka yadawo inda ya barta ganin bata motsaba,hannunta yakama sannan yabude bayin that is veryclean yasamata bucket din da basket na soso yace"shiga bathroom" hannu tasa tagoge fuskantatadaga kafanta da kyar ta shiga bayin, shikumayakoma daki yabude wardrobe nasu but almostduka kayan wajen na Mama ne daga yanayinsu waniganamasgo daya gani yaje wajen yabude kayan tane duka agage very neat Dogowar riga daya fara

duka kayan wajen na Mama ne daga yanayınsu wanlganamasgo daya gani yaje wajen yabude kayan tane duka agoge very neat dogon rigan daya faragani a sama na atampa ya dauka yaga pant yagabra dudda sun tsufa but they look neat daukansuyayi yakoma hanyan bayin yace "here are theclothes nasa miki akan rope" yawuce yadawocompound ya tsaya andan jima chan sai gata tafitobutansu tadauka ta tsugunna tana alwala sai kukamara sauti take sannan ta tashi takoma ciki yabi tada kallo yakalli kayanta dayaga ta shanya ma tawanke abayi dawowa yayi dakin yaganta kandadduma tana salla tana kuka zama yayi yanakallonta ta rama sallolinta na jiya sannan ta kwantatana kallon gefe daya yanajin sheshekan kukantahar aka kira asuba yatashi yatafi mosque.


Bayan yayi sallan asuba hotel nashi yakoma yayiwanka ya chanza kaya dan nan Munir yakaimaikayan, wajajen 7 yadawo gidan with breakfast natabut luckily yaga tana bacci Mrs Bugaje itamahartazo tanaso tamai magana but tanaso tagamainvestigation.


Yau 3days da rasuwan Mama, Riyad shi kadai yakekwana da ita ganin yanda babu wanda zaiyi hakan,he noticed batada friends, wayanta has been withhim but babu wani wanda yakirata banda some fewplaces datake aiki dasuka kira suna nemanta yaamsa da tadena aiki. Bata magana da kowa, theonly thing dayasan yana bata ta amsa is that coffeeko abinci bataci, dudda kawunta Sama'ila try talkingto her amman ko kallo bai isheta ba haryau takidaga fuska ta kalleshi.


Wuraren 8 Riyad yayi parking akofar gidan yagaSama'ila akofar gidan dawani mutumi kalakalan sadan kauye da Baba Liman, kashe motan yayi daidai lokacin yane salIama da mutane yana kurban ledan

more, Rashida have to start a new life away fromthis hausa da Mama ta raineta ta girma ta tasoaciki, death is painful! Rashida yakalla yaje indatake hannunshi yasa yadagota tadan bude idanuntakadan dasuka kumbura ahankali yace "let's gohome" hijabi yadauka yasamata sannan yadagatayajata dan kaman bata gane komi harzuwa waje,bayan mota yabude mata yasata aciki ya kwantarda ita sannan yarufe kofan yakarasa zuwa wajenmasallaci yasami Baba yace "Baba zamu tafikayansu na dakin za'a iya rabarwa idan da masu so,ko akai gidan marayu, sai watarana Baba" yabamaBaba hannu, Baba Liman ya amsa yace "karikeRashida amana marainiya ce ba uwa ba uba kawukuma kaga kalansa, duk randa ta zama likita kugayyace mu zamuzo Allah maka albarka Riyadyanda mahaifiyarta ta yarda dakai haka nima nayarda dakai dari bisa dari, nasan bazaka cutar daRashida ba dan haka Allah baku zaman lafiya, Allahya albarkaci aurenku" ahankali yace "Ameen" harmota Baba Liman yarakoshi ko kallon Sama'ilaRiyad baiyiba ya shiga yadauko kudi yabama yarananguwa, sannan yakara dauko bandır na 1k gudabiyar yabama wani babban matashi yace yakaimaBaba Liman yasan yabashi bazai amsaba, sannanyaja motan yabar anguwan feeling emotional,rayuwa kenan! Kowa fa saiya mutu is just time!.


*EPISODE 36*

Bini bini yake tuki yana lekata ta mirror na motaidanunta a lumshe suke fuskanta is swollen isreddish, tun ranan datai wanka haryau bata karaba,wayanshi yadaga yakara a kunne yana driving dahannu daya chan yace "idan akwai any bayi a sidenaku or ma'aikata send them away, and stay wajengate idan nazo i will call you to open it for me"katse wayan yayi ya ijiye yasake kallonta kusan20min tafiya sukayi dan akwai holdup a hanyasannan yakai zagaye yayi again sabida ta indayakeson ya shiga yana sake kiran Munir sannan yaijiye wayan yana kaiwa gate din Munir yagani tsayeyabude gate shiga da motan yayi Munir ya maidagate din yarufe sannan yajuyo da sauri yatahoshima Riyad na saukowa daga mota Munir yatahowajenshi da sauri cikin whispering yace "tarekuke?" Gyadamai kai Riyad yayi Munir yace"mezamu gayama Ammi cus kasan Buba baigayamata ba, wat are we going to say?" Dan ijiyanzuciya yasauke ahankali yace "I don't know" shimaMunir shiru yayi Riyad yajuya yabude bayan motanjakan goyonta yafara dauka yajuyo yabama Munir yakarba sannan yakalleta ahankali yanda idanunta kearufe kafin yasa hannunshi gently yadagota kamanbabu jini ajikinta tasowa tayi tana bude idanuntakadan hawaye na zubomata shiru yayi yana kallontakaman yazare kowani irin pain takeshi shi ya karba,saikuma ahankali yasa hannunshi yakai kanfuskanta ya share fuskan nata murya chan kasayace "we are home let's go" hannunta yakamayafito da ita da kyar take tafiya haka sukai cikiMunir biyedasu abaya ahankali yasa hannunshiyabude kofar flat din Ammy da callama yar gajera

Munir biyedasu abaya ahankali yasa hannunshiyabude kofar flat din Ammi da sallama yar gajeraabakinshi Ammi na zaune a falo kan kujera ta ijiyeMacBook akan cinyanta tasaka glasses tana aiki,sallaman dataji yar kadan yasa tajuyo da kanta hadaido tayi da Riyad dake kallonta dasauri yasaukekanshi kasa tabishi da kallo da yar matashiyandataga yarikema hannu kanta na jikinshi ta jinginadashi idanunta a lumshe saikuma Munir dataganiyarike bagpack yayi tsuru kawai ranta yabata waniabu amman tadaure tace "kushigo" shigowadukansu ukun sukayi suka sake tsayawa duk sunkasa magana sun kuma kasa wani abu, itama Ammisaita tsaya kallonsu batace komiba da kyar Riyadyadago kanshi yakalli Ammi hada ido sukayi dasauri yasake maida kanshi kasa saikuma chan dakyar yace "can I take her up Ammi?" Yarinyar looksick hakan yasa tace "okay" juyawa sukayi Muniryayi gaba Riyad biyedashi ganin bata iya daga kafatahau bene yasa Riyad ya dauketa ahankali sukaisama duk Ammi na kallonsu.


Dakin dake next to na Ammi Munir yabude dakinyahadu is very simple daki yarinyar Sister Ammi kezama aciki duk idan tai hutun school tazo gidaawajen Ammi take zama, har gado Riyad ya kaita yakwantar da ita, ijiye jakanta Munir yayi yafice,ahankali Riyad yasa hannu yacire mata hijabin dakejikinta ya ijiye gefe yana kallon atampan dake jikintatun na ranan nan yasauke ijiyan zuciya sannanyasake kwantar da ita ahankali yadanja duveeyarufe mata kafafu saikuma yaduko saitin fuskantaya matso da bakinshi ya manna mata kiss a goshikafin yatashi ahankali yafita daga dakin yawucekasa tundaga kan staircase ya hango Munir tsaye afalon Ammi na kallonsa saikuma yakarasa saukowaahankali yana satan kallon Ammi dake kallonshianatse yasauke kanshi kasa yasami kujera yazaunada sauri Munir ya zauna gefensa Ammi tabisu dakallo kafin amatse cikin muryanta da baya nuna

anatse yasauke kanshi kasa yasami kujera yazaunada sauri Munir ya zauna gefensa Ammi tabisu dakallo kafin anatse cikin muryanta da baya nunafushi ko ihu kokuma wasa tace "wa kuka kawomingida?" Dan dago kai Riyad yayi yakalli Ammisaikuma yasauke kanshi kasa yakasa maganaahankali Munir yace "matar Riyad ce Ammi" DasauriRiyad yadago kanshi yakalli Munir dashima kekallonshi saikuma yadan juyo kanshi akasa ahankaliyace "Ammi I married her 6days ago" sosai Ammike kallonshi cus bataji any labari a gidan nan ansanda sarki zai kara aure ba, koko anmasan inda sarkiyake tadaiji anata cewa wai yayi tafiya, urgenttafiya, anatse tace "Riyad" gently yadago kanshi yakalli Ammi ahankali tace "wayansan kayi aure bandaMunir? Mai babban daki tasani?" Girgixa mata kaiyayi, ahankali tace "Baffan ka yasani?" Nan magirgiza mata kai yayi alamun a'a chan kuma tace"Mom dinka tasani?" Sake girgiza mata kai yayistrictly Ammi tace "who knows about thewedding?" Ahankali yace "Buba" da sauri ta gyarazama jin Babanta yasan about the wedding saikumatace "how did Buba yasan about this wedding"?Ahankali Munir yace "shine ya karbamai auren"sosai Ammi ke kallonsu baki tabude zatai maganaahankali Riyad yace "she's our cousin Ammiyarinyar Baffa ne" dawani irin sauri Ammi takalleRiyad kafin ahankali tace "wat do you mean yarinyarBaffa? Is that Maryam?" Shiru Riyad yayi Munir yace"Ammi we are talking about biological yar Baffanmu not su Maryam" Munir yahau bama Ammilabarin komi daga A zuwa Z da rasuwan Mama dakomi ba karamin girgixa Ammi maganan yayi ba taishiru tana kallonsu daga ta kalli Riyad saita kalliMunir, Riyad dinma har ya rame kana ganinshikasan he has not been eating and resting properlysabida damuwa, ahankali tace "katashi kaje kaiwanka kaci abinci and rest I will take care ofRashida in the mean time dole na sanar da maiBabban dak da II Kkoma meka fa'uwa da 

yarinyar Baffa ne" dawani irin sauri Ammi takalleRiyad kafin ahankali tace "wat do you mean yarinyarBaffa? Is that Maryam?" Shiru Riyad yayi Munir yace"Ammi we are talking about biological yar Baffanmu not su Maryam" Munir yahau bama Ammilabarin komi daga A zuwa Z da rasuwan Mama dakomi ba karamin girgixa Ammi maganan yayi ba taishiru tana kallonsu daga ta kalli Riyad saita kalliMunir, Riyad dinma har ya rame kana ganinshikasan he has not been eating and resting properlysabida damuwa, ahankali tace "katashi kaje kaiwanka kaci abinci and rest I will take care ofRashida in the mean time dole na sanar da maiBabban daki da Baffan ku koma meka faruwa theyneed to know wa kuka kawo gidan yasan yarshi kaauro accepting nata or not as yarshi is totally up tohim, kaidai ka aureta matarka ce so dama ba zamanshi zatayiba, so I will tell them" dan dagokai Riyadyayi yakalli Ammi adan shagwabe mugun kalloAmmi ta zubamai tace "me kake kallona?" Ahankaliyasauke kanshi kasa murya chan kasa yace "Ammiplease don't tell them now at least tadan warketasami kanta for now let's keep her wajenki secret"kallonshi Ammi tayi saikuma tace "tashi kaje kaciabinci" tashi yayi ahankali babu musu yatafi dinningMunir yabishi sosai yaci abinci rabon dayaci abincihaka harya manta itakuma Ammi tawuce ta tafisama yadan saci kallonta saida yaci yakoshi sannanya tashi sanin Ammi na sama yasa yawuce yafita. 


*SANYI DA ZAFI*

*EPISODE 37*


Haryakai kofa ya tsaya yadaga kanshi yana kallonsama hakan yasa Muneer yace "idan Ammi tafitadaga dakin I will call you don't worry" wani mugunkallo yama Munir saikuma yafita yana basarwa,wucewa yayi yafice daga flat din yahade rai yawuceflat nashi yana zuwa fadawa suka zube akasa."Maikawa sannu a lafiya, in ka dabka alkhair in kamaika alkhair, dauka da karfin Allah ka maika danufin Annabi, gabanka Allah bayanka Annabi damada hauni ikon Allah mai ado da kuran doki..."hannu yadaga musu alamun suyi shiru sannancikeda isa da iko yace "kar abar kowa yashigobangarena sai idan nabada izini" sunsan wayandayake nufi Matarsa da Mai Baban daki da saurisukace to yawuce yashiga ciki cus yanaso yayibacci.


Wanka yafada yasakinma kanshi ruwan zafi yanalumshe idanu kissing scene dayama Rashida nadawomai fresh arai ijiyan zuciya ya sauke sannanyakarasa wankan yafito daure da towel most timeidan yagaji baya iya komi gadon yahau ya kwantaahankali almost half of tunani shi is Rashida,ahankali yace Allah ya jikan Mama sannan ya kulleidanunshi dan yayi bacci kanshi ya huta he needsto focus and know yanda he will handle komi.


Bude kofan dakin da suka sata ciki Ammi tayi taishiru tana kallon Rashida da sai bayan su Riyad sunfada mata waye ita saita fara ganin yanayinta damahaifinta Mujitappa dudda bawai tana kamadashine gabaki daya bane dan tana kama damahaifiyarta but wlh tayo yanayin Mahaifinta sosai,gakuma kama na jini Allahu Akbar! Ammi saita faratuna sandamahaifivarta o kuka sosai tana cewa

anatse yasauke kanshi kasa yasami kujera yazaunada sauri Munir ya zauna gefensa Ammi tabisu dakallo kafin anatse cikin muryanta da baya nunafushi ko ihu kokuma wasa tace "wa kuka kawomingida?" Dan dago kai Riyad yayi yakalli Ammisaikuma yasauke kanshi kasa yakasa maganaahankali Munir yace "matar Riyad ce Ammi" DasauriRiyad yadago kanshi yakalli Munir dashima kekallonshi saikuma yadan juyo kanshi akasa ahankaliyace "Ammi I married her 6days ago" sosai Ammike kallonshi cus bataji any labari a gidan nan ansanda sarki zai kara aure ba, koko anmasan inda sarkiyake tadaiji anata cewa wai yayi tafiya, urgenttafiya, anatse tace "Riyad" gently yadago kanshi yakalli Ammi ahankali tace "wayansan kayi aure bandaMunir? Mai babban daki tasani?" Girgixa mata kaiyayi, ahankali tace "Baffan ka yasani?" Nan magirgiza mata kai yayi alamun a'a chan kuma tace"Mom dinka tasani?" Sake girgiza mata kai yayistrictly Ammi tace "who knows about thewedding?" Ahankali yace "Buba" da sauri ta gyarazama jin Babanta yasan about the wedding saikumatace "how did Buba yasan about this wedding"?Ahankali Munir yace "shine ya karbamai auren"sosai Ammi ke kallonsu baki tabude zatai maganaahankali Riyad yace "she's our cousin Ammiyarinyar Baffa ne" dawani irin sauri Ammi takalleRiyad kafin ahankali tace "wat do you mean yarinyarBaffa? Is that Maryam?" Shiru Riyad yayi Munir yace"Ammi we are talking about biological yar Baffanmu not su Maryam" Munir yahau bama Ammilabarin komi daga A zuwa Z da rasuwan Mama dakomi ba karamin girgixa Ammi maganan yayi ba taishiru tana kallonsu daga ta kalli Riyad saita kalliMunir, Riyad dinma har ya rame kana ganinshikasan he has not been eating and resting properlysabida damuwa, ahankali tace "katashi kaje kaiwanka kaci abinci and rest I will take care ofRashida in the mean time dole na sanar da maiBabban daki 

Rashida tayi ita kadai tasan metakeji Ammi tace"gashi jikinki zafi tashi muje kiyi wanka | will call Drtazo tadubaki" dagata tayi zuwa bayin dake dakintabude ta shigar da ita itama ta shiga hannu tasaabayan zip na riganta taja mata shi kasa tace "barinakawo miki soap da brush" fita tayi bata jimabatakawo soap brush sannan tafita ta tsaya bakin kofatace "imaxa ina jiranki" tawuce tabude wardrobe nadakin taciro mata wasu simple black-shirt da skirthar kasa English shima mai slit ta back kafan ta ijyemata akan gadon sannan takoma jikin bayin tace"imaza gani nan fa" ruwa Ammi taji na zuba hakanyasa ta tsaya almost 5min sannan tadan bude kofankadan ganinta tayi tsaye gaban shower ruwan nadukanta da rigan da komi da sauri Ammi tashigotana kashe shower tana kallon yanda take kukakafin ahankali taja towel saida tafara kara matasannan taja rigan kasa tadago ta kulla mata toweldin ata gefen armpit sannan tadauki karamin toweltasa mata asaman gashinta daya jike sharkan takwashe takamota suka fito zaunar da ita tayi abakingado takai hannunta tana share mata fuska tace "yaisa" tadauki rigan tasamata takai saida tagamasamata sannan tasauke towel din zuwa waist nataskirt din shima takama kafanta tasa aciki tadagatataja skirt din har waist nata kafin taja towel din nasaman kanta ma ta tsani kan kafin taja towel dintawuce takai bayi tadaga riganta dake bayin tasa awashing machine sannan tafito sauka tayi tana kiranDr nata tashiga kitchen Ammi nada son girke girkeda kanta dudda tanada masu aiki lafiyayyen tuwo tadebo mata da miyan kuka da man shanu tahayosama inda ta barta anan tasameta Ammi tace "youwill have to eat koba yawa okay" hannunta tasa tagutsuro tuwon takai bakinta ahankali Rashida takalli hannun Ammi dake miko tuwon bakinta kawaisaita fashe da kuka tana bude bakinta emotionallyAmmi tai murmushi kadan tasamata sabida taganeMamanta ta tuna mata sosai taci tuwon tana kallonfuskan Ammi AnnnebuWeesha sannan

maka usulin mutanen"? Anatse yace "a'a" fadamaikomi Ammi tayi tace "Buba banson matsala bayanmijinmu yarasu nasamu Sa'ida da fitinan matansa,banson wani matsala kuma wlh" anatse Buba yace"babu matsalan dazaki shiga shi Allah ba azzalimkowa bane sannan Allah yarnada hanyoyi da damanayin abubuwa, ba wayon Riyad bane yasa yafarahaduwa da yarinyar nan tun lokacin rasuwanmahaifinshi ta ceci rayuwar sa ba, ba wayansa banekuma yasa yakara haduwa da ita bayan shekaradaya tana aiki a hotel dinsa ba, kome kikaga yafaruYar budurwa haka Allah yaso yafaru kuma yanadadalilin dayasa komi yafaru ahakan wanda idan akaiwalkiya zamuga abinda ke cikin duhun inamaitabbatar miki idan sherima akama mahaifiyaryarinyar nan aka sama ciwon nan da gangan komiyakusan bayyana, abinda nakeso gareki shine kirike yarinyar amana be a mother to her, batarigatasanmu ba tunda Riyad bai sanar dasu ba tukunnaAllah kadai yasan yanda zataji idan taso tasanniuntil then just take care of her sannan tazauna dakea sirri sai bayan ta warware kafin gidan susan da itakar hayaniya yasa zuciyanta ya buga kinajina"ahankali Ammi tace "to Buba" yace "akullum addu'ana tana kanki da jikokina Allah zai tsareku dukababu wanda ya isa yacutar daku wlh saidai idanAllah ne yaso hakan yafaru ban barku hakanan baaddu'a da saukan Al Qur'ani kullum cikin yinsa nakeso calm down Allah na tareda mai gaskiya"gyadama Buba kai tayi tace "toh Buba nagode"katse wayan yayi tawuce tadauki kasa.


EPISODE 38

Bude kofan dakin da suka sata ciki Ammi tayi tai shiru tana kallon Rashida da sai bayan su Riyad sun fada mata waye ita saita fara ganin yanayinta da mahaifinta Mujitappa dudda bawai tana kama dashine gabaki daya bane dan tana kama da mahaifiyarta but wlh tayo yanayin Mahaifinta sosai, gakuma kama na jini Allahu Akbar! Ammi saita fara tuna sanda mahaifiyarta ke kuka sosai tana cewa bata taba fasikanci arayuwanta ba, duk alokacin cikinsu babu mai iko ko wanda ya isa yaja damai Martaba a fada hakan yasa kowa yayi shiru, ijiyan zuciya Ammi ta dauka ta shiga dakin ahankali ta zauna bakin gadon tana kallon fuskan Rashidan da hawaye ke bin idanunta hannunta Ammi takai ahankali tadaura saman wuyanta wani irin sanyi ni’ima Rashida taji yasauka ajikinta kalan wanda takeji idan Mama ta tabata hakan yasa tabude idanunta ahankali batare data juyoba, ahankali Ammi tace “Rashida” tunda Rashida take arayuwa bata tabajin murya daya mata kusan shige dana Mamanta akunne ba saiyau hakan yasa tajuyo da jajayen idanunta ahankali takalli Ammi kaman yanda Ammi ke kallonta dudda yanda take cikin bakin ciki but saida taga kamannin matan da Riyad hakan yasa tagane mahaifiyar Riyad ce, ahankali Ammi tanuna kanta tace “sunana Ammi, I’m your new Mama take me as one kinji Allah jikan mahaifiyarki” hawaye taga sun taru sosai a idanun Rashida dayasa ahankali Ammi tasa hannunta tadagota takawota jikinta kankameta Rashida tayi kawai saita fashe da kuka sosai, Ammi bata hanata kukaba sai bayanta datake bugawa tace “Rashida bana fata wata rana na mutu yarana su kasamin addu’a sai kuka, burin kowace uwa shine yaranta suyita mata addu’a kidena kuka I know it’s painful but Mama tafi bukatar addu’a awajenki kinji” gyadamata kai Rashida tayi ita kadai tasan metakeji Ammi tace “gashi jikinki zafi tashi muje kiyi wanka I will call Dr tazo tadubaki” dagata tayi zuwa bayin dake dakin tabude ta shigar da ita itama ta shiga hannu tasa abayan zip na riganta taja mata shi kasa tace “bari nakawo miki soap da brush” fita tayi bata jimaba takawo soap brush sannan tafita ta tsaya bakin kofa tace “imaxa ina jiranki” tawuce tabude wardrobe na dakin taciro mata wasu simple black-shirt da skirt har kasa English shima mai slit ta back kafan ta ijiye mata akan gadon sannan takoma jikin bayin tace “imaza gani nan fa” ruwa Ammi taji na zuba hakan yasa ta tsaya almost 5min sannan tadan bude kofan kadan ganinta tayi tsaye gaban shower ruwan na dukanta da rigan da komi da sauri Ammi tashigo tana kashe shower tana kallon yanda take kuka kafin ahankali taja towel saida tafara kara mata sannan taja rigan kasa tadago ta kulla mata towel din ata gefen armpit sannan tadauki karamin towel tasa mata asaman gashinta daya jike sharkan ta kwashe takamota suka fito zaunar da ita tayi abakin gado takai hannunta tana share mata fuska tace “ya isa” tadauki rigan tasamata takai saida tagama samata sannan tasauke towel din zuwa waist nata skirt din shima takama kafanta tasa aciki tadagata taja skirt din har waist nata kafin taja towel din na saman kanta ma ta tsani kan kafin taja towel din tawuce takai bayi tadaga riganta dake bayin tasa a washing machine sannan tafito sauka tayi tana kiran Dr nata tashiga kitchen Ammi nada son girke girke da kanta dudda tanada masu aiki lafiyayyen tuwo ta debo mata da miyan kuka da man shanu tahayo sama inda ta barta anan tasameta Ammi tace “you will have to eat koba yawa okay” hannunta tasa ta gutsuro tuwon takai bakinta ahankali Rashida ta kalli hannun Ammi dake miko tuwon bakinta kawai saita fashe da kuka tana bude bakinta emotionally Ammi tai murmushi kadan tasamata sabida tagane Mamanta ta tuna mata sosai taci tuwon tana kallon fuskan Ammi, Ammi tabata ruwa tasha sannan takaita bayi tayo alwala ta daurata kan dadduma tace “yi salla bari nashigo da Dr” fita tayi daga dakin bata wani jimaba ta shigo tareda wata Dr zama sukayi saida Rashida ta idar Dr tace “sannu” dan dudduba Rashida tayi tace “bari namata allura da magani” allura tafara mata sannan aka bata maganin tasha zama kusada ita Ammi tayi takama kanta tasa ajikinta wannan dumin uwa dataji daga jikin Ammi



EPISODE 39

yasa within seconds tai bacci Dr tama Ammi sallama ta tafi Ammi tadade tana kallonta yarinyar ko Masha Allah she’s very young and so pretty daga yanayin jikinta kasan kamilan yarinya ne maza basu taba tabata ba boobs dinta kaman balbalam acike, gyaramata kwanciya Ammi tayi taja bargo tarufa mata sannan takashe wutan dakin ta tashi tafita tana rufo kofa, dakinta ta shiga taciro wayanta Babanta takira ringing daya yadaga yace “Yar Budurwan Babanta” murmushi sosai Ammi tayi tace “Buba mesa zaka biyewa shirmen su Riyad kaje ka karbamai aure batare da yan uwan mahaifinsa sun sani ba” anatse yace “Riyad namiji ne dayasan meyake arayuwa yasan inda yakemai ciwo, idan baiso yafadi agida yanada dalilansa dakuma hujjojin sa, ba yaro bane kuma ba aurensa na farko bane, jikana bai taba neman abu daga gareni ba the only time dayayi kuma bazan taba kinmai ba”. DUK WACCE TAKARANTA MIN LITTAFI BATARE DATA BIYABA BAN YAFEBA Dan shiru Ammi tayi sai chan tace “Buba sun fada maka usulin mutanen”? Anatse yace “a’a” fadamai komi Ammi tayi tace “Buba banson matsala bayan mijinmu yarasu nasamu Sa’ida da fitinan matansa, banson wani matsala kuma wlh” anatse Buba yace “babu matsalan dazaki shiga shi Allah ba azzalim kowa bane sannan Allah yanada hanyoyi da dama nayin abubuwa, ba wayon Riyad bane yasa yafara haduwa da yarinyar nan tun lokacin rasuwan mahaifinshi ta ceci rayuwar sa ba, ba wayansa bane kuma yasa yakara haduwa da ita bayan shekara daya tana aiki a hotel dinsa ba, kome kikaga yafaru Yar budurwa haka Allah yaso yafaru kuma yanada dalilin dayasa komi yafaru ahakan wanda idan akai walkiya zamuga abinda ke cikin duhun inamai tabbatar miki idan sherima akama mahaifiyar yarinyar nan aka sama ciwon nan da gangan komi yakusan bayyana, abinda nakeso gareki shine ki rike yarinyar amana be a mother to her, batariga tasanmu ba tunda Riyad bai sanar dasu ba tukunna Allah kadai yasan yanda zataji idan taso tasanni until then just take care of her sannan tazauna dake a sirri sai bayan ta warware kafin gidan susan da ita kar hayaniya yasa zuciyanta ya buga kinajina” ahankali Ammi tace “to Buba” yace “akullum addu’a na tana kanki da jikokina Allah zai tsareku duka babu wanda ya isa yacutar daku wlh saidai idan Allah ne yaso hakan yafaru ban barku hakanan ba addu’a da saukan Al Qur’ani kullum cikin yinsa nake so calm down Allah na tareda mai gaskiya” gyadama Buba kai tayi tace “toh Buba nagode” katse wayan yayi tawuce tadauki kasa.

EPISODE 35

Misalin 9 ta turo kofan dakinshi tashiga da sallama takai hannu tana kunna wutan dakin, wani irin lafiyayen bedroom ne dayaji komi gawani ubansun royal bed da Muji ke kwance akai yana sanye da farin jallabiya, hasken daya gani yasa yadan bude idanunshi kadan ya kalli kofa ganin wacce ta shigo yasa ya maida idanun yarufe maida kofan tayi tarufe ta taso har zuwa bakin gadon ta zauna tace “na gaida mijina Namijin Muji! Gaisuwan girma dakuma kasaitacciyar asuba tagari gareka Mujitappa na” dan bude idanunshi kadan yayi yamaida yarufe yace “da fatan kin tashi lpy?” Gyadamai tayi tana dan murmushi tace “najika shiru tunda kadawo daga asuba kashige daki, hope lafiyanka kalau?” Dan bude idanunshi kadan yayi saikuma ya maida yarufe hakan yasa ahnakali ta mika hannu ta shafa kanshi tace “menene ke damunka eh Mijina? Nasha gayamaka matsalanka matsalata ce, farin cikin ka farin ciki nane, damuwarka damuwata ce, I’m your best friend tell me menene” dan shiru yayi saikuma yadan yunkuro hakan yasa dasauri ta dauki pillow takai bayanshi tasamai ya zauna da kyau tareda dan sakin mata murmushi yace “thank you Jummai” gyadamai kai tayi tace “bawan nan ba idan baka sanar dani abinda ke damunka ba bazan tabajin farin ciki ba, dan Allah kagayamin” ahankali yace “Jummai ni kaina bansan meke damuna ba, natashi kalau naje masallaci kalau, amman dazun nan kawai najini inajin kaina wani iri, I’m just feeling so lonely and so empty wani iri zuciyana yakemin kaman wani abu nawa dana dade ina nema yana kusadani yanzu” yadanyi shiru saikuma yasake kallonta yace “nasan munriga munyi alkawari nida ke mun rufe chapter nan tunda yan uwanki suka bamu yara har uku tun suna jarirai mu muka rainesu sun dawo namu amman yau kawai natashi inajin ni haihuwa nakeso!” Wani irin mummunan faduwa gaban Jummai yayi tacigaba da kallon mijin nata ahankali cikeda damuwa Muji yace “I want my own flesh and blood Jummai!” Yasake shiru yace “I’m 65yrs banso na mutu ban kawo d’ana dubiya ba, kina ganin ba gwara na kaara aure naga ko Allah zaisa mudace ko zamu sami baby”? Yayi maganan yana kallon Jummai data hadiye wani abu da kyar awuyanta tace “kasan duk abinda kakeso arayuwan nan inasonshi, nariga na manyanta dazanji kishi ko wani abu, nasan Samha, Badariya da Musa duk sun bamu yara tun suna jarirai ma mun karba mun raina amman hakan bai kore cewa mijina baida yaro na jininsa da tsokansa har yanzu ba, dan haka na yarda kayi auren muga abinda Allah zaiyi, kanaso na samo maka wacce zaka aura ne kona barka kasamo ko kanada wacce kakeso?” Dan yatsine fuska yayi ahankali yace “banda kowa amman akwai wata baiwa dakika taba aikowa office takawomin abinci na yaba da natsuwan ta ki aika gidansu ko ki tambayamin ita muji” murmushin yake tayi aranta tace “wato kaga yar fara yar fulani shikenan ita kakeso mayen fararen mata to da bakar mace zakai rayuwa harka mutu” azahiri tayi mutmishi tace “anjima kadan zanje dakaina na ganta namata magana, yanzu tashi to kai wanka ka warware kaji ko kanaso ni namaka da kaina?” Dan kallonta yayi saikuma yataso da kanshi yadaura akafadanta ahankali yace “ina alfahari dake Jummai, dakowani namiji zai sami mata tagari irinki da alokacin zai tabbatar lallai aure nada dimbin ni’ima, thank you Jummai for always supporting me, akwai wasu kudi a akwatina konawa kikeso ki dauka harda dollars” murmushi tayi tace “to godiya nake mai gidana, tashi kagani muje na wankeka subul” dagashi tayi tawuce dashi bayi tsaf ta wankoshi suka fito ta shafamai ta shiryashi sai hira takemai suka fito breakfast sukai tare bayi sai kaikomo suke, Jummai takalli wata baiwa tace “je sama ki taso Maryam tazo ta gaida Babanta”suna zaune awajen wata yar budurwa dazatayi sa’an Rashida ta sauko tana sanye da rigan bacci iya guiwa tana goge idanu tazo dinning din, tabaya ta rungume Muji tace “morning Dad” tasakeshi tawuce wajen Jummai ta rungumeta tace “good morning Mommy” washe baki Jummai tayi tace “sai yanzu aka tashi sabida anzo hutu daga school ko, Allah kaimu next month ki koma Istanbul zamuga karyan iskanci” Muji dake binta da kallo idanunshi suka sauka kan Nail polish dake kumbunan


EPISODE 40

ta shi dama yanada fada sosai cikeda fada yace “wat is that kikasa a nails naki?” Da sauri ta kalli kumbunan saikuma ta boye hannun abayanta cikeda fada yace “Maryam kina yar musulma zaki dingasa nail polish?” Ashagwabe tace “Dady is normal thing fa” zabura Muji yayi zai tashi ganin haka yasa Jummai ta tashi da sauri kafin kace me ta kwashe yarinyar da mari tace “how dare you Babanki na magana kina bashi amsa are you Mad? Tarbiyan dana baki kenan Maryam? Ke” tadaga hannu zata sake kwasa mata mari dasauri Muji yariketa yace “common it’s okay! She’s just a child” cikin fushi Jummai tace “23yrs ne a child, noo babu wacce ta isa tai talking back at her Dad” dan lumshe idanu Muji yayi yadaga mata hannu ahankali yace “it’s okay koma ki zauna” zama Jummai tayi ba musu shikuma yakama hannun Maryam dake kuka yace “don’t mind Maman ki da saurin hannu” rungume Baban yarinyar tayi da sauri ashagwbe tace “Dady I love you alot I don’t love Mom she always hit me” hararanta Jummai tayi dayasa Muji yayi dan dariya yace “ya isa to Mommy ki is just trying to correct you kinsan Maman ki mace ce datasan values na rayuwa ga ilimi ga hikima, ga dabara, I want you to grow up and be like her okay, dan haka kada ko kara shafa this abu on your nails kinji”? Gyadamai kai tayi tace “okay Dady” sakinta yayi yace “bari naje wajen Mai Babban daki zauna ki break” yayi maganan yana wucewa yafita Jummai tabishi da kallo yana karasa ficewa da sauri ta tashi tazo wajen Maryam tana duba fuskan ta tace “ohh my child na mareki sosai? Yakuri kinji?” Tureta Maryam tayi da karfi saida ta dafa kujera kaman zata fadi, yarinyar ta nunata da hannu cikeda tsiwa tace “Momy idan kina act naki stop hiting me banso, haba zaki illatamin face ne kija Kamal yace I’m looking ugly wat is wrong with you”? Cikeda lallabawa tazo kusa da ita takai hannunta tana shafa fuskan tace “yakuri my baby, bazan karaba i promise, haba Yamyam dina, sorry sorry, Mommy is sorry gayamin mezan miki kihakura” Dasauri Maryam tace “to kibarni naje party Kamal in kinaso na hakura” Dasauri Jummai tace “nabari but kidawo dawuri before your father notice baki gida”.


EPISODE 41

Around 5 yafito daga part nashi yana tafiya daidai kaman baiso yataka kasa yana zuba uban kamshi. "Bijimin Sarki, sadaukin Sarki, adalin Sarki, ci gari yaya ka kwana, ci gari yaya ka tashi, ka kwana lafiya ka tashi lafiya, da kai da mutanen gidanka, dogo da gajere, da mai tsawo da, mace da namiji, da babba da yaro? Ci gari yaya ka tashi. Sadaukin sarki adalin sarki, Kano garinka ne, Kanon dabo kasar ka ne, da anki da anso, Allah ka taya maka, Annabi ka taya maka, ci gari zauna daidai." Ahankali yake takawa harya shiga fadan yadan zauna yayi magana da mabiyansa dan an kwana biyu ba’a gansa ba inda wasu kemai yajiki wasu namai an dawo lafiya yagaisa da Waziri daketa kallonshi yana murmushi bai wani dadeba ya sallami mutane yatashi yabar fadan zuwa side na Mom wanda yaga miss calls nata yafi a kirga this past few days yaki dagawa, shiga ciki yayi da sallama zaune yaga Mom kan kujera Haleema zaune kusada ita tadaga kafafun Mom din tadaura kan cinyanta tanama Mom tausa suna hira, kallo daya yama Mom bala’in daya hango a fuskanta saida gabanshi yafadi sauke kanshi kasa yayi yamaida kofan yarufe yashigo cikin dakin waje yasamu yazauna akan kujera ahankali yace “Mom ina yini” Haleema da tunda yashigo take kallonshi kaman tsohuwar mayya wani azaban sonshi na tashi azuciyanta tace “ina yi……” hannu Mom tanuna ma Haleema ranta a bala’in bace kaman zata yanka mata mari tace “karki kuskura ki gaida tambadadden yaron nan, wanda bai girmamani ba bazaki girmamasa ba Haleematu” dan lumshe idanu Riyad yayi kafin yadaga kanshi yakalli Haleematu anatse yace “dan bamu wuri nai magana da Mom” cikeda fada Mom tace “taje ina? Wani wuri zata bamu? Haleema is part of familyn mu babu wani sirri na jikinka dabata sani ba so she’s not going anywhere” dauke kanshi kasa yayi yarasa mesa tunda yazama Sarki shi da Mom ke having issues, baison abubuwan datakemai, and bai isa yayi magana ba tahau fushi da fada, daurewa yayi yadago kanshi yakalleta ahankali yace “I’m sorry Mom for not answering calls naki I was in the middle of something sai…….” “Kana tare da karuwan dadiron ka ko!” Dasauri ya kalli Mom hakan yasa ta karbe kafafunta da Haleema ke matsawa har lokacin ta sauke kasa tace “inace ita takiraka tsakar dare ka mike jiki narawa ka shiga saka kaya katafi”? Ahankali yakalli Haleema data sauke kanta kasa dasauri kaman munafuka ganin bazata taba chanxawa from telling Mom everything about them ba saikuma yasake daurewa yace “Mom ba abinda kike tunani bane” “abin miye to eh stupid boy? Kana ganin kazama sarki an fara huremaka kunne ni zaka watsama kasa a idanu? Bayan I was the one that made you the king? Munir dinma dagayau na rabaka dashi wlh!” Dasauri yakalli Mom tace “yes and duka mukaman daka bashi na company ka ka karbe yaje ya nemi nasa kudin ya bude nashi company atoh! Dagayau d’ana bazai kara feeding nashi ba harma kayi sponsoring lavish lifestyle dinsa nan ko ba’asan uban mamarsa malamin zaure bane anzo an mannema nawa yaron dakeda grandfather attorney na federal republic gabaki daya” sauke kansa kasa yayi kasa ganin ran Mom abace yake yasa ahankali yace “Mom kiyakuri” cikin fushi Mom tace “tun ranan hawan salla an rasa ina kake ni ni uwarka bankai matsayin ka dauki wayana ba ka zama gantalallen sarki Allah kadai yasan inda kake zuwa ka saki matarka kaman kaza baka iya gamsar da ita lusarin namiji dakai!” Dan ijiyan zuciya Riyad ya sauke kadan saikawai ya mike tsaye yajuya yayi hanyar kofa kai yanda Mom taji jikinta kaman an kwara mata wuta ganin ita kemai magana agaban Haleema zai kunyatata haka yatashi zai tafi yasa batai wata wata ba ta tashi kawai Riyad jiyayi an kama bayan riganshi da sauri yajuyo, Mom batai watawata ba ta yankamai mari ganin yajuyo jikake tasssss!

EPISODE 42

Saida Haleema tai ihu taredakai hannunta da gudu tarufe bakinta ganin yanda Mom ta daurama Sarki gabaki daya Riyad mari tana huci, chak Riyad ya tsaya yanama Mom wani irin kallon dabata taba ganin yamata irinshi ba, tunda yataso Mom bata taba daga hannu tadakeshi ba tun yana dan kankani sai yau, cikeda hargowa tace “kake kallona haka daga hannu karama mana ko bazaka iya bane eh? Ai na dauka kakai karfin tunda kazama Sarki rama marin Riyad” kasa daina kallon Mom yayi, Mom ta nunashi da yatsa tace “kai harka isa ni Mamanka ina maka magana ka mike and walk out of me? Who are you? Are you mad? Go back there and sit down!” Tanunamai kujeran daya tashi dagakai har lokacin kallonta yake ihu tamai tace “Wlh Riyad bazan sake magana ba kuma ka wuce kaje ka zauna kona mummunar bata maka rai, zan maka abinda bantaba maka ba, I said go and sit!” Tayi uban ihu, ijiyan zuciya ya sauke ahankali yakoma yaje ya zauna mamaki ya kashe Haleema yanzu biyayyan Riyad yakai haka dama? Wlh wlh Mamanta bata isa tamata irin marin da Mom tama Riyad ba har gefen idanunshi yadan tara jini sabida tasami wajen idanunshi dan yajuyo ne without knowing zai sha mari tasameshi awajen. Komawa Mom tayi ta zauna tana facing nashi tana dukan kirjinta tace “the slap is for walking out on me ina maka magana, for not answering calls dina for days, Riyad ba sarki ga ko president kazama zan hukunta ka sabida you’re my Son! And you’re a boy in my eyes, dagayau inhar bawani uziri bane katashi kafita kabar gidan nan wlh saina wulakanta ka saina cimaka mutunci, Haleema” dasauri Haleema tace “na’am Mom dina” cikin iko da isa tace “duk randa yasake batamiki rai koyatashi kuna kwance yafita ki sanar dani” ahankali Haleema tace “to Mom dina” dan huci Riyad yayi ahankali, Mom takalleshi tace “if you like kazama 90yrs you are my baby and zan hukuntaka if you misbehave stupid boy kawai” ta tashi tawuce sama abinta dasauri Haleema tabita sama gudun kar Riyad ya huce akanta tace “Mom don’t be angry”.


EPISODE 43

Yadade rabon da ranshi yayi irin bacin nan dayayi ahankali yatashi yafito kanshi namai zafi wucewa flat dinshi zaiyi daidai Munir na zuwa wajen yace “Ammi na kira” baiso yajeba but sanin Rashida na wajen yasa yabishi yaki kallon Munir karya lura da fuskanshi shiga side din yayi da sallama ganin Ammi bata falo yasa yawuce sama ahankali yayi knocking gaban dakinta Ammi tace “come in” bude kofan Ammi yayi ahankali yashiga ciki magana taso tamai kan Rashida amman fuskanshi datagani abinka da farin fata barin wajajen idanunshi yasa ta mikeda sauri duk yanda taso ta daure karta tambaya takasa hakan yasa tace “meya samekaa fuska?” Dan dago idanu yayi yakalleta jin tambayan datamai hakan yasa taga dan jinin daya taru a idanunshi da kyau da sauri yadauke kai yace “fuska na? Meya sameshi”? Tashi Ammi tayi tazo dab dashi ta tsaya saikuma tace “Riyad!” Ahankali yadago kanshi ya kalleta gefen fuskanshi tabi da kallo kafin tahade rai tace “who slapped you?” Sauke kanshi yayi kasa dasauri baitaba sanin Ammi zata gane anyi slapping nashi ba bazai taba iya mata karyaba nor bata amsa Ammi jitayi zuciyanta yamata badadi ranta yabaci haryakai ga batasan sanda tace “ban haifeka sabida wata ta dakamin kai ba!” Ahankali yakalli Ammi, jaa Ammi taga idanunshi sunyi dasauri tasa hannunta takama hannunshi takaishi gaban gadonta zaunar dashi tayi ya zauna tabude karamin fridge na dakinta taciro ice bag tawuce bayinta da sauri tai wrapping nashi cikin towel tafito tsayawa tayi agabanshi ahankali tasa hannu takama habanshi tadago da kanshi ta daura ice bag gefen idanunshi lumshe ido yayi yanajin saukan ni’ima ajikinshi tunda yake baitaba jinshi this close to Ammi ba sai yau, ahankali kaman dan Baby ya rungumeta yadaura kanshi akan cikinta tareda kulle hannunshi tabayanta batare dayace komiba, mutuwan tsaye Ammi tayi cus bata tabajin dumin yaronta like this ba tunda yana jariri, murya chan kasa tace “this should be the first and the last time dazaka tsaya wani ya kaimaka duka kowaye kai koda nine! Riyad dudda nasan forcing naka akayi kazama sarki that doesn’t change the fact that you are a king! Kafadi dole aji! Dole abi! Kowa na fadan nan abayan ka suke! Stand up for yourself and be a man! Idan you can’t protect kanka how can you protect marainiyan yarinyar nan daka aura?” Dago kanshi ahankali yayi yakalli Ammi ahankali Ammi taduko tai cupping face nashi tace “kai Gwarzo ne jarumin jarumai! Zaki dodon kowa! This incident should never repeat itself am I clear?” Gyadamata kai yayi ahankali saikuma yakara hugging nata he’s feeling wani irin strong love for mahaifiyarshi da bai tabaji da ba sai yau.

EPISODE 44

Sun dade ahaka batare daya saketa ba, bude kofan dakin da akayi yasa yasaki Ammi da sauri, Munir ne yashigo yana kallon fuskanshi yace "meya sameka?" Ammi bata tanka ba tawuce tafita daga dakin, dan lumshe idanu Riyad yayi yace

"I'm fine don't worry Munir" sosai abin yataba Munir cus yasan aikin Mom ne amman ya kyaleshi yace tashi muje mosque" tashi yayi Munir yabashi wani bakin glass karba yayi yasaka suka fice tare, har isha'i a mosque sukayi sannan suka fito tare suka koma side dinsu babu kowa a falo hakan yasa ya wuce sama hoping Ammi na salla adakinta.

Ahankali yabude dakin da Rasheeda keciki yashiga tana kwance kan dadduma ta cire hijabin ta ijiye a gefe gashin kanta abarbaje wanda har yanzu da danshi, idanunta a lumshe haryau fuskanta a kumbure suke, tundaga kan kafafunta yabi da kallo dake sanye da skirt din daya kama hips nata zuwa dan navel dinta daya leko sabida yanayin yanda ta kwanta yasa rigan yadan dage sama, kallo daya yama chest nata ta rigan yacire idanunshi da sauri kafin ahankali yadaura idanunshi kanta.

Bawai tayi bacci bane idanunta biyu yanzu kawai batajin dadin rayuwanta ne, batajin dadin zuciyanta batajin dadin komi she knows she's alive but noting makes sense again, kamshin turaren shi dataji yasa ahankali tadan bude idanunta, daga inda take take kallonshi kaman yanda Riyad ya tsaya yana kallonta daga kofa, akwai something about Riyad presence that gives mind nata peace, and that is just how she felt yanzu ma data ganshi sai kawai ta tsareshi da idanu tana kallonshi batako kyaftawa kaman yaune rana na farko data fara ganishi, ahankali yazo wajen kafin gently yazauna yana kallonta kaman yanda take kallonshi cikin tsantsan care yace "how are you? Are you okay?" Wani abu taji ya tsayamata awuya tana kallonshi baitaba expecting zatamai magana ba sai chan cikin muryanta da idan baka natsu ba bazaka tabaji ba tace "Mama left me l'm all alone yanzu" hannunshi yakai ahankali ya sharce hawayen daya gangaromata zuwa hanci saikuma ya tsareta da idanu murya chan kasa yace "you are not alone Rashidahh!" Lumshe idanunta tayi saikuma ta tashi ahankali tana dafa gado tajuya zata wuce bayi karaf yarike mata hannu hakan yasa ta tsaya kaman yabude mata fanfon kuka sai kawai tafashe da kuka, ahankali yatashi yajuyo yasha gabanta ya tsaya yana kallon yanda take kuka tana kallonshi kafin ahankali yabude hannuwanshi yace "I will always be here for you come" tadade tana kallonshi ganin taki motsi yasa gently yajawota jikinshi kankameshi tayi sosai tana kuka sun dade ahaka atsaye kafin yafara tafiya ahaka yazauna bakin gado tana jikinshi ta kankameshi shima haka, bayanta yake tapping ahankali yace "cry as much as you want too l will not leave you" she's just feeling maganganun shi da yanda yake lallashinta like a little girl yana patting bayanta, dago kanta tayi tana kallon idanunshi yasan abinda take kallo hakan yasa ahankali yace "it's just a little accident Ammi tabani magani, and bayamin zafi" yayi maganan looking cute da kwai saitaji kirjinta ya buga maida kanta kirjinshi tayi back tai Kano yana patting bayanta har lokacin, sun dade ahaka tai lamo ajikinshi tana lumlumshe idanu kafin bacci yayi nasaran awon gaba da ita.

Ahankali ya kwantar da ita agadon yana kallon fuskanta daurewa yayi kawai be nuna komiba but the way ta kankameshi yana feeling every bit na boobs nata da yaji ba bra ajikinsu yakusan loosing control lips nata ya tsare da idanu sannan yatashi ahankali yaja bargo yarufa mata yawuce kofa ya kashe mata wuta yafito yana tafita ahankali yanda baiga kowa a falon ba ba bakarakin dadi yajiba yawuce yafita.Rabon dayaje flat na Haleema da kansa harya manta but yau kawai yawuce wajen, kai tsaye ya shiga gidan, jakadiya da wasu bayi yagani a compound nata suna bawa shuka ruwan dare suna gainshi kowa yazube. "An gaida mai Martaba sarkinmu mai adalci...." kofa yabude yashiga ciki Haleema yagani a falo tana zaune ta daura kafa daya kan wasu bayi na matsa mata kafada suna ganinshi suka zube.

"An gaida sar....." sama yayi yace "meet me upstairs" faduwa gabanta yayi takalli bayin tace "kutafi bangaren ku" sannan tamike ahankali gabanta na faduwa saikuma ta dauki wayanta ta shiga kitchen dasauri tai dialing number Mom tana dagawa tace "Mom ga Riyad yazo flat dina yawuce sama yace na sameshi achan, Mom idan ya rama marin dakikamai akaina fa"? Dan murmushin keta Mom tayi tace

"shi ya isa! Yasanni ai! Jeki sameshi kiji dame yazo kome yace ki kirani ki sanar dani" ahankali aleema tace "tom Mom dina" ta katse wayan tafito tawuce sama, dayake yanada still dakinshi asama hakan yasa tawuce wajen tareda bude kofa ahankali ta shiga yana zaune kan couch dake dakin yaciro waya yana dannawa hakan yasa tawuce bakin gado tazauna gabanta na faduwa still, tabude wayanta dake hannunta da sauri ta danne recording sannan ta kifa wayan akan cinyanta murya kasa kasa tace "gani Mai Martaba" kusan one minute yabata sannan yadago tareda ijiye wayan nashi a gefensa yazubamata wani irin matsiyacin kalio da saida gabanta yafadi tasauke kanta kasa da sauri strictly yace "are you married to me to married to my Mother?" Kallonshi tayi dasauri cikin muryan nan kaman na munafukai tace "haba Baby wat are you implying......"Answer the question!" Riyad yayi maganan azafafe babu wasa kodaya a harshen sa dayasa Haleema taji kirjinta na bugawa dim dim dim ahankali tace "kai nake aure!" Yana kallonta yace "do you think is okay kidinga fadama Mom every bit of details na auren mu?" Kanta akasa dan tasan takalleshi bazata iya bashi amsaba tace "ai Maman ka ce, ba wata naje na samu na fadimawa ba, and Mom is a strong Mom strong enough to bend you ko kanaso ko bakaso, idan tace kayi dole kayi Mai Martaba!" Sosai Riyad yake kallonta yace "in that case" yamike tsaye yace "forget cewa ni mijinki ne continue serving Mom" yajuya dasauri kirjinta nawani irin bugawa tayi sauri tasha gabanshi ta jingina da kofan tana kallon fuskanshi tace "me kake nufi da nacigaba da serving Mom na manta da kai mijina ne? Ban gane ba, sakina kayi"?

Yana kallonta right in the eyes yace "saura kiris!" Jitayi zuciyabta yahau bugawa tace "wih wih baka isa kasakeni ba

Mom bazata taba barinka ba, bama ka isa bane" wani irin mugun kallo yamata yace "tashi ajikin kofa nafita" wih ayanda yayi magana saida ta tsorata ganin yanda taga tsantsan tsanarta akan fuskanshi saita fashe da kuka kuma sabida bala'in sonshi take tace "nika tsana haka kakema kallon tsana" yana kallonta yace "i hate any woman dabatasan values na aure ba, and you happen to be one, I wish ban aureki ba ballema nahada jiki da kalan ki, but yanzu you can do whatever you want, it's obvious kinsan wakike aure cus as far as i know I was never the husband" yana maganan yasa hannunshi yajata ya matsar daga jikin kofa yawuce yabude kofa yafice fashewa da kuka sosai Haleema tayi ta tashi da gudu taje gado tadauki wayanta ta turama Mom voice record din.


EPISODE 45

Tsaf Mom ta saurari voice record din sannan takirata back fashewa da kuka sosai Haleema tayi tace "Mom idan Riyad yasakeni ina zansa kaina? Ta ina zan taba samin miji irin sa daya hada komi Mom? Mom please talk to him wih Mom ina mutuan son mijina bazan iya rayuwa bashi, wih Mom Riyad ba lusari bane, Mom baitaba barinaba saiya ga bana iya motsi, Mom Riyad is the best husband ever, he's soft, kind and sweet, please Mom do something" katse wayan kawai Mom tayi jin yanda Haleema ke kuka tai dialing wayan Riyad harya katse Riyad bai dagaba kuma yana kallo akaro na biyu yadaga strictly Mom tace "kazo ina nemanka" shiru yayi kusan na 1 min itama Mom haka tana jiran taji mezaice chan adake yace "I can't Mom! Nariga nai shirin bacci I will see you tommorow" mutuwan zaune Mom tayi jin maganan da Riyad yamata jin batai magana ba yasa Riyad ya katse wayan ya ijiye yatashi yafada bayi dan wanka, wanka yayi yafito daure da towel a waist yaji wayan nashi na ringing karasawa wajen yayi yakalli screen din ganin Mam yasa yadanyi jim sannan yakai hannunshi yadauki wayan yakai kunne Mom da kaman zata kama da wuta tace "Riyad ni kake gayama bazaka amsa kiran dana maka bangarena ba sai gobe" shiru yayi baice kala ba Mom tace "naji every single thing daka fadanma matarka I heard everything ka kirata yanzu kabata hakuri kona saba maka" without any fear yace "Mom I'm not doing that!" Dasauri Mom tace "me kace Riyad!"? Calmly cus baiso yamata raising voice yace "Mom enougl with the whole bossing me around kina controlling dina, allow me to be the man in my life, as for Haleema I don't care ko ke ko mamanta ku koya mata darasi akan menene aure before I take her back again! Inhar bata chanza dabian ta ba l will not do this marriage with her again, godd night Moml" Yazare wayan daga kunnenshi ya kashe wayan gabaki daya ya ijiye baiso abin yama batamai rai hakan yasa yawuce closet dinshi yashiga shiryawa yasa kayan bacci.

Mom da ranta inyayi dubu yabaci tana tama kiran Riyad cataji ya kashe wayansa tana kokarin sake kiranshi wani kira ya shigo wayanta gain Jummai yasa tai shiru tana kallo kaman bazata dauka ba wayan na gab da katsewa tasa hannu ta dauka takara wayan a kunne batace komi ba daga ta dayan bangaren Jummai tace "uhnn kaman ba tare aka jefe mushe ba, anata jamana aji ana jiji dakai ana papa ana kuma tunkaho sabida danki ya zama sarki bayan kinsan cewa inda Muji na son sarautan nan da wih saiya karbe babu wanda ya isa yaja dashi amman bayaso ba itace agabanshi, saikuma uwa uba jininshi ya mugun hadu da Riyad" dan ijiyan zuciya ta sauke tace "I called you because of something very important da I think you need to know" ahankali Mom tace "me kenan?" Jummai tace "tsakanina dake ba boye boye sabida duk kanwan ja ce like I said munsha jehe mushe tare, tom naje normal business dina dana saba na wanchan matan na shirya komi tsaf da yan sandana na kama yarinyar nasa aka kulle a cell muna cikin cooking lafiyayyen abinda zaisa akaita prison for life guess what happened?" Ahankali Mom tace "wat happened kinsan dai I'm not good at guessing" ijiyan zuciya Jummai ta sauke da mugun mamaki tace "danki Mai Martaba Riyad da kansa yaje yaciro yar daga police station" komawa Mom dake tsaye tayi ta zauna tana gyara wayan a kunne face "are you telling me matar nan da aka kora ni ya ma sunanta me HIV nan dai kishiyarki to diyar cikin data haifa kin kulle a cell sannan Riyad dina yace yayi bailing dinta?" Cikeda gasgata magana Jummai tace "kwarai! Kinini tsaf da kyau, yanda mamaki ya kasheki haka ya kasheni" dasauri Mom tace

"Riyad dai da kanshi yaje police station yayi bailing ta bama yatura representative ba? Cus nasan as sarki alot of cases comes to him kinsanshi da tausayi he try as much as possible ya taimaki kowa wat I don't get is yanda zaije da kanshi, baisan this people ba fa lokacin da aka koreta i remember correctly Riyad was 13yrs old kuma yana Abuja boarding school achan turkish school" Jummai tace

"nimadai abinda nasani kenan but here comes the most interesting part of my story abinda yahani sukuni naga is better I called you" gyara zama da sauri Mom tayi tace "ina jinki Jummai" Jummai tace "I have lot of informant a anguwansu dake bani daily and steady info, Riyad has been in there life for quite some time now!" Dasauri Mom tace

"wat!" Jummai tace "wih da gaske ai in the first place yadade arayuwan su ne saisa har shine yacirota daga cell, she works in his hotel banda haka Mamanta tamutu about 3days ago da Riyad dawani yaro which 100% nasan Munir ake magana sune sukai handling komi guess wat ance yau da safe anga Riyad yafito da ita daga gidan yasata a mota sun tafi God knows where, I'm telling you this sabida ni yanzu my biggest threat is gone" tai wani murmushin keta me sauti tace "as for the girl she's just a tiny abu dazan iya kaudawa at any moment but danki ki bincika shi i just hope ba affair yake having da yarinyar ba tunda a hotel nashi take aiki kokuma sonta yake ba duba da yanda yaje da kanshi yacirata a ceil sannan yau yatati da ita cus ance an saida gidan sa ina yakenal Mom mutuwan zaone tayi dummai tace I just hage dank is net aboat ta create a mesai ba gidan nan zai kevia yannyar nan ba, yay aure dari is not my business but yarinyar nan is my so damn business sabida jinin Zainabu ce data kwacemin miji ashekarun baya which ke kika bani idea the whole HIV stuff na kawar da ita so think of something ki raba danki da ita! Fast good night!" Jummai ta katse wayan mutuwan zaune Mom tayi tana kokarin linking abun to wat has been happening with Riyad gabaki dayan yaron lost focus tundaga kan issue na dankunne so Halima was not wrong da suspicion nata da gaske ne akwai wata mace arayuwan Riyad, kwanan nan dayazo tundaga salla zuwa yau bayanan wajenta yaketa zuwa to ina yadauki yarinyar yakai? Noo! Bazataba taba bari yayi wani aure ba sannan the last thing she will allow him do shine ya auri diyar Zainab inaaaa!

Dasauri tasake dialing number Jummai yana ringing tadaga dasauri Mom tace "what's the plan for cooking the girl?" Dan murmushin keta Jummai tayi tace "kin ijiye girman kan

Maman Sarki kinhau kan layi" Dasauri Mom tace "you don't understand Riyad nata acting wired narasa dalili all labaran nan naki nayi linking nasu up da yarinyar i believe you dari bisa dira, how do we cook the girl? Kinada plan ne" dasauri Jummai tace "cooking that girl is as simple as ABCD dan mahaukaciya ce tanada temper na bala'i, so yara irinsu easily suke stepping on trap but problem din shine ina danki yakaita? That I don't know" dasauri Mom tace "I.will find out gobe I promise saida safe" takarse wayan ta tashitana taiya ita kadai ta warware ta kulle ta.



EPISODE 46

Bacci yadade bai mata dadi kaman na jiyaba ahankali tabude idanunta ta kalli saman dakin dudda wuta akashe tana iya ganin komi shiru tayi shikenan Mama tarasu? ljiyan zuciya tasauke mai huci ta tashi zaune ahankali tadaura hannunta kan kumatu she can't even explain yanda takeji in words idan ta tuna da Mama tarasu all this while she has not been praying for Maman ta kuka kawai take tashi tayi ahankali gabaki dayan jikinta smells like Riyad kaman har yanzu tana jikinshi gently ta tashi tawuce bayi ta shiga maida kofan tayi tarufe saikuma ta tsugunna zuciyanta namata ciwo Mutuwan Mamanta is hurting her is even killing her slowly takasa yarda Mama tarasu shikenan bazata kara ganin Mama har abada ba? Taya zata cigaba da rayuwa batare data kara ganin Mamanta ba brush tadauka tasa toothpaste tahau wanke bakin tafashe da kuka sosai taba brush tana kuka mutuwan Mama is just too much for her to handle da kyar tagama tayi abinda zatayi tayo alwala tafito hijabin dake kan dadduman ta dauka tasaka tai sallan asuba Qur'ani daya gani a drawer ta mike hannu tadauka tana kallo rabon datai karatun Al Qur'ani harta manta kullum saidai taita jin waka batada yawan bautan Allah wani zubin harda how busy her life is da ayyuka da sauransu but that is not an excuse maybe sabida ma hakane yasa Allah ya karbi ran Mama she promised dagayau saita karanta Al Qur'ani everyday of her life.Bayan hannu tasa ta goge hawayen sannan tabude Khafi tafara karantawa Ya ilahi! Ashe muryanta dakeda dadin waka was trash tana rera kirala kaman balarabiya and yawanoi kuka take tana karatun Ammi tadade tsaye jikin kofan tana juyota she's happy yanda ta mike dakanta yau hartai salla tana karatu May Allah comfort her and ease her pain Ammi tafadi sannan tawuce tasauka kasa.

Wuraren 8 ya shirya yasauko kasa hannu yasa yadanna wani boturi cikin sec wani bafade yashigo falon yawani zube gaban Riyad din dake zaune yadaura kafa daya kan daya yace "na gaida Sarkina Mai darajoji daban daban, kwana lafiya Sarki na...." "Sarkin Gida!" Riyad yakirashi kai tsaye hakan yasa yatashi yana zaune akasa agabanshi yace "Allah taimaki me Martaba" agogo Riyad yadauka yashiga daurawa a writs nashi yana kallon wayanshi dake vibrating akan kujera Mom ne ke kiranshi yace "bayan nahau kujeran mulki akwai abubuwa da dama dana nuna banaso" da sauri Sarkin Gida yace "kwarai! Irinsu shiryaka, masu aiki awajenka, Mai soro, shamaka baya muna maka tattaki duk inda zaka da

sauransu"

anatse Riyad yace "yanzu duk inaso kufara yi, ka

shiryamin fadawa wayanda ka aminta dasu" dasauri Sarkin gida yace "angama ranka shi dade" he wants to punish Haleema hakan yasa ayangance yace "Sarkin Gida" dasauri yace "ubangidana Babana Sarkina kuma gani nan me kake bukata?" Karasa saka agogon shi yayi tasss sannan yadago yakalleshi yace "ka dakatar da duka bayin dake aiki a bangaren Sarauniya Haleema na kwana bakwai cikinsu harda jakadiyanta, sannan a tsare bangaren nata ban yarda kowa yakai mata ziyara ba ko ita tafita ba saida babban dalili wanda sai an sanar dani" dasauri Sarkin Gida yace

"angama ranka shi dade" da hannu yamai alamu yatafi sannan yadaura kafa daya kan daya still yana kallon call din

Mom bai dagaba he's just feeling lack of attachment towards her after abinda tamai jiya, yana zaaune awajen har lokacin zuwa fada wasu fadawa guda biyu suka shigo aka shiryashi tsaf sai walkiya yake yafito aka maramai baya zuwa fada bayan yama Haleema sako tamai breakfast.

"Mom menamai haka zaimin wannan hukuncin? Ba'a taba yin matan sarki da sarki ya hukuntata hakaba sai akaina kaman ina gidan yari kuma wai ya aiko nahadamai breakfast yagama da fada zaizo yaci taya zan fara aikin banda wacce zata taimakamin" ran Mom yariga yagama baci da kyar tai controlling temper nata tace "kije kimai abinda zaki iyayi, na ganshi zan mai magana za'a dawo miki da ma'aikatan ki" Mom ta katse wayan ta ta tashi kitchen tashiga saita tsaya tana kallon kitchen din bawai bata iya girki bane but she just realized cewa tadade tanacin banxa she can count how many times tama mijinta girki bama tacika yi ba, kotayi ma itada yan aikinta ne, ganin yanda zata fara aikin yanzu take kaman wani uwan tashin hankali ruwan shayi tasa a wuta saitai frying egg tasa a kula da bread tai arranging a dinning around 11 taji adawa na sanarda ya iso bude kofan flat nata yayi yashigo dasauri ta tashi daga jikin kujera tana kallonshi yayi wani irin mahaukacin kyau ahankali tace "ina kwana" batare daya kalleta ba yace "kalau" zama yayi akan kujeran falon yace "kawomin abincin nan" danjim tayi gabanta na faduwa kada yace bazaici ba tawuce dinning flask na shayi tafara daukowa ta ijiye kan table takoma tadauko tray na cup da bread da spoon sai honey ta ijiye sannan takoma ta dauko wani kula mai kyau takawo ta ijiye gabansa still kallonsa take, yadan jima yana amsa wayan dayake sannan ya katse yakalli komi na gabanshi kafin yasa hannu yabude kulan yaga egg datamai frying sai yaji abu ya tsayamai awuya Haleema knows the way he eats atleast tana gani adakin Mom.

Dan lumshe idanu kadan Riyad yayi kafin yabudesu yadaura akanta ganin yanda idanunshi sukai ja batasan sanda ahankali tace "Baby ni kadaine fa kasa an sallami ma'aikata na, this is the only abinda na iya maka fixing quick" ahankali yatashi dan komawa baya tayi ganin yanda yayi kaman zaki baice mata komiba yabude kofa yafita dag dakin tadan harari kofan tace "what is bad about this continental breakfast please? Da kanason abinci dayawa da baka sallami yan aiki na ba, akanme ina matar sarki zan dinga wahala ina shiga kitchen? Antaba hakane?.

Har bangaren Ammi fadawa suka biyoshi ciki ya shiga

Ammi bata falo dinning yawce one thing about gidan Ammi is there's always food anytime kaje gidan zama yayi a dinning yasa masa da pepper soup da shayi ya jera a tray dake wajen, kallo sama yayi ganin bai hango Ammi ba yasa yatashi manyan kayan jikinshi yacire na ciki ya ijiye awajen yabar jumper dake jiki na soft milk yard yawuce sama ahankali hannu yasa yabude kofan dakin, zaune yaganta ita kadai tana sanye da wani A-shape gown na atampa sabo kal dasafen nan Ammi takawo mata sababbin atampopi 10 set taga ledan an rubuta SapphirebyAishaSambo, gold atampa ne yamata kyau yabi jikinta tass dan size din Meenat Ammi ta bada, kawai burst dinne sukaso su mata kadan dan tafi Meena boobs but still kayan sun shigeta and she looks so beautiful aciki, kanta ba dankwali tadalyi parking gashinta kawai tana zaune ita kadai tana kallon window dakin da Ammi tabude mata sabida haske ya shigo dakin looking super lonely.

Kamshin turarenshi kadai taji yasa tajuyo da kanta tazubamai idanunta dahar yau suke a kumbure lumshe idanu kadan tayi tabudesu still kallonshi take kaman yau tafara ganishi maida kofan yayi yarufe yashigo cikin dakin har zuwa wajen datake tray abincin ya ijiye sannan yajuyo da kanshi ya kalleta hakanan kawai taji gabanta yafadi motsi lips dinta sukayi murya chan kasa tace "ina kwana" dan tsayawa yayi yana kallon kwayan idanunta da sauri ta sauke idanun nata kasa, saukan hannunshi taji kan wuyanta da saida kirjinta yabuga dasauri takalleshi hada ido sukayi still kallonta yake batare daya cire hannun nashi daga wuyanta ba ahankali yace "have you eaten"? Gyadamai kai tayi ashagwabe da shima saida heart dinshi yabuga yadaure murya chan kasa yace "me kikaci"? Wani iri hannunshi yakesa takeji ajikinta amman da kyar tace "tea" ganin yanda takeyi yasa yadauke hannun daga wuyanta waist dinta yakai hannun yakama tareda dagota tashi daya yakawota dab da jikinshi kaman zai hada fuskansu numfashi tafara da sauri da sauri dake sauka a fuskanshi tana kallonshi kaman yanda yake kallonta tamai bala'in kyau ya tsare lips nata da idanu yana tuna how they felt ranan a mouth nashi kafin ya janye idanunshi da kyar daga lips din ya daura kan idanunta murya chan kasa yace "I want to feed you banson gardama okay" gyadamai kai tayi da sauri gently yasaketa ya zaunar da ita gefenshi yasa spoon ya yanki sinasir din yasa miya yakai bakinta batai musu ba tabude baki tana kallonshi murmushi yamata yasa mata abincin abaki tafara taunawa ahankali tana kallon yanda yake murmushi dimples dinshi ke motsi yana smiling he's so handsome kaman mace wih, gutsura shima yayi yakai bakinshi yaci sannan yasake kaiwa bakinta tabude ahankali ta amsa shima yakai yaci karan shattering glasses sukaji dayasa afirgice Rashida tarikemai riga da sauri daidai nan yaji muryan Mom tace "fitomin da d'ana ko badake nake magana ba kika maidani mahaukaciya Riyad! Alkyabban waye anan?" Lumshe idanu Riyad yayi yabude ahankali yakalli Rashida data rikeshi tana kalion kofan dakin itama murmushi yamata yakama hannunshi daga jikin rigan yace "cigaba da cin abinci ina zuwa! Don't come out kinji" gyadamai kai tayi gently yatashi yana gyara riganshi yawuce kofa Rashida tabishi da kallo gabanta na faduwa dum dum dum sosai kaman wani abu zai faru da ita cus haka tadingaji ranan da Mama tarasu. 


EPISODE 47

Yanda gabanta ke faduwa da yanda takejin hayaniya akasa ga kirjinta sai dum dum dum yake yasa ahankali tamike tsaye tana tafiya kadan kadan gabanta mugun faduwa yake kaman akwai something that is calling her, arayuwanta ansha fada agabanta but ko kallo wasu basu isheta ba she has never ever been curious about anything in her life but today she just wanna go out, bones na jikinta na cringing, gently tabude kofan dakin tana tafiya ahankali babu takalmi a kafanta karasowa jikin karfen benen tayi ta kallo kasa the first abinda tagani is fadawa kusan 8 dake tsaitsaye a falon daidai lokacin cikeda izza Riyad yace “zaku iya tafiya” zubewa sukai akasa agabansa atare sukace "Sadaukin Sarki! Adalin Sarki, ka shekara dubu bisa dubu muna tare da kai, ci gari zauna daidai, Sarkin mu Baban mu Sarkin Kano Sarki Riyad Baba Aliiiii!" Dum! Dum! Dummm! Rashida taji kirjinta na bugawa taga fadawan sun juya sun fita, bayin dake dakin suma dukansu suka fita, kaman daga sama taji ance “why did you send us messege muzo nan”? Da sauri Rashida ta juyar da kanta zuwa inda taji muryan magidancin! Chak taji jinin jikinta ya tsaya bata taba ganin mahaifinta face to face ba but tsaf tasanshi tun tana yar budurwa take browsing nashi cus tasan waye shi, Mama told her about heritage nata, biography Babanta na google with lot of pictures nashi dan yana alot of humanitarian activities ya karbi lot of award yanada registered NGO that is even affiliated to UNICEF, so she knows fuskan mahaifinta tsaf cus she wanted to see mutumin daya wulakanta mahaifiyarta, ganin Jummai kusa dashi tsaye just cleared the entire confusion nata batasan sanda tai baya ba tana buge flower verse dake wajen yafadi hakan yasa kowa na kasa yadago kanshi sama, ganin Rashida da Riyad yayi tana ta daura hannunta akan bakinta idanunta sunyi jazur yasa gabanshi yayi mummunar faduwa dasauri yayi staircase yashiga hayowa sama da sauri yazo daidai inda take yakai hannu zai tabata yace “Rashida I can explai…….” Wani irin baya tayi tadaga hannuwanta biyu tadaura akan kunnuwanta tai wani crazy ihu dayay echo agidan. “Don’t touch me!”. 


EPISODE 48

Wlh saida gidan gabaki daya ya amsa ihun Rashida, mummunar faduwa da gaban Jummai yafarayi hango Rashida datayi asama hakama Mom dan daga ganin yanda Riyad yayi sama tagane waye ita, Muji ya tsare Rashida da idanu, Ammi itama tana tsaye awajen takasa motsawa komujima komu dade this will happen dama and it just happens to be today. Cikeda damuwa sosai Riyad dake gaban Rashida yace “Rashida I’ve been wanting to tell you everything but nasan you’re not fine, ina jira ki warke ne, I wanted to tell you waye ni cus Mama told me about you, da labarin ku gaba daya” wani irin bude idanun Rashida tayi tana kallonshi idanunta har wani kalan spark na wutan bala’i ke fita daga ciki tace “dama kasan wacece ni ka aure ni still sannan ka kawoni this cursed family and cursed house dinku da evil people suka cikashi!”? Kasa magana Riyad yayi cus he sees how hurt she’s yarinyar da she’s grieving see abinda Mom tajawo, ganin yaki magana yasa azuciye tabi ta tawuce tahau sauka daga bene Riyad na binta, daga Muji har Gwaggo kallonta suke hakanan Muji yaji gabanshi na faduwa da ganinta, daidai ta karasa saukowa Riyad yasha gabanta hakan yasa taji burki takalleshi kaman zata kasheshi tace “katashi daga gabana!” Azuciye Riyad yace “baza’a tashi ba!” Azuciye Rashida da idanunta sunyi kaman jini tace “nace katashi daga gabana nabar gidan nan, bazan taba auren dan gidan nan ba! Ko kaine last Man aduniya wlh I rather die with dignity and alone dana aureka, so end our marriage bazan taba zama gidan nan ba!” Ran Riyad ya masifan baci jin maganganun datakeyi hakan yasa yamata ihu da saida falon ya amsa yace “why do I have to pay for abinda bani nayiba bansan sanda akayi ba? Why does it have to affect auren mu? The person that hurt you and your Mom is my Uncle not me! I was not even in this house alokacin, I don’t know Mama at all! The first ever time dana taba ganin Mama was when tazo hotel dina? Why must I pay? Why our marriage? Why why why?!” Wani kalan kallon Riyad dake nuna mata Baffa Mujitappa take hawaye na cika idanunta, jijiyoyin goshinta na fitowa with the deepest sorrow tace “you asked why? Mahaifiyata suffered for 23yrs harta rasu because you your family! Wanda kake nunamin na kalla bai chanchanci kallo awajena ba! Baida matsayin da Rashida zata daga idanu ta kallesa sannan baida darajan sabida shine mutum mafi kaskanci kaf aduniya awajenta! Dan haka Riyad! Just like yanda shekaru 23yrs back kuka nuna this entire household da mutanen cikinta basuson anything to do with My Mother, aka mata koran kare nima I don’t want anything to do with this house ko wayanda ke cikinsa and you happened to be a member of this house! Dan haka kabani hanya nafita nabar gidan nan daga baya katuromin takardan saki na I don’t care, just know cewa ko sama da kasa zata hade bazan zauna agidan da akama mahaifiyata koran kare ba!” TO JOIN IS 1k CHAT ME UP AND JOIN 07012181461 Wani azababben tafarfasa zuciyan Riyad yake sabida yanda yakejin duk duniya baiga wanda ya isa yasashi yasaketa ba dan yana mugun sonta, he loves Rashida sama da yanda yama dauka yana sonta, dan yanda take maganan tagama aurenshi din nan is triggering him, yana kallonta right in the eye da kakkausan murya yace “ko sama da kasa zata hade bazan taba sakinki ba! Nor nabarki kije ko’ina! I will never let you go away from me because I love you!” Dasauri tawani irin kallonshi kaman yanda kowa na dakin yakalli Riyad har Ammi, kirjinshi ya nuna idanunshi sunyi jazur yace “I’ve already fallen in love with you Rashida Al Mustapha! Jika Ina I don’t know how much love nake miki but Riyad just love yo…….


EPISODE 49 

!” “Stoppppp!” Rashida tai ihu tana taushe kunnuwanta dan kalman soyayyan kaman yana zuba mata guba ajiki takeji, Riyad na kallonta yace “I will never let you go bayan ni Mama tabama amanarki” Mom dake tsaye tana kallon drama tama Rashida wani wulakantaccen kallo tana matsowa kusada Riyad tace “waye kuma wannan dakake gayama kanaso? Wacece ita”? “Wacce ta isheki riga da wando!” Rashida tabata amsa tana juyo da kanta tazubama Mom wani dirty look, Mom takalli Riyad tace “Riyad who is this mara kunya”? Kafin Riyad yayi magana tace “your biggest nightmare inhar ba’a barni na bar gidan nan ba” baki Mom tabude zata kara magana Riyad yace “Mom kiyi shiru mana haba! Shut up!” Yabugama Mom tsawa dayasa tai shiru ganin ran Riyad yabaci, Riyad yakalli Muji dake kallon Rashida har lokacin yagama mutuwa atsaye yace “Baffa Yarka ce Rashida!” Rashida jitayi zata kama da wuta ta kalli Riyad tace “yar wa? Baffan ka baida darajan haihuwana! Wallahi yayi kadan!” Durun uwa! Dakin kowa kallon Rashida yake kai! Yarinyar itace fire 🔥 Dudda gaban Jummai na faduwa saida ta daure tai taking risk tace “yarinya bi a sannu da mijina kike magana! Bazan dauki raini ba!” Juyoda kanta Rashida tayi ta kalli Jummai tana tuna gabaki dayan ciwon Ammi ta dalilinta ne, ta dalilin kulleta datayi was the reason jikin Ammi ya birkice saitaji emotions yazo mata wuya tai wajen Jummai din da gudu taku daya biyu Riyad yayi yakamata kokawa tashigayi da Riyad tana cewa ka sakeni, ka sakeni nace, garin haka hannunta ya taba Mujitappa wani kalan sanyi dayaji yashigeshi baisan lokacin daya zauna waje dayaba ahankali kan kujera dasauri Hambali yaduka yace “Yaya? Sannu menene are you okay?” Jummai itama tace “Mijina are you okay?” Hannu yadaga musu yakasa magana direta Riyad yayi nisada su, cikeda lallashi yace “Rashida please listen to me, please” kaman mahaukaciya Rashida tashiga kabar da hannunshi tace “wlh wlh I will not, Riyad Mamana, my mother fa” tanuna kirjinta tace “Mamana tarasu bazata taba dawowa gareni ba har abada! Bazan kara ganin Mama ba har abada, Mamana na kabari, and family ku killed my Mom!” Takai bayan hannunta ta share hawayen daya zubo mata dasauri tace “dukan ku familyn ku gabaki daya bakuda imani!” tasake share hawayen dasuka zubo mata da bayan hannu tace “kun kori mahaifiyata da cikin wata shidda batare da kun damu ba sabida tanada HIV, ta rantse tasake rantse wa bata taba zina ba amman babu wanda ya yarda da ita, cikin dake jikinta kukace banaku bane, you guys sent her away bayan kun tara mutane kun toxarta mahaifiyata matar da rannan da safe akai discharging nata daga hospital, baku tausayama a sick pregnant woman ba, wlh bantaba jin tsanan wasu arayuwana irinku ba”. Muryanta yafara rawa sosai tana tuna wahalan dasuka sha arayuwa tace “Mama suffered ba ko biyar a hannunta, My Mom suffer…….


EPISODE 50

” Takasa karasa maganan sabida kukan daya ciyota tace “that woman………” tanuna Jummai tace “she keep tormenting us tana zuwa gidanmu tana azabtar da Mamana itace da reason yan layinmu akasan Mama nada HIV kowa was stigmatizing ni d Mamana” duk yanda Rashida taso karta fashe da kuka takasa saida ta fashe da kukan tana pointing Jummai dake fiki fiki da ido tana addu’a inama wani abu yasa Muji ya sume karyaji abin da Rashida ke fadi tace “Mama was fine but wannan wicked matan tazo gidan mu ana gobe salla ta dagamana hankali tasa police suka kamani the fear, da shock da Mama ta shiga was the cause of her death, and you dare tell me na rayu dakai Riyad? Riyad do you know what a harsh life is? Do you know wat rayuwa da tabo da sheri da kazafi is? Do you know wat rayuwa is da cutan da bakasan yanda kasameshi ba and you have no way to prove innocence naka? Riyad do you know wat stigmatization is? Riyad kasan menene kunci bakin ciki damuwa da azaba? Riyad kasan zafin ciwo? Riyad kasan azaban da Mamana ta shiga da zata rasu tana ihu cikina jini na fita daga hanci da bakinta? All this abubuwan sabida gidan ku!” Tasake fashewa da kuka da kyar tace “wlh, wallahi! I know Mamana idan da tasan Kai dan gidan nan ne bazata taba baka aurena ba! Wallahi no condition zai taba barin Mama tabarni na auri Dan gidan nan cus gidan nan shine gidan dayama Mamana tabo dahar takoma ga Allah bai gogu ba, Riyad ko kaine last man aduniya i will never ever marry you! I hate you Riyad! Na tsaneka, I hate your family! I hate this house! I hate everything about you people, bazan taba hada jini da ku ba!”. 

 Babu wanda yakai Maman Kabeer enjoying this drama, ganin yanda Riyad ke kallonta ma speechless yasa tai ihu tace “kabani hanya nabar gidan nan!” Da kakkausan murya Riyad yace “you are not going anywhere” tashi Gwaggo tayi ahankali tazo kusada Riyad tana kallon Rashidan da tun dazu data kalleta taga jikanta, takalli Rashida taga Muji, daman kafin ta mutu zataga jinin Muji! Allahu Akbar! Baki tabude zatai magana saikuma ta kasa hannunta tadaga dake rawa sosai hawaye na saukowa daga kan idanunta zatakai hannun kan fuskan Rashida dasauri Rashida takoma baya tamata wani kallon uku saura kwata dayasa Riyad yakama hannun Gwaggo ahankali hakan yasa Gwaggo tafashe da kuka sosai tana wani irin kallon Riyad tana kallon fuskan Rashida data hade rai tajuyar da fuskanta ma dan bata kaunar kallon any of them, tace “jikana ne wannan? Riyad dama zan taba ganin jinin Mujitappa na? Riya…..” tari Gwaggo tafara dayasa kowa yataso Riyad ya zaunar da ita yana riketa, da sauri Ammi takoma Kitchen dan dauko ruwa ganin haka yasa Rashida tayi kofa da sauri tabude daidai Riyad na dago kanshi yace “Sarkin Gida kutareta” ahankali Muji ya karbi Gwaggo yakalli Riyad cikin soft voice yace “follow her” tashi yayi dasauri ya wuce waje inda Rashida ke rigima da fadawa dasauka zagayeta in circle batare dasun riketa ba tana nunasu da hannu tana ihu. “Kutashi daga gabana, kubarni natafi gidan nan, ihuuu ana kidnapping dina agidan nan, wallahi ko zaku kasheni bazan zauna agidan nan ba, bazan zauna ba” jama’a Rashida tashiga tarawa bayi da ma’aikatan gidan sai shigowa flat din suke, yana zuwa wajen fadawa suka budamai circle din yashiga ciki yana azuciye kawai yasa hannu yakama hannunta dasauri tajuyo tashiga kokawa dashi tana kokarin fizge hannunta tana bori tace “kasake ni let go off my hand, wlh bazan zauna agidan ku ba, I hate this house, I will never ever live here kun kashemin Mamana, stop touching me, I hate all of you” ganin yanda takemai tirjiya tagama ficewa hayyacinta yasa yadauketa chak azuciye fadawa suka warware rigunan su suna kare Sarkinsu suna binsu abaya,Riyad yayi gaba har zuwa flat dinshi yawuce wajen motanshi yabude ciki yasata tataso kaman zakanya yarufe da sauri yayi locking motan yakoma gaba yashiga yatada motan yaja motar yabar gidan. Gudu kawai Riyad yake zubawa akan titi yana kallon yanda Rashida ke kuka abayan mota, yarinyar is deeply hurt, duk yanda mutum zai gwada maka yanda abu ke damunsa idanba kaikeda rayuwan mutumin ba bazaka taba gane meyakeji ba. Sunyi tafiya mai nisa kafin su shiga GRA gaban wani mahaukacin gida fari yayi horn wani security ne yabude kofa ya leko ganin motar yasa yakoma ciki da gudu bude gate akayi Riyad ya shiga cikin gidan wow gidan ya mugun hadu sabon gidane daya gina to his taste wanda duk randa yayi aure zaisa matarsa ciki before zamanshi Sarki yabata komi.

EPISODE 51 

Wasu manyan security ne guda biyu sukazo wajen motan da gudunsu dan gaidashi jin ihu yasa duk suka kalli motan daidai Riyad na bude kofa yafito yace “you can go” sannan yabude bayan motan yakalli Rashida dake kuka sosai ba takalmi ba dan kwali harda majina ahancinta tanamai wani irin kallon tsana tace “Wlh I will report you for kidnapping me cus ni ba yarinya bace that you can force me to stay with you, I know my right, I’m not your prisoner banayin auren,! Bazan aureka ba! Bazan zauna da family dasuka kashemin Mama ba, wlh ban yafe muku gabaki dayan ku, Riyad na rantse da Allah I hate you I can’t even stand looking at you” wlh kanshi har wani irin sarawa yake sabida ciwon kan fitinan Rashida, kaman kanshi zai rabe yakeji, ahankali yana kallonta yace “let’s go inside, na chanza miki gida tunda bakison chan” ihu tayi tace “not just gida kaima gabaki dayanka banson ganinka, I said i hate you Riyad bakaji bane? Let me go kasakeni! Ka sakeni! I don’t want you dole ne” hannunshi yamiko mata yace “let’s go inside” kabar da hannunshi tayi harsaida hannun yadaki kofan mota yasake kallonta, ganin bazata taba fitowa daga motan inba ta karfi ba yasa yashigo ya dauke ta by fire by force yafito yawuce cikin gidan da ita, woww falon kaman ba a Nigeria ba sama yayi da ita, yabude wani mad hadadden room yasauketa ciki ta zabura ta tashi tace “wlh bazan zauna agidanka ba” cikeda lallashi Riyad yace “Rashida please listen to me, dan girman Allah, I know you’re hurt! But dan Allah please listen to me” hannu tasa ta tureshi da duka karfinta ganin yana tahowa gab da ita, yayi baya cus da duka energy ta ta tureshi tace “don’t you dare come close to me, na tsaneka Riyad, na tsaneku duka” sarawan da kanshi yafarayi baisan sanda yadafa bangoba jin kaman jiri na neman kwasheshi, hakan yasa yajuya drawer dake gefe yabude yaciro bundle na key yayi kofa yabude, ganin tabiyoshi yasa ya kulle kofan yasa key yanaji tana ihu tana bugawa yawuce yasauka kasa ya dafe kanshi yazauna a last staircase yana dauke ijiyan zuciya kanshi kaman zai fadi kasa.


EPISODE 52 

Yana zaune awajen dafe da kanshi dake neman tsagewa yana jiyo yanda Rashida ke buga kofan kaman zata sauke kofan kasa tana kuka tana ihu wayanshi yahau ringing, hannu yakai aljihunshi yaciro wayan yaga Mom, chan saiga yaga Munir duk yaki dauka, ganin Gwaggo na kiranshi yasa ya dauka batare dayay magana ba cikin muryan kuka tace “Riyad kana ina? Ina ka kaita?” Da muryanshi datadan dishashe yace “Gwaggo na kaita somewhere da zata natsu ta saurareni in that house she will never calm down” cikin wani irin emotional kuka Gwaggo tace “Allah na tuba, Allah ka yafeni, wani kalan kuskure da shirme muka tafka shekaru 23 dasuka wuce, Innalillahi wa innailaihi raji’un Ya Allah Ya Allah natuba Ya Allah mun tuba, Ya Allah mun tuba…..” ganin yanda Gwaggo tarude take sambatu yasa ahankali ya tashi yana dafa kanshi yawuce waje da hannu yakira security yace “be on alert, I will be back soon” ya shiga mota suka budemai gate yafice gida yakoma yanda yabar kowa afalon Ammi ahaka yazo yasamesu har lokacin Gwaggo kuka take, suna ganinshi duk suka juyo Gwaggo tashare fuskanta tace “Riyad gayamin komi da komi dakasani game da Rashida, wlh ina ganin yarinyar nan naga jinin Mujitappa na, tell me everything about her” waje yasamu ya zauna yayi shiru anatse yace “almost dukanku kun ganta in that CCTV footage one year ago I guess sabida is not clear saisa baku ganeta ba, ranan da akaso akasheni a airport was the first ever time danasan Rashida……” yashiga bada labarin Rashida daga farko har zuwa karshe all abinda yasani without hiding anything kowa ya shiga kallon Jummai da gabanta ke faduwa babu kakkautawa, babu wasa akan fuskan Muji dan yanada zafi bana wasaba yace “ya akayi har kikasan wajen zaman su? Har kinsha zuwa ba sau daya ba biyu ba uku ba? Why did you lock My daughter a police station”? Yanda yafadi my daughter saida Jummai taji kaman wuka aka chakamata aciki amman ta daure cikeda makirci tace “na farko dai na yarda nayi laifi tunda har nine na dauki kafafuna naje gidansu da sunan bada zakkan fiddakai, na biyu shine matar nan tarasu balle asan gaskiya asan karya, ita da diyarta dole su hada baki suso ganin nima karabu dani yanda karabu da uwarta” Coincidentally nasan gidansu shima was just ranan naje anguwan tunda naga mabukata ne a anguwa naje raba abinci gida gida tana ganina tanunama yatta ni wai nine kishiyarta yarta ta shakeni ta shake bayina harda fasamus…..

 saikuma tai shiru ganin Riyad na kallonta yace “wat about the ICU part Jummai?” Kasa magana Jummai tayi Riyad yace “I can call the Inspector right away suyi presenting case din for mijinki” yakalli Baffa yace “Baffa matarka lied cewa bayin suna ICU aka kulle Rashida in one of the worst cell dasuke dashi, she was planinnig on sending her to jail and she stood there lying comfortably cewa ranan tafara zuwa gidan idan ranan ne maisa daga ganinsu zataso tai locking yarta a cell?” Dasauri Jummai tashiga kallon Riyad da bata taba tunanin sun bashi labarin su ba, saikuma ta kalli Muji dake mugun kallonta, yau for the first time ta fuska daban yake ganin ta kaman an yaye wani lullubi, he trust Jummai blindly amman yau yaga he was wrong cus she’s lying, da mamaki Muji yace “kece kikaje gidansu kika hada tashin hankalin dayayi sanadiyan mutuwan Zainab?” Dasauri Jummai tashiga girgizakai tace “wlh wlh bahaka bane” wani tsawa Muji yamata da saida dakin ya girgiza yace “tell me Yayane to Jummai? Matar da tunda na rabu da ita kowa na gidan nan bai karabi takanta ba we simply close her chapter and moved on ya akai kika cigaba da bibiyan rayuwanta tunba yauba har just gab da this salla da akayi few days ago?” Baki Jummai tabude zatai magana Muji yanunata da yatsa yace “don’t you dare lie to me! Wlh I can pick you up naje dake koma inane anguwansu nashiga dake gida gida ina tambayansu ko sun sanki, sau nawa kenan suna ganinki a anguwan, idan Riyad yamiki karya ai yan anguwa bazasu miki karyaba, why did you do that why? Tell me Jummai”? Jinzai kaita anguwan kuma tsaf zai iya gashi ko Baba Liman kadai ya isa yace tazo anguwan nan tana damun su tana tara musu jama’a yafi akirga, how come asirinta ya tonu haka? She messed up big time, bata taba sani a day like this zaizo ba, mesa ma Allah zai wurga Riyad rayuwan su Rashida? Kai Innalillahi, yanzu yaxartayi? Saima tarasa abinda zatace saikuma chan ganin yanda kowa ke kallonta tace “wlh sherin shedan ne da sherin kishi Muji you’re the Man dana taba so arayuwana Zainab na zuwa tarabani dakai bawai wani abu bane kawai…” cikin fada sosai Muji yace “is that the reason why kika dinga yadasu a anguwa cewa tanada HIV aka hana y’ata zaman lafiya”? Kallonshi tayi ganin yanda yake ihu kaman shima ba abinda yayiba kenan ahankali tace “but kaima ai haka kayi katara jama’an fada ka sanar HIV gareta kasa aka watso kayanta ka korata, it’s just a replic…….” Tass Muji ya kwasheta da mari dayasa tai baya tana tangal tangal zata fadi ta dafe kuncinta tana kallonshi yana wani huci yace “kome nama Zainab atleast ni mijinta ne alokacin, kuma nitama laifi, kefa? Wayeke gareta? Kin ijiyeta ne? Ko zamanki take a anguwan how dare you Jummai, why are you so evil and wicked and bad dama haka kike? Na sakeki saki biyu!” Da sauri takalli Muji gabanta na faduwa saikuma tafashe da kuka tana dukawa zatai magana Riyad yace “not a word!”.

Ahankali Ammi tabar yan falon na lallashi Muji dat is completely heartbroken filled with regrets da danasani, tawuce sama dakinta tabude ahankali akasa taga Riyad yazauna ya kife kanshi kan kafa Munir na gefenshi yadafashi, wucewa tayi inda yake gently ta daura hannunshi saman kanshi dago kanshi yayi idanunshi sunyi jajir ganin Ammi yasa yakasa hadiyewa yakasa daurewa sai hawaye masu zafi yace “Ammi how can I even look at Rashida na gayamata yan gidanmu killed her Mother? How Ammi? Ammi tayaya zan gayamata poison akaba Mama eh?” huci yayi me zafi yace “Ammi if I were in Rashida shoe ni kaina bazan taba zaman aure da mutum daya fito daga gida filled with evil killers menene menene ba, Ammi we wronged Rashida da yawa, how can I look at her nagaya mata all this I can not do it Ammi I can’t, I can’t Ammi, Ammi she will hates me more, Ammi wat do I do now? Yazanyi, Ammi why do I have to come from this kind of family???”. NOW ADVICE RIYAD HOW IS HE GOING TO HANDLE RASHIDA??? YAGAYAMATA YAN GIDANSU SUKA KASHE MAMA HAR LAHIRA??? KO YA BOYEMATA??? HELP HIM OOOO


Kowa kallonta yake tace “nasan zata iya karyatani amman kun ganni nan kap rayuwana bansan wani me HIV ba ita ke gayamin cikin bayin da aka kawo mata daga wani yaki lokacin akwai wata daketa ciwo takaita asibiti akama yarinyar gwaji akace HIV ne inhar zaku tuna cikin bayi da aka rarraba lokacin wata mai suna Safara’u Mamanka akaba” Gwaggo tace “kwarai natuna Safara’u idan naje dakin Maryam ina cewa ke bakicin abinci ne amman daga baya nadena ganinta, Jummai tace “bayan tagano tanada HIV ta sallami yarinyar a boye tabata kudi takula da kanta shine take gayamin zata iya kiran yarinyar awaya mu mata allura mu debi jininta musan yanda zamuyi mu sama Zainab jinin ajiki” Kowa kallon Jummai yake adakin tace haka takira yarinyar ita oo baniba tasa hannu tadauki sirinji taja jinin yarinyar tabani natafi dashi lokacin Zainab batada lafiya cus cikin na wata guda mugun laulayi take, ana ma kara mata ruwa ne tana bacci kuma tanada nauyin bacci, lokacin yayi daidai da lokacin da babu kowa adakin, Muji yafita aiki naje na zare karin ruwan kaman yanda ake dura maka allura ta wajen yashiga jijiya haka na kafa gindin sirinjin a ramin na fesa jinin ina kallo ina murmushi cikin bacci tadanyi motsi ta tashi da sauri naja ruwan ina maidamata nace yacirene ruwan koma baccin ki, takoma bacci natashi natafi naje na jefa syringe din abola. Nadinga cewa zaiyi kuwa Mrayam nacemin ai zaiyi menene menene ahaka data fara ciwo awata na shida akace HIV n…..” wani irin fizge kanshi Muji yayi yay wajen Jummai yafara dukanta tana ihu saida aka rikeshi tahau dariya kaman mahaukaciya tace “ku kasheni to me yarage narasaka Muji I’ve lost komi, kome nayi aduniya sabida kaine dan haka tafashe kawai guess wat har asibiti na bita nabata guba ta mutu! Yes i poisoned her” Innalillahi yanda kirjin Riyad ke bugawa yakusa barewa so Mrs Bugaje was right data kirashi just last night harya fara bacci tace tana suspecting poisoning Mama akayi cus bakinta was green datana mata wanka tagani but tanakan investigation. Wannan karan wani kalan zubewa Muji yayi akasa yana kallon Jummai dake kallonshi tace “I was a good wife babu abinda bana maka, kusan bautamaka nakeyi, after Allah da shine ubangijina wanda nake bautamawa you were the next person in my life, ka kama kayimin kishiya ka manta dani da duk abubuwan dana maka, wata ta dauke maka hankali dare daya, nikuma nai alkawari saina rabaku har abada!” Runtse idanu Riyad yayi duk yanda yaso yadaure saiga hawaye sun zubo daga idanunshi, ko shine Rashida bazaiso yayi zaman aure da wanda members of his family are like this ba. Fuskanshi ya share yamike tsaye tareda juyawa yace “ku kulle both Maryam and Jummai and call the police they will both pay for crime nasu, Mama will get justice” dasauri Mom tace “Riyad Riyad” wani ihu yayi yace “take this two women out of this room now!” Fita dasu fadawa sukayi shikuma Riyad yawuce sama da gudu. Hatta Maman Kabeer saida jikinta yayi sanyi tasan da sunso su kashe Riyad but bayan yazo yazama sarki sun hakura ganin be wani iyaba sunsan zaiyi making mistake daga baya, or da kanshi ma yace yasauka, wickedness din Jummai da Mom bazata taba iyawaba, haba HIV fa ina mata zasu da kishi, itada mijinta yayi mata hudu curr da kwarakwari fa tace me? Ina mata zasu da kishi? What is this? Infect innocent woman da HIV Ya Allah, jitayi jikinta yayi sanyi wani tuba da tsoron Allah na shiganta, remembering yanda Mama ke kuka alokacin tana cewa ita ba fasika bace Allahu Akbar! Allahu Akbar! Inama tana raye! Wayyo Allah.


EPISODE 53

Cikin wani kalan izza da kamala Riyad yace "already gidan sarauta yayi suna ganinmu ake like wicked people, masu bakar zuciya, masu neman dukiya da power at all cost, wayanda can do anything to get abinda sukeso harda kisan kai, masu danne wanda sukaso su danne, i want to be a king that will make a change na nunama duniya cewa good people exit agidan sarauta! Masu purest of heart, marasa ill intention" cikin kakkausan murya yace "ayau zan kafa sabuwan doka agidan nan Sarkin Gida" Sarkin Gida yashigo da gudu da sauran fadawa zasu gaida Riyad ya daga musu hannu irin baiso yace "ku saurara ku rubuta acikin littafin dookoki Masarautan Kano cewa duk wanda aka kama dawani hali na makirci, kona sheri, kona mugunta, ko cutar da wasu mahalukin, dan Adam ko babba ko karami, kowa waye masarautan nan zata kori mutumin mu yanke alaka dashi!" Dasauri Jummai takama wandon Muji tana "dan Allah dan Allah kayakuri Mijina, kasa baki" kowa kallon Riyad ake kusan duka family basu taba ganin this brave angry Riyad ba, today is the first day dasuke ganin Riyad as king, idanunsu ada suna ganinshi as just Riyad ne but yau Riyad yazama real Sarki a idanunsu, Juyowa yayi yakalli Jummai yace "wannan matar mai suna Jummai an kamata da sherin kazafi! Sheri.takurama bayin Allah, musguna musu, makirci and duka lokacin datake aikata ayyukan nan tana nuna eh daga masarauta na tafito bawai ta boye identity nata bane dan haka zan aikata gidan alkatau na nan gidan saurauta dazatai aiki na sharan masarautan nan ko'ina na tsawon wata daya kafin bayan wata dayan akoreta tabar gidan har abada!" Dasauri Jummai tamike tsaye tana kallon Riyad da mijinta dakuma fadawa dataga suna zuwa kanta zasu kamata ganindai da gaske ta kwana ciki yasa ta kalli Mom dataga taki kallonta daidai fadawan sunzo sunwani jata kaman jaka ihu tayi Jummai tace "inhar zaka hukuntani haka Mai Martaba kasan cewa harda uwarka yakamata kahada" dasauri Mom tace

"kujata kufita da ita mana ta ishe mutane da surutu" fadawa suka wani jata Mom Riyad yakalla kafin adake yace "wait!" Tsayawa fadawan sukayi dasauri Mom tace "Riyad mehaka? Kabari atafi da ita mana" Murmushi Jummai tayi Riyad yace "wace mahaifiyata kike magana?" Tana kallonshi tace

"wacce harta tsargu tafara magana" dasauri Mom tace "nikuma zakima sheri makira irinki is capable of doing anything" ihu Riyad yama Mom yace

"quiet! Mom don't speak again idan bance kiyiba" yakalli Jummai yace "idan kika kuskura kikama mamana sheri bazakizo abinda zan miki ba Jummai" dasauri tace "bazan tabama mamanka sheri ba cus inada evidence ga wayata nan tsakar falo dauka kabude kaje call log zakaga nakirata last night itama takirani i record call namu play it" daukan wayan bafade yayi yabama Riyad ya karba, Playing voice din Riyad yayi kawai sai jikin Mom yahau rawa kaman kasa ya tsage tashiga ciki takeji, tunda yafarajin maganan su akakai inda Jummai ke cewa Mom was behind HIV Mama kawai wayan yafice daga hannun Riyad yafadi akasa yanda Riyad ya shiga shock na Muji was even was even worst, saida Hambali yarikeshi Mom kawai ta dafe kanta  kunya ya shigeta but deep down bata wani damuba sabida Babanta is attorney general kuma ai is a plan she suggested not executed.

Jummai ganinsu yanda kowa ke cikin shock yasa takwashe da dariya tace "yes yes yes! Na tsani Zainab sabida tashigo gidana ta daukemin farin ciki, shekaranmu nawa muna neman haihuwa ita tazo ta samu mijina ya manta dani, nadawo banda amfani da amaryansa yake naje na sami Maryam nagaya mata tace min idan inaso na maida soyayyan da Muji kema Zainab zuwa kiyayya tanada plan!

Kowa kallonta yake tace "nasan zata iya karyatani amman kun ganni nan kap rayuwana bansan wani me HIV ba ita ke gayamin cikin bayin da aka kawo mata daga wani yaki lokacin akwai wata daketa ciwo takaita asibiti akama yarinyar gwaji akace HIV ne inhar zaku tuna cikin bayi da aka rarraba lokacin wata mai suna Safara'u Mamanka akaba" Gwaggo tace "kwarai natuna Safara'u idan naje dakin

Maryam ina cewa ke bakicin abinci ne amman daga baya nadena ganinta, Jummai tace "bayan tagano tanada HIV ta sallami yarinyar a boye tabata kudi takula da kanta shine take gayamin zata iya kiran yarinyar awaya mu mata allura mu debi jininta musan yanda zamuyi mu sama Zainab jinin ajiki" Kowa kallon Jummai yake adakin tace haka takira yarinyar ita oo baniba tasa hannu tadauki sirinji taja jinin yarinyar tabani natafi dashi lokacin Zainab batada lafiya cus cikin na wata guda mugun laulayi take, ana ma kara mata ruwa ne tana bacci kuma tanada nauyin bacci, lokacin yayi daidai da lokacin da babu kowa adakin, Muji yafita aiki naje na zare karin ruwan kaman vanda ake dura maka allura ta wajen yashiga jijiya haka na kafa gindin sirinjin a ramin na fesa jinin ina kallo ina murmushi cikin bacci tadanyi motsi ta tashi da sauri naja ruwan ina maidamata nace yacirene ruwan koma baccin ki, takoma bacci natashi natafi naje na jefa syringe din abola. Nadinga cewa zaiyi kuwa Mrayam nacemin ai zaiyi menene menene ahaka data fara ciwo awata na shida akace HIV n...." wani irin fizge kanshi Muji yayi yay wajen Jummai yafara dukanta tana ihu saida aka rikeshi tahau dariya kaman mahaukaciya tace "ku kasheni to me yarage narasaka Muji I've lost komi, kome nayi aduniya sabida kaine dan haka tafashe kawai guess wat har asibiti na bita nabata guba ta mutu! Yes i poisoned her" Innalillahi yanda kirjin Riyad ke bugawa yakusa barewa so Mrs Bugaje was right data kirashi just last night harya fara bacci tace tana suspecting poisoning Mama akayi cus bakinta was green datana mata wanka tagani but tanakan investigation.

Wannan karan wani kalan zubewa Muji yayi akasa yana kallon Jummai dake kallonshi tace "I was a good wife babu abinda bana maka, kusan bautamaka nakeyi, after Allah da shine ubangijina wanda nake bautamawa you were the next person in my life, ka kama kayimin kishiya ka manta dani da duk abubuwan dana maka, wata ta dauke maka hankali dare daya, nikuma nai alkawari saina rabaku har abada!" Runtse idanu Riyad yayi duk yanda yaso yadaure saiga hawaye sun zubo daga idanunshi, ko shine Rashida bazaiso yayi zaman aure da wanda members of his family are like this ba. Fuskanshi ya share yamike tsaye tareda juyawa yace "ku kulle both Maryam and Jummai and call the police they will both pay for crime nasu, Mama will get justice" dasauri Mom tace "Riyad riyad wani ihu yayi yace "take this two women out of this room now!" Fita dasu fadawa sukayi shikuma Riyad yawuce sama da gudu.

Hatta Maman Kabeer saida jikinta yayi sanyi tasan da sunso su kashe Riyad but bayan yazo yazama sarki sun hakura ganin be wani iyaba sunsan zaiyi making mistake daga baya, or da kanshi ma yace yasauka, wickedness din Jummai da Mom bazata taba iyawaba, haba HIV fa ina mata zasu da kishi, itada mijinta yayi mata hudu curr da kwarakwari fa tace me? Ina mata zasu da kishi? What is this?

Infect innocent woman da HIV Ya Allah, jitayi jikinta yayi sanyi wani tuba da tsoron Allah na shiganta, remembering yanda Mama ke kuka alokacin tana cewa ita ba fasika bace Allahu Akbar! Allahu Akbar!

Inama tana raye! Wayyo Allah.

Ahankali Ammi tabar yan falon na lallashi Muji dat is completely heartbroken filled with regrets da danasani, tawuce sama dakinta tabude ahankali akasa taga Riyad yazauna ya kife kanshi kan kafa Munir na gefenshi yadafashi, wucewa tayi inda yake gently ta daura hannunshi saman kanshi dago kanshi yayi idanunshi sunyi jajir ganin Ammi yasa yakasa hadiyewa yakasa daurewa sai hawaye masu zafi yace "Ammi how can I even look at Rashida na gayamata yan gidanmu killed her Mother? How Ammi? Ammi tayaya zan gayamata poison akaba Mama eh?" huci yayi me zafi yace "Ammi if I were in Rashida shoe ni kaina bazan taba zaman aure da mutum daya fito daga gida filled with evil killers menene menene ba, Ammi we wronged Rashida da yawa, how can I look at her nagaya mata all this I can not do it Ammi I can't, I can't Ammi, Ammi she will hates me more, Ammi wat do I do now?

Yazanyi, Ammi why do I have to come from this kind of family???". 


EPISODE 48 

Ammi na tsaye a kitchen tareda 3 ma’aikatan ta tana gwada musu yanda zasu zuba kullin alale data gama mixing da kanta a gwangwani dan alalen gwangwani ne a timetable na abincin yau taji an bankado kofan falo hakan yasa tace “ku zuzzuba ku inazuwa” dauraye hannunta daba wani datti tayi taja paper towel tana goge hannunta tana tafiya tafito daga kitchen din daidai Mom na daga Alkyabban Riyad da rawani datagani akan kujeran dinning hakan yasa ahaukace taja tray na glass cups dake kan dinning din tawani barar akasa suka watse tace “fitomin da d’ana ko badake nake magana ba kika maidani mahaukaciya? Riyad!” Strictly Ammi tace “sorry wani d’a kike magana exactly? Cus I know you don’t have one saidai nawa dan dake hannunki” huci Mom tahauyi tajuyo dasauri ta taho ta tsaya dab da Ammi dake kallonta tace “remember tun kinada cikinsa namiki alkawari I will make sure mijinmu ya karbeshi yabani i make sure all this years Riyad bai kalleki ba, and ko yanzu in gayamiki baki isa kice zaki karbe Riyad daga wajena ba, you can’t seprate me from my Son” murmushi Ammi tamata tace “with haukan nan you’ve lost him already” wani kallon uku saura kwata Mom kema Ammi kaman zata shaketa ta mutu, jin sahun tafiya yasa tajuyo takalli Riyad tawani irin bubbuga kirjinta tana kallonshi tace “ban hanaka shigowa dakin nan ba”? Riyad kallonta yake with I don’t care attitude yace “yes but I feel like coming shine nazo” zuciya ne ya dauki Mom ta daga hannu zata daurama Riyad mari chak Ammi tarike hannunta gam, Mom takalli Ammi tace “saken mini hannu” rike hannun Mom Ammi tayi gam with so much anger Mom tashiga kiciniyan kwace hannun ganin takasa yasa takalli Riyad tace “kagaya mata tasaki hannuna” Ammi na kallonta tace “kul Maryam! Ban haifo yarona dan wata ta daka ba, duk randa kikai kuskuren taba Riyad saina ijiye kunya a gefe wlh na baki kashi” sosai gaban Mom ke faduwa takalli Riyad ta kalli Ammi data kama hannunta gam tarike taki saki, Ammi tace “take your madness da mutanen dakika kawo bangarena kufita, you have no business here” Ammi tasaketa Mom na kallon hannunta ranta na bala’in kunfa, baki Mom tabude zatai magana Riyad dake kallonta yace “Mom don’t try halinki anan please mutafi” yataho wajen kai tsaye yakama hannunta wani irin fizge hannunta tayi tanuna Ammi tace “ni zaka disga sabida matan nan, sabida wannan munafuk……” “karki zagi mahaifiyata Mom!” Yanunama Mom yatsa dayasa Mom takalli Riyad kanta na neman juyawa da mamaki, azuciye Riyad yace “Sarkin Gida!” da sauri Sarkin gida yashigo tareda sauran fadawa dan tuntuni sukejin hayaniya but ba’a basu izinin shigowaba, yace “gani ranka shi dade, waya batama shalelen mutanen Kano rai”? Ranshi amugun bace yanuna Mom yace “escort her back to her quarters” dasauri fadawan suka zagaye Mom dakema Riyad wani irin kallo yakalli ma’aikatan da Mom tazo dasu yace “clean this mess!” cikeda girmamawa sukace “to Mai Martaba” Mom jitayi Ammi taci riba dayawa zatai magana daidai ana bude kofa Mai Babban (Gwaggo) tareda Mujitappa dakuma Hambali sai Jummai da Lami (matar Hambali) da Maman Kabeer, dakuma Binta (3rd Matan sarki)suka shigo falon suna kallon kwalaben dake falon tace “meke faruwa ne anan? Ke lafiya Maryama kika mana messege dukan mu kafin muzo gulma sai yawo take cikin gida kinzo kina neman Hajara da dambe” Muji ne yabi dakin da kallo sannan yakalli Riyad yace “what happened Riyad”? Dasauri Mom tace “ina zai iya gayamaka an zugashi yana zagina” 


EPISODE 54

Ahankali ta tashi tsaye takai bayanta ta goge fuskanta sannan tadaga jajayen rinannun idanunshi takalleshi tace “Riyad bana sonka! Ganinka na karama zuciyana azaba da ciwo, ganinka reminds me of yan gidanku, my mother’s killer, ganinka reminds me of mutuwan Mama na, Riyad kasakeni!” “Nasakeki ina zaki? Your uncle sold gidanku, where will you go?” Cikin ihu tace “it’s none of your business! Zan koma hostel a school namu, ni ba yarinya bace I can take care of myself I’m 23yrs tun ina 13yrs nake kula da kaina na kula da Mamana on my own so just free me aure is not by force, I refuse to stay with you, bana auren kuma, sadakinka yana cikin black jakan goyona dake wajenka take d bag carry your money” tajuya zata wuce saiya sake tareta yama kasa magana yanda zuciya ke dibanta batasan sanda ta dauki flower verse dake wajen zata bugamai ba tana ihu tace “ka barni natafi or i will kill you kaima” hannunshi yasa yakama hannunta yacire verse din ya ijiye kawai yadauketa tako’ina kaimai duka take a kirji da wuya harda kunne, badadan shi namiji bane da wlh bazai iya dagata ba yanda take fada dashi dan tanada karfi da zuciya, bude kofan yayi ya maidata dakin yafito da sauri ya kulle kofan yana saka key yarasa yanda zaiyi yanaji tana jijjiga kofan, wlh dabadan standard security door bane da rashida taballa kofan ayanda take dambe da kofan, saukowa falo yayi ya zauna yadafe kanshi ganin yarasa yanda zaiyi ga kukanta har zuciyanshi yakeji yasa yafito waje sai kawai yawuce mota ya shiga yazauna shi kadai chan saiga driver yazo yashigo ahankali riyad yace “general hospital” yashiga kiran dr bugaje ta amsa yace gashinan zuwa.

Direct office nata yawuce ganinshi kawai tayi tagane da wani abu waje ta nunamai hakan yasa yawuto ya zauna yakasa magana sabida yanda heart nashi ke racing, ahankali tace “meke faruwa? You look kaman kafito daga gidan dambe” tai maganan tana kallon wuyanshi dataga scratch harda dan jini amman batai magana ba, shiru yayi jijiyan gefen kanshi kadai ta kalla tagane ciwon kaima yake hakan yasa tabude fridge taciro bottle water mai sanyi tabashi karba yayi yabude yasha sannan tace “menene Riyad talk to me? Wayayi fada dakai haka”? Ahankali batare dayace Rashida bane yace “Ma tunda nasan su Rashida you’re the second person banda Mahaifiyarta danaga tana girmamawa, please I need your help” baimata boye boye ba yabata labarin komi komi har zuwa kan kisan Mama daya gano, batare daya fada mata Rashida ne tai fada dashi ba. Dr Bugaje tai shiru tana kallonshi da ace batasan yanda Mama ke son Riyad ba dako ita saitai supporting yasaki Rashida kowa yakama gabansa, but then again, Mama tells her deep deep abu wanda bata sharing da kowa, irin adult talk din nan cus she sees Mrs Bugaje as a friend, cikin maganganun Mama harda Riyad shine mutum na biyu data yarda dashi zai rike mata yarinya amana, Mama ta bala’in nuna mata yanda take matukar kaunar yarta da Riyad and she can never ignore it, she saw how Mama miraculously got better bayan an daura auren Rashida da Riyad, and ita babba ce she can’t hold Riyad responsible over abinda baidama wayau sanda abin yafaru, he’s just a 13yrs old boy dake boarding house ma then, that’s not fair, and taga yaron dudda bai fadiba taga zafaffen soyayyan dayake ma Rashida, he told her everything now but bai aibanta matanshi ba koyace tanata zaginshi ko fada dashi, instead he’s here to find a way to calm her down and to listen to him this alone show cewa Mama was not wrong about the boy! Riyad yakai miji! That aside, idan Rashida ta barshi ma taje ina? Watake dashi Uncle nata daya kori uwarta yanzu ya saida gidansu ne zata wajenshi ko ina? Tun yaushe aka rufe portal na hostel tun wace shekaran balle ma ace zata samu, how will she survive dudda tasan yarinyar can work, duk wuya duk dadi she must accept family ta yanda batada Mama and again mahaifinta shima yagano gaskiya zaizo ya neme gafara wajenta duk ataru azauna lafiya tunda an kama wayanda sukai laifin haka rayuwa take kowa da kaddaransa rayuwan da Mama tayi was her destiny she fulfilled it and left dunya. Ijiyan zuciya Mrs Bugaje tasauke cikeda hikima irin na manya tace “karka saketa! I don’t support kasaki Rashida!” Gyara zama Riyad yayi tareda sauke ijiyan zuciya karfi na shiganshi, Dr Bugaje tace “I understand Rashida sosai kome tama don’t blame her but then karka saketa zata sauko daga baya but I don’t think tadadi zata sauko” tai shiru kaman mai tunani chan tace “people like Rashida that are stubborn you have to device a stubborn plan dazakai pinning nata down dashi, dazai hanata tafiya sannan ta zauna dakai dole, and again free her kadena kulleta kaman prisoner, gobe idan tacemaka zata tafi kabarta karka hanata but find something dazaka kamata dashi like a hook, something dai I don’t know just think of something kune yaran zamani mu mun kwana biyu” shiru Riyad yayi chan yace “I think I know mezan mata” Ahankali Mrs Bugaje tace “mene?” Dan ijiyan zuciya yasauke yace “dan zaman danayi da ita Rashida mutum ce that self respect is everything to her batason taimako, batason raini, batason that feeling of entitlement, sannan she’s not a coward she don’t run or beg, gwara ta tsaya ayita akare, lokacin danakai Mom nata another hospital tace she must pay me back so I think….” Yadanyi shiru Dr Bugaje tai murmushi tace “perfect Riyad! Stubborn gurl stubborn plan Goodjob! Free her gobe let her be I know she will come her tagayamin komi I know wat to do idan tazo, tashi kaje ka huta and remember this” dasauri ya kalleta tace “it’s not your fault abinda yafaru dasu don’t be too hard on yourself kaddara ce and Rashida also it’s not her fault kaddara ce kome tayi don’t take it to heart she will come around Rashida is a nice girl, tazo gobe I will tell her to resume anata abubuwa suna wuceta maybe resuming zaisa damuwa yaragu azuciyanta just promise me you will always stand by her Riyad don’t betray trust da mahaifiyarta tamaka” ahankali yace “I will always stand by my wife Dr Bugaje” murmushi tamai tace “to saida safe, put balm on those scratch na wuyanta after shower” dan taba wajen yayi saikuma yajuya yafita da sauri akunyace yanajan riganshi yana rufe wajen.


EPISODE 55

Har yanzu yanada damuwa aranshi but dayama Mrs Bugaje explains komi about 40% na damuwan yatafi gida chan yakoma flat nashi yafada wanka yafito ya shirya cikin wasu kaya daban sannan yadauki laptop dinshi yashiga typing ba kakkautawa kafin yayi printing abinda yagama typing ya dauka ya kalla sannan yatashi yadauki wani envelop yasa aciki kafin yadauki pen da paper yazauna yayi wani rubutu shima yasa a envelop sannan yafito rike da abubuwan guda biyu yawuce side na Haleema.Wuraren 11 ya shiga gidan ya maida kofa yarufe yahayo sama ahankali yabude kofanta yaganta kwance akasa tana bacci awahale sai munshari take shiru yana yana kallonta, ko hayaniyan datayi yau ya isa yasata minshari, he just loves everything about her and overall yana tausayinta kaman me, shigowa dakin yayi yamika hannu kaman yadauketa but yana tsoron karya tadata saikuma yadaure after all kota tashi yanzu yanada plan gently yadauketa ko alamun tashi batayiba dan akwai ta da nauyin bacci sata yayi kan gadon ahankali yakai hannunshi yadaura saman kanta kaman yar yarinya gently yace “I’m sorry about your pain Jewel! I promise I will make it all go away” hannunshi yadaura kan kumatunta cikeda tsantsan so yace “just let me in, you don’t have to go through this difficult time alone, let me in Rashida, let me in please” yayi maganan yana dukowa ya manna mata kiss a goshi sannan yatashi bargo yaja yarufa mata ya kunna AC dakin ya kashe wuta sannan yafito yakoma dakinshi wanka yasakeyi ya kwanta wanda baiyi wani bacci ba yatashi yahau sallan dare da asuba yawuce mosque.

Jin gaisuwa da akema sarki yasa Haleematu ta mike tsaye da sauri tana kwashe plates na abincin dataci tun safe dasuke falon, plate dataci indomie yanzun nan shima yana wajen ta kwasa dasauri but kafin tagama hadawa yabude kofa yashigo suka hada ido kallonta yayi sannan yabi dakin da kallo dasauri tayi kitchen ta ijiye plate din tafito tace “inata kiran Mom tamaka magana kadawomin da bayina bata dauka badai kahadani da ita bane tana fushi dani ba” ijiyan zuciya yayi sannan yazaro envelope din daga aljihu ya ijiye mata akan kujera faduwa gabanta yayi tayi kujeran da gudu tadauka tashiga bude takardan. “NA SAKI HALEEMATU SAKI DAYA!” Reason sabida bani ta dauka amatsayin mijinta a auren mu ba, there’s a third party. Kallonta yayi strictly yace “park your things kitafi gidanku ki koyi zaman aure then give me a call idan kin shirya maidani mijinki sannan kin shirya zaman aure” yana maganan ya bude kofa yafita yana jiyo kukanta. Ahankali take bude idanunta tabi saman dakin da kallo kafin ta tashi zaune tareda taba bango luckily taji switch ta kunna wuta ganinta akan gado bayan tasan akasa tai bacci yasa tadinga mamaki tagumi tabuga saikuma tafashe da kuka tunawa da kashe Mama akayi cikin muryan Kuka tace “why did you sleep kema kikai bacci kaman kin mutu? Anyi poison Mama but bakusan ta yaya ba, kofan ta kalla tunanin a kulle yake yasa ta tafi bayi tabude akwai sabon brush da toothpaste dauka tayi shima dan kawai batajin dadin bakinta brush tayi tai wanka tayo alwala tafito bargon data dauka na gado tun jiya tana salla dashi takara dauka ta kabbarta sai hawaye take sharewa jitake kaman ta ramama Mamanta abinda aka mata, tunawa tai alkawari zata dinga karatun Al Qur’ani yasa tafara karatun daka mulk ta karanta gabaki daya tana zaune ahaka awajen taji an bude kofa ko kallon wajen batayiba, anatse Riyad dake kallonta yace “I’m ready to let you go but kifito falo I have something to tell you” dasauri tadago kanta ta kalleshi yana kallonta shima yace “Ammi tasamiki hijabi in that box kibude ki saka ki dauki takalmi also kifito” yana maganan yajuya dasauri ta tashi box din ta kalla daidai da tsinke nasu bataso amman kuma bazata iya fita ba hijabi ba hakan yasa tawuce box din tasauke ta bude taciro hijabin dayake dark blue tasaka har kasa yakaimata me hula gata fara saiya mata shegen kyau slippers tadauka tasaka shima sannan tabude kofa tashiga saukowa tundaga sama yake kallonta hijabin yamata wani kalan arnen kyau kaman ba gobe idanunta a kumbure gwanin ban tausayi karasa saukowa tayi batare data kalleshi ba ta tsaya wajen wani kujera tace “gani” dan ijiyan zuciya yasauke yadauke envelop na kusa dashi yadauka yabude yajawo papers na ciki guda uku yamika mata daga xaunen dayake yace “read this” kallon hannunshi tayi batare data kalli fuskanshi ba taki motsi, strictly yace “wannan ne ticket naki na amsan saki I will leave you for Good bazan taba tursasaki kiyi zaman aure da ni bakiso ba so gashi” jin maganan dayayi yasa tadanyi jim sai kuma chan cikeda taurin kai ta taho cikin falon yana kallonta babuko kyafta idanu ta taho tasa hannu ta karbe takardan tashiga karantawa anatse babu alamun wasa kan fuskanshi yace “this was drafted by my lawyer” anatse yace “as you said ke ba yarinya bane I can’t forced you to leave with me nor kidnap you tunda ni ba kidnapper bane but I can do one thing shine na karbi duka kudade na dana kashe akanku!” Dasauri Rashida data gama karatun komi na takardan ta kalleshi dan she’s very fast in reading, hade fuska yayi tamau kaman ba shi ba cikeda rashin mutunci yace “tunda na sanki I spent about 22Million naira akanki da mahaifiyarki kaman yanda kika karanta a papers din” Riyad ya gyara zama yana kallonta kyar kaman yanda take kallonshi kallon haka dama kake,  yace “incident daya faru a hotel I had to pay for medical treatment na yarinyar dakika daka and settle parents nata sabida karsukai kara, then Mahaifiyarki” yadanyi shiru yace “Allah jikanta! I spent money a hospital dana kaita, then nazo na kawo muku kayan abinci gidanku, kudin salla, saikuma rashin lafiyan nan datayi last that I paid everything which komi na rubuta kudin akasa, I break down the details inhar you pay me all of this money I will let you go forever!”

Kallon tsantsan tsana Rashida kema Riyad, sabida tace yasaketa shine yake cemata tabiyashi everything daya kashe akanta, tama kasa magana cus kudin slamp head and mouth dinta taji she’s speechless, anatse Riyad yace “your Mom tabani amanarki agaban kowa dudda is not on papers but kaman tayi assigning dina as next of king dinki ne, inhar baki biyani kudina ba you can’t leave my house haka lawyer na yace, idan kin bari kuma I can take legal action against you! Bazan takuraki ba anytime kika shirya biyana you can! But you have to leave with me and under me, while kina living dani bazan taba miki kallon matata ba cus nasan kince kin tsaneni but ni a matsayina na mijinki hakki na kaina ma ciyar dake da tufatar dake that I will do banda haka you are a nobody banmasan kina existing ba, thank god bake kadaine mace aduniyaba! And I have another wife!” Yadanyi shiru sannan yakalleta yace “as long as baki biyani ba kina karkashina the only aiki dana yarda kiyi kuma kije is your school and clinic, ni Sarki ne those shara and washing of toilet you dare not do such!” Yafadi da kakkausan murya yana mikewa tsaye yace “you are free Rashidah ke ba prisoner bane idan kinada anywhere dazaki you can go but dole ki kwana agidan nan inhar baki biyani ba or else duk inda kika shiga zansa akamoki aduniya” yayi maganan yana jefa mata key na gidan kan kujeran dake kusa da ita yace “that’s your key and this is your house bazan dinga zama anan ba inada Masarauta to run” haryahau bene yace “ohh I remembered something” saiya dawo da sauri yana ciro iPhone nata daga aljihu yace “nasa kudin wayan nan a list din so ita yours not mine tunda zaki biyani kudinshi take abinki, ur sim is inside ga school bag naki chan” yawuce sama abinshi Rashida mutuwan tsaye tayi 22Million naira ta ina zata fara biyanshi? Yanzu dama duk abubuwan daya musu ba kyauta bane? Saikuma wani bangare na zuciyanta yace keda kanki kince zaki biyashi ai lokacin saisa, hawaye ta share tasake sharewa tana kallon kudaden she has mugun self respect and she’s not a coward she rather die tana aiki danta biyashi than ta cemai ya yafemata kudin koya yakuri, wallahi bazatayi ba! Bayan hannu takai kan fuskanta sannan tace “Riyad Rashida tamaka alkawari she will pay you this money ko mujima komu dade!” Jakanta ta dauka da wayan tunda yasaka kudin kawai tayi kofa tafice batare data dauke key nashi ba.   DID YOU SUPPORT DECISION DIN RIYAD???? 


EPISODE 56

Dasauri Rashida takalleshi jin abinda yafadi saikuma ta dauke kai takasa magana, cikin dan kakkausan murya yace “nima bawai inayi bane cus i want to do nope, as long as igiyoyin auren mu are intact you’re my responsibility and dole na cika hakkokina dake kanki you are too small kisa Allah yakamani” dasauri tadago kanta ta kalleshi wani shu’umin kallo ya zuba mata yace “get in cus I don’t want to ever force you kiyi wani abu, this is hakki akaina!” Abu tahadiye awuya kaman ta shakeshi ta fizge hannunta da karfi tanaji kaman ta kurma ihu cikeda taurinkai tashiga bayan motan ta zauna kaman bataso ta shiga, driver dake wajen gate yataso dasauri ganin ta shiga ga mamakinta gani tayi yashigo bayan shima dasauri ta kalleshi danta dauka agaba zai zauna, gyara zama yayi sai kamshi mai bala’in dadi yake, matsawa tayi chan karshe da sauri driver na zuwa ya duka yace “Barka da fitowa Ranka shi dade, Allah ya taimakeka, Allah ya karamaka daraja!” Gyadamai kai Riyad yayi ahankali, driver yasake dukawa yace “barka da fitowa ranki shi dade uwar dakina” juyo da kanta Rashida tayi haushin Riyad yasa tawani ballamai harara, da hannu Riyad yamai alamu ya rufo musu kofan, rufowa yayi yakoma ya shiga gaba yatada motan sukabar gidan sundan shiga hanya chan Riyad yace “what time zaku gama?” Kaman bada ita yake magana ba tai banza dashi, anatse yace “ban baki izinin hawa any form na abin hawaba, I asked you wat time zaki gama?” Yayi maganan yana zubamata idanu kaman bazatai magana ba chan tace “nima bansani ba” authoritatively yace “mukaje zaki shiga ciki ki duba roaster and call me ki sanar dani, i will send my driver ya dauko ki” cikin fushi tace “ko an tashi inada wajen zuwa?” Ahankali yace “where?” Shiru tayi tai banza dashi unexpectedly kawai taji ya fizgota ta taho jikinshi lokaci daya hannunshi yasa kan waist nata yarike gam, arude ta kalleshi jin yanda yakama mata kwankwaso hada idanu sukayi kawai taji gabanta na mugun faduwa sabida yanda yake mata wani shu’umin kallo takasa magana sai kokarin kwace kanta datakeyi takasa tana numfashi da sauri da sauri, hannunshi akan waist nata kaman shock, strictly yace “next time idan namiki magana open mouth ki bani amsa” yadanyi shiru kadan yana kallon fuskanta kaman yau yafara ganinta kafin yakara pressing waist nata dayaga tawani zabura yace “ina zakije after school”? Wlh she’s breathing way to fast sabida yanda take kan jikinshi ga wani irin abu da hannunshi kema waist nata, ga driver na tukasu kuma babba ne driver ba yaro ba, kunya ma taji tanaji kaman ta shige kasa batasan sanda tace “saloon zani nai kitso 4 zamu gama” yana kallonta yace “bazaki je ba!” Da sauri ta kalleshi dudda gabanta na faduwa saida ta turomai baki cikeda stubbornness, lips dinta yabida mayen kallo yana tuna randa yayi kissing nata dasauri yazare hannunshi daga waist nata hakan yasa tasauka daga jikinshi da sauri takoma waje ta zauna har lokacin kirjinta bugawa yake har sukakai school babu wanda yasake magana Riyad yace “ina zamu ijiyeki”? ahankali tace “gynae” har gaban department din sukaje sukai parking dasauri tashiga kiciniyar bude kofan saikuma ta tsaya chak takasa magana duk yana kallonta ahankali yataho wajen mannewa tayi jikin kujera kallonta yayi suka hada idanu dasauri yadauke

Tadauke kanta cikeda jin haushin shi tarasa mesa gabanta ke faduwa ahankali yasauke hannunshi daya kan cinyanta da sauri ta kalleshi hada ido sukayi hannun nakan cinyanta yana kallonta bayama kiciniyar bude kofan ture hannunshi tayi da sauri hakan yasa yakoma ya zauna wajenshi chan yace “open door for her” Dasauri driver yace “to Yallabai” haushi Rashida taji yakamata wato da gangan yahana abude mata bude mata akayi tajuya da sauri zata fita karaf taji yarike hannunta da sauri tajuyo ta kalleshi yana kallon cikin idanunta yace “today should be the last day dazaki bar gidana bakiyi breakfast ba” haderai tayi hannu yasa a aljihunshi yaciro kudade dabaisan yawansu ba zai samata a hannu azuciye tace “ni banson kudin ka karike kayanka, Allah kyauta” hannunta yabude da karfi yasa kudin a tsakiya yace “hakki nane na ciyar da matata! U can trash them kika fita idan kinga dama but dai use it eat” yana maganan yasaki hannunta zata ijiye kudin kan kujeran azuciye yace “kika ijiye kudin nan bazaki school din nan ba saikin deba kin tafi dasu” sosai taji ranta na baci ganin zai samata bakin ciki yasa kawai tajuya fuuuu tafice rikeda kudin a hannu ta shiga department dinsu.


EPISODE 57 

Gida yawuce zuwa bangarenshi soya ke ya kwanta he’s feeling very sick, jiya baiyi bacci ba sabida zazzabi, yana zaune trying to rest kanshi aka sanarda shi Baffan shi wants to see him bada izini yayi yasauko kasa daidai Muji na shigowa daya rame sosai yau kwananshi biyu baida lafiya kallo daya Riyad yamai yace “good morning Baffa” gyadamai kai Muji yayi saikuma yasake shiru, duk sukai shiru chan yace “Riyad ina tsananin and matukar fushi dakaina how could I blindly do abinda nayi” shiru Riyad yayi hakan yasa Muji yace “say something please Riyad” shiru Riyad yayi sai chan yace “Baffa in as much as banaso nai blaming naka inaso nace laifin Jummai ne wlh I can’t you’re also 💯 at fault” Riyad yadanyi shiru yace “all your life agidan nan kake tun zamanin su grandfather namu Baffa you know wat gidan sarauta is don’t you for once ever think cewa this HIV might be a set up tunda matarka tanata rantsuwa bata taba fasikanci ba”?Lumshe idanu Muji yayi Riyad adan zafaffe yace “wat is the point na aure idan we can not protect our love ones? Uncle kaje har kauye ka auro innocent girl dake middle of secondary school nata ka kawota masarautanku as a very healthy girl, tazo tayi ciki lafiya lau bayan some months ace tanada HIV Uncle even me I will investigate the matter! I will want to know how? Tayaya? Waye tayi fasikancin dashi yasamata, tana fita ne ina take zuwa? This are all questions daya kamata ka tambaya but baka tsaya ka saurareta ba tunda kukai test kaida Jummai kaga negative kawai kayi concluding….”Riyad yadanyi shiru cus he’s hurting and kanshi is pounding, chan yace “Baffa tell me menene meaning of tara mata, bayi, jama’an fada ka tona mata asiri a watsar mata da kaya a koreta and Babana shima ya tsaya yana kallon komi wat was that? Uncle sabida tanada HIV? Ko fasikancin tayi did she deserve that tozarci? Eh?” Hannu Muji yadaura akan fuskanshi yafashe da kuka sosai kaman yaro yace “Riyad bana iya bacci, bana iyacin abinci, nayi nadaman abinda namata, bansan abinda ya shigeni a lokacin ba all I know is naso Zainab kaman raina danaji tanada HiV na yanke shawaran maza takebi dan tanada kyau, lokacin damukaje Umara wani yataba tareta agabana wai yana sonta bazai karyaba saiya gayamata, danaji batun HIV babu abinda ban ayyana ba I was madly jealous and angry Riyad, na shiga uku Innalillahi wa innailaihi raji’un, look at shirmen dana tafka ni karan kaina nakasa forgiving kaina, I don’t even know tayaya zan tunkari y’ata da batun yafiya bansan yaya zanyi ba”.

Shiru Riyad yayi yana kallonshi he’s angry with Uncle but then wats the point of anger, fushin shi zai chanza abinda yafaru a baya ne? Idan yarike Uncle nashi a zuciya what’s the difference between shi da Rashidan? Tashi yayi ahankali zuwa inda Muji yake gently Riyad yadafashi dago idanunshi yayi ahankali yace “it’s okay Uncle stop crying please” ahankali Muji yace “Riyad yaya zanbi Rashida tayafemin” ahankali Riyad yace “I don’t know! Kabari tafara saukowa tukunna just put yourself back together Uncle we will all get through this phase Insha Allah, be strong kaji” gyadamai kai Muji yayi Riyad yace “how is Gwaggo zanje na dubata anjima?” Gyadamai kai Muji yayi yace “tell me about my daughter Riyad…….”

EPISODE 58 

 Tadawo normal shift by 4 aka sallamesu, masallaci tawuce harta shiga ciki tana shirin yin alwala aka kwala mata kira dasauri tajuyo Maimoon tagani tana zuwa batai wata wata ba tawani rungumeta cikeda kauna tace “I heard you lost your Mom, Allah ya gafarta mata, I asked number ki kowa yace baidashi, gidanku ma babu wanda yasani sorry kinji Rashida, I’m so sorry about your Mom, sorry Rashida Allah jikan Mama” wlh tunda tashigo asibitin nan yau adai cikin colleagues nata Maimoon is the first person data mata genuine gaisuwa, ciwon Mama made her realize how important people are in life and yanzu she wants to let people in, ahankali taji hawaye sunhau zubomata kawai saita fashe da kuka dasauri ajikin Maimoon hakan yasa sauran mataye dake wajen suka tsaitsaya suna tambaya lafiya, dan juyowa Maimoon tayi ta kallesu tace “mahaifiyarta ne tarasu” kawai sai aka taru awajen kowa sai gaisuwa akema Rashida ana lallashinta and abin yamata dadi sata akai tai alwala sannan duk suka shiga mosque tare sukai salla sai suka kara zagaye Rashida tareda Amiran MSS aka mata proper gaisuwa wlh she felt good and happy Mama tasami addu’a. 

Tareda Maimoon suka fito tamikama Rashida hannu tace “bani wayanki nasa number na ciki, and tell me inane gidanku zanzo” dan shiru Rashida tayi saikuma ta mika mata wayanta dake aljihun lab coat nata Maimoon ta karba wayan tace “wow nice phone” samata number ta tayi ciki tace “saura gidanku ina ne gidanku?” Dan shiru Rashida tayi batasan me zata ce ba batasan yaya ake friendship ba ahankali tace “an saida gidanmu da Mama tarasu” dasauri Maimoon da zuciya ta daya tace “oh okay but a ina kike zama ke yanzu incase zanzo?” Nauyi abin yake mata tace gidan mijinta da kyar tace “uhmm uhmmm” tsayawa Maimoon tayi tana kallonta da kyar Rashida tace “GRA” murmushi Maimoon tayi tace “muna kusa kusa ma ni area dinmu is kafin GRA, zomuje mu shiga adaidaita sahu mutafi” gyadamata kai tayi harsun fara tafiya dan wlh ta manta da zancen da Riyad yamata taji ance. “Ranki shi dade” Dasauri Rashida tajuyo har gabanta na faduwa driver dazu da safe ne ahankali yace “Mai Martaba ya aikoni na maidaki gida” kallon yanda driver kema ta magana da respect Maimoon tayi har yana duddukawa ranta abace Rashida tace “ni dakaina zan koma kaje” dasauri yace “ranki shi dade kimin rai! Yace idan bai maidaki gidaba abakin aikina” wani iri Rashida taji she knows aiki is important for lot of people bataso ta zama sanadin wani yarasa nashi saitai jim ganin haka yasa Maimoon tace “bishi nima natuna zan biya wani waje I will call you anjima bye” kafin Rashida ta amsa tawuce abin ta badan tasoba Rashida tabishi zuwa parking space yabude mata baya ta shiga sun fara tafiya yace “Yallabai yace na kaiki saloon Hajiya, yace na sanar dake wanke kan za’ayi kada a kitsa yamma tayi” batacemai komiba sai zuciyanta dake tafarfasa wayeshi dazai gayamata mezatayi hardly daman take kitso sai Mama tayi da gaske dan yawanci batada time dazata zauna ta bata tai kitso gani take lokacin ya isheta yin wani aikin dazata sami kudi wani babban saloon yakaita suka shiga ciki da driver taga yayi magana saikuma akazo nan nan ake da ita nan da nan aka wanke mata kan akai blow drying akai parking gashin tayi bala’in kyau sannan suka fito tasake shiga motan suka wuce gida lokacin 5 na yamma sai kallon gidan datake rayuwa ciki take kaman dream, sauka daga motan tayi tadauki jakanta tawuce ciki falon tabude bakowa sama tawuce zuwa dakinta komi na nan yanda tabari kaya tacire tafada wanka bayan ta wanke lab coat nata tafito tabude wardrobe din taciro wata english gown pink tasaka sannan tasa hijabi tafito tayi baya tana shanya labcoat taji daya daga cikin security yace “wlh yunwa nakeji kaje kasiyo mana abinci tunda nina siyo jiya”.

Wani iri taji jin maganansu bayan plenty abinci data gani agidan, kawai saitaji wat if tamusu girki tabasu sukaji dadi ladan yaje wajen Mama komawa ciki tayi taje sama ta ijiye bowl din saikuma ta sauko itama karan kanta so take tarage damuwa dazu datana aiki a hospital damuwan yatafi she was just caring for 5 patients da aka mata assigning she forgot everything bari tai girki cus yunwa takeji bataci komiba tun safe. 

Dirty rice tadafa dayaji mince meat, saikuma tayi pepper meat na naman rago, tayi fresh watermelon juice da oranges da pineapple dataga yasoma baci ana kiran magrib ta gama, zubawa tayi awani kula me kyau ta ijiye a dinning, tafito da juice data hada ta ijiye a dinning gwanin ban sha’awa da kulan naman da plates da spoon dan tanaso taje tayi salla saita fito taci sannan takoma kitchen tashiga kwacema security a wani babban kula ta zuba musu ta zuba musu nama dayawa saikuma juice nasu awani babban gora abubuwan sun mata yawa, dauko kulan abincin su tayi hankalinta gabaki daya yanakan marfin kulan data saka musu abincin takasa rufewa da kyau tana kiciniyan rufewa tama manta ba hijabi ajikinta balle dankwali tayi kofa kafin takai hannunta tabude kofan aka rigata bude kofan dasauri ta dago kanta hada ido tayi da Riyad da wannan karan yana sanye da 3quqter wando daya wucemai guiwa kadan black yasaka wani is white V neck shirt daya kamashi ya bala’in fito da muscles na hannunshi da broad chest nashi dakake iya ganin hair na chest nashi, bala’in faduwa gabanta yayi dayasa dasauri ta dauke kanta binta yayi da kallo daga sama zuwa kasa kawai saiyaji ranshi yayi masifan baci akufule yace “ina zaki”? Haderai tayi tana turo baki murya ciki ciki tace “abinci zan basu” “ahaka!” Yanunatada yatsa dayasa da sauri ta kalli kanta normal gown ne just that yabi jikinta da kyau rigan looks so sexy ajikinta, zatai magana kawai yasa hannu ya karbe flask din yajuya yafita yabugo kofan dayasa taballama kofan harara takoma kitchen tadauko dayan kulan da juice din tazo kofan daidai yana shigowa ganinta kuma yasa cikeda fada yace “go and join reality show sabida kowa ya ganki” tsayawa kallonshi tayi turus dan bata gane meyake nufi ba sai kawai ta duka ta ijiye kulan akasa tana kokarin ijiye juice din idanunshi suka sauka kan boobs dinta dake showing sabida yanda wuyan rigan ya zazzago in the process, damn! She has the sexiest balloon boobs kaman an saka mata silicon and so bouncy.


EPISODE 59

 Mugun tashi tsigan jikin Riyad yayi hango boobs nata dayayi da kyau dasauri ya runtse idanu itakuma ta tashi tajuya samin kanshi yayi da bude idanu da sauri yabi bayanta da kallo baitaba sanin tanada diri hakaba sai yau wat! Rashida nada crazy shape kaman ita tai kanta dudda batada wani kiba, baitabajin suran jikin wata mace ya burgeshi ba sai nata, ganin tajuyo yasa yadauke kanshi daga kallonta da sauri yaduka yana daukan kulan yafice itakuma tawuce sama da sauri ta shige dakinta bayi tawuce tai wanka tafito daure da towel tawuce wardrobe wani red rigan bacci tadauka that looks like singlet tasaka ya tsaya mata a cinya yanada hannun taliya tsaki tayi gajere ganin kalan kayan, is showing almost half na boobs nata, hijabi tasaka tai sallan magrib tana kan dadduman har akai isha’i tayi. Yau banda patient an musu lectures hakan yasa tabi lecture tai revising da duka abubuwan datayi yau da patients data duba takaranta komi

Ijiye komi tayi jin cikinta na kuka bataci abinci ba yau gabaki daya ahankali ta tashi tazo wajen kofa tabude kofanta kadan taga falon saman ma duhu babu kowa that means koya tafi ko yana dakinshi, afalo take hango haske, fitowa tayi ahankali tajawo kofan tarufe tashiga sauka staircase zuwa dinning din, kulan tabude taga anci abincin sosai hararan kulan tayi tace “saikace shina dafamawa” ahankali tadauki plate ta zuba daidai cikinta tasa nama guda daya tasaka spoon sannan tazauna tafara ci abincin yayi dadi sosai juice ta deba tanasha dayake daidai cikinta ne tadeba tass ta shanye ta tadauki plate din da cup takai kitchen ta ijiye tadawo tadauki kulan da juice din takai kitchen ta kwashe abincin daya rage tasa a packs tasa a fridge sannan ta wanke komi tadauki bottle water guda daya a hannu tafito daga cikin din ta taho zatahau staircase din taga Riyad na saukowa dagashi sai wandon pajamas dayadan zame kasa kadan kana hango boxers din dake cikin jikinshi na Calvin Klein white, ga kirjinshi awani bude ga strong 6 packs dinshi that made Jim looks hot, hannunshi data rike da waya yana tafiya ahankali kaman baida lpy, mugun faduwa kirjinta yayi jikinta yayi wani yirrrrr kasa motsi tayi, ita takasa tafiya takuma kasa matsawa kaman an dasata awajen kawai tasauke kanta akasa, sosai Riyad ke binta da kallo tundaga kan santala santalan cinyoyinta zuwa boobs nata dake neman sakashi loosing control, he feels like grabbing them and just suck some imaginary breast milk. 

Ajikinta taji ana kallonta danhar yanzu be karasa saukowa daga staircase dinba hakan yasa tadago kanta kaman matsoraciya ganin yanda ya kasa ya tsare yana kallon boobs dinta yasa tama tuna da kalan rigan dake jikinta dawani irin sauri takai hannunta tana kare kirjinta tawani irin juyamai baya tana kallon cikin falon, dan murmushi kadan yayi yacigaba da saukowa ahankali dan duk staircase dazai taka har kanshi yakeji, yana zuwa daidai inda take a tsaye ba zato ba tsammani Rashida taji yawani irin rungumeta tabaya yakai both hands nashi yadaura kan cikinta ya matse jikinshi abayanta, dudda yanda taji jikinshi ya dauki zafi saida muryanta yahau rawa sosai tace “m…..mm…..” tama kasa magana sabida yanda kirjinta ke bugawa da kyar tace “me haka?” Shiru yamata kawai ya kankameta gamgam, cikeda fada tace “wai me haka banace kadena tabani ba, ka saken!” Tamai ihu dayasa yazare hannunshi daya daga cikinta yadaura saman kanshi dake neman cirewa cikin wani murya da ko kadan bata sanshi dashi ba yar karama ashagwabe yace “stop screaming my head is banging!” Da kyar yace “ke baki gajiya da fada!” Dudda yanda gabanta ke faduwa bai hana kartaji how hot jikinshi is ba amman cike da karfin hali tace “eh anyi fadan, ai to ba jikina ne magani ba, kasaken nidai Malam” makemata kafa yayi saikuma ashagwabe yawani saketa tareda juyo da ita tai facing nashi yakai fuskanshi dab da nata yabude idanunshi da sunyi jaaaa yakalleta,trembling lips nata suka fara sosai ganin idanunshi da how close he is to her, gashi ba riga ajikinshi, saita ma kasa magana sai nishi datake kaman kirjinta zai tsage, cikin muryan da batada karfi yace “zoki bani magani” yasa hannunshi daya ya karbe bottle water na hannunta sannan yasa dayan hannunshi yakama hannunta kawai yaja hannunta yashiga tafiya tana bishi kawai tarude tama kasa anything dakin dake facing nata taga yayi da ita yabude kofan yashiga da ita ya maida kofan yarufe dakinshi ya bala’in hadu lafiyayyen gado ne adakin saikuma wani lallausan carpet daya cika ko’ina adakin taushinsa zaka dauka katifa ne magungunan tagani harda drips dakuma papers a gefen gado, hannunta yakama yajata zuwa wajen gadon ya zaunar da ita shima yana zama a gefenta yadau takardan just to make her comfortable yace “My Doctor wanted to admit me nace yabani komi zan kawoma matata” dasauri ta kalleshi tana hadarai hakan yasa softy yace “sorry I mean I’m married to Dr Rash” dauke kanta tayi takalli paper description na abubuwan da za’amai Dr yarubuta, he’s really sick yanada high fever dakuma typhoid, rashin bacci da stress ga damuwa suna complain da Dr yace yayi, cikin magungunan harda wanda zai sashi bacci, hakanan batasan mesa ba sai kawai taji she felt bad ganin baida lafiya dudda bala’in haushinsa takeji, dan dagokai tayi ta kalleshi hada idanu sukayi kallonta yake da sauri ta dauke kai sai kawai ta tashi ta tsaya wajen magungunan tana daukan drip din ta makala jikin gado tadauki kanulan tajuyo ganin sun sake hada ido kallonta yake yasa azuciye ta ijiye komi tazo zata wuce, kama hannunta yayi juyowa tayi tafizge hannunta tace “don’t touch me” dan kama kanshi yayi da hannu dan kaman kanshi zai cire yanda yayi saitajishi har zuciyanta tadanyi shiru danda masifa zatamai, ahankali ta sassauta muryanta tace “ni Hijabi zan dauko?” Murya chan kasa yace “why?” Cikeda masifa tace “kallona kake” saikuma tasake rage murya da sauri ganin yanda yasakeyi tace “banson kana kallona” ahankali yana kukkulle idanunshi yace “nadena to” ganin yanda yakeyi kaman zai sume dan da mace ke kalan ciwon kan dayake data suma sai kawai tadawo batare datai magana ba tadauki kanulan da auduga datagani da aka jika da spirit tsayawa tayi agabanshi gabanta na faduwa sabida yanda ba riga ajikinshi hannu ta mikamai tace “bani left hand naka i want to create a line” cikeda iskanci dudda yanajin jiki Riyad yawani narke mata yace “bazakimin da zafi ba?” Wlh yanda yayi maganan saida taji wani zirrr, daina kallonshi tayi tama kasa magana the way he’s acting like a baby is messing with her, is making her heart melt towards him itada ta tsaneshi, ganin takalli gefe taki kulashi saiya mika mata hannun, ahankali tasa hannunta ta kama nashi shock dukansu sukaji atare da kyar ta iya rike hannun da karfi karya gane, shafa audugan tayi saikuma tadan kalleshi yanda yayi yana kallonta kaman baby that is very scared yasa, danne zuciyanta tayi and try acting professional kaman yanda takema patients nata tace “hannuna ba zafi, relax it won’t hurt” har ranshi yaji dadin maganan ta, ita true Rashida is a sweet girl wlh one just need to look deep, gyadamata kai yayi looking super cute da sauri da dauke kai ta saita mishi IV line, shi wlh ko zafi daya baiji ba kodan yana kallonta ne oho, yaga plaster tayi ta manna sai kallonta yake sannan takoma ta debo allura da Dr yarubuta na IV tamai dan runtse idanu yayi dan alluran IV da zafi har kasan zuciyanta taji she felt his pain hakan yasa tace “sor..……” saikuma tai shiru tajuya tama drip din alluran dazatayi cikinsu Riyad sai kallonta yake sannan tazo ta makala mai kafin ahankali tadan kalleshi tace “nagama, sleep” tajuya zata tafi hannunta yakama dasauri tajuyo zatakai masifa taga yarike kanshi making sick baby face hakan yasa tai shiru sai kawai taga wutan dakin ya dauke kafin tai wani motsi taji Riyad ya mugun fizgota fadawa tayi jikinshi kirjinta na hadewa da nata, cikeda masifa gabanta na faduwa tace “me hak…….” Bakinta kawai taji yakama yawani irin kankameta ajikinshi dake yana kissing nata kaman maye…….


EPISODE 60 

Rashida so take ta hankadeshi but takasa sabida igiyan ruwan dake hannunshi, she just couldn’t bataso tai hurting nashi dan he’s already very very sick, he’s kissing her kaman akwai wani abinci mai bala’in dadi acikin bakinta, tanajin yanda yake fitar da nishi akan fuskanta dake kamshi sosai dakeda zafi hakan yasa jikinta gabaki daya yadauki kara, yanda jikinta yake wani irin kakkarwa tsigan jikinta ko’ina na tashi tanajin some wired feelings da in her entire life bata taba jin irin abin ba is making her mugun uncomfortable barinma the sounding dayake making yana kissing nata. “Muahhhh…… uaaaahhhh……yiiiiishhhhh”.

 Bala’in firgita Rashida tayi jin yanda Riyad yahada bakinshi da nata ba zato ba tsammani, kokarin magana tayi arude. “Me h……” sake shigar da bakinshi yayi cikin nata da kyau dan kokarin maganan datayi ya mugun bashi opportunity na tura harshenshi cikin bakinta, today is his second kiss bayan ranan nan daya mata, baitabajin yanason bakin wata ba kaman na Rashida, he just wants to get close to her ya lallasheta internally tunda she don’t understand external lallashi bama ta sauraron mutum at least yanzu she will feel him lets see idan bazata lallasu tahakaba.

 sound na kissing dana zuko yawunta kaman irin tsohon mayen nan taji jikinta yana amsawa her organs na motsi dakawai taji takasa daurewa tashiga turemai kirji back but kaman maye me lasisi yawani biyota yana turata back shima cus baiga abinda zaisa yasaki bakinta ba the way he’s enjoying kissing her, turata yayi da karfi kawai tafada kan gadon flat cus kaman yama karfinta wani abu, kwance flat yabiyota yana hawa kanta yadan danneta ganin har tafara kokawa tashi, matseta yayi ajikinshi yakai fuskanshi saitin nata yana kissing ko’ina a fuskanta tana wurwurga kafa ta damke bakinta cus tasan tana kara budewa zai kamasu, yanda yake zuba mata kisses a every corner na fuskanta yasa taji kaman jinin jikin ta baya functioning da kyau, kankameta da kyau yayi kaman za’a kwaceta tanajin how fast kirjinshi ke bugawa ga mugun zazzabi dayakeyi gashi takama bakin ta damke, cikin muryan zazzabi sosai yace “I cant control myself Jewel!” Juyarda fuskanta tayi gefe da sauri cus muryanshi is making her entire body weak manna bakinshi yayi akan kunnenta cikeda zazzabi yasaki sound. “Ahhhhh I feel kaman zan mutu!” Dawani irin sauri Rashida tajuyo da kanta ta kalleshi gabanta yawani buga rass jin maganan dayayi kawai tsoro yashigeta har kasan ranta taji bataso ya mutu she don’t want to loose him shima, dudda duhu yaga yanda kwayan idanunta ke kallonshi ganin yanda tayi yasa ahankali yakai hannunshi da akwai drip ajiki yadaura kan fuskanta softly yace “Please kiyafemin kinji kidena fushi dani, stop hating me kinji” dasauri ta juyarda kanta gabanta na faduwa dim dim dim gabaki daya yanda he’s this close to her jikinshi manne da nata is making her feel abinda bata tabaji arayuwanta ba, kokarin tureshi tafarayi hakan yasa yakama hannunta dasauri tace “saken” makemata kafada yayi like a baby yace “banda lpy take care of me, and kidena min ihu kaina zai fadi kasa” wani iri taji maranta yana mata kaman wacce zata fara period sabida yanda yake mata magana dawani shedanin murya da batasan maza nada kalansa ba, sai kawai kirjinta yashiga bugawa non stop baki tabude zatai magana takasa sai numfashi datakeyi dasauri dasauri kawai ya birkitamata lissafi she doesn’t even know wats happening with her, her body doesn’t feel like hers, she’s feeling kaman tai hugging nashi maybe zata denajin yanda yake, she’s feeling kaman yacigaba da mata kiss din, she feels kaman they should stay like this forever irin kar moment din yayi ending and kuma she’s feeling irin mesa take feeling all this abubuwan towards mutumin data tsana sosai dashi da yan gidansu sunefa suka kashe Mama.

 Wuraren 7 tashiga bude idanunta ahankali, haske tagani kadan dake shigowa ta inbetween dark curtains nasu, fuskanshi ta kalli ahankali dayake manne da boobs nata dawani irin sauri gabanta na faduwa tasa hannu taja rigan bacci ta tarufe boobs din daidai lokacin idanunta suka sauka kan scratch din datamai a wuya dasauri ta dauke idanunta sabida yanda taji badadi hakanan sake juyowa tayi ta kalleshi faduwa gabanta yayi dasauri ta dauke kai cus he's so handsome hannunshi takalla gain drip din yakare harya soma jan jininshi yasa ta tashi daga gadon ahankali ta sauka sannan tasake kallon fuskanshi saikuma takai hannunta takama hannunshi gently dan bataso vatashi tafara kokarin zaremai Karin ruwan, ahankali taciremai tana kallon nails nashi that are squeaky clean gas farare sannan ta ijiye hannun da sauri tawuce koa saiya tashi yayi salla zata mai second batch a treatment nashi.

Tana fita ya bude ido dan tunda ta tashi yajita hannunshi data kama tarike ya kalla saikuma yasaki murmushi ahankali yace "I will teach you how to love me ta yanda bazaki iya rayuwa without me ba" ahankali yatashi zaune kanshi yayi sauki sosai but yanaji kadan kadan bay yafada.

Tana shiga dakinta tafada bathroom maida kofa tayi tana tuna wat happened jiya da sauri ta duka sabida yanda taji maranta yarike again tayi shiru, batasan mezata ce ba but the way he kissed her saikuma tai shiru cus bataso tagayama kanta taji dadin abinda yafaru, saikuma da sauri takalli kirjinta saikuma tadauke idanunta tadaura hannuwanta kan bakinta tana tuna vanda bakinshi ke tasting acikin nata da yanda numfashinsa ke sauka akan fuskanta da vanda vadaura hannunshi kan pants nata da sauri takifa kanta kan kafafunta takankame kafafunta maranta rewo again she just keeps remembering everything all over again and again and again barinma yanda any motsi tayi take kamshin jikinsa saikuma ta dago kanta da sauri tadaga hannuwanta dataga tsigan jikinta duka sun tashi she's having goosebumps sabida Riyad data tsana saikuma ta tashi azucive tadauki brush tashigayi kafin tawuce tai wanka.

Tana fitowa wata yar riga tasa tayi salla sannan ta tashi tashafa cream tabude wardrobe din tana kallo kafin tazaro wani atampa datagani mai yellow flower but sauran zanenshi black ne ta warware A-line gown ne shiryawa tayi tsaf tashiga sakawa yamata kyau bana wasaba bata daura dankwali ba saita zauna tai shiru saikuma ta runtse idanunta da sauri bala'in tunanin Riyad take he needs to eat this morning kafin yakarbi dose a maganinshi wani iri takeji tamai girki saikuma tace koba komi shike kawo musu abinci a hospital bari tai returning favor din sharp sharp kafin ta tafi school tunda 9 suke shiga anything from now zuwa 8:30 tafito saukowa bude kofa tayi ta leka babu kowa awajen dasauri tawuce ta sauka kasa kitchen ta shiga ta tsaya tayi shiru saikuma ta shiga kitchen tadebo su Irish da eggs da kayan Miya tafito tabude fridge taciro minced meat, was kayan hada shayi tagani suma duk taciro saikawai tafara aiki if there one abu aduniya data iya dasauri is work nan da nan tahau aiki, around 8:40 tagama shima sabida tavi davawa ne harda su security shayinshi tazuba Awani flask mai shegen kyau ta ijiye wani tea mug da tea spoon da honey mai kyau da sugar tafito ta ijie a dinning sannan takoma on another tray tasami play na fluffy pancakes datamai ta yanka strawberry da bananas da blackberry akai tayi drizzling honey plates din looks so appealing a idanu sannan tasa plate na loaded chips saikuma karamin bowl datamai heating pepper soup data rage jiya shima tafito ta ijiye a dinning tasake fitowa ta ijiye glass of fresh orange juice datayi yanzun nan cus orange is good for marasa lafiya takoma kitchen tahadama securities nata komi tafito zatai kofa ta tuna batasaka hijabi ba sai kawai ya ijiye abincin awajen tazo tafara daukan tray na tea kawai gabanta yashiga faduwa bataso tahadu dashi mugun kuna takeji amman tadaure tawuce har gaban dakinshi hannu tasa tai knocking daga ciki da muryan daya wani narke yace "come in Wife" dan jimmm tayi takasa shiga sai chan tadaure tabude koan kanta akasa yana zaune akan gado yay wanka ya chanza kaya ma but yar singlet ce ajikinshi da 3-quarter wh baitaba expecting zatamai breakfast ba but ganinta rikeda tray sai hakan yay wani irin warming zuciyanshi karasowa tsakiyan dakin tayi tasami gefe na wajen kujera sabida idan yazauna ya jingina da kujera ta ijiye sannan tadago dasauri muryanta na breaking tace "sa…....uran bar nakawo" tawuce kofa da sauri vabi bayanta da kallo the way ass  Nata    shakes and whine idan tana tafiya.


EPISODE 61

Dakinta tashiga taja mayafi tarike a hannu tafito tana yafawa sannan tasauko cikin falon tadauki abinci tabude kofan su yanda taga yabude jiya tafito securities din na hangota da kula dasauri sukazo cikeda girmamawa sukace. "Hajiya barka da safiya, angode Hajiya Allah Kara girma" basu tayi takoma ciki tadauki dayan tray din tayi sama dashi zuwa dakinshi wanna karan batai knocking ba kai tsaye ta shiga wajen taje ta sake ijiyewa yabi abincin da kallo saikuma yayi murmushi, batare data kalle inda yakeba tace "y.......a jikin?" Cikeda iskanci yana wani kashe mata murya yace "I dont know I guess saikin dubani Dr Rashida Riyad" da dan sauri ta kalloshi kasa kasa saikuma tadauke kai ganin yanda yake kallonta murya chan kasa tace

"come and eat you have injection this morning" wani laushewa yayi yace "I can't get up Doctor I need help" dadan sauri tasake kallonshi for the first time sai suka hada idanu wani erotic look daya zubamata yasa tadauke kanta dagudu gabanta na faduwa sosai cikinta kawai vafara murdawa again taki motsi, ahankali yace "pleaseeeeeeeee" kai! Wai wat is this abubuwa da Riyad ke mata yanda yawani ce please vaja sai taji tsigan jikinta na amsawa daurewa tayi tajuyo tazo gaban gadon sai kawai ta tsaya batare datai wani abuba, binta yayi da kallo da vanda yaga gashin hannunta sun mike ahankali yakai hannunshi vasa cikin hannunta dakeda taushi dasauri takalli yanda yasa hannunshi cikin nata ashagwabe yace "pull me up Dr" dan kallonshi tayi suka hada ido wh uncontrollably kirjinta kawai yafara racing he looks damn hot rashin lafiyan saiyasa lips nashi suka kara pink, dena kallonshi tayi dasauri sannan tadan jashi kadan da gangan yawani taso kawai saiya rungumeta yana sata a kirjinshi da kyau placing head nashi a shoulder nata yace "wayyo kaina!" Kasa wani abu tayi tanajin yanda kawai ya kankameta yana sauke ijiyan zuciya ahankali yakai kusan 1min ahaka takasa tabukakomi sannan yasaketa murya chan kasa yace "dafatan kin tashi lafiya Amarya" kasa amsashi tayi kawai yakama hannunta suka tafi wajen abincin zama yayi vana jawota hakan vasa dan dole tafara yunkurin zama gefenshi sai taga ya fizgota zuwa jikinshi kusan akan cinyansa take ahankali yakai hannunshi bayanta yakwanto da ita she just couldn't say no yayi placing head nata a chest nashi yasake kankameta tai lamo dukansu sukai shiru tarasa meke damunta tunda Mama tamutu she has been sad kullum but the moments she spent with Riyad and now yanzu saitaji kaman yana cire mata kuncin da zafin zuciyanta cus abin varagu hannunshi taji abayanta yana patting kaman me lallashinta on wani abu murya chan kasa yace "I don't remember anything daya faru jiya naga kin samin ruwa but thank you for taking care of me" nutsar da kanta tayi a kirjinshi kuna na kamata da gangan yafadi haka cus tasaki jiki, murya chan kasa yace "I don't want to do anything without your permission Ammi da Munir naso suzo su dubani later" dan shiru yayi yace "if you're not okay with it nasan bakison kiga yan gidanmu i can tell them not to come" dan leko fuskanta vayi a kirjinshi yace "na barsu suzo ko no?" Idan yana mata magana jikinta duk mutuwa yake da sauri ta fito daga jikinshi zata sauka daga jikinshi dasauri yariketa hakan yasa ta kalleshi shima ita yake kallo saikuma cikeda lallashi yakai hannunshi yayi placing akan kumatunta lumshe idanu yayi yabude ahankali yace "I will never go against wish naki, I will always respect your decision kinji" wani irin melting zucianta yayi naban mamaki dayasa batasan sanda ta kabar da hannunta ta juyamai bayaba what is wrong with her? Me Riyad ke mata hakane? Mesa zuciyanta ke narkewa haka akanshi? Asiri yamata ne? Murya chan ciki tace "suzo" kokarin tashi tayi saikawai taji yarike waist nata yajawota baya yataho yana ijiye fuskanshi a gefen wuyanta yace "let's have breakfast kafin kitafi!" Ya Allah! Yanda kanshi ke gefen kafadanta hannunshi a waist dinta ikinshi manne da bayanta yasa taji kaman something is wrong with her body, ahankali yakai hannunshi daya yadauki tea ya tsiyaya a one cup dake wajen yadauki honey yayi drizzling sannan yadauki fork yadebo loaded chips din yakara kwanciya da kyau abayanta vana leko fuskanta ya jaye hannunshi daga waist nata yakawo hannun kan cikinta yawani shafa dayasa kawai taji few drops of water na diga daga jikinta batasan sanda ta sauka daga jikinshi da sauri ba tazauna akasa tana cire hannunshi daga saman cikinta tasa hannunta dake rawa sosai tadauki spoon dake kan tray tasaka a chips din tadebo da sauri takai bakinta tanaci binta Riyad yayi da kallo he can't even explain how much he loves her she's indeed a soft girl da you just have to look deep kafin kaga this side nata, everything datamai ya bala'in mishi dadi arai he loves aka bashi different abinci dazaici daban daban vataba wannan da wanchan and he enjoys abincin ta sosai she knows how to cook everything is perfect, bata wani ci sosai ba ta ijiye spoon din mug na tea yadauka yabata dan kallonshi tayi saikuma tasa hannu ta karba tafara sha tea yayi dadi sosai abakinta tana kurba ahankali he was eating and looking at her tass yayi clearing entire tray din saida tai mamaki ijiye cup din tayi yazubama kanshi tea din zaisha hakan yasa ta tashi tawuce wajen magungunan shi yabita da kallo tablets da zaisha da safen nan tadauka just magani guda uku ne tajuyo tataho wajen tana bashi maganin kawai taga ahankali yace

"Doctor must I take this?" kallonshi tayi daga yanda yay da fuska kasan bayason magani hakan yasa kawai ta gyadamai kai tana bashi a hannu girgiza mata kai yayi yabude baki yace "samin aciki" dan kallon bakinshi dava bude tayi faduwa gabanta yayi yayi saikuma ahankali ta mika hannunta zuwa bakinshi daya bude ta watsa maganin aciki dasauri ya kora da tea vahadiye yana tabe baki kaman zaiyi kuka abin ya mugun bata dariya dayasa tajuyarda kanta kadan tayi murmushi daya kasheshi completely tunda ya santa today is the first ever time daya taba Ganin murnmushinta. 


EPISODE 62

 Hannunshi yakara daurawa kan fuskanta yajuyo dashi yana facing nashi dasauri ta ture hannun tajuya ahankali ya ijiye bakinshi kan wuyanta yasauke mata kiss da kawai taji jikinta ya hargite tajuyo da sauri tana tureshi daga wuyan nata,sake matsowa dab da ita yayi ya manna fuskanshi jikin nata ahankali yakama soft hand nata yadaura akan kirjinshi murya chan kasa yace “you’re the reason nake rashin lafiya kinaso nima na mutu?” Dudda batai magana ba wlh yaga tsoro da fargaba akan idanunta murya chan kasa yace “talk” baki tashiga budewa sai tajima tayi loosing voice nata maranta juyawa kawai yake hakan yasa ta maida bakinta tai shiru saikuma ta daure karya gane wani abu tadanyi gyaran murya but still voice nata was a bit cranky tace “ni…..dakina zan tafi ka sakeni” dan shiru yayi yana kallonta dasauri tai yunkurin juyarda kanta dawo da fuskanta yayi da sauri yace “i want to calm my temperature down with your body nagama saiki tafi” baki tabude zatai magana yasake kama bakinta da hannunshi me drip kaman bakin yar baby yasa mouth nashi aciki numfashinta har neman daukewa yake tana tureshi ganin yanda take tureshi yasa yahada hannunta yamaida su bayanta ya matseta da kyau ko motsi bata iyayi she thought tanada karfi but kaman Riyad yamata wani abu daya sagar da all joints nata, hannunshi daya yakai kan cikinta ta saman rigan bacci ta yana shafawa saikuma chan taji hannunshi around cinyoyinta yana jan rigan sama, shaking tafara seriously trying to free hands nata cus sensation datakeji was beyond abinda brains nata suka sani,“Wat is this? Are you trying to rape me? Kadena tabani wlh ko I will report you to police” wani irin nishi Riyad yake he’s sick he wants her so bad kozai sami comfort and feel better ahankali ya rungumeta ta baya yakai hannunshi daya ta gabanta trying to touch kirjinta amman ta kankame hannunta awajen, cikin muryanshi da bata fita sosai yace “I love your boobs just help me na iya bacci, there are always too few perfect boobs in this world, yours is over perfect Rashidahhhhh…….” yakira sunanta dataji har kasan ranta, ahankali yace “I want to sleep ina shan nonon ki!” Yanda maganan yamata yirrrrr batasan sanda tazare hannunta daga kirjin takai kunenta tana dannewa ba cus bataso tanajin maganan iskancin dayake mata maranta na mahaukacin murdamata, kawai jitayi Riyad yajuyo da ita before ta ankara tai wani abu yaja rigan kasa kaman yana race kawai ya manna kanshi kan boobs din yana bude bakinshi yaja dan karamin innocent nipples nata da kana gani kasan bamasu taba tashi sun fito hakaba ba in their little life sai yau dayasa sukai erecting haka.




EPISODE 63

Yaune rana na farko yaga murmushinta wow yafadi ahankali sannan yakai hannunshi yakama habanta yajuyo da fuskanta takalleshi yace “did you just smile?” Hade fuska tayi batai magana ba fizgota yayi tazo dab dashi kirjinta yashiga bugawa yace “dariya kikamin yanzun nan”? Yanda ya tsareta da idanu yasa tabude bakinta zatai magana sai kawai yayi grabbing lips nata yajawota da kyau ya mannata ajikinshi yana kama hannayenta datake tureshi dasu,“Ahhhhh” ta duke da sauri tana kama cikinta dawani irin sauri Riyad yataso yace “menene? Bakida lafiya ne? Wat is it? Meke miki ciwo?” Sosai tarike cikin nata innocently tace “cikina ke ciwo” cikeda damuwa Riyad yace “yaushe yafara?”

Tanadan sauke ijiyan zuciya ahankali tace “jiya da daddare” sake kama cikin tayi tace “bana kalan wannan ciwon cikin me rike mutum” Dasauri yakai hannunshi yadaura acikinta dan kara tayi tana kabar da hannunshi da zuciya daya tace “dazaran katabani yakeyi kadena” chak Riyad ya tsaya yana kallonta da yanda takeyi, she might really be a Doctor but she have zero idea on wats is going on with her, just karfin hali da taking responsibility yasa akema Rashida kallon she’s matured enough but she’s just a child wlh, she knows nothing.Turarenwutabybaheerah: Ahankali yace “sorry wat can I do to help in daukeki mukoma gado?” Dasauri tabude idanunta takalleshi ganin kallon dayake mata yasa ta mike tsaye cikeda tsiwa tace “ka kira Dr ka yamaka sauran treatment naka natafi school” dasauri yakamata wannan karan batasan sanda tace “na shiga uku” tasake rike cikinta hawaye na taruwa a idanunta ahankali Riyad yace “yacigaba?” Gyadamai kai tayi tama kasa magana cus abin namata kaman an jera mata ice blocks a maranta hakan yasa sun mata kaman stones na kankara suna hurting nata, cikeda so Riyad yadan tarota yace “come zoki zauna kidan huta kadan yasakeki saiki tafi” yakamata zuwa gadon yazaunar da ita gaban yazauna a gefenta ahankali yasa hannunshi yadaura asaman kanta zai kwanto da ita kirjinshi dasauri ta kalleshi da idanunta dahar sunyi jaaa lumshe mata idanu yayi yabudesu yadaura akanta ahankali yace “I want to kiss you Rashidahhhh!….” Wani irin yammmm jikinta yamata dayasa kawai ta koma baya da sauri lips nata narawa yana matsota da sauri ta tureshi tace “karkazo kusa dani” yana kallonta yana biyota yace “why? Ni ba mijinki bane?” Tana sake komawa tana shigewa cikin gadon da kyar tace “ai rabuwa zamuyi dazaran na biyaka kudinka cus bana son yan gidanku” dan lumshe idanu yayi yau yan gidansu tace bataso not him, murya Chan kasa yace “that doesn’t change the fact ni ba mijinki bane na sunma ba ko?” Dasauri tace “to nidai don’t come close to me” ahankali yace “I am coming close to you sabida inaso kibani hakki na ne” wani irin zaro idanu tayi tace “Wlh if you rape me zan gayama yan sanda” yana kallonta yace “can husband rape his wife?” Baki ta turo tace “to ai banyi accepting naka ba” dasauri yace “you will accept me today idan na sadu dake” ahhhhh! Takai hannuwanta tana taushe kunnuwanta jikinta ko’ina narawa zatai magana yasa hannu yajawo kafafunta ta kwanta flat agadon yataho dasauri tashiga kokawa dashi yabiye mata tace “wlh wlh don’t do anything to me Allah nagayamaka” biyemata ayi yace “naki why will I be looking at you saikace banda lafiya kina matana, we’re having sex now” fashewa da kuka tayi tana kokawa dashi da duka karfinta dan he looks so serious saida yaga tasoma gajiya tashi daya yadagata yaja zip dın bayan riganta kawai yaja rigan kasa ya yar ihu tayi zata juyamai baya yakamota yana kallon black bra da pant dake jikinta dake cikin kayan daya siyo dudda he just guess the size kankancewa idanunshi sukayi yace “wowww! You’re body is art” gently yakamata ahankali yasauke bakinshi yahada da nashi yakai hannunshi saman bra nata matsa boobs nata yayi yana wani irin juya idanu sabida dadi Rashida na motsi da kafa da sauri hannu yasa yawani ja bra din yana kallon boobs nata da yanzu ne yake ganinsu cikin haske bakinshi tacire daga nata yace

“Jewel you have an epic breast! Wai!” Tashi tsigan jikin Rashida yayi dayasa tafara juyawa tana neman inda zata boye kanta a kirjinshi sake squeezing boobs din yayi dayasa tai kara sosai. “Mmmmmm” kallon fuskanta yayi yanda ta runtse idanunta ahankali yasauko yana kama hannuwanta dasuka sage yadaura abayan kanshi yace “zansha nono” sannan yadaura kanshi kan boobs nata yafara sha tun Rashida na iya daurewa takasa tafara kuka hannunshi yakai kasanta yafara playing da clit nata yanashan boobs yanda jikinta yake rawa ko’ina tadauka maybe wani ciwo takeda shi ita kanta kankaran datakeji since amaranta taji sun farayi kaman zasu fashe hannun Riyad na wajen ta feso ruwa a hannunshi still bai bari ba saida yaga kafafunta sun dena trembling sannan kawai ya rungumeta ahaka yana suking boobs nata wlh ko 3min bata karaba bacci yayi awon gaba da ita agogon dakin ya kalla yanashan boobs nata 9:30 yautai fashi tunda yau daman Thursday, gobe Friday Monday she will resume fully.


 EPISODE 64 

Tashi yayi ahankali yana bin ko’ina na jikinta da kallo barinma boobs dinta dakenan abude wlh jikinta kaman na wata cleopatra, she’s extremely beautiful bazaka taba cewa tayi uba uban aiki arayuwanta ba, rungumeta yayi ahankali yakai hannunshi yana pressing boobs nata ahankali sabida baiso yatasheta maranshi and dick nashi duka sunamai ciwo which is so unlike him basu mai da shide yake watanni abu bai hadashi da Haleema ba, idan yaso he can do anything to her but yanaso tasan he meant love din dayace he had for her he wants her to let go off the anger and understand cewa he’s with her and will always be, ahaka shima dan baccin ya kwasheshi.

 Gently take bude idanunta baccin yamata mugun dadi bargo taga an rufa mata agogo takalla taga 2:00 na rana haka tai bacci bata bacci haka da banda na dare dan hayaniya taji agidan hakan yasa da sauri ta tashi bra nata tashiga gyarawa sannan taja riganta daya gani gefen gadon an linke mata tashiga sawa da gudu tana mikewa tsaye gashin kanta duk ya ruguje tashiga gyarawa sannan ta tashi da sauri tana gyara rigan, kafin ahankali tabude kofanshi kadan ta leka babu kowa a falon saman that means suna kasa dasauri tawuce dakinta tana juyo muryan Ammi dake magana tace “jeka tadata tayi salla” da sauri ta maida kofan tarufe ahankali tafada bayi ta maida kofan tarufe haushin kanta takeji sosai sabida yanda bataje school ba duk ya gama tabata kayan tacire da sauri tai wanka sai dirje jikinta dake kamshin shi take tafito wani dogon rigan abaya tasaka tasa hijabi tahau kan dadduma tai sallan tanakan dadduma taji ana knocking saikuma aka bude kofan Riyad ne kin kallonshi tayi dan murmushi yayi yace “Ammi na kiranki” da sauri ta dago kanta takalleshi kin kallonta yayi dan baisan wani reaction dazatayiba yamaida kofan yarufe yawuce abinshi takai kusan 2min ahaka tanaso taki zuwa but saitaji duka jikinta yahanata hakan yasa ahankali ta taso kanta akasa tasaka hannu tacikin hijabin ta cus babu bra ajikinta bata tsaya tasaka ta daura doguwan riga kawai and tarasa mesa nipples dinta are standing tun jiya itada nipples nata basa tashi, tunda take saukowa daga staircase din Ammi ke kallonta kaman yau tafara ganinta. Saida takawo karshen staircase din sannan tawani juya takalli bango batare data kallo cikin falon ba tadan turo baki ahankali tace “ina yini Ammi” exactly yanda yara keyi idan suna fushi da Mamansu, daga Ammi har Riyad dashi kanshi Munir saida sukai murmushi cus she looks super cute and adorable wlh Rashida is just stubbornly sweet, tashi Ammi tayi saita taho wajen ahankali tasa hannunta takama hannunta tace “harda Ammin ki kike fushi look at me” kin kallon Ammi tayi tana kokarin sake juyamata baya cus bazata iya kallon fuskanta ba dasauri Ammi tajuyo da ita ahankali tai cupping face nata tace “Rashidah na” dasauri ta kalli Ammi saikuma hawaye ya cicciko idanunta ahankali tace “Ammi da ana koran Mamana bakice komiba” saikuma tafashe da kuka Ahankali Ammi tarungumeta murya chan kasa tace “Rashida I have no excuse to defend actions dina but one day zaki fahimci not just me kowa na fada bai isa yaja da Sarki ba abainar jama’a ba, but wlh da Mai Martaba yashigo wurina namai magana na gwada mai hakan be dace ba koma menene, Rashida life is complicated beyond yanda kike ganinsa one day idan kikai girma you will understand, yanzu dai kiyakuri I can’t stand kina fushi dani but kiyi dakowa harsai kin wuce but ni Maman ki ce kinji” Ammi takara matdeta ajikinta dayasa tai lamo wlh tanason Ammi she can’t even explain why she feel Mama ajikin Ammi, dagota Ammi tayi tace “muje namiki pepper soup ke kadai dakaina” biyo Ammi sukayi suka shigo falon Riyad sai kallonta yake Munir yace “Hi Cousin” kallon Munir tayi da sauri saikuma ta ballamai harara dayasa Riyad yakara murmushi wlh shi masifan nan nata ma mugun burgeshi yake yarinya kawai gabaki daya mafadaciya ce, Munir zai kara magana Ammi tace “kutashi dagakai har Riyad kubar mana falon nan tunda damunta zakayi you guys should go for a walk Riyad ya motsa jiki kadan” tashi Riyad yayi hakama Munir suka wuce abinsu suka fice, Ammi taciro kazan daga kula da romo na magani tabata tace “sha zan baki wasu magunguna ki dinga sha kullum is good for lafiya da tsari kar wani yamiki asiri kisan gidanmu kuma Buba yace nagayamiki ki dage da shansu dakuma yin azkar kinji” gyadama Ammi kai tayi she ate cikin din sosai dan ba me girma bane kazan hausa ne ta shanye roman da Ammi tasata tasha ta karbi kasusuwan sauran 3 batches na kazan taje tasa mata a freezer tace kullum tadinga microwaving daya tana shanyewa ta hadamata magungunan ta nuna mata yanda zataaha duka ta sha takora da tsumi. 

Sannan Ammi tabata magungunan nata tawuce takai dakinta na sawa a fridge kuma takai fridge sannan ahankali tace “Ammi bari na miki abinci” kafin Ammi tai magana sai kawai ta shige kitchen tuwon shinkafa tadaura a wuta da miyan wake dayaji naman rago saikuma tai white rice da stew, daidai sun shigo gidan bayan sunyi asır a mosque itakuma Ammi nakan dadduma a falon tafito da kula dasauri Riyad daya ganta yataho wajenta chak ta tsaya ganin yataho feeling uncomfortable kawai ta sauke kanta kasa hannu yasa ya karbi kulan tajuya da sauri Munir yabita yace “mezanyi nima Cousin?”

 Ammi tai murmushi tana kada kai ganin Munir na neman fada, another kula tadauka tana hada fuska tabashi dasauri yataho dan bai dauka zata bashi ba ya karba yawuce Riyad ya shigo daidai inda take ya tsaya dasauri ta dauki another flask tabashi batare daya karba ba yace “why are you not wearing bra? Seducing dina kikeso kiyi agaban Mamana da kanina?” Dasauri ta kalleshi karban kulan yayi yajuya itakuma tadauki jar na fresh watermelon juice datayi da Munir yazo yamika mata hannu bashi tayi saita kwaso plates daidai tafito sukaci karo da Riyad karba yayi yadan duko saitin fuskanta yace “go and put on bra ur nipples are shooting out” juyawa tayi dasauri zata shiga kitchen yarike mata a hannu a kunyace ta fizge hannun tana kallo Ammi dataga tana kokarin shafa addu’a Munir kuma na danna waya tawuce da sauri tai sama shikuma yawuce dinning bata wani jimaba ta sauko duk suna zaune a dinning suna jiranta kujeran kusada Riyad ne yakeda empty takalla kaman kartazo tazauna Ammi tace “zoki zauna My Baby” ahankali tazo tazauna Ammi tabude kulan tuwo tadauka tazubama kanta miya shikuma Munir yace “rice rice” yazubama kanshi rice da stew datayi Ammi tace “zuba naki kici” gyadama Ammi kai tayi tasa tuwo a plate ta zuba miya dayaji nama saikuma tasake daukan plate ta debi rice tasa stew asama tadauki glass cup ta tsiyayya juice ahankali ta tura duka gaban Riyad kowa na kallonta batare datama luraba tasake daukan wani plate taxuba rice kadan tasa stew da nama sannan tazauna shima Riyad saiyadau glass cup yazuba mata juice ya ijiye agabanta dasauri ta kalleshi hada ido sukayi dasauri ta dauke kai basusan daga Ammi har Munir kallonsu ba Munir sai mamaki yake ubanme Riyad yama fitinanniyan cousin dinnan nasu data sauko haka har take kula da shi haka, Ammi kuma kawai tayi murmushi dan for the first time saitaga yarinya has feelings for Riyad tana bala’in sonshi but it seems bata sani ba tukunna tacigaba da cin abincin tana yaba yanda ta iya girki sosai bana wasaba suna gamacin abincin Ammi tace “kaga Munir tashi ka kaini gida, Rashida jekisha magungunan tsarin da Buba ya aiko miki dashi na yamma, kaikuma Riyad ka zauna amaka fixing dripn naka finish your treatment” tasake kallon Rashida tace “kinganshi bayason magani please make him take it kinji my baby” gyadamata kai Rashida tayi ahankali, Ammi tace “I will call you ko bye Allah miki Albarka” ahankali tace “Ameen” Ammi tawuce Riyad na tashi tabisu itakuma tashiga clearing table din takai komi kitchen ta wanke plates din takifa tazo ta tafara goge dinning din dawani rag ringing taji wayanta nayi a sama daidai Riyad na bude kofa dasauri tabar rag din tawuce sama tabude kofan dakinta tadauki wayan tana dagawa taga Maimoon dasauri tadauki wayan. 


EPISODE 65

Wayan takara a kunne tana fitowa sabida tazo takarasa goge dinning din tasa wayan a speaker tashiga saukowa daga bene daga dayan bangaren Maimoon tace “Hello Rashida” itafa har yanzu she’s not use to having friends awkwardly tace “uhn” Maimoon tace “bakizo clinic ba, na dubaki ban ganki ba, are you fine?” Ahankali tasake cewa “uhm fine” daidai tana karasa saukowa dinning din taga Riyad na goge dinning din yajuyo suka hada ido dasauri tadauke kai Maimoon tace “but mesa bakizo ba”? Da sauri ta kalli Riyad hada ido suka karayi hakan yasa tajuya tace “uhnn bacci nayi” Maimoon tace “kai wani irin bacci ko nabiyo nadubaki dai? Inane gidan naku?” Tsayawa tayi saikuma tajuyo takalli Riyad hada ido sukayi saitaga ya gyadamata kai ahankali tace “GRA1 House 2B2” dasauri Maimoon tace “to gani nan zuwa gobe munada test I want you to teach me wannan course na pediatric surgery guy din nan wlh nakasa” ahankali tace “toh” dan murmushi Riyad yayi ganin tayi friend dan Mama tacemai batada friends and shima bai ganiba and from the way she’s talking to the girl sef kasan basu wani dade da haduwa ba batama iya kwancen ba karasa goge dinning din yayi yawuce kitchen everything is clean properly arranged murmushi yayi yayi dialing number security shi yana hawa sama yana dagawa yace “my wife’s friend is coming over tazo let her through” dudda tana daki but she heard maganan dayayi yawuce dakinshi books nata taciro daga jaka da pen tafara budewa da dan jitter nata tana ahaka taji karan an taba doorbell nasu da sauri ta tashi rikeda books din tafito tasauka kasa ganin baya falo taji dadi tawuce bude kofan tayi Maimoon na ganinta ta rungumeta tace “Rashidaaa” dan murmushi tayi tace “come in” shigowa tayi bayan tacire takalmi tashigo falon sai kallon falon take kitchen Rashida tawuce takawo mata abinci da drinks abinci tahau ci ta kwaso yunwan school tace “ke kika dafa abincin nan?” Gyadamata kai Rashida tayi Maimoon tace “you’re such a great cook wlh wow” cinyewa tayi tadauki juice tanasha tace “ina mutanen gidan lemme great them” dan kauda kai Rashida tayi ta tashi tana daukan tray tunda tagama ci tace “basa nan” sannan tawuce kitchen Maimoon tabita da kallon ganin kaman she’s hiding something from her, fitowa tayi hakan yasa Maimoon tace “but gidan waye nan din? Tunda kin cemin an saida naku?” Books tashiga dauka tana budewa tace “bazan dade anan ba zanbar nan shima yauwa kinada textbook din ni banda shi” tai maganan trying to kore conversation din dasauri Maimoon itama taciro suna fara karatu duk Riyad na jiyosu dan kawar akwai katon murya tasaki jiki sabida ance yan gida basanan sosai Rashida ke koya musu karatu har aka fara kiran magrib.

 Tashi tayi tana kokarin goya jakanta danzata wuce Riyad yashiga saukowa ahankali gadan ruwa a fuskanshi cus masallaci zashi ko kallon inda suke baiyiba jin sahun tafiya dasauri Maimoon tajuyo ganin wani kyakkyawan guy yasa dasauri dan tanada faram faram tace “ina yini” dan gyada kai yayi alamun yaji kafin chan ciki ciki yace “fine” yabude kofa still bai kallesu ba yafice dasauri Maimoon takalli Rashida tace “dama da wani agidan muketa surutu haka Rashida? Waye this fine Man?” Hakanan Rashida taji wani abu yataba zuciyanta yanda Maimoon tace fine Man sai kawai tai banza da ita tace “bari na dauko hijab na rakaki” wucewa sama tayi tadauko hijab tasaka tasauko suka fice tare har zuwa gate tai waving nata tace “bye” Maimoon tace “bye see you tomorrow a auditorium na CMD za’ayi test din” gyadamata kai Rashida tayi sannan tafice daga gidan itakuma tajuya takoma cikin gida. Salla tayi tasauko wlh sabida kawai baida lafiya ne dakuma masu gadin hakan yasa tashiga kitchen sai kawai ta dafa stair fried couscous tayi salad, tayi chicken pepper soup da juice again takawo komi dinning ta ijiye tadauki kula zatakai waje daidai ana bude kofa hannu kawai yabata tasamai tajuya tawuce sama wanka tayi tai salla tana zaune wayanta yahau ringing around 9 Riyad tagani kin dagawa tayi tunawa da maganinshi sai kawai ta tashi da hijabin har kasa tafito falo ta leka baya ciki hakan yasa tawuce hanyar dakinshi kawai taji batajin yin knocking itama direct tabude kofan wannan karan dagashi sai towel a waist ga karami a hannunshi sannan acire IV line datamai jiya kasa shigowa dakin tayi ta tsaya saikuma ta juya tace “idan kasa kaya ka kirani” dasauri yace “wait bari nasa” tashi yayi yaja wandon pajamas nashi yasaka shi kadai yace “come to” shigowa tayi taki kallonshi magungunan shi tadauka tadauki dripline tahada tace “why did you remove line dinka?” Ahankali yace “zafi yakemin nacire yanzu da ina wanka” bata sake magana ba ranta sai baci yake dük ta tuna maganan Maimoon saida taki kallonshi cus ita bata wani ga fine din da ake fadi ba dalla hannunshi ta karba nan da nan tamai fixing wani line tasakemai injection sannan tasaki hannunshi tajuya tafita yabita da kallo baice mata komiba tasauka kasa tahada maganin tsarin duka tasha, masu dadın da marasa dadin tana tabe baki sannan takoma sama dakinta tabude tashiga tasaka key tai bacci Washe gari da wuri ta tashi tai breakfast lafiyayye ta hada a dinning takoma sama tai wanka abaya black tasaka tasaka lab coat nata dataga an goge again yau sannan tawuce kasa tai microwaving kazam Ammi taci tasha magungunan sannan tai rolling gyalenta tafito goye da jaka harzata wuce saikuma ta kalli kofan dakinshi atleast taduba drip data sakamai. Knocking tayi murya chan kasa yace “come in” bude kofan tayi ganin yariga yacire drip din yasa taki kallonshi tadan juya tace “your breakfast na kasa, natafi school” tajuya zata tafi ahankali yace “Rashidah!” Chak ta tsaya saikuma ta juyo ahankali yace “your driver is waiting for you a compound all the best, your CA” samin kanta da kallon fuskanshi tayi murmushi yasakin mata ahankali dayasa taji gabanta yafadi dasauri tawuce a compound taga wata sabuwan benz fan kujeran da leda gawani dattijo haka yana ganinta yace “barka da zuwa hajiya” dasauri tace “ina kwana” shiga motan tayi yaja suka fita har zuwa makaranta dayake this morning suke da test din auditorium yakaita tasauka yace “ina nan zanyi parking” dasauri tace “katafi” yana murmushi tace “dan aikinki zalla aka daukeni duk inda na kaiki zan kira mukoma tare ranki shi dade” kallonshi tayi ganin student nasu na zuwa wajen yasa tajuya tatafi.


EPISODE 66

 Hall din tashiga rabon dataga duka student nasu andan dade cus kowa da inda yake yauma sabida test ne saisa suka hadu haka, hada ido da Bilal tayi daketa kallonta kaman zai cinyeta tun ranan daya ganta tareda Riyad yakejin wani bakin kishi da bakin sonta tashi yayi dasauri yabita yace “Hi Rashida ya karin hakuri” tsayawa tayi chak saikuma tajuyo ta kalleshi tace “fine thank you” zata juya yace “kinsan har gidanku nazo gaisuwa but I know you will not know then but Mrs Bugaje ta ganni ta

am so sorry about Mama Rashida” shiru Rashida tayi saikuma ta gyadamai kai tawuce chan kasa ta zauna kusa da Maimoon yabita da kallo wani mugun sonta yake now that the Mom is dead za’a iya barinshi ya aureta kobazasu yardaba zai tada bala’i shi wlh mugun son Rashida yake yarinyar tahadu taji komi sai kallonta yake yanda itada Maimoon ke karatu shigowa lecturer dayayi yasa yamaida hankalinshi gaban allo sukai test din wanda sharp sharp aka gama dan 30min test ne ya karbi takardun yafita student aka tattashi dan atafi clinic, Rashida na jerawa tareda Maimoon dan group nasu daya Bilal yasha gabansu tsayawa sukayi duk suka kalleshi ahankali yace “Rashida please I want to talk to you give a minute dan Allah dan Allah kada kice a’a” dan hararanshi tayi tace “munyi magana dazu ai muje Maimoon” sukazo zasu wuce sai kawai yasake shan gabanta yazube tareda kneeling agaban kowa big boy irin Bilal bai damu ba yahade hannunshi yace “Rashida I’m sorry for hurting you! I’m sorry for playing with your feelings and emotion, I’m suck a jerk I’m sorry kinji” tafi some guys da girls suka fara banda Layla da crew nata dasuka fice daga ajin dan sunyi fada da Bilal din, folding hannuna Rashida tayi a kirji tace “menene” ahankali cikin murya mai sanyi yace “Rashida I’ve realized my mistakes dudda nasan na kofsa da farko but wlh wlh wlh Rashida I still have feelings for you ina bala’in sonki and I’m serious aurenki zanyi my parents will never say Noo ko lokacin nan Zubin yan ajin nan ne wlh but I swear Rashida ina masifan sonki bana iya bacci har layinki nakoma akace an saida gidanku wasu ne aciki I couldn’t sleep kullum kafin nabar clinic din danake nazo naku kin tafi I’ve been trying to talk to you for days jiya har roaster naje na nemi clinic dakike naje bakınan Rashida I love you da duka zuciyana, please give me a second chance” yayi maganan hawaye na cika idanunshi tayi shiru tana kallonshi she really had feelings for Bilal da, hurting nata dayazo yayi yasa tarufe chapter shi but confession din nan dayazo yanayi dakuma the way he’s talking yasa taji wani abu ya motsa azuciyanta game dashi ahankali tace “nariga nayi aure!” Baya yayi wlh yakusa fadi dasauri yadafa chair yace “me……mene?” Gyadamai kai tayi tace “wlh nayi aure”

 dukawa yayi agabanta sai kuka, be damu da few student dake hall dinba bakaramin taba zuciyan Rashida kukan yayi ba dawani irin sauri tace “Bilal me haka please stop?” Ahankali yatashi tsaye yakai bayan hannunshi yana goge idanunshi yace “wannan guy din dana ganku tare ne?” Gyadamai kai tayi dasauri yace “why will you marry dan wulakanci irinshi eh did you see the way he treated me ranan kaman ba mutum ne ni ba, why did you marry him eh”? Ahankali Rashida tace “nima bada son raina bane babu yanda zanyi ne” dasauri Bilal yace “tell me wat happened? Wlh you can trust me now Rashida ina masifan sonki, tell me mesa kika aureshi to?” Dan shiru tayi tana karanta Bilal din he looks so worried and disturbed about her hakann yasa tace “yana bina bashin 22M kudin hospital na Mama da duka dawainiyan daya mana, yace saina biyashi duk randa na biyashi zai sakeni tunda banason auren” tadan yatsine fuska cus abin yafara bata mata rai tace “ita a long story I don’t wanna talk about it” dasauri Bilal yace “Rashida look at me” ahankali ta kalleshi Bilal yace “nasan at first damuka fara soyayya na kwafsa I’m not proud of my behavior then, but look at me yanzu da soyayyan danake miki was fake da bazan taba dawowa gareki ba, Rashida I want to show you I’m your true love and we’ve been through alot together and I will support you in every every, nothing beat ka auri wanda yasanka kasan shi, we’ve been together in this school for years muyi aurenmu muzo aiki tare mu tafi tare and train yaranmu tare” yadanyi shiru ahankali yace “wlh Rashida I will love you and I’m ready to support you with my life if possible” yasake yin shiru kafin ahankali yace “wat if nabaki 22M din kibiyashi!” Dawani irin sauri Rashida kalleshi batai expecting maganan ba, dasauri Bilal yace I got you Rashida I will never betray you I will be your best friend, nabaki 22M din zaki amsa” shiru tayi cus bata taba sanin zata sami offer this quick ba and ta yarda da Bilal idanunshi kadai zai nuna maka yana bala’in sonta and tasan ya chanza shikadai yazo nemansu yakawo mata kudi as soon as yaga message nata a group that alone is sign yana sonta da gaske, sannan yazo mata gaisuwa yakara komawa again, wannan da Riyad yasoma tabata she wants to pay him tabar gidan abinta, tabar rayuwan su har abada cus su suka kashe mata Mama ganin takasa magana yasa Bilal yace “Rashida even my parents will not know kenaba kudin is just between us, indai Dad ne he can always give me another money, wlh kyauta zan baki kudin basai kin biyani ba I will settle you down a hostel, bikinmu you choose yaushe kikeso muyi, I will be your only family Rashida, no one can take care of you better than me, that man is not a good man tunda har yanada bakin cewa kibiyashi kudin daya kashe ma mahaifiyarki, ki karbi kudin ki bashi kafin ya ceci rayuwa ki still yasakeki daga baya” Rashida jitayi maganan shi ya zauna aranta zama daram da gaske ne Bilal can be her biggest support tunda ya santa suna koyan abu daya, he will be her best patner and she loves him tanaso ta aureshi, ahankali Bilal yace “Rashida say something” ahankali tace “naji but ba kyauta zan karbi kudin ba nafara internship zan biyaka” anatse yace “maybe munada yara biyu ma then okay if you insist shikenan but yaranmu zan budewa company da kudin danni nabaki ne” dan murmushi tayi kadan maganan yamata dadi ahankali yace “inada number ki i will call you today gobe kizo school by 9, zan kawo miki check din ki kaimai yabaki sakin saiki dawo yau din nan zan miki arranging space a hostel kinji my Rashy” dan murmushi tayi saitaji kaman he just solved duka problem na rayuwanta in just this moment, ahankali yace “muje narakaki clinic dinku” tare suka fito yarakata. yace “I told you I will support you koda rayuwanae idan kinaso, wlh Rashida nagaya miki nine true love dinki saisa soyayyan danake miki yaki mutuwa” yayi shiru yace “I don’t have the money but Dady nadashi i will collect kudin dayakeso yabani na business nabaki you will pay him yasakeki muyi auren mu nan da immediately mun gama exam, tunda an saida gidanku zan nema miki hostel I know lot of student na saimiki bunk space nasu,


 EPISODE 67

Ranan gabaki daya da farinciki ta wuni a asibitin irin wanda rabon datayishi tun Mama na raye, wuraren 4 taji watsapp message yashigo dasauri ta duba ganin number ne na Bilal dayake batada number shi tagoge bayan sun rabu, budewa tayi da sauri taga yatura mata hoton bunk mai kyau a hostel room yayi typing akasa yarinyar ta saidamin 150k kinada wardrobe space I’ve paid her already so ita yours, wani irin murmushi tayi ahankali tace “Alhamdulillah Allah you’re the best, thank you for giving me Bilal”Mosque tawuce tai salla suka jero itada Maimoon tare suka shiga motan Maimoon kanta saida tace “lafiya kike farin ciki haka” tasakeyin murmushi Maimoon sai kallonta take cus hardly take yawan murmushi, abakin anguwansu suka sauketa ita ta tafi sauka tayi tashiga gidan ganin babu motarsa tagane yafita tawuce dakinta kiranta Bilal yayi tadauka dasauri yace “kin koma gida Rashy” gyadamai kai tayi tace “eh?” Ahankali yace “abinci fa” murya chan kasa tace “wlh banajin yunwa kasan mene rabona danaji farin ciki haka tun Mama na raye I can’t wait nabiyashi gobe nai tafiyata” dasauri Bilal yace “park all your things, mara mutunci like him me gori damiki gadaran da kuri na kudi baiyi deserving naki ba wlh, mutum like that bai cancanci yazama mijinki ba, I thought abinda namiki abaya yasa nine the worst man on earth but this guy proves to be the worst aduniya, I’m sorry for hurting you back then Baby” murmushi tayi heart dinta na melting tace “yawuce wlh I forgive you BB” haka takecekai then hira sukahau yi har sai magrib ya katse wayan dan mosque itama ta tashi tayi salla tashiga hada books nata da komi bata dauki anything kayan su ba. 

Sake kiranta yayi bayan magrib suna hira sai da isha’i yamata sallama cus yasanta da bacci da wuri salla tayi tai wanka tasa key ta kulle dakin tai bacci abinta yau ko girkin ma batayiba yanda ta kwana da excitement dasauri ta tashi ta kunna data watsapp tashiga taga Bilal yatura mata messege na hoto da gudu tabude taga check yamata snapping na 22M wani ihu tayi tai tsalle tana kama bakinta saikuma tafashe da kukan dadi tace “Mama I did it, yau zan rabu da wayanda sukai hurting naki forever mama na”

tashi tayi tafada bayi tayo alwala tai salla sannan tashiga wanka tafito ta shafa mai tadauki atampa tasaka ta daura dankwali Allah Allah take 8 tayi yau bata damu tayi girki ba zuciyanta yace mata baida lafiya fa kiduba shi ahankali tace “bazanyi ba, mara mutunci mara kirki kawai wlh da gaske he’s worst than Bilal, Allah ya tsareni daga yan gidansu gabaki daya” agogo tadinga kallo 8 na bugawa tadauki lab coat tasaka ta goya jaka abaya tafito a falon kasa ta hangoshi zaune yadauki laptop yana aiki yanajin tafiyanta yadago kanshi yazuba mata idanu dasauri tadauke kanta kasa tazo zata wuce karaf yarike mata hannu faduwa gabanta yayi da sauri ta fizge hannunta tace “sauri nake test mukeda 8:30” ahankali ya ijiye laptop din yamike tsaye da sauri takoma baya cus batamaso yatabata kallonta yayi yace “i have something to give you” kitchen yashiga saikuma chan taga yafito da jakan cafe haka yazo har gabanta yace “stop going to school baki breakfast ba, have cake a hanya all the best on your test” dan kallonshi kadan tayi saikuma tasauke kanta kasa dasauri tasa hannu ta karba tajuya tafice harda dan gudu gudu, yabita da kallo saikuma yasami kanshi da tsayawa jikin window yadaga labule yana kallonta he’s just having strange feelings kaman she’s up to something, mota tashiga driver ta yabata suka fice har school dayake sunata chatting da Bilal da already yana school dake jiranta a auditorium sukace zasu hadu parking driver ta yayi tafito, yana tsaye gaban hall din yasa manyan kaya brown yayi kyau sai murmushi yake itama haka harda dan gudunta tatafi wajen tana zuwa yayi murmushi yace “are you happy My Rashy?” Gyadamai kai tayi tace “I’m very very happy” yana kallonta cikeda so yace “I will always keep you happy I promise you, gashi jeki kaima ina jiranki, idan bai bari a daukeki a mota ba call me kokihau adaidaita sahu kizo I will pay dakaina saina kaiki hostel kinji” gyadamai kai tasakeyi yasa hannu a aljihunshi yaciro check din yabata yace “take” kallon check din tayi saikuma tasa hannu takarba ga signature ga date ga komi an rubuta kawai saita fasheda kuka tace “thank you Bilal wlh kamin rana I will never ever forget this” yana kallonta yace “stop crying I will always support you clean those tears, Bilal will always solve problems naki for you clean them”.Goge fuskanta tayi dasauri yace “yauwa yanzu tafi to kiyi sauri kidawo” gyadamai kai tayi tajuya yana kallonta cikeda sonta tawuce motan ta shiga Baba driver yaja motan abinshi yace “sai ina Hajiya” tana kallon check din tace “gida” gyadamata kai yatada motan sukabar hospital din.  


 EPISODE 68 

 Cikin 10mins sukakai gida, parking yayi tabude motan ta sauko tanajin wani dadi aranta ganin motanshi that means bai fitaba kofan falo tabude ta shiga, yana zaune a falon ga MacBook kan cinyanshi ga waya a kunnenshi yana magana but still kallonta yake ganin duka duka da fitanta da dawowanta yanzu is not up to 25 good minutes,maida kofan tayi tarufe tana kallonshi tashigo falon ta tsaya agabanshi hakan yasa anatse yace “I will call you back Munir, just check the document da kyau” zare wayan yayi a kunnenshi ya kalleta kaman mai kokarin karantan wani abu game da ita, dan bugawa kirjinta yayi amman tadaure tace “kace duk randa nabiyaka kudinka ranan zaka rabu dani aurenmu yakare ko”? Tsayawa yayi yana kallonta baice komi ba, jakanta dake bayanta ta sauke taciro book data saka check din a tsakiya ta maida book din cikin jakan sannan takalleshi tareda mikamai check din hannunta tace “take!”Kallon fuskanta yayi saikuma yasauke kanshi kasa yabi abinda take bashi da kallo ganin kaman check yasa gently yasa two fingers nashi ya amsa yakalli check din na 22M da akai signing akai komi, ganin yanda yake kallon check din yasa with confidence irin yaron daya sami power dinnan ya karbi yancin sa tace“ga kudinka nan ni Rashida na biyaka in full” kafin cikeda rashin kunya tace “yanzu sai kowa yakama gabansa dan haka bani takardana sharp sharp, rubutamin saki uku na ko 1min banso ka batamin jirana ake kuma sauri nake” dago da kanshi yayi yazuba mata kallo jin yanda takemai magana kaman uwarsa, kafin strictly babu wasa akan muryanshi yace “who gave you this check?” Ihu Rashida tamai tawani tubure uwa tijararriya tace “is none of your business! Nidai nabiyaka ka sallameni zan tafi ne jirana ake, kabani sakin tunda nabiyaka Malam!”.

Takai kusan 5secs sannan ta soma iya ganin gabanta dan she went blind, tadafe kuncinta dake mata radadi, takalli Riyad da jajayen idanunta dasukai kaman wuta, tunda aka haifeta ba’a taba marinta ba ko Mama bata taba marinta ba, sai yau Riyad ya daga hannu ya wanka mata mari, kallon Riyad take da bata taba ganin fushi, anger, da mugun temper akan fuskanshi ba kaman yanda take gani shi yau, nunata yayi da yatsa sannan ya nuna kanshi cikin bakar bacin rai voice yace “kina matata kikaje kina magana dawani!”

Wlh rawa jikinta yafara yanda taga Riyad yayi fushi amman bakinta bai mutuba, cus tabiyashi kudinshi ko sama da kasa zata hade saidai tahade yau tace “I don’t love you! Bana sonka, bansonka bansonka who are you to say saina zauna dakai? Who do you think you are? Kai waye kai? Nabiyaka kudinka kasaken!” Kyaaaassssese! Taga ya yaga check din dayasa tayi wani ihu tace “Riyad!” Yaga check din yayi gutsi gutsi yazubar akasa tabi pieces of paper check din da kallo bakin ciki na kamata saikuma ta kalleshi kaman mahaukaciya tace “check din kayaga? To ba yagawa ba ko ubanme kama check din nagama zama dakai, Bilal is waiting for me” taduka tadauki jakanta tazo azuciye zata wuce wani irin fizgota yayi kawai yakai hannunshi wuyanta idanushi sunyi jazur.

 Azafafe yace “Rashidaaaaaahhhh!” Ganin idanunta na ja tana kakari yasa yasaketa ta duke awajen dasauri tana tari, Riya totally lost it yace “you are telling Riyad zakije kiga wani? Are you seeing someone da aurena akanki? I try to be patient with you, I try to reason with you cus nasan an miki badai dai ba which was not me, but I still took the blame cus family nane, na lallasheki, na lallaba ki, I respected you, I’ve never forced my self on you even though we sleep agida daya,how dare you kikaje wajen wani namiji, how dare you talk to another man aduniyan nan sama da ni, how dare you kika gayama wani namiji situation naki har ana baki check, Rashidaaa!” yayi maganan yana dakan center table dake kusa da inda take duke yadaki bango jikake rassssss! Kwalba sun fashe dayasa Rashida tai ihu tana matsawa gefe jikinta narawa yana bari bata taba sanin Riyad nada fushi hakaba, bata taba samin kanta in situation data firgita irin na yau ba kankame jikinta tayi ko’ina na rawa taki kallonshi dan tsoron kallonshi take tana kuka sosai still bakinta bai mutu ba tace

“wlh, wlh bazan zauna dakaiba bazanyi auren dakaiba wajen Bilal zani wlh shi nakeso, shi zan aura, mun shirya komi he’s waiting for me” kallonta Riyad yayi ganin bakinta bazai taba shiru ba no matter wat ita me taurin kai, is time to deal with this iron girl the right way, yana kallonta yace “okay kin cigaba da kiramin sunan wani agidana ne?” Yana maganan yana tahowa kaman zaki, baya tashiga komawa tana runtse idanunta hartakai bango ta dukunkune tana kuka, yana zuwa hannunta yaja ya fizgota ta taso ihu tayi sosai. “Jama’a ku taimakeni zai kasheni zaiyi kidnapping dina, Bilalllllllll” ta kwalama Bilal kira dayasa Riyad yajuyo zuciyanshi yagama lalacewa tass! Yadaura mata mari na biyu dasaiga jini gefen bakinta ya jata da karfi da yaji har sama zuwa dakinshi ya wurgata ciki tafadi akasa ya maida kofan ya datse a zuciye yajuyo cikin kakkausan murya yace “dauka kinfi karfin kowa ko? Or you think i can’t deal with you, kokinfi karfina sabida inata lallashinki and petting you? You think I can’t handle stubborn girl like you? Yau I will properly legalize aurenmu, I will show you cewa I own you! I will show you the power danake dashi akanki! I will sleep with you today! I will make you my rightful wife duk ubanda ya isa a Kano yazo yahanani cinki Rashida!” Yayi maganan yana wani fizge rigan dayasa dasauri Rashida ta tashi tana ihu sosai. “Somebody help me wayyooo Allah na zai kasheni, security” Tashiga waigawa baya tana ihu, ganin yafara bude belt yasa tai hanyar bayinshi da gudun bala’i, hannu yasa ya fizgota tazo jikinshi tashiga kaimai duka tako’ina da duka karfinta tadauka Riyad kalan sauran mazan datake dambe dasune, ko’ina tasamu kaima duka take baidamu ba kawai taji ya yaga lab coat nata ya yar dudda sabon atampa ne ajikinta tashi daya taji kyaaaaaa shima ya yaga tsabagen yanda ya zuciya yau, kokarin fita tayi daga jikinshi ganin daga ita sai pant and bra tana juyawa yakama pant nata ya fizgota back to his body kyaaaa ya yagashi yasa bayanta a kirjinshi kawai taji  hannunshi kan saman boobs nata ta gaban breziyan ya yaga bra din in just 5secs Riyad yayi ripping nata off na clothes dake jikinta, ihu tayi dan tagama firgita tace “na shiga uku” tashiga fada dashi sosai bana wasa ba tana hayagaga tana throwing every punch data iya all special skills nata tana ihu. “Wlh bakamin komiba, wlh bazaka tabani ba, Bil……..” hannunshi yadaura abakinta dan he don’t want to slap her again nor hit her amman ta masifan kololuwan batamai rai ya hankadata gado, ahaukace ta taso ya sauke wandonshi duka biyun kasa kulle idanunta tayi da gudu tana dirkowa daga gadon ganin nakedness nashi jin yadauketa yasa tabude idanunta tana ihuuuuu tana kokawa maidata gadon yayi yashiga bude mata kafafu tana harhardewa tana kuka tacigaba da kokawa dashi saida daga hannu yasoma mata wahala tsabagen yanda ta galabaita sannan abayyane taji yafara karanto addu’an saduwa da iyali tashi daya yabude mata kafa yakama kan dick nashi yakai wajen yabuga da karfi. “Billallllllllll…….” Kai Riyad jiyayi zai hadiye zuciya ya mutu yasa hannu ya danne bakinta azuciye yashiga dambe da vijay nata ba imani nor tausayi…….. DAN ALLAH WAYE DA LAIFI?? RIYAD YAYI KOKARI DA RASHIDA KO BAIYIBA?? ABINDA YAKE SHIRIN MATA YANZU KUNYI SUPPORTING??? SEE YOU SUNDAY❤️


EPISODE 69

pains dindatakeji yamata yawa ko tausayi bata bashi ba, dan tariga tagama batamai rai, bugamata dick yashigayi ciki yanajin abinda baitaba ji arayuwanshi ba kaman zai haukace, Rashida na kuka tana cizonshi amman kaman ba mutum ba wlh saida ya shige gabaki daya ciki sannan yafara sex din da kyau pussy ta kaman zai hadiye mai dick tsabagen yanda is extreme tight dakuma dadi tun muryanta na fita harya dishashe sabida ihu da kuka da kururuwa da rokonshi, tun safen nan data dawo sai wajajen 2 yakawo Dagata yayi gently yakai hannunshi yazaro da kyar dick dinma yafito daga jikinta yana kallon yanda take numfashi da kyar harwani ijiyan zuciya wanda yasha kuka take, idanunta biyu amman a lumshe, ga duka kumatunta a kunbure hannunshi sun fito dan lafiyayyen mari yamata sabida fushi, gently yakai hannunshi yajawota yasata ajikinshi rungumeta yayi sosai yayi shiru na kusan 5min yana patting bayanta da hannu without telling her anything sannan ya maidata ya kwantar, yatashi ahankali yana sauka daga gadon yawuce bayi wanka yayi yafito bayan yatara ruwan zafi a bathroom din, jallabiya yasaka yayi salla sannan ya tashi yacire jallabiyan yazo gadon yadagata chak yawuce bayi da ita yasata aruwan zafi, ihu tayi baya fita cus muryan yashake yau tasha kuka, ruwan kaman barkono take jinsa hakan yasa tafashe da kuka na azaba Riyad sai kallonta yake cus shima yasan ta wahalu, stubbornness dinta yaja ta wahala baitaba planning first night nasu to be this chaotic ba but rigiman caused this.Yafito ya shimfida wani ganin ta idar yazo yadagata ya maida gadon sannan yawuce yasa kaya yafita daga dakin kasa yasauka yaduka tareda daukan wayanta daya gani awajen yafito, babu ma’aikatanshi acikin gidan hakan yasa ya shiga mota kawai ya danna horn shigowa sukayi suka budemai gate yafice, dailing wani number yayi ana dagawa daga dayan bangaren yace “na gaida Mai Martaba” anatse yace “prescribe drugs for me na arhmmmmm” yadanyi shiru sai chan yarage tone yace “virgins” professionally Dr yace “akwai much ciwo ne?” Ahankali yace “I don’t know but I think yes, it’s kind of a forceful one” yafadi yana kallon hanya yahade rai, dan murmushi Dr yayi mai sauti hakan yasa Riyad yace “idan bazaka fadaba i will call another Dr” dasauri Dr yace “zan fada mana” kaman Riyad bazai ce wani abu ba yace “I want wanda zai kori zafin cus I wanna go again more like clearing the pathway, ina jiran text din” yayi maganan yana katse wayan yacigaba da tuki kafin yakai babban pharmacy yaji karan sako parking yayi yashiga yasayo yafito yayi dailing number Munir yana dagawa yace “call CMD general hospital Masarauta call not personal, I want to know waye Bilal a yan year 5, I need everything about the Boy ASAP” ya katse wayan yana parking gaban wani eatery.


EPISODE 70

 Fitowa yayi yashiga eatry din yasayo abinci sannan yadawo mota daidai wayan Rashida daya dauko na ringing, maida kofan motan yayi yarufe yasa hannu yadaga wayan Bilal yagani akan screen din yanda kirjinshi kemai zafi kaman yafito dashi Bilal din daga wayan yasamai wuka aciki haka yakeji, shi yafi karfin yadaga kiran Bilal No! Yana kallon kiran harya katse yayi shiru sannan yashiga calls nata yaga duk shine take waya dashi and kiran just starts from jiya Friday tundaga sanda yabata wayan babu wani call history saina Maimoon, fita yayi yashiga message nata batada any message banda na network provider nata saikuma bank charges alert da aka mata na end of the month ancire 200 Balance na acct dinta is just 1350, fita yayi yashiga watsapp banda group na ajinsu Year 5 Med batada wani personal chat sai Bilal da Maimoon, na Maimoon yafara budewa dan yaga ko tana zugata or anything but babu anything like that, bamata iya kawancen ba at all Maimoon talks to her trying to start conversation but batama iya reply ba, daga ok sai to sai uhm shine amsanta, Koda yakai gida falon ya kalla yanda kwalabe ke everywhere saikuma ya wuce kitchen ya ijiye komi yadauko broom da Parker yashiga shara da kasan bawai ya sabayi bane but he tried ya kwashe duka kwalaben yakai bola sannan yadauki tray yayi arranging magungunan ta akai yamata tea yasa abincin daya sayo mata daga eatery which is rice and curry soap yasa water yadauki tray din yafito ahankali take tafiya har zuwa sama dakinshi yanda yabarta akan gado haka take kwance a lullube tana baccin wahala ga gashinta abarbaje dayasa tai looking super gorgeous maida kofan yayi ahankali yarufe yataho wajen ya ijiye tray din kan side drawer na bed yazauna yana kallonta, he’s very very angry with her tunda yadan ta he has been overlooking kome zatayi baya bashi haushi but magana da wani this guy datake in contact with him yabatamai rai beyond explanation, hannunshi ya dunkule ya kalla he’s feeling pains na marinta dayayi dabai mareta ba and just sleep with her make her his completely but he couldn’t hold it, tunda yayi wayau yasan kanshi kai ko Munir kanninshi baitaba kaiwa duka ba talk more of wani, ko wata, imagine Haleema that’s always annoying him but baitaba kaimata mari ba, fuskanta yasake kallo saikuma ya lumshe idanu ahankali he’s not proud of actions nashi, shi baimasan he can get this angry ba dan he hardly gets angry gaskiya baida yawan fada baida yawan fushi.

 Motsi yaga zatayi cikin bacci tahada kafafunta saiyaga tafashe da kuka cikin baccin tace “Mama zan mutu zafi” wani kalan tausayinta yaji yaji ahankali yashiga cikin gadon yaye bargon yayi ahankali yadagota bude idanunta Rashida tayi ganin Riyad saida ta firgita dudda muryanta baya fita sosai saida tace “dan Allah kayakuri Yaya Riyad, wlh wlh wlh bazan karaba dan Allah” tai maganan tana kuka sosai, dudda batada karfi she’s trying tafita daga jikinshi, tabashi tausayi but he don’t wanna show her, is time to show Rashida water na cup dinta yacika atleast ko shi kadaine aduniyan nan yanzu tadinga tsoronshi even though bayason matarshi na tsoron sa but dole hakan yafaru this period cus bazaiyu karaman yarinya ta taso batada wanda take tsoro ko wanda zai fada mata tajiba sabida taga Mamanta bata raye.Hade giran sama da kasa Riyad yayi cikin kakkausan murya yace “quiet!” Wlh kaman anyi ruwan sama an dauke hadiye kukan Rashida tayi ko motsin ma tadena sai kirjinta dake mummunan faduwa ta bala’in firgita da Riyad bata taba sanın baka yake ba mutumin datake gani so kind and simple, ahankali yasata a kirjinshi batare dayayi kaman lallashinta yake ba dudda he put her there just to comfort her, yadauki tea daya mata yasa spoon yajuya yakai bakinshi yaji zafin is okay, sosai yakejin yanda kirjinta ke racing tana jikinshi tea yakai bakinta yace “drink” bakinta abude da sauri takai kan tea duka jikinta rawa yake sha take batare data damu tanaso ko bataso ba batason tasake batamai rai dazaisa yamata kwatankwacin abinda yamata dazu ko enemy ta bataso yaji that pain ganin tasha kusan rabin kofan yasa yacire mata daga baki yadauki magungunan guda tea ne ya ballo yabata su a hannunshi yanda hannunta data kawo zata karba ke rawa Riyad ya kalla sai kawai yafasa bata dan zamata iya zubarwa yakai hannunshi bakinta budewa tayi da sauri ta karba yasake bata ruwa ta kota dashi rice din yadauko instead of yabata dakanshi nope baison taga any care ko affection daga gareshi yasa ya ijiye mata akan cinya yace “eat” yabata spoon karba tayi dasauri tafara ci saida yaga tayi rabin rice din and yasan she doesn’t eat much hakan yasa ya karbi abincin yabata ragowan tea yace “finish this” dasauri takai bakinta ta kafa ta shanye ya karba ya ijiye yayi shiru yanajin yanda she’s trembling har lokacin ajikinshi sai ijiyan zuciya take saukewa saikuma chan muryanta a shashake tace “Yaya Riyad” kallonta yayi yanda kanta ke kasa ajikinshi hannayenta na rawa yaki magana, hannuwanta duka biyun Rashida takai kan idanunta tana goge hawaye tace “dan Allah kayakuri bazan kara ba, dan Allah kayakuri wlh wlh kuwa” baitaba sanin after mutuwan Mama this girl can get soft like this ba, har muryanta yayi rauni haka tana bada hakuri, baki tabude zatai magana cikin kakkausan murya Riyad yace “I’m not interested in talking to you, Malama kimin shiru” gyadamai kai tayi jikinta har kyarma yake sai kawai yatashi yacireta daga jikinshi yadauki sauran abincin data rage da tray din yafita.

Rashida ta kankame kanta, she works in gynea, tana ganin patient matan aure amare none of them yataba complain abin is this painful, da hakane da ai duk sun gudu gidansu, da Mama na nan yau data kira Mama tazo ta tafi da ita, babu abinda bata sani game da reproductive system ba, she knows idan za’ayi breaking hymen na virgin ana danjin a little discomfort which ko alokacin datake karatun nan she knows she can handle it idan lokacin yayi cus tanada mugun dauriya ko Mama always says Rashida kinada dauriya, she’s a Doctor, she knows everything about sex reproductive health da komi da komi bata taba sanin haka akeji ba kodan batada wata close tight friend dazata bata labari ne oho, ita kadai tasan abinda Riyad yamata, goge hawayen dasuka zubo mata tayi da sauri, ko tausayinta daya bejiba, he was f*cking her for hours bayan takaranta a textbooks nasu sex baya wuce 1-2min hightest 5minutes, all abubuwan nan tasansu takarance su tsaf a theory, abin 1-5min hightest shine shi Riyad tun safe kaman around 9 suka dawo fa itada driver nan tun lokacin, tun tana kirga hours dayanayi har she passed out, anya is he a human kuwa? Who is Riyad?She’s so scared and afraid of him cus he’s a monster! Riyad ba mutum bane.

Bude kofa yayi na dakin mummunan firgita tayi dashi kanshi Riyad saida yagani amman yadauke kai kaman baiganta ba yawuce bayi alwala yadauro magrib tayi sannan yafara tara another hot water yafito dakin yazo ta wajen gadon bai kulata ba hannu kawai yasa yadauketa suna shiga bayin yasauketa kasa yakai hannunshi saman riganta yana kallon fuskanta kankame idanunta tayi sosai hawaye na fitowa daga cikinsu jin zai ciremata kayane yanzu shikenan haka zai dinga ganin jikinta shikenan ya ganta, ciremata rigan yayi tajuyarda kanta gefe tana kuka sosai takai hannayenta tana kokarin rufe kirjinta Riyad yabi hannun da boobs dinta da kallo sai kawai yadena kallo shima dan yayi alwala kafin yabaci, daukanta kawai yayi yasata a ruwan zafin fashewa da kuka sosai tayi banawasaba kuma tsoronshi yasa takasa mikewa amman kaman ta kurma ihu takeji, kaman yacirota daga ruwan but ya daure yaki gayamata sorry saima daina kallonta dayayi cus kukan na tabashi, 10 good minutes ya tsaya tayi a ruwan sannan yacirota yadauki towel ya goge mata kafafu sannan ya maida mata rigan ya kunna tap yace “perform ablution kije kiyi salla” yana fadin haka yabarta abayin yawuce yafito he wants her to walk let her get use to it cus yanda yamaidata matarshi yau yanzu proper married couple living zasu fara, mosque yawuce yayi magrib anan ya zauna har akai isha’i sannan yadawo gida. Kofa ya kulle ya kashe wutan kasa ya kashe na sama ma yataho dakin nashi yabude kofa ahankali akan dadduma yaganta kwance bacci ya dauketa, kayan jikinshi yarage yawuce bayi fitowa yayi daure da towel yawuce yayi shirye shiryenshi ya feffesa turarukan shi sannan yafito har lokacin dagashi dai towel din, tsugunnawa yayi gaban dadduman yadagota Rashida dakeda nauyin bacci but sabida abin na ranta bala’in firgita tayi tana bude idanunta suka hada ido rawa jikinta yafara da sauri tasauke kanta kasa bakinta na rawa cikin raunanniyan muryanta tace “ina yini” hannu yasa ya kwashe hijabin jikinta yacire mata sannan yadauketa zuwa gado ya kwantar da ita yadauki remote na AC yakara AC gabaki daya sannan yahayo gadon yana kwanciya gefenta hankalin Rashida yatashi, ahankali yasa hannu yajaye towel dake waist nashi yacire, datse idanunta Rashida takara yi ganin al’auranshi again for the 2nd time yau amike sambal ga kauri, bata taba ganin nashi a practicals dinsu ba, har na corpses ma bata gani ba, why is he different from anything data koya a med school? Crowns na penis nashi kaman na mutum biyu aka hadamai paskeken kai gareshi, rawa ko’ina najikinta yafara saita fashe dakuka kawai kaman wacce aka make, wurga towel din yayi kan kujera chan sannan yasa hannunshi bargon gadon yaja musu yarufa musu yakwanta yajuyo yakalleta yace “kidenamin kuka anan”. 


EPISODE 71

Gyadamai kai tayi kaman yar marainiya, cikeda karfin hali tashiga komawa chan karshen gadon ta matse awajen bayanta na manne da bango, hannunshi yasa ya kashe musu wutan dakin dakin yayi duhu yabiyota karshen gadon hannunshi yadaura kan bayanta yace “wayace kidawo nan?” Cikin muryanta da kasan kuka take tace “bakowa kayakuri” dan murmushi yayi yace “zoki bani hakki na so nake nagama nai bacci” yanda kirjinta ke bugawa zaka dauka tanada ciwon zuciya takasa ko motsi, azafafe yace “bakijiba” in kuka tone gwanin ban tausayi tace “naji” “to me kike jira”? Numfashi har neman kufce mata daga baki yake tace “bansan yaya zanyi ba” “come here” yafada with so much authority, tahowa tayi ta sadakar yau kawai zata mutu, shigowa jikinshi tayi sai shi yasa hannunshi yayi resting head nata akan shoulder nashi daya kwantar mata yanajin yanda gabanta ke faduwa da yanda take kuka yace “idan baki denamin kuka awajen nan ba zan baki mamaki Rashida!” Atsorace ta danne kukan tace “nadena dan Allah kayakuri” kai wani irin dadi dayakeji ko wato yagama firgita Rashida bana wasaba yarinyar nan ta mugun tsorata da firgita da lamarinshi, daurewa yayi with so much anger yace “bani hannunki” dasauri tabashi karban hannun yayi saida taji shocking daura hannun yayi kan sajenshi zuwa kunnenshi, softly yace “you will bring mouth naki kiss me and gently kina shafa sajena da kunnena kinasa smallest finger naki in my ear poking it,now starts” kuka ne awuyanta bana wasaba amman yahanata yi, dudda dakin da duhu but yana iya ganin kusan komi datake, ahankali ta matso da fuskanta dab da nashi yanajin yanda take fitar da numfashin tsoro akan fuskanshi, dudda akwai duhu taga yanda yake kallonta dayake atsorace take saitaga kaman kallon bacinrai ne da tsana yake mata, tana nishi non stop na tsoro dake sauka akan fuskanshi ta kalli lips nashi, yanzu lips dinshi zata sha cikin kakkausan muryan yace “idan kikai kuskuren sa raina yabaci zakiji ajikinki” girgizamai kai tayi da sauri sannan adan rude tadaura lips dinta saman kan lips nashi ta lumshe idanunta ahankali, she knows wat kiss is, tana gani a movies and yamammata taji yanda akeyi, gently kaman irin baby da baitaba shan abu ba this is the first time aka bashi yake kuma trying haka tai grabbing buttom lips nashi ahankali, Riyad jiyayi kanshi zai fashe sabida dadi yadai daure yayi lakur feeling every bit na abunda takeyi, ahankali tasake sucking bottom lips din, bakinshi is actually very sweet kaman ya goga alawa, saikuma tahada both lips na sama da kasan ta tsotsa baisan sanda yakai hannunshi yakama dick dinshi dayaji yana zabura ba yafaramai ciwo feeling both of his lips acikin bakinta is something dabai taba picturing zai faru ba, dan bude bakinshi yayi alamun ta shiga daga ciki yawani matsota jikinshi, ahankali tasaka tongue nata abakinshi tama begginers licking na harshen shi dataji salty and sweet taste combine. “Mmmmmmmm” yasaki wani dirty sound kafin yayi grabbing mouth dinta ganin ta tsaya chak bata cigaba ba yasa ahankali yace “continue kissing me don’t stop, do my ear” sannan ya shiga kissing nata tana kissing nashi back tana shafa mai saje kafin chan tasaka small fingers nata cikin kunnenshi rirriketa yayi kaman anzo kwacemai ita yafara making crazy sounds suna kissing one another. “Muahhhhhh………aarrrrrrrhhhh……..mmmmmm……. Pusssss……urrrgghhhhh” sound din dayake making zaka dauka ragone hannunshi taji yacire daga bayanta yadawo dasu tagaba kasa taji yaja riganta dasauri sannan yakai hannayenshi biyun duka yadaura akan each boobs squeezing nasu yayi da karfi hakan yasa Rashida ta zura yatsanta da kyau akunnenshi cus zafi taji. “Ahhhhhhhhhh!” Yayi ihu sosai abakinta, nipples nata yaja da karfi dayasa tayi kokarin fizge bakinta daga cikin nashi cus ciwo suke mata bakaramin shansu yayi dazuba kasa daurewa yayi yanda yaji nipples din sun fito yasaki bakinta da sauri yanadan dagowa hannunta yakama yashigar cikin bargon yakai saman dick dinshi yadaura axabure tayi kokarin cirewa yana kallon cikin idanunta yace “ play with my di*k” gyadamai kai tayi da sauri tana rikewa, kan gabaki daya yajike da pre cum jin hannunta saman gindinshi baisan sanda yayi karaba kaman dan yaro. “Ahhhhhh! My di*k!” Da kyar cikin muryan kololuwan sha’awa yace “give me bweez wife saiki matsemin di*k din da kyau” rasa tayaya ma zata bashi nonon tayi hannunshi Riyad yasa ya tattara riganta yazare mata daga jikinta ya cillar kawai ya fizgota zuwa jikinshi yakama right boobs nata yafara sha yana bucking up hitting dick nashi in palms nata alamun tarikemai da sauri tarike not knowing metakeyi yanda yake nishi yana zukan nipples nata dake mata ciwo zaka dauka mutuwa zaiyi, ahankali Rashida takama kan crowns din dataji ruwa na fita tarike gam dan batason ruwan natabata cus tajishi da yauki ita adole tarufe bazai kara fitowaba ashe taba mumu button din Riyad tayi. “Wayyyyooooo gindina!”Riyad yafadi in thick voice yana sakin boobs nata kawai yatashi kaman zai shide yakeyi kafafunta kawai yadaga yakai shoulder nashi yana grabbing dick nashi dakemai tsananin ciwo food kawai yakeso yakai wajen ya buga Rashida tayi ihu tana karbe kafafunta tai wani burgima zata fadi akasa yatarota dagudu yana dawo da ita gadon, ahaukace tace “wlh wlh Yaya Riyad nace maka bazan kara maka laifi ba, na rantse kuwa, amman dan Allah kada kamin abin nan dan Allah” cikin muryan mugun mabukaci yace “ban gama hukunta ki ba, laifinki nada girma” kokawa tashigayi dashi da karfinta da babu tafashe da kuka sosai, ayanda yake abukace kawai ninketa yayi yayi folding nata da kyau and just hit on her pussy but baya shiga, ihu Rashida tafara jin yanda yake mata da gaske yake, saida Riyad yayi da gaske yashiga wasu mahaukatan hawaye na fita daga idanunshi sabida yanda dadi ke ratsamai jijiyoyin kai, manta komi yayi yafara mata lafiyayyen strokes dayakeyi da kyar dan she’s so tight baya iya movement in the vijay freely hakan shike kara haukatashi.

Rashida tayi kuka tayi kuka tai nadaman duk wani abu daya tabasata tama Riyad rashin kunya da tsiwa da tsaurin ido dan maybe duk inda batai hakaba daya tausaya mata, but Riyad cinta yake kaman kin shiga uku, tun tana kirga juye juyen dayake da ita harta bata, saitamazo ta sume cus wannan yafi na dazu yimata azaba dan na dazu at least bata sumeba.“Ahhhhh zan kawo, zan kawo, Jewel I love you, wlh ina sonki Jewel, you’re the best woman aduniya, ahhhhhhh wayyyoooo zan mutu dadi Jewel dadi ahhhhhhhhhhhhhhhh” yayi ihun da saida gidan ya amsa yariketa kaman zai karyata yana zuba uban juice nashi cikinta dazaikai one cup, daga kanshi yayi ya kalleta yasan ya sumar da ita ahankali ya kankameta wutan sonta na karuwa aranshi bacci kadan ya kwasheshi baiyi 30minutes a baccin ba lafiyayyen sha’awa na asuba yatasheshi dick dinshi ya mike sambal acikin jikinta dan baiciro ba baiso yakara mata wani abu ba wlh, amman yanda yaji yayi girma yasa ahankali yafara grinding nata idanunshi na juyawa daman vijay na wannan dadin? Wlh baisani ba, dadın da vijay din Rashida ke mai is beyond comparison ko explanation gently yaso yayi grinding nata dayaji ina bazai iyaba yafara zubamata lafiyayyun gwatso daya tadata daga suman datayi tafashe da kuka jikinta duka ciwo suke, boobs dinta ciwo suke, kasanta ma yake, thighs nata, hannuwanta kai komi najikinta ciwo suke, ci me kyau Riyad yamata da asuban nan saida yarasa jam’i da kyar da kyar yakawo dick din yafito daga vijay nata shima da kyar abinda yafi kasheshi kenan yanda yake fitowa daga ciki da kyar.

Riyad is f*cking d girl like machine he feels kaman yanzu ne yake sex arayuwanshi he wants to do it, he’s doing the sex yanda yakeso, kaman dadi zai kasheshi sakin boobs nata yayi ya kankameta yakai fuskanshi wuyanta baimasan yanayiba kuka yafara sosai like a baby.



EPISODE 72


Tashi Riyad yayi yana kallon yanda ta galabaita

gabaki daya, ta wajigu iya wajiguwa, ta galabaitu, yawuce bayi da sauri yayo wanka yafito yasa kaya yayi salla yana idarwa yataso yana cire jallabiyan jikinshi yazo gadon ahankali yasa hannunshi yadauketa hatta yatsanta ba karfi, jikinta yayi zafi zazzabi ya rufeta bana wasaba, bayi yakaita yasata aruwan zafin azaban dataji sai kawai tafara kakarin amai bamata da karfin babu komi acikinta, da sauri

Riyad yakai hannunshi yatare dan abinda yafito daga cikin bakin nata which is mostly water and saliva sabida karya shiga ruwan datake ciki yana kallonta, tabashi tausayi, ta wahalu a hannunshi, tashi yayi yawuce basin yazubar yana wanke hannunshi yadawo wajen daidai tana karayo kakarin aman hannunshi yatara awajen still just mucous ne, tashi yasakeyi yaje ya zubar yafara wanke hannun kafin yagama tafara kakarin amai dayasa yajuyo da sauri da gudu yatafi wajen sai kawai ya rungumeta aman na zubowa abayanshi yashiga patting bayanta yace "what is wrong with you Jewel? Baki da lafiya" kakarin amai take da dan muryanta da baya fita tana mikewa da kyar kaman zata mutu, jikinta ciwo yake mata, jikinta kaman wuta, wanka yamata yamata na tsarkin da kanshi yafito da ita amai kawai take ba kakkautawa gashi ba baki bamata iya magana balle tace ga abinda ke damunta, wih tsoro yaji yanda kaman ma bata gane kome yake gayamata wayanshi yadauka da sauri yafito falo sai kallon wayan yake da kyar ya iya yayi dialing number Ammi ringing daya, biyu ana uku ta daga kafin ya gaidata tace "yaya jikin kaji sauki"? Shiru yadanyi yama rasa mezaice chan yace "Am.....mi" dan faduwa gaban Ammi yayi jin yanda yakirata ararrabe dasauri tace "na'am Riyad, wat happen?" Dan shiru yayi saikuma yadan sosa kai kaman tana gabanshi. "Nace wat happen kamin shiru" ahankali yace "ahmmm she's sick Ammi, ahmmmm bansan mezanyi ba" strictly Ammi tace "meke damunta?"Dib ya katse wayan Ammi tabi wayan da kallo chan tashiga kwalama Munir kira. "Munir, Munir" saukowa yayi daga sama yace "Ammi yanzun nan fa nabarki are you missing me already" dan hararanshi tayi tace "dauko key zoka kaini gidansu Riyad Rashida is sick".

Kitchen Riyad ya shiga yahada mata tea yadauko yahayo sama, tana kwance abakin gado daya ijiyeta tana amai har lokacin tana rawan sanyi, da sauri ya jiye tea yakoma yafita zuwa dakinta yasami mata wani gown mai shegen kyau na cotton that's soft yellow and red ne yadawo dakin yaga tana aman yataho yadagata yasamata rigan yasata ajikinshi like a little girl ya kankameta sosai yace "I've called a doctor you will be fine kinji, he's coming sorry my baby" ya kankameta kawai ajikinshi, jin an taba door bell na falo yasa yayi tunanin Dr ne room nashi is so messy hakan yasa yadauketa zuwa dakinta yabude a gadon ya kwantar da ita yarufamata bargo cus she's shaking sannan yawuce yafito yakoma dakinshi yadauko wani white jallabiya yasaka yazura slippers yafito yasauka kasa yana zuwa kofan yabude ganin Ammi tsaye da Munir saida gabanshi ya bala in fadi baitaba tunanin Ammi zatazo ba, fuskanshi kadai Ammi tagani tasha jinin jikinta, ganin yakasa matsawa gefe yasa tace "ina Rashidan?" Dan sauke kanshi kasa yayi yace "her room" ta gefenshi Ammi tabi tawuce sama shikuma Munir ganin yanayin dan uwanshi yasa sidif sidif yajya yakoma mota yana murmushi kasa kasa aranshi yace "Welldone Bro Yayana namiji ne wih, brotherhood is proud of you, yacinye lioness koba komi yanzu zamu huta, zanga bakin Rashin kunya".Dakinta Ammi tashiga ahankali daidai tanayo wani aman dasauri Ammi tayi wajen tana yaye bargo tadagota tace "subhanallahi Rashida" zafin jikinta harya baci, idanunta kadan tabude ganin Ammi yasa takama hannun Ammi tarike gam gam bakinta yashiga motsi dasauri Ammi takai kunnenta saitin bakinta. "Ammi karki tafi ki banni, wih Yaya Riyad zai kasheni, Ammi zan mutu, kicemai nace wih, wlh bazan karama kowa rashin kunya ba, Ammi dan Allah karki tafi ki bar.......

.." daidai ana bude kofan

dakin yanda Rashida ta firgita tarirrike Ammi tana wani irin kuka saida Ammi tadago kanta takalli kofan dakin ganin Riyad ne saikuma takalli Rashida da yanda takeyi takalli fuskan yarinyar yanda sukai ja saikuma tashafa fuskanta tace "Rashida kinga kinga babu inda zani, nothing will happen to you I'm here now, bari nazo, yanzu zan tafi dake zaki bini gidana"? Kallon Riyad Rashida tayi da idanunta da basa buduwa atsorace tace "sai abinda Yaya Riyad yace Ammi" mamaki kashe Ammi yayi saikuma tace "shikenan to kwanta ina zuwa" ta kwantar da ita dasauri Rashida tajuya ta kalli bangon gado, Ammi taja bargo tarufa mata, sannan tawuce wajen kofa kawai takama hannun Riyad tace

"come with me".

Bin Ammi yashigayi dake jan hannunshi gabanshi na faduwa har kasa, kitchen Ammi suka shiga ta maida kofan kitchen din tarufe takalli Riyad da kanshi ke kasa tace "me kama yarinyar nan?" Shiru yayi batare dayayi magana ba, adan zafafe Ammi tace

"did you slap that girl Riyad cus fuskanta shows alamun slap harda injury a gefen bakinta, Riyad did you beat her?" Da sauri ya girgiza kai muryanshi chan kasa irin na mara gaskiya yace "I slapped hertwice Ammi" Ammi jitayi ranta yayi masifan baci tace "Riyad you slapped that poor marainiyan yarinya har sau biyu sabida kaga babu kowa, sannan kabita kai amfani da ita!" Cus tana ganin Rashida from yanayinta da yanda gashin kanta yake ajike yasa tasan wani abu ya wakana tsakaninsu, rawa bakinshi yafara ahankali yace "Ammi is not wat you think I was ang...." "karufemin baki!" Ammi tayi maganan ranta a bala'in bace, tace "you don't have to tell me anything nasan waye kai! Kome Rashida tamaka there's no excuse na dukan mace, Riyad that girl is just a child! Just a child! For Godsake she's only 23! Rayuwa made her to act matured not that she's actually matured har brain nata, Riyad kome Rashida tayi you need to understand yarinyar is grieving! She lost the only person data sani in her life Mahaifiyarta! She lost her Mom! Yara in grieving state tends to act irrational, I know Rashida da rashin tsoro, rashin kunya da sauransu but you went tooo far! She's traumatized, ka tsoratata down to bone marrow, ka mareta and ka karbe hakkin ka ta karfi wayake haka? Riyad you've hurt me this morning" Ammi tafadi ahankali sounding so bitter tace "haba yarinyar da mahaifiyarta dakai kadai ta yarda tabaka ita amana shine kama diyarta haka I'm not proud of your action" Ahankali Riyad yadago kanshi ya kalli Ammi dayaga ranta yabaci sosai da gaske tace "kuma wih wih bari ta warke yarinyar nan tace bazata zauna da kai ba saika saketa! I'm taking her with me ko flat dina kashigo sainaci kwal ubanka wh" Ammi tayi maganan cikin fushi tawuce

kofa tabude cikin fushi tace "Munir" Dasauri Munir yafito daga mota yace "na'am Ammi" rai abace tace

"zoka tayani daukar kanwarku mutafi gida" tahowa yayi yabi bayan Ammi yadan saci kallon Riyad daya gani tsaye agaban dakin ya tsaya hijabi Ammi ta nema tasaka mata sannan tace "shigo" shigowa Munir yayi dashi da Ammi suka dauketa atare suka fitoda ita har waje suka sata abayan mota Ammi tadaura kanta kan cinyanta sannan suka wuce gida.

Sama Riyad yakoma ahankali dakin nasu ya gyara tsaf yasake chanza duvee na jiya yacirosu yasakasu a dryer ya maida na jiya washin machine din yafito ya gyara gadon yashimfida wani bedsheet, riganta dasu lab coat nata da atampata harda bra daya yayyaga ya kwasa sai shima yayi shiru cus he actually went far, tayaya yayi fushin nan ya manta she's just a helpless girl that lost Mom nata and Mama trusted him, ahankali yace "Mama forgive me I hurt Rashida for the first time" saikuma yayi shiru yawuce yakai wardrobe nashi ya ijiye safe sannan yafito zai fada bayi ya dakata sabida kiran dayaji daga wayanshi yawuce Sarkin Gida yagani hakan yasa yawuce yadaga wayan yakara a kunne yayi shiru chan yace "akaisu secret fada gani nan zuwa" ijiye wayan yayi yawuce ciki yayi wanka yana tuna moments nasu, well as far as he knows Haleema was also virgin but she was never as tight as Rashida da kyar yake fitowa daga jikin Rashida fa, vijay nata grips him irin shakeshi dinnan yakeyi and banda haka she's very sweet and hot to ko masifaffen mutum yanada zafin vijay ne cus yarinyar nada zafin jini? Baitaba Jin abinda yaji ajikinshi Rashida in jikin Haleema ba.

Ganin he's getting erection yasa yadaina tunanin yafito ya shirya tsaf sak sarkinshi yafito aka tukashi zuwa fada.

Sarkin Gida na jiranshi already hakan yasa direct suka wuce secret fada tundaga nesa Bilal ke hango Riyad na tahowa cikin alkyakbba da rawani fadawa na binshi sunamai kirari yana taka kasa kaman bazai tabaka, faduwa gabanshi kawai yake yasauke kanshi kasa sabida yanda yamai kwarjini, same with Babanshi cus basusan mesukayi ba kawai an taho dasu, shigowa yayi yasami waje ya zauna fadawa namai fifita dudda akwai AC a falon Riyad yaki kallon Bilal wani mahaukacin kishi dayakeji he feels idan ya kalleshi zai iya tashi ya shakeshi.

Sarkin Gida yace "Mai Girma Ranka shi dade mutanen dakace akawo maka gasunan da yaron da mahaifinsa" dasauri Baban yace "Ranka shi dade laifi nayi ne? Nayi submitting all report kuma na dauki permission na leave saisa ma har nazo nigeria" anatse for the first time Riyad yajuyo da kanshi ya kali wanda yayi magana ma'aikacin sa ne he's the manager na hotel dinshi na Uk sai yanzu ma kanshi yayi ringing ganin name dake jikin check din saikuma anatse ya sauke idanunshi kan Bilal da duk yayi zuru zuru dudda baisan me sukayiba but jikinshi na bashi laifi sukayi kallonshi Riyad yake daga head to toe shine yaron da ranan yakawoma Rashida 100k, baijin Bilal yakai 28yrs ba highest yabashi 26-27yrs, yarone danye irin yaran dake tashen samartakan nan jaye idanunshi yayi yamaida kan Baban yace "kaine kabawa danka check na 22M yakawo ma matata!?" Yanda gaban Baban yafadi hakan na Bilal yafadi dasauri Baban yakalli Bilal saikuma ya kalli Sarki Riyad saikuma yasake juyowa yakalli Bilal yace "me kayi da check na business dana baka jiya?"

Saikuma yajuya yakalli Riyad da sauri yace "WIh wlh

Mai Martaba duka yarana not just Bilal dazaran na haifesu ina bude musu savings account wanda idan

sunyi girma zan basu su kama sana'a dashi, ranan juma'a da daddare yatasani gaba yanason nabashi nashi zaiyi business banso bashiba amman harda kukan sa shine na bashi da daddaren ranan bansan meyayi dashi ba" dasauri yakalli Bilal yace "mekai da kudin Bilal? Talk!" Baban yamai ihu dayasa sai jikinshi yafara rawa yadan kalli Riyad daya kasa ganeshi yama kasa tsayawa yamai cikakken kallo sabida kwarjini dayamai dan yasa rawani saikuma yace "Dad wata yar ajinmu nabamawa shima aro ne zata biyani, hauka nake zanma wata kyautan 22M azamanin nan" ahaukace Baban yace "bakaji maganan da Mai Martaba yayi ba iyalan Mai Martaba kabawa kudi!" Faduwa sosai gaban Bilal yayi yanzu mai Martaba ne dama shine Ogan Dady fa, shine mijin Rashida, dasauri ya kali me Martaba saikuma ya sauke kanshi akasa yace "wlh bata gayamin tanada miji ba kuma ni bama wani sonta nake ba Dad tausayinta kawai naji naga yanda take son....

." "Sarkin Gida!" Riyad yakirashi azafafe da saida dakin ya amsa,

dasauri Sarkin gida ya zube agabanshi hakan yasa Riyad yace "menene hukuncin wanda yaje yake neman iyalin Sarki?" Dasauri Sarkin gida yace

"bulala dari bakwai! Kullum anamai dari dari har tsawon kwana bakwai a baya tare aiki amatsayin bawa, banda haka ai duk garin kano babu wanda ya isa ya nemi iyalin sarki koda sarki yarabu da iyalansa ne, bata isa tasake aure acikin kano ba saidai tafita taje chan wata kasar tai aure! Wannan shine sharadin auren sarakuna".

Babu mutunci ko kawaici Riyad yace "a hukuntasa" dasauri Bilal yarike Babansa ganin fadawa sunyo kansa yace "Dad please save me wih, wih bansan wa take aure ba, Dad I just wanted to help the poor innocent girl tunda bata sonshi nasan nima da wuya nasan zaka banni na aureta, please kayakuri wh banasonta, waye ni dazan nemi iyalan Sarki ban isaba" kawai kallonshi Riyad yake he's not even Man enough yayi admitting yana sonta in trouble, how could Rashida be this gullible, this is a boy not a Man! Dagashi akayi yana mikama Babanshi hannu yafashe da kuka akai waje dashi.

Daga Riyad sai Baban Bilal yarage da mutanen dake fifita shi, da hannu yama masumai fifita alamu sufita daga dakin, dasauri Baban Bilal yace "Mai Martaba temper justice with mercy dan Allah, wih Bilal yaro ne baida wayau he's 26yrs and last month ma yayi 26din, dan Allah amai afuwa ni wih zan cire shi daga school dinma wh, dama daga Sudan yadawo nan sabida yakin dasukeyi but namaka alkawari zan karbi transfer zan maidashi Egypt yaje yakarasa awajen dan Allah kayakuri he's just a child, dan Allah me Martaba dan Allah, namaka alkawari shi da Iyalinka ko hanya bazasu kara hadawa ba, Bilal yayi kuskure ina rokonmishi afuwa" kallonshi Riyad yayi saikawai yatashi yafice daga fadan yafito yanajin yanda ake ma Bilal bulala a bombom yana ihu ya kalli Sarkin gida yace "after 100 bulalan kabawa babanshi shi su tafi no need for the remaining 6days cane" yana maganan yawuce yafito daga bangaren Waziri yagani tsaye tareda amininsa suka kalleshi tareda dukawa atare sukace an gaida mai Martaba munzo wajenka ne" wucewa yayi yazauna wajen yar shakatawa sa yasa aka musu iso suka taho zama duk sukayi ya zuba musu idanu baice uffan ba, anatse Waziri yace "ahhhm Mai Martaba nasan an maka laifi" yadanyi shiru yace "dudda nai kokarin maka magana hakan be yu ba, still yauma bazan gajiba, burin kowani mahaifi yasa diyarsa agida mai kyau hakika nasan Haleema tai kuskure shirmene kuma da yarinta wanda har zata dauki wata ta maidata kaman ita take aure ga mijin nata bazata girmama shi ba" yasake shiru sannan chan yace "Haleema tagane kuskurenta Allah taimaki me Martaba, da ni da amini na nan Muntari munzo mu nema mata afuwa ne tadawo dakinta duk ku taru da amaryan taka ayi zaman Ipy" baiyi wani mamaki ba yasan by now maganan ya auro Rashida yazagaye fada dakuma wacece Rashidan.

Anatse Muntari aminin Waziri yace "abata second chance dan Allah" shifa to be honest bayason Haleema he can't lie about it ne, forget about abubuwan datamai basune agabansa but wannan soyayyan baya jinsa game da ita, but then baitaso yaga Babanshi yarabu da kowace matarsa ba duk dadi duk runtsi ana tare banda haka he knows Haleema loves him kawai she prioritized Mom over him ne, he saw calls nata, messeges nata telling him sorry so he will give her second chance, idan she fails yarabu da ita gabaki daya, kallonsu yayi yace "tadawo dakinta!" Wani dadi sukaji sukahau mai godiya gaisawa yayi dasu yawuce Allah Allah yake yagama da mutane yaje yaduba Rashida fada yawuce.

Suna shigowa gidan sama Ammi suka wuce da ita sharp sharp takira Jakadiyanta wasu itatuwa da ganyayyaki aka samo aka girka a murhu aka kawoma Ammi sama, ijiye kunya Ammi tayi a gefe tunda ba Mama Rashida ke dashi da zata mata ba itace Maman yanzu, tagasa Rashida da kyau ita kanta saida ta tausaya mata ta wahalu fa, sannan ta matsa mata jiki gabaki daya da towel dake mata ciwo, suka fito daidai Dr Ammi na zuwa dubata tayi tacema Ammi basai anyi dinki ba but taji ciwo sosai tacema Ammi please kar abari yasake mata wanitacema Ammi please kar abari yasake mata wani abu harsai ta warke sannan tamata allurai tabata magani harda na tsayar da aman duk tasha Ammi da kanta Ammi tasauka kasa tamata kunu takawo mata sha tayi kadan sabida yanda ta matsu sai bacci Ammi sai shafamata kai take dayake ajike tayi shiru tana kallonta on her hand, she's happy Riyad yayi consummating aurensu wih har ranta she's, azamaninsu da suna yara idan yarinya ta taso da tsaurin ido bata tsoron kowa ga rashin kunya akance amata aure zata natsu, murmushi Ammi tayi tabude balm tana shafa mata a gefen baki wat she's certainly not happy about is marin daya mata!

Da kuma forcing nata dayayi no ba'a haka dudda tasan waye Riyad wih bakaramin abune aisa yadaga hannu ya mari Rashida ba ayanda yakesonta it must be big abu dudda taki bashi listening ear but tasan abu tamai dayakaishi ga marinta haka, ijiye balm din tayi har zuciyanta takeso Rashida taso Riyad itama suyi zaman su lafiya cus she knows and sees yanda Riyad ke sonta, ahankali tace "I pray Allah ya sanya miki son d'ana aranki Rashida, please love Riyad kinji he's a good boy" Ammi tayi maganan ahankali daga sama tanajin kamshin tsumin da Jakadiya ke hadawa, ahankali ta maida kanta filo ta kwantar sannan taja bargo taruta mata tafito tasauka kasa magunguna na gargajiya suka shiga dafamata harda gyaran jiki Ammi zata mata takuma gyarata da turare dan wih bazata bashi itaba saiyaga chanji zaici kaniyansa.

Shigowa Jakadiya tayi dawani leda a hannu na magunguna dataje tasayo takawoma Ammi a kitchen tace "Uwardakina Sarauniya Haleema tadawo" dan kallonta Ammi tayi saikuma tace

"Masha Allah, bani ledan kigani kin sami sassaken danace" karba tayi suka cigaba da aiki batare dadanace" karba tayi suka cigaba da aiki batare da

Ammi tace wani abuba.

After magrib Riyad yashigo gidan tareda Munir Ammi na zauna akan dadduma a falon tanajan charbi waje suka samu suka zauna har Ammi ta shafe ta kalleshi da sauri ya sauke kanshi kasa Ammi tace "banace karka sake ka shigomin flat dina ba" kanshi akasa yace "Ammi kiyakuri" shiru tayi sai chan tace "Haleema tadawo ko"? Aahankali kanshi na kasa still yace "yes" shiru tasakeyi sai chan tace "an ina kakeso Rashida ta zauna anan masarauta ko chan GRA"? Shiru yayi baiso ya ijiye Rashida a masarautan nan cus baiso wani ya cutarda ita, yarinyar has been through alot already he don't want any more drama a life nata, peace kawai yakeso yabata ahankali yace "GRA is her house Ammi" anatse Ammi tace "good! Sai magana ta biyu dazan maka karaba musu kwanaki?" Girgixama Ammi kai yayi, anatse Ammi tace "don't think sabida Mahaifiyar Rashida tarasu batada me tsayamata Riyad wih she has me! Mata biyu gareka even though she's here with me pending decision nata idan ta warke whether tana sonka ko bata sonka you have to raba musu kwanaki cus matarka ce, ranakun Haleema kaje kayi da ita ranakunta kayita walagigi a fada that's your punishment" danne dariya Munir yayi yanda yaji Ammi tace

"walagigi" juyoda kai Ammi tayi karaf suka hada idanu da Munir tace "zan cimaka mutunci fa ina magana da yayanka kake dariya tashi kabarnan" Sadaf sadaf yatashi yayi sama kaman munafuki Ammi takalli Riyad da kanshi ke kasa tace "ka manta yarinyar nan na school ne kamata abinda kayi ko? Ai kaji dadi dan yanzu she will stay at home harta warke ana maganan nan da 2weeks ko 3 kenan, idan wani abu yasami karatunta just know cewa its on you!" Har lokacin kanshi akasa saikuma ta sassauta murya cikeda motherly love tace

"yarinyar danakeso tasoka why will you hurt her like this eh Riyad? Metayi maka haka?" Ahankali yace

"Ammi kiyakuri" shiru Ammi tayi tasan bazai taba gayamata abinda yahada su ba haryakai ga marinta hakan yasa tace "anyway kazama mai adalaci problems naka da Haleema sort them out, be a man manage family naka da kyau, ko kaje dakin matanka ko call them to turakanka banso na karaji kaman yanda kayi da kabar Haleema for months baka ganta ba bata ganka ba, idan namiji yayi tsaye kan mace shine zatasan eh inada miji and do the right thing, dan haka from now henceforth do your part kayi adalci kaji ko" gyadamata kai yayi Ammi tace "and make her cook for you daga yanzu bazaka dinga zuwa side dina cin abinci ba, the only day dazan daga maka kafa is ranakun girkin Rashida tunda tana wajena batada lafiya you can come here kaci abinci amman other days baka isaba kaji ko"? Gyadamata kai yayi Ammi tace "tashi katafi to" kasa tashi yayi kanshi na kasa tsaf Ammi tagane meyake nufi Rashida yake son gani tace "ni zaka firgitama yarinya takasa bacci taga dodo da daddaren nan ai ina Riyad! Tashi kabarmin daki koni yanzu kazaman mini ojuju calabar a idanu balle muku baiwar Allah Rashida, tashi kaje wajen matarka Haleema saida safe" ahankali yadan kalli Ammi ganin da gaske take yasa yawuce yafita zuciyanshi ba dadi.

Tunda ya auri Haleema baitaba kwana a side nata ba dudda yanada dakinshi awajen kawai he just wants to be a better husband after maganganun da Ammi tamai, side nata yawuce Haleema na zaune taji ana sanarda zuwanshi gabanta sai faduwa yakeso many things ke damunta ciki harda mugun kishi jin yayi wani aure kuma wai yar Baffan da Muji ya aura duka labarin taji tsaf gadhi haryau takasa getting Mom dudda taji ance kotu za'a shigarda su, shigowa gikin dakin yayi yakalleta ta rame sosai sai kallonshi take maida kofan yayi yajuyo yasake kallonta cikeda so da kewa tace "barka da shigowa mijina mijin Haleema" dan gyadamata kai yayi anatse yace "how are you?" Ahankali tace "fine" gyadamata kai yayi yazo zai wuce dasauri ta taho takama hannunshi dasauri yajuyo yazubama

idanunta idanu cikin raunin murya tace "dan Allah kayakuri bazan kara maka abubuwan dana maka abaya ba, l promise to be a better wife, daga yanzu kaina jagaban rayuwana, bazan kara kuskuren danayi abaya ba" yana kallonta ahankali yace "are you sure"? Gyadamai kai tayi da sauri hakan yasa gently yabude mata hannu dasauri tazo ta shige kirjinshi ta kankameshi sai kawai tafashe da kuka hannunshi yadaura abayanta yana patting sai kawai yafara tuna Rashida cus this is how he pets her sauka hannunshi yayi da sauri yace "I'm hungry kinyi girki" dasauri tafito daga jikinshi tace "eh nayi girki muje Kaci" takama hannunshi zuwa dinning two kula yagani kujera tajamai ya zauna ta bude rice and beans tadafa white da miya dayaji naman kaza he loves plenty meal on table, yaga varieties daban daban this is just him but still she tried da happiness tashiga xubamai takawo gabanshi tasamai spoon sannan tawuce kitchen tafito da cres da bottle water takawomai zata bude cres din yace

"No just give me water nadena shan all this kind drinks make me fresh fruit juice next time" gyadamai kai tayi tace "to Sarki na" itama zuba nata tayi suka faraci abincin is good sundanyi nisa suna cin abincin ahankali yace "Haleema" dasauri ta kalleshi tace "naam" ijiye spoon yayi yace "| know kinji labarin but is my duty to tell you, nayi aure! I have a second wife sunanta Rashida, she happens to be yarinyar Baffa na Muji" abu taji ya tsaya mata awuya tadaure tace "eh nasani" ahankali yace "our marriage was not like the usual one but still kirubutamin anything kikeso I will give you" murmushi tayi tace "nagode mijina" ahankali yace

"presently tana wajen Ammi but a GRA zata zauna ita not here" wani kalan dadi Haleema taji cus tafison ita kadaine Sarauniya agidan nan gently yace "how many days kikeso nadinga muku?" Dasauri tace "kwana uku uku" Gyadamata kai yayi yace "okay!" Yayi shiru sai chan yace "banson tashin hankali, banson damuwa, banson gulma, banson makirci or anything, I want peace of mind! I will never intentionally hurt you to please anyone, same goes for my second wife" wani abu Haleema taji jin yanda yake addressing nata wani wife, ahankali yace "ke babba ce act like one okay, kome aka miki talk to me, report to me not to wasu" gyadamai kai tayi ahankali tace "In sha Allah bazan taba zama sanadin bacin ranka ba, and I pray Allah baku zaman Ipy, and I have good news" dasauri ya kalleta dan murmushi tayi tace "I've missed period dina for 7days yanzu, Maybe we are having a baby" murmushi yasakin mata mai laushi ahankali yace

"Allah ya tabbatar mana da Alkhairi" Dasauri tace

"zaka kaini hospital gobe" gyadamata kai yayi yace

"yes idan nagama da fada" wani irin dadi taji bana wasaba tahau murmushi shikuma ya tashi yace

"lemme go and shower" ganin yawuce sama bakaramin dadi hakan yamata ba, sama yawuce itakuma ta tashi agurguje tai clearing table din takai kwanukan kitchen tafito tawuce dakinta magungunan matan ta da Ita da Mamanta suna kashe kusan 5M aka mata tunda takoma gida ta dauka ta sha tafada wanka tafito ta shafa turaruka sannan tasa wata rigan bacci na net babu abinda ba'a gani aciki tabude kofa tafito tawuce dakinshi tabude kofa daidai yana fitowa daga bayi tsayawa yayi chak daure da towel a waist yabi jikinta da kallo yana tuna every single detail na jikin Rashida yanda ya tsareta da idanu wani dadi Haleema taji that means tafi matarsa komi wannan daya kafeta da idan dauke kai Riyad yayi da sauri yanama kansa fada not all fingers are equal wasu mata sunfi wasu mata wani abu so Haleema is beautiful just the way she is, she don't have to have body like Rashida wucewa yayi wajen kayan shafansa yashiga shafe shafe tabaya Haleema tazo ta rungumesa tana mannamai boobs cus tasan yanda yakeso tace "do you need any help yallabai? Assistance dinka is here" tai maganan tana tura hannunta akasa ta cikin towel dinshi tadaura akan dick dinshi, dan lumshe idanu Riyad yayi yace "are you sure? Is that's assistance job" matse jikinta tayi a nashi tace

"I just happen to miss that particular something" murmushi kadan yayi yadau turare yafesa yanajin yanda take tabashi sannan yajuyo yataho gadon dasauri tasa hannunta ta kashe wuta taja towel nashi ta yar tashiga cire riganta ta yar wurga ta gadon kawai Riyad yayi atleast yabata hakkin ta, yashiga in between legs nata yana turawa kawai Rashida tafadomai arai girgiza kanshi yayi yanaso ya kore tunaninta but yakasa, ahankali yafara hitting nata yana tuna yanda na Rashida ke restricting movement nashi but this pussy kam he moves freeely acikinsa, he was just remembering moments nasu soyake yaji abinda yaji ajikin Rashida ajikin wata hakan yasa yafito ya linke Haleema kaman yanda yama Rashida itama, yafara hitting nata pat! pat! Dakin keyi ashedai ya wahalar da Rashida ihu Haleema tayi tana tureshi da karfi har saida yakoma bayi tace "me martaba zaka kasheni har magaifata nakeji, idan inada ciki ai saikasa nai bari, you are too long I'm feeling you inside my placenta wlh nagaji dan Allah ka barni haka" gyadamata kai yayi 

sai kawai ya kwanta anatse yace "play with me nakawo" hannunta daya tasaka tafara wasa da dick din almost 30min yaki kawowa tama gaji bata iyayi da kyau, ganin takasamai kaman yanda Rashida tamai takama kanshi rannan yasa kawai ya karbi dick din ahankali yace "it's okay sleep" dasauri ta shige jikinshi ta kankameshi ko 5min batayiba tai bacci, shikuma yatashi yabude bayi yashiga ya sakinma kanshi shower gindinshi amike wih kaman Rashida tayi bewitching nashi he terribly wants her Kamal dick nashi yayi gangan dakemai ciwo gashi be iya soapy ba da kyar ya lallashi kanshi yayi wanka yafito daga bayin kawai yazo ya kwantar yayi bacci.Yana zaune a fada kawai yaji gabanshi na faduwa hannunshi yadaga yakalli agogon hannunshi yaga

11:45AM there's still hour plus kafinsu tashi, kasa natsuwa yayi sai fadomai Rashida take arai which is so unusual sallaman mutane fada yayi yafito fadawa na binshi abaya wayanshi yaciro kawai sai yayi dialing number Ammi dake wajenta amman har yagama ringing ba'a dagaba, wucewa flat din Ammi yayi yashigo talon Ammi na magana da Munir suka ganshi zama yayi yanayinshi yasa Ammi ta taho wajen tace "lafiya naganka wani iri ko bakada lafiya ne"? Kallonta yayi kafin ahankali yace "Ammi I feel uneasy wih, I don't know why" anatse tace "kayi azkar na safe?" Gyadamata kai yayi yana kai hannu yana bubbuga heart nashi dasauri Ammi tace "bani ruwa Munir kaga" da dan gudu Munir yakawo ruwa daga dinning karban ruwan Ammi tayi tabude tana kallon Riyad din still da yanda yakeyi kaman zuciyansa zai fashe yafito, fatiha kawai ta iyayi cikin ruwan takai bakinshi tace "sha" ahankali yakai ruwan bakinshi yadan kurba saikuma ahankali yace

"Ammi Rashida!" Cikeda damuwa Ammi tazauna kusada shi saikuma ta rungumeshi da sauri ajikinta tana shafamai baya tace "Riyad calm down calm down, kace Innalillahi wa innailaihi raji'un" ahankali Riyad yace "Innalillahi wa inna'ilaihi raji'un" sai alokacin yaji natsuwa ya shige shi Ammi ta dauki dayar wayanta tai dialing number wayan dake hannun Rashida kafin tace "tashi kuje school din kaida Munir tunda you feel troubled, Munir kuje" tashi Riyad yayi yabi bayan Munir Ammi tabisu da kallo kafin ta zauna sai itama kawai taji tadamu tacigaba da kiran numberta but still Rashida bata dagawa.

Wuraren 12:20 sukakai hospital din gaban hall daya jiyeta dazun yayi parking daidai student na fitowa

Maimoon itama tafito looking so worried ga waya ahannunta tana karawa a kunne alamun kira take da sauri Riyad yabude kofa bai damu da daliban dake fitowa ba yayi wajen ganinshi yasa tacire wayan daga kunnenta da sauri tace "laaa ina yini" bai amsa maganan ba yace "where's Rashida?" Dasauri tace "wlh nima ita nake kira na nemeta har mosque bata wajen gashi test din nan damukayi batai attending ba" faduwa gabanshi Riyad yashigayi da sauri Munir yace "but when last did you see her" cike da damuwa tace "after 10 bayan mun fito daga last test munje common room ni da ita, we spoke she remembered Mama and went out" nima nabita na dauka mosque ta tafi but bata mosque duk inda nasan zan ganta ban ganta ba so I thought ta koma gida nema since ina kiranta bata dagawa" bubbugawa kan Riyad yafara sai kawai yajuya kaman wanda yasami tabin hankali yace "Munir I need to see the chief security na this hospital, 1 need to report my wife missing, she might be in trouble, she's a small girl she's...." dasauri Munir ya rikeshi yace "Riyad calm down" "don't tell me to calm down!" Riyad ya dakama Munir tsawa da saida attention yadawo kansu yace "I told you she's in danger you're asking me to calm down banga matata ba" taruwa aka farayi awajen wasu security suka fiffito da uniform ajikinsu harda mutane ana tambaya meya faru Munir ya sanar dasu Riyad yawuce sama direct CMD office.

Dudda baisa kayan sarki ba normal kaftan ne ajikinshi direct yashiga office din CMD yace "ranka shi dade barka da safiya" muryanshi na rawa sosai yace "i want to check CCTV naku ina neman matana" CCtv room aka wuce suka shiga harda Munir da CMD na hospital din da ko'ina daga hall da Rashida tafito aka fara tracing nata zuwa dajin dataje wajajen babu camera amman wani van dake binta abaya gray Riyad ya nuna security yace "1 think muje inda mukaga tayi" duka su fitowa sukayi 

awajen yasa Riyadh yayi wajen da gudunsa ya taugunna daidai zai dauki jakan natane yaga jini akasa ga pen nata guda biyu datake makalawa jikin aljihun lab coat nata rawa hannunshi yafara CMD yace "call the police"

Yanda Riyad kawai yaduka jikinshi na shaking yasa hannu ya dangwalo jinin ya kalla jikinshi na bashi jinin Rashida ne yasa jikinshi yafara rawa idanunshi har kukkulewa suke, dasauri Munir yayi kanshi yana dagoshi idanunshi juyawa suke kawai hakan yasa Munir yayi gefe dashi yana kokarin yama dagashi but kawai ya sumema Munir, arude Munir yace

"help me" dasauri aka dawo kansu tayashi rike

Riyad sukayi har zuwa wajen mota yasashi a mota yana watsamai ruwa yadau wayanshi yashiga kiran Ammi yana sanar da ita kai tsaye Ammi takira Muji ringing daya yadaga ahankali Ammi tace

"something happen Rashida is in trouble" zumbur ta mike tace "meya faru Munir"? Fadamata komi Munir yayi dasauri ya katse wayan Ammi tashiga kiran Buba shima kafin itama tafita tashiga mota sai hospital din.

Ahankali yake bude idanunsa kanshi na daukan ringing yana kallon saman dakin da drip daya gani yana shiga hannunshi da sauri yatashi yana cizge ruwan hannunsa baidamu da jinin da hannun keyi ba yawuce kofa da sauri Ammi ta sallame salla ta tashi takama hannunshi tace "Riyad ina zaka?" Juyowa yayi yace "Rashida Ammi" dasauri Ammi tace "zoka zauna kaji" kasa motsi yayi jawoshi tayi yabiyota ahankali zaunar dashi kan gado tayi tace

"Riyad kasan karfe nawane yanzu is 3:00AM nadare tun Rana you were unconscious" Ammi tai dan shiru tace "ka tattara hankalinka kabani cus kowaye yayi aika aikan nan anaso aga kadawo haka ne kaman wanda baida cikakken lafiya" still kallon

Ammi yake anatse tace "da su Baffan ka, harda yan uwanka ma da Buba da yan sanda da hospital din at large are on the case, an dauki number license plate din don tracking but it's fake, duk wani investigation da za'ayi anyi babu wani lead" runtse idanunshi Riyad yayi sosai jikinshi yafara rawa Ammi ta rirrikeshi tace "police sunce suna suspecting kidnappers ne wai sabida anga matarka ce da kalan motocin dake kawota school, but ajira within 48hrs for calls na kidnappers din idan basu kiraba sai anemi next course of action".

Runtse idanunshi yayi da karfi yace "Ammi I can't sit still for 48hrs she's hurt Ammi, l've seen her blood, Ammi Rashida is in danger how can I stay still" tashi zai sakeyi dasauri Ammi tarikeshi tace

"tsaya to kaga nakira Buba" dasauri tadauki wayanta dan bataso yafita he doesn't look okay, ringing daya Buba yadauka cikeda damuwa tace

"Buba kaga ya farka yakijin magana na" dasauri Buba yace "bashi wayan" karban wayan Riyad yayi anatse uba yace "Riyad idan har ayar Al'Qur'ani gaskiya ce! Rashida zata kubuta daga hannun duk wani mugu dayake nufinta da bakin nufi ina mai tabbatar maka, wih wih ko sunso cutar da ita bazasu iyaba, ban runtsa ba addu'o'i nake, abinda nakeso dakai kaima jekayo alwala kahau kan dadduma ka gayawa Allah bukatunka Rashida zata fito" gyadama Buba kai yayi ya ijiye wayan yawuce bayi kayan jikinshi yacire ya kunnama kanshi shower kaman zai haukace yakeji kaman yayita ihu wanka yayi yadaura towel yayi alwala yafito ganin baiga 

 Ammi a dakinba vasa vashida closet nasho ya sakajallabiya yazo yahau kan dadduma.

Gently take bude idanunta dake juyawa sosai tanajin gaban goshinta lema lema na jini, inda take duhu sama sama takejin magana dudda bata ganin daga inda ake maganar ko inda maganan ke tashi.

"Mom, Mom dan Allah kar akasheta kawai dai aje a wurgar da ita chan wata uwar duniya" sai kuma chan taji maganan namiji yace "kashe wayan Haleema batada hankali" sai kuma taji wata muryan mace again tace "wat do we do with her"?

Daidainan idanunta suka kara lumshewa.

Ahankali ta zare P-cap din dake kanta Waziri yace

"wai ya akayi aka sako ki ne Hajara"? Murmushi Mom tayi tazauna akan plastic chair dake wajen tace "idan ba'a sakoni ba ai Babana baicika attorney general na Nigeria ba, banyi any crime ba, sannan banyi confessing anything kaman Jummai ba, sun duba footage din, basu da wani abu to hold me for, no evidence, law works with evidence, abinda Jummai tace game dani were baseless accusations, itako Jummai har cleaner data bama poison an ganota, cus police sun bincika every single mutum daya shiga dakin matan that day, akaga cleaner itane last person and tafito dawani bottle water a hannunta aka kawota tayi confessing poison ne, aka sake tracking abun back to car parked inda tafito daga motan Jummai ga plate number da komi, next week za'a kaisu court niko 2days nayi aka bada belina Papi paid everything nafito muka wuce Abuja since, I'm sure yaronchan (Riyad) bai saniba cus he was busy da amaryansa da uwarsa" Mom ta kwashe da dariya tace "but I promise he will lose everything that is important to his life starting from this girl" duk kallon Mom suke tace "I wanted na samata HIV kaman mamanta but mai HIV nan dana sani na nemeta wai tarasu" ta yatsine fuska sannan takallesu tace "the only reason yasa zanbar Riyad sabida ku da diyarku ne Wallahi!" Ahankali Waziri yace "godiya muke Hajara" ahankali tace "zan kashe yarinyar nan, na kashe Ammin sa! Na kashe Munir! Ta yanda dolensa yadawo dani mamarsa na zama mahaifiyar mai Martaba daya tak!" tai murmushi tace "ku shigo!" Wasu manyan gardawan maza ne guda biyu suka shigo wajen ta nuna musu wani lungu dasuka zubar da Rashida tace "jeku duba idan ta margaya ku dauketa kuje ku zubar idan bata margaya ba ku karasata" wucewa wajen sukayi

Sukasa hannu suka jawo kafafun Rashida da labcoat dinta da yariga yakoma blood sukakai hannuwansu hancinta jin bata numfashi yasa suka dago suka kalli Mom dasu Waziri sukace "ta mutu Hajiya" wani kalan hatsabibin murmushi Mom tayi tace "ku kawo tabarma ku nannadeta aje a zubar" dauko tabarma daya yayi yakawo wajen ya warware suka daga Rashida da hannunta ke lilo suka sata aciki suka nannade daya ya dauketa yasa awuya sukai waje da ita Mom ta kalli Waziri tace "I hope I've solved problem naku" Waziri yace "kinyi Hajara" Mommy Haleema ta zube awajen tace "uwar dakina Allah dai yajamiki tsawan kwana, kin share mana hawayen mu kin tsayama Haleema, godiya muke" murmushi tayi tace "kuwuce kutafi" wucewa sukayi.

Suna fitowa wajen cikin tsakiyar dajine da babu kowa sai machina dasukai parking gaban yar gidan dasuke ciki tafiya suke da sauri da sauri daya yarike kasan tabarman daya yarike sama har sukakai wajen wani babban kogi dayan yace "mesa zamu aka kira da Baaba yace "dayake kanada shovel dole kahaka" yayi maganan yana fincikan tabarman daga hannunshi kawai ya wurga cikin ruwan duk suka tsaya suna kallon rafin ganin tabarma kadaine yadawo saman ruwan babu yarinyar yasa suka juya sukace suka wuce.

Dirkowa wani bafulatani yayi daga daya daga cikin bishiyoyin dake ta dayan side of the river, dan tsohone haka dayar sandarsa a hannu hakama wani dan yaro ya dirko daga wata bishiyan wanda bazai wuce shekara goma ba yace "Bap...." hannunshi tsohon yasa dasauri yadaura kan bakin yaron alamun karyayi magana, sannan suka shiga tafiya suka gangara kasa wajajen rafin kafin Baban yabashi sandar yaron ya karba yarike, Baban yayi tsalle yafada cikin ruwan kusan 2min yayi saigashi yafito rikeda Rashida da ruwa ke tsayaya daga ko'ina na jikinta tsohon yajawota bakin rafin yana duddubata saikuma yashiga bubbuga mata ciki amman ko gezau kafin yarike hannunta gam na kusan minti daya sannan yakalli yaronshi yace

"kwabe riganka kabani Iro" dasauri yaron yacire yakawo yabama Baban ya karba ya yaga sannan yadaga kan Rashida ya daure kan gam gam sabida jini yadaina zuba, sannan yadauketa da kyar yana nishi dan ya tsufa ba karfi yafito yayi wajen shanayensa yadaura Rashida akan daya sannan yashiga kadasu suna tafiya yaron yace "Baba bata mutu ba"? Dasauri Baban yana gudu gudu yana kada shanun yace "jijiyoyinta na motsi" da sauri sauri gudu gudu suke kada shanayen, kusan tafiyan awa daya sannan sukakai wata karaman karkara ta yan fulani, ga bukkokin su ahaade in circles dabazasu wuce 30 ba, duk inda zasu wuce yangarin biyosu suke ganin sun kawo wata akan shanu har zuwa kofar gidansu duk suka taho suka tayashi aka sauko da ita aka shimfide kasa, Dattijon yace

"ina Hawaro"? Da sauri aka hau kwalama Hawaro kira. "Hawaro, Hawaro" chan saiga wani dan matashi yataho yana sanye da kayan Fulani harda hula da sanda a hannunshi ya bullo daga daji, mutumin ya nuna Rashida dake sheme a kasa yace

"kaga yanzu mukaga wasu miyagu na jefata a rafin buluduwa, naga kaman likita ce kaga kayansu ajikinta, kaga tasamu lafiya kaida ita saiku zama likitocin garinmu" dukawa matashin yayi ya dago kan Rashida yana warware daurin da Dattijon yamata, yadaga gashinta ya kalli ta wajajen keyan dayaga ya tsage sosai da sauri ya maidata ya ijiye yatashi saiyahau gudu kaman tsuntsu ya shiga daji yana ihu a izamin garwashi akawomin, wasu ganye ya tsinko sannan yafito ya shiga daki yafito dawasu kananun wukake da allurai da zare yana zuwa ya jiyesu acikin gareashin da aka kawomai dan su

kone alluran sannan yaduka yadauki dutse yana daddaka ganyen yana gamawa yatashi yadauki alluran dake wutan ya goga a jikin dutse mai tsafta sannan yasake warware zaren yace "riketa Modibbo" dago Rashida Dattijon yayi yarike shikuma yazo ya dage gashinta yasa wata wukar da itama ya kona awuta ya aske gashin wajen kadan sannan yafara mata dinki kusan stitches guda 6 sannan yadauki ganyen daya daka ya mammanna awajen sannan yakoma daki yafito dawani kyalle yashiga daurawa a kanta yana zagayewa ya daure tamau sannan yakama tafin hannunta yasa yatsushi biyu aciki ya kama sannan yafito da yatsun yadaura a julyan gefen wuyanta saikuma chan yabude kwayan idanunta ya kalla kafin yakalli Modibbo da sauran mutanen garin dasuke tsaye sun zagayesu yace "juna biyu ke gareta ai Modibbo da bazai wuce kwanaki sha hudu ba!" Shiru duka mutanen karkaran sukayi kafin yace "sa mata su kaita daki achanza mata kaya kar sanyi yashiga kasusuwanta kar abin cikinta ya shiga hatsari ruwan rafi baida kyau ga mai karamin danyen gudan jinin ciki" dasauri kafin Modibbo yace wani abu da matansa da sauran matan garin sukazo suka dagata cikeda care sukai ciki da ita Mazan kuma suka jaye gefe dan shawara da maganan yanda za'ayi. 


EPISODE 73 

Duk tsaitsaye sukayi kusan Moddibo shine babba agarin, so ana jin maganansa sosai, shi likitan Hawaro ne yace "Modibbo yaya za'ayi yanzu?

Yanda takeda juna biyun nan da mijinta kenan yakamata anemo yan uwanta" dasauri daya daga cikin jama'an yace "binni zamu shiga muje wajen yan sanda mu fadi abinda yafaru" dasauri wani daga cikinsu yace "amman kuma likitoci nada amfani ga al'umma mesa bazamu barta taji sauki ta taimaka mana ba da likitancin zamani, takoyama Hawaro abubuwan zamani na lafiya amatsayin tukuicin cetota da mukayi saita tafi, yanzu rayuwanta na cikin hatsari idan mukaje muka fada mutanen sukazo har nan suka kasheta fa"? Sai abun yakoma wannan yafadi nasa wanchan yafadi nasa gyaran murya Modibbo yayi yace "ku dakata" duk shiru sukayi suna kallonshi, cikeda dattaku yace "na farko dai rayuwan yarinyar nan nacikin hadari gata da kankanin ciki tareda ita, idan kunga gardawan dasuka daukota a tarbama a hadamu mu goma sannan za'a samu daya" yasake yin shiru sannan yace "abarta tafarfado muyi magana da ita da kanmu sannan tafadi mana waye mai gidan nata saimuje da kanmu mu shiga binni mu nemosa yazo ya dauki matarsa gudun kar miyagun su biyota, idan tanaso zata iya koyama Hawaro likitancin zamani saitayi idan bataso saisu tafi kun yarda?" Atare kowa yace "eh" hakan yasa suka zauna suka shiga zantawa yana kara basu labarin yanda yafada kogin.

**

Wasa wasa yau kwana 7 babu Rashida babu labarinta kowa yakasa gane kan Riyad, labari yabi ko'ina afada Sarki na neman haukacewa sabida anyi kidnapping matarsa haryau kuma kidnappers sunki kira, Haleema karan kanta saita fara regretting komi cus attention datake nema wajen Riyad ma tarasa, he's not even himself, komi ya tsayamai chak baya  baya gane komi, sannan komi no fada ya tsaya allbecause of shegiyar Rashida.

Ammi dasu Buba da Muji da babu inda bai shigaba har wajen yan sanda saida yaje yaga koto Jummai ce yaga tana kulle but ansaki Mom yazo yafadi Riyad kanshi baya wajen su Ammi ke mamakin yanda aka saki Mom, an baza hotunan Rashida ko'ina da news da tv ana cigiyanta, Riyad yadawo abin tausayl.

Ahankali take bude idanunta dasuka mata shegen nauyi tana kallon saman bukkan dakin kafin gently tayi yunkurin tashi taji sharp pain akanta dayasa ta daddage ta kwala uban ihu. "Wayyyyyoo kaina" da gudu aka shigo dakin wata yar matace sanye da kayan fulani yaro goye abayanta tana kallon Rashida dake ihu sosai tana kokarin cire kyallen da aka daure mata kan dake mata shegen azaba, da sauri matan takama hannunta tarike tace "yakuri, sannu sannu, Hawaro yace kar abari ki kwance idan kin tashi saiya zo dakansa yakuri" fashewa da kuka sosai Rashida tayi tana rawa da fuskanta tace

"kaina zafiliiii" daidai nan Hawaro ya shigo da dan kofi a hannunshi tareda Modibbo ya duka ata bayanta yakai hannu yana bude kyallen kan yakai cup din yanaba matan ta karba tace "ungo sha maganin zafin zai dena" bakinta takai kofin tana lekawa datagani baki saikuma tace "menene shi?" Dasauri matan tace "magani"? Dasauri Rashida tace

"menene magani?" Dasauri dukansu suka kalleta saikuma matan tace "shine zaisa kan yadena zafi"

Dasauri tabude baki aka samata kofin ta kurba kadan tacire fuska tana yatsine fuska sabida daci daidai lokacin Hawaro yashiga kankare maganin daya shafa akanta daya bushe, ihuuu tayi zata yunkura ta gudu, da idanu yamusu alamu su riketa suka riketa yahau cirewa tana ihu sosai tana kuka, haka yacire ya maida wani madani wajen sannan suka saketa yadauki wani kyalle ya zagaye kan dashi, Modibbo yabata nono a kwarya yace "sha" kallon nonon tayi saikuma tana goge fuska tace

"menene shi?" Ahankali yace "nono sha" karba tayi takai bakinta ta kurba kadan saikuma ta ijiye ta shiga kallonsu yanda suke kallonta suma kaman sun sami tv zafin kan yasoma rayuwan mata, ahankali Modibbo yace "ya sunanki?" Bakinshi take kallo saikuma ahankali tace "sunana?" Saikuma tashiga kallon jikinta tanabin fararen kayan fulani dake jikinta da kallo takai hannunta ta taba kanta kafin takara kallonshi tace "sunana" saikuma tace

"sunana" ijiyan zuciya Modibbo yayi yace "kin manta sunanki" dasauri tace "sunana" tashi

Modibbo yayi kawai yafice waje dasauri Hawaro yabiyoshi, Modibbo yakalleshi yace "zan dauki Liti, da Anas mutafi binni muje wajen yan sanda mu bada sanarwa, banson na je da ita, amman kai ka zauna dasu sabida kar jikinta ya rikice bari muje" gyadamusu kai yayi yawuce su uku suka tafi daga kauyen zuwa wajen gari kusan tafiyan machine awa daya, sannan sukahau mota dazai kaisu Kano about 2 and half hour journey in total, the nearest police station dake nan tashan dasuka sauka suka shiga, ihu yan sanda suka musu ganin su wani kala. "Me kukezo yi nan"? Ahankali Modibbo yace "munzo fadan wani abune daya faru sirri ne gaskiya opisa" wani kallo dan sandan yamusu yace "fada ina jinka" kallon wajen Modibbo yayi saikuma yace "gaskiya muje daga ciki" dan jim dan sandan yayi saikuma yace "okay muje" sukai ciki wani office yabude musu suka shiga yazauna yace "ina jinka" anatse Modibbo yashiga koro bayani sannan yace "yarinyar ina kyautata zaton likita ce tana sanye da fararen rigan likitoci mun batta chan kauyenmu sabida kanta dakuma bamusan ko za'a sami mijin nata ba Ambato rigan likitoci dayayi yasa dan sandan yace

"kujirani" yawuce yafita office na ogansu yawuce ya sanar dashi komi da sauri yasa akawosu office nashi, shigo dasu office na Ogan yayi exact bayani sukamai wayanshi yaciro dasauri yaciro hoton

Rashida yanuna musu yace "itace?" Atare dukansu ukun sukace "eh" wani bala'in farin ciki dan sandan yayi promotion guaranty kenan, dasauri yashiga kiran asalin ogansu kwata kwata ya sanar dashi komi.

Daga Ammi har su Buba dasu Gwaggo da Muji duk an taru ana kan Riyad da aka kasa gane kanshi

Sarkin gida yabuga uwar sallama.

"Assalamuuuuuuuu Alaykum, nazoma da sarkina babban gagaruman sako amin izini" kallon kofan Muji yayi yace "shigo" dasauri yashigo yana gyara malum malum yayi wajen Riyad dake kwance kanshi akan cinyan Ammi gashinan ne kawai ya rame looking sick sosai, zubewa yayi inda Riyad yake da waya a hannunshi ya nuna wayan yace "yanzun nan commissioner na yan sanda yakira masarautan nan" da kyar Riyad yajuyo da kanshi yakalli sarkin gida, sai kawai sarkin gida yafashe da kuka yace "Mai Martaba ana kyautata zaton anga Sarauniya Rashida!" Wani kalan zabura Riyad yayi yatashi yazauna yana kallon Sarkin gida yana kokarin kara gasgata abinda yaji, Muji yace "mene mene? An ganta? Anga Rashida? Aan ina"? Sarkin Gida na kuka yana kallon Riyad yace "wasu bafulatanai guda uku sukazo offishinsu na tashar riya sukace sun tsinceta sany da kayan likitoci ajikinta an nuna musu hotonta sunce itane" wani irin tashi da Riyad yayi sai kawai yadauki key mota daya gani kan table yayi waje da gudu biyoshi kowa yayi harda sarkin Gida da Ammi dake neman lullubi da Gwaggo da Muji yarike tana kuka sosai duk aka wuce aka shishiga mota Sarkin gida na nuna hanyar police station din da akace suke, suna kaiwa parking sukayi Riyad yasauka ya shiga police station din da gudu kowa yabiyoshi Sarkin Gida na ihu "gafaradai gamai Martaba" ana kallon Riyad da babu rawani ko alkyabba ajikinsa.

Babban su ne yataresu yanuna yan fulanin yana farin ciki yace "gasunan mutanen Ranka shi dade dasukazo mana da bayanin" kallonsu Riyad yayi dasauri yayi wajen babban cikinsu bakinshi har rawa yake yahada hannayenshi biyu yace "dan Allah ku kaini wajen Matata!" kallonshi duka suke

Moddibo ya gyadamai kai yace "bismillah mu, muje Alhamdulillah tunda an sameku" yan sandan ma suka dauki mota guda, Modibbo yashiga motan Riyad, sauran suna motan yan sanda aka dau hanya Allah yasa Munir ke tuki cus Riyad can not even drive 2hrs suka bata a hanya motocin nasu ma basu karasa shiga kauyenba haka duk suka sassauka akahau machine harda Gwaggo tace baza'a barta a mota ba.

Har kauyen nasu kafin sukai wajen bukkan duk akai parking suka sassauka dagakan machine yara da manya na zuwa suna kallonsu ganin fuskokin baki, chak Riyad ya tsaya yana kallon Rashida dake zaune kan tabarma agaban bukkan matan Modibbo tana sanye da kayan fulani farin rigansu da zani, babu dan kwali akanta amman an nannade kanta da kyalle har zuwa goshinta, ga kwarya daban daban na abinci agabanta kusan guda biyar wayanda matayen kauyen duk suka kawo mata ganin takicin abinci har yanzu gashi tuntuni ta tashi kuma yunwa takeji, daya tuwo da miyan kuka, daya usulin awaran nono, daya kuma shinkafa da miyan ja, daya namomi cike ne da aka soyamata da manja, sal dayan kwaryan kuma fura, sai kallon abincin take,ayanda take kallon abincin kasan kaman batada lafiyan kal.

Nunata Moddibo yayi da hannu daga inda suke tsaye wajen masu machina da akace su jirasu yace

"gatachan" kowa kasa motsi yayi har Buba, cikin muryan kuka Gwaggo tace "meya sameta naga an daura mata tsumma aka?" Ahankali Modibbo yace

"dana cirota daga ruwa kanta afashe jini na zuba daga kanta, to tafarka muna tambayanta ya sunanta kaman ta mance komi banda haka kuma akwai juna biyu ajikinta yanzu zaiyi sati uku!" Dawani irin sauri Riyad ya kalleshi hakama kowa ke kallonshi jin abinda ya ambato ganin yanda suke kallonshi yasa Moddibo yadaga hannu yakira Hawaro dake cikin tarin jama'an yan kauyen dake kakkallonsu yace

"Hawaro taho" dasauri matashin yazo Moddibo ya nunashi yace "ni kawai na cetota daga ruwa ne amman ga asalin wanda ya ceci rayuwarta dana halittan datake dauke dashi nan Hawaro" yadan sauke ijiyan zuciya yana dafa Hawaro yace "yasan magunguna shine ke bamu magani idan muna ciwo, ya gaji magani daga kakanninsa, Hawaro gayamusu meke damunta".


EPISODE 74

Cikin hausansa da bata fita sosai yace "¡iee to!

Kanta ya bugu sosai, ta zubar da jini sosai dudda ina bata ruwan ganye dake kara jinin amman dudda haka bai ishetaba jinin sosai batada karfi zatana dinga yawan sumewa, buguwan da akama kanta yasa ta mance komi amman bazata dauki lokaci ne zata warke, komi zai dawo mata, ruwan data shiga ciki yasa sanyi ya taba abin cikinta amman tagama magungunan danake bata za'a dace, shima kan za'a dace da izinin Allah" kowa shiru yayi suna kallonta barin Riyad daya tsareta da idanu yana kallon yanda tadauki naman takai bakinta ta tsotsa tafito dashi kuma ta ijiye sai chan tasa hannu ta dauki wara tana kallo sai ta ijiye saita dangwalo nono takai bakinta tana tsotsan yatsanta, ahankali Riyad yafara tafiya kowa binshi yake da kallo har zuwa inda take gently ya tsugunna gaban tabarman yana wani irin kallonta, wasa take da abinci but jin mutum agabanta da kamshin turare mai dadi daya daki hancinta yasa tafara kallon tundaga kafanshi yana sanye da bakin crocs da dark brown yadi mai bala'in kyau sannan tadago kanta ta kalleshi hada ido sukayi ta tsareshi da idanu kaman yanda ya tsareta shima da idanu, wani irin lankwasa kai tayi tana kallon fuskanshi kaman taga abinda bata taba ganiba tanabin tundaga idanunshi har zuwa dogon hancinshi da kallo down to his lips, wani irin kyau yamata wanda ya banbanta da sauran mutanen yan garin har kayan jikinshi ma, saikuma tadauki kwaryan naman dasauri tasa hannu taciro nama daya ta mikamai, kallon naman yayi sai kawai hawaye ya cika idanunshi, ahankali yasa hannu ya amsa murmushi tamai daya bayyana duka hakoranta jin sahun tafiya yasa dasauri tajuyo takalli sauran mutanen dasuka taho, Muji ta hango yana kallonta shima rikeda soda a hannunshi na Gwaggo dawani irin sauri tashiga kokarin tashi tasa hannunta duka biyun tana kama kanta alamun yana mata zafi tana yatsine fuska dasauri Riyad yatashi wucewa tayi dasauri tana tafiya ahankali kowa na kallonta har gaban Muji hannunta tasa da sauri ta karbi soda a hannunshi tashiga kokarin budewa takasa saikuma tasake kallonshi tabashi, karba yayi ahankali muryanshi har rawa yake yace "nabude miki? Okay zan bude miki" dasauri yabude mata karba tayi takafa abakinta tass ta shanye tana lashe baki tasake saka empty bottle din abaki tana girgijewa saikuma ta kalli Muji dayakai bayan hannu yana goge idanunshi ahankali tace "bani" da sauri takai hannunta takama nashi tana budewa tana neman drink din ashagwabe tace "banimmili" wih duk yanda Muji yaso yadaure saiya kasa yafashe da kuka, he can't believe for the first time yau yanajin dumin hannun yarsa da tun tana ciki ya kada uwarta, ganin yana kuka yasa ta tsaya tai shiru tana kallonshi saikuma tafashe da kuka takai nata hannun tana gogemai hawayenshi Buba yataba bayanshi alamun yayi shiru, daurewa yayi yadena yace "nadena kuka to kinason soda?" Yanuna goran hannunta gyadamai kai tayi da sauri tana dakatar da kukan yace "to mukaje mota zan baki" ahankali tace "mota"? Gyadamata kai yayi yace "eh mota" juyawa tayi tana fadin mota mota mota mota mota tawuce wajen tabarman taxauna ahankali, tana kallon Riyad data sakemai murmushi tace "mota, mota, mota, mota" saikumai tamai murmushi again, kafin tazo dasauri takama hannunshi tarike tana kallon agogon dake writs dinshi saikuma takalli fuskanshi tace "mota?" Hannunshi Riyad yakai ahankali for the first time yadaura akan fuskanta dasauri takalleshi ta tsare idanunshi da kallo dataga suna tara hawaye, tace "sunana mota".

EPISODE 91

Buba ne ya iya katse shiru da akayi ana kallonsu yace "yamma na gabatowa, Mun gode da taimakon dakuka mana, baxamu taba mantawa da taimako da hallacin ku ba" duka kudin dake aljihunshi yaciro, shima Muji haka, duk suka ijiye Moddibo yace "a'a" Buba yace "dan Allah ku amsa" Modibo yakalli matarsa yace "kawo kayanta Hawaro kawo magungunanta" shigowa sukayi suka kawo Ammi takarbi maganin Hawaro na mata bayani, gently Riyad yakama hannunta vace "muie gida" "gida?"Gyadamata kai yayi yatashi amman taki tashi, ganin haka yasa Muji yace "muje mota nabaki soda" yanuna mata goran sodan, da sauri ya tashi ta kalli Riyad tace "soda" gyadamata kai yayi yace "muje mubaki" yana rike da hannunta suka taho har zuwa wajen machine, ahankali Riyad ya kalli Mai machine yace "bani key saika hau na wani kabiyomu" dasauri Mai Machine din yabashi sukuma yan sandan sukace muje ku nuna mana inda kuka ganota, hawa machine din Riyad yayi yajuyo yakama hannunta yarike kafanta yayi guiding nata tahau hannayenta yakama yasa ajikinshi dasauri tai lamo abayanshi kamanyar baby tana shakan kamshin dayake dakemata dadi har zuciya, yadan kallonta sannan ya kunna machine din duk sukaja har zuwa wajen motocinsu suka sassauka da sauri Muji yabude mota yadauko drink yabata karba tayi sai tahau tsalle tace "yayyyyy" riketa dasauri Riyad yayi dasauri ta kalleshi saita bashi drink din karba yayi yana mata murmushi yabude bayan motan yace

"shiga" shiga tayi yazauna yabude yabata sannan yashiga shima ya zauna Munir da Sarkin Gida suka shiga gaba akaja motan sai Kano.

Ko nisa basu yiba ta Shanye drink din takalleshi tareda bashi goran tana turo baki kaman zatai kuka alamun she wants more, cikeda so yace "I will buy for you soon" tsayawa tayi ta kafe fuskanshi da idanu sai shima ya tsaya yana kallonta ahankali tasauke idanunta takalli agogonshi da sauri tadaura hannunta akan agogon tashiga shafawa hannunshi yasa sai ya kwance Rolex din yakama hannunta yashiga samata wani tsalle tayi tana kallon agogon sai rawa take da kafa chan kuma saita kwanto jikinshi tana hamma kallonta yayi yace "kinajin bacci?" Lumshe idanunta tafarayi, ahankali yakai hannunshi kan waist dinta dasauri ta kalleshi jinjikinta yamata wani iri daban da yanda takeji since, batare daya damuba yasata ajikinshi kaman yanda ake daukan babies da za'a shayar sai kallonshi take kafin gently ya rungumeta a kirjinshi ya kankameta yana sauke ijiyan zuciya lamo tayi ajikinshi within few minutes bacci yayi gaba da ita. Kiss Riyad ya manna mata gently a forehead kafin ahankali yadaura hannunshi saman cikinta Hakkika Allah shine mai azurta bawansa da haihuwa aduk sanya yaso yakumaga dama! Sex din dayayi da ita that was unplanned and out of anger but Rashida got pregnant dashi, he slept with Haleema on so many occasions cikinsu harda ranakun ovulation nata but shiru babu ciki. Allah is the greatest of all mankind!!!

Babban private asibiti suka wuce da ita har lokacin da sukakai bacci take, daukanta Riyad yayi zai daura ta kan gado da aka kawo musu tabude ido, rirrikeshi tayi tana dirkowa daga gadon tafashemai dawani irin mugun kukan shagwaba tana shishigemai jiki shikuma duk yawani daburce wucewa kowa yayi suka shiga asibitin aka barsu ganin da Riyad kawai jininta yahadu.

Ganin haka yasa Riyad cikeda lallabawa yace "why are you crying" kallonshi tayi saikuma tasa kanta a kirjinshi tana rike riganshi tashiga makemai kafada, ahankali cikin lallashi yace "let's go inside kanki za'a duba dake miki ciwo" yakai hannunshi yataba kanta wajen ciwon hakan yasa itama ta taba kan nata tana kallonshi gyadamata kai yayi yama nurses din alamu da hannu sutafi sannan yarike hannunta tabishi ciki har lokacin tana taba kanta yanda yayi har office na

Dr dayasa kawai suka wuce wajen MRI nan ma da ihu da kuka ta shiga akayi aka fito da ita aka debi jininta akakai lab, daza'a taba kanta nanne Riyad yaga tashin hankali ba karamin zafi kan yake mata ba tadinga inu ahaka aka cire all magungunan aka mata proper dressing dan local stites din yayi aiki nan da nan aka kawo result her head its fine kawai short term memory loss ne dazai dawo with help na medication saikuma she's truly pregnant Riyad sai kallonta yake tana wasa da agogonshi daya daura mata a hannu, she's truly pregnant!.



EPISODE 75

Anatse Riyad yace "why is she acting like a baby?"

Dan murmushi Dr yayi yace "kowa da yanda memory loss ke zuwanmai, tamanta ita kanta wacece, yanda ake magana da sauransu, just manage her and make sure tasha maganungunan ta, zaku dawo next week, and make sure she's eating healthy she needs blood harda blood tonic a magungunan dana rubuta mata, she will be fine in sha Allah, zaku iya tafiya" gyadamai kai Riyad yayi yatashi daga kujera dawani irin gudu itama ta tashi takai hannunta takama nashi wannan karan ya kalleta ahankali itama haka, wucewa sukayi suka fice zuwa inda kowa yake ganin sun tattashi yasa dasauri tashiga bayan Riyad ta labe tana bubbuga kafa akasa tafara bori, magana yakeso yayi but yanda tahau buga kafa akasa yasa dasauri yajuyo ya kalleta wata patient dakecin indomie a takeaway rubber ta nunamai tana kuka tana rike cikinta bala'in rudewa Riyad yace "zakici indomie? Stop crying, stop stamping feet naki akasa haka is not good you are not alone, you want indomie wanchan?" Yanuna abincin, Gyadamai kai tayi, dasauri yace "let's go home namiki toh stop" yakama hannunta tabishi still tana waigawa tana kallon maicin indomie, mota suka wuce suka shiga Munir ya karbi takardan pharmacy yawuce saida a karbo sannan yadawo sukaja motan suka tafi gida suka dawo duka a side na Ammi suka sassauka

Ammi tashiga kwalama jakadiyanta data kira ta dafa indomie tun suna hospital da sauri tafito da plate mai kyau da indomie ke ciki hannu Riyad yasa ya amsa he hardly eats indomie amman yau yadeba yafara kaiwa bakinshi sannan yabata dasauri tasa hannu ta amsa tana daukan spoon ta deba indomie dasauri zatakai baki dasauri Riyad yarike hannunta yace "ita hot wait" raurau tayi da fuska zatai kuka dasauri Muji yace "akwai fanka agidan nan Munir?

AC nan kafin yasa abincin ya huce an dauki lokaci, she seems hungry"

Dasauri Jakadiyan Ammi tace "akwai wata yar fanka a dakinmu amman bama amfani da ita bari nakawo"

Dasauri tawuce takawo aka kunna aka saita a abincin sannan Riyad yasaki hannunta yace "ci to" dasauri ta debi indomie takai bakinta da sauri sauri takecin abinci sai yanzu takecin abinda cikinta keso kowa sai kallonta yake, kwai tadauka takai hanci dasauri tadauka tabama Riyad ahankali yasa hannu ya amsa tacigaba da ci, tasake daukan second boiled egg din daga zaunen tamikama Muji, dasauri yataho yasa hannunshi biyu ya amsa ahankali yana kallon fuskanta yace "Allah baki lafiya Rashida" murmushi tamai tacigaba da cin indomie ta tana kallonsu ganin duk sunacin egg din tasake musu murmushi, da Riyad da shi kawai takeso acikin duka mutanen, Ammi tabude magungunan dazata sha taciro mata tazo ta tsaya gefen Riyad dasauri ta kalli Ammi ganin Ammi na mikama Riyad abu yasa da sauri ta ijiye plate na abincin takama duka hannayen Riyad tarike tana makema Ammi kafada wai bazai amsaba, sosai abin yasa Ammi tai murmushi tace "to gashi ke amsa kisha" Ammi ta mika mata maganin kallon maganin tayi saikuma tajuyo ta kalli Riyad ya gyadamata kai alamun ta karba dasauri ta amsa takai bakinta tasa Riyad yasaamata bottle water tahadiye tana bata fuska duk sukai dariya Ammi tace "cinye indomie to" daukan indomie tayi tacigaba da ci atsaye kusada Riyad taki xama sabida kar Ammi tasake dawowa kusadashi, tass ta cinye which is not like Rashida that hardly eat, Ammi tace "zo muje kiyi wanka kiyi salla" sake makemata wuya tayi tana shigewa jikin Riyad da ahankali yakama hannunta yace "let's go" binshi tayi sukai stairs suna hawa sama Ammi na binsu abaya.

Da kyar ta yarda Ammi ta tayata yin wanka ana gamawa tafito daure da towel da gudu daidai tana fitowa tana zamiyewa dasauri Riyad yatareta ba wasa a muryanshi yace "stop running" dagota yayi yace "Ammi tafito tace kisa kaya" turo baki tayi tana nuna Ammi, Ammi tai dariya tace "nazama kawar fadarki ko, yakuri to zogashi kisa" ahankali Riyad yace "je Ammi is calling you" wucewa tayi Riyad yawuce yafita sauka kasa yayi duksu Buba sun Riga sun fita yafice shima dan zuwa flat bashi yayi wanka.

Salla yayi bayan yayi wanka yana kan dadduma wayanshi yashiga ringing hannunshi yasa yadauki wayan Haleema ce hakan yasa yakai wayan kunnenshi murya ciki ciki tace "ya jikin?" Ahankali yace "dasauki thanks" mahaukacin kishi ke damunta dantaji labari an ganta that means bata mutuba, duk zuciyanta ya lalace ya baci da dan fushi kan voice nata tace "ni ina bukatanka yau kwanan ka saman da bakwai baka kusance ni ba period yazo nagama but shiru kaki nemana" ahankali yace "I'm not in the mood for anything Haleema, good night" ya katse wayan, daidai wayanshi na daukan another ringing yadauka Haleema ne saiyaga Ammi dasauri yadauka kafin yayi magana ma yaji kukan Rashida bana wasaba dasauri yatashi dagakan dadduman Ammi tace

"kaga waikai take nema tana jikin kofan falo ta makale kaman soja munyi lallashin duniya ta maidamu shegu yanzu haka wai saita fita abude mata kofa" anatse yace "I'm coming" fitowa yayi har zuwa flat din Ammi yana bude kofan Rashida dake kuka sosai takalli kofan ganinshi da gudu ta rungumeshi, ahankali ya rungumeta back yace

"stop crying I'm here" yashiga patting back nata, dauke kai Ammi tayi daga kallonsu dago kanta yayi ya share mata fuska sannan yakama hannunta yace

"muje ciki" tsayawa tayi kikam ta makemai wuya alamun ita bazata shiga ciki ba ya kalleta kofa ta nunamai baki Ammi ta tabe tace "wuce kutafi tunda taki nan wajen, kaita wajenka, saida safe" adan kunyace ya sunnar dakai sannan yakama hannunta, kanshi akasa yace "Ammi adan bani hijabinta" cus ba hijabi ajikinta is just rigan bacci iya cinya ga ba hula.

Dogon hijabi Ammi takawomai tabashi karba yayi yana kallon yanda take kara shigewa jikinshi, ganin Ammi tazo wajen Ammi tai murmushi tace "zanga me baki indomie gobe" tai dan dariya she's happy tana yarda da Riyad that's the only relief data samu from the whole memory loss saga, hijabin yasamata sannan yakama hannunta da har yanzu agogon daya dauramata ke kai suka fice, gajiya da tafiya tayi dasauri ta tsaya tana taba guiwanta takalleshi zatamai kuka dasauri yace "lemme carry you" dagamai hannu tayi yadauketa ahankali yana kallon yanda fuskanta brighten up sabida yanda yadauketa ahaka har side nashi fadawanshi na gaidasu ciki ya shiga yamaida kofan yarufe yawuce flat nashi yashiga da ita sannan ya sauketa dasauri ta cire hijabin daya isheta ta yar awajen akasa tashigo cikin hadadden babban falon tana juye juye tana kallon chandelier sama tsayawa jikin kofan yayi ya rungumeta hannunshi a kirji yana kallonta yanda take wasa ta taba wannan ta taba wanchan just like a baby, ga bandage a kanta ga ciki ajikinta who kidnapped her? Who? Yacigaba da tambayan kanshi, that means they wants to hurt her just like yanda sukai hurting Mamanta, he will never allow it, he's feeling so bad, he's feeling responsible for condition nata, he feels kaman he's the reason she's like this, da ace datake gayamai yarabu da ita batason shi batason family shi ya barta non of this would've happened, baisan waye yayi this ba but he just knows cewa is from family nasu, he's 100% sure about that, he is ne kawai, hannunshi yaji an rike dasauri ya kalleta daidai hawaye na fitowa daga idanunshi kwaba kwaba tayi da fuska looking so sad ganin yanda fuskanshi yayi sai kawai ahankali ya rungumeta yasata ajikinshi murya chan kasa yace "I'm sorry Rashida, l've caused you pain! I'm sorry, I'm responsible for your condition Rashida I'm" ciro kanta daga kirjinshi tayi takalleshi ahankali wani irin pain da sadness takeji akirjinta sabida yanda taga fuskanshi yayi, he looks so sad and worried, ganin yanda take kallonshi tayi shiru looking very very sad yasa yamata murmushi yakama hannunta yace "'m not sad, smile Jewel" sannan yashiga tafiya da ita tana binshi ahankali suka wuce sama second master bedroom nashi ya shiga da ita yawuce a ita bakin gado yazauna tareda zaunar da ita kusa dashi har lokacin kallonshi take looking sad still saikuma da sauri ta tashi sai kawai ta zauna akan cinyanshi looking so sad takai hannayenta tadaura akan wuyanshi tana kallonshi har wani lelleka fuskanshi take kaman zata cinyeshi tanajin wani iri ajikinta, ahankali yakai fuskanshi yadaura kan nata duk suna kallon fuskokin juna murya chan kasan makoshi kasa yace

"Rashidahhh!" Faduwa gabanta yayi hakan yasatakara matsoshi tana manna boobs nata

a chest

nashi gashi babu bra ajikinta tace "sunana mota Rashida soda" murya chan kasa yace "no! Sunanki Rashida Rashida Almustapha Riyad" dasauri tace

"Rashida Almustapha Riyad" tana kallon bakinshi dake motsi da idanunshi dasukadan kankance, hannunshi yakai gently yakama hannunta daya daya wuyanshi yadaura akan sajenshi ya goga fuakanshi cikin tafin hannun nata jikinta yamata yirrer yana kallon fuskanta, murya chan kasa yace "Rashida!" Dasauri tace "uhnn" tana kara matsowa jikinshi sosai sabida yanda jikinta keyi, yanajin yanda nipples nata ke erecting yace "Rashidahhhh" sake shigewa jikinshi tayi ta kankameshi sosai tace

"uhnnnn" yana kallon kwayar idanunta kaman yanda take kallon nashi like a small boy yayi magana yace

"zan miki wani abu but don't tell anyone keep quiet" yadaura hannunshi akan baki yace "don't tell Ammi ko kowa" ya makemata kafadanshi just like she use to do yace "kinji"? Gyadamai kai tayi tana kallonshi kaman zata hadiyeshi wani irin kawai takeji ajikinta, hannunshi yakai kan lips dinta yana tabawa ahankali yace "open your mouth" yamata alamu da bakinshi daya bude dasauri ta hangame bakinta har uvula dinta yana hangowa, hannunshi yadaura kan idanunta yace "close your eyes" dasauri tarufe idanunshi gently yadaura bakinsh kan nata, kafin ahankali yashigar da tongue nashi cikin bakinta yana sweeping everywhere down to her uvula, karaf tarike bakinshi sabida dadi dataji yamata abaki tana numfashi sama sama, gently ya karbe nashi ahankali yayi magana abakinta. "I will do the kissing Jewel come here" yajawota jikinshi ta kwanto kanshi yana kwanciya kan gadon yakai hannunshi kan ass nata that's very soft yayi squeezing yanajan rigan sama yadaura hannunta kan cotton innocent and decent pant da Ammi tasamata yana tabawa yana kissing nata jikinta ko'ina namata dadi kamanjuice din da mutumin nan yabata dazu......


EPISODE 76

Anatse take bude idanunta tayi shiru tana kallon sama dudda AC dake aiki adakin but zufa goshinta yake, tundaga ranan da aka saceta har zuwa abinda yafaru jiya akan carpet adakin nan suke dawo mata wani irin kunya taji yakamata tana kara tuna mahaifinta da yanda yayi kuka da borin datama Ammi da muryan su Mom da Haleema da wasu dataji gently ta taso tazauna takai hannunta tana taba kanta tayi shiru sai kawai takai bayan hannunta ta göge fuskanta kallon dakin tashigayi hango hijabinta akan kujera yasa ta tashi takai hannu ta dauka ta saka tabude kofa, Ahankali tana addu'a Allah yasa bayanan don batason abinda zaisa su hadu ganin baby kowa yasa tafito tana kallon ko'ina dakin yahadu na bala'i saukowa tashigayi harta karasa saukowa falon saikuma ta kalli kitchen da kofan yake abude dasauri ta dauke kanta tunawa da abinda tayi, bude kofa tayi tafito tana kallon hadaden compound din tayi hanyar kofan datagani tana budewa taga fadawa yanda suka zube suna gaidata saida ta firgita da sauri tawuce su tafice tana kalle kalle ko za'a kasheta batasan wani hanya zatabi taje side din Ammi ba amman haka tacigaba da tafiya ahankali babu wani abu fake mata ciwo kawai bakinta ba dadi ne kadai hango wani flat datay exactly irin na Ammi yasa tai wajen tabude kofa ta shiga komi iri daya da side na Ammi bude kofan flat din tayi tana budewa tayi ido biyu da Muji daya watsa magani abaki yahadiya da sauri ya kalleta saikuma yataso yazo wajen dagudu juyawa

tayi dasauri karaf taji yakama hannunta cikeda so yace "Rashida"

Chak ta tsaya taki juyowa jikinta kawai yayi sanyi tadawo daidai ahankali yace "Ya jikin?" Kin magana tayi, ahankali yace "dan Allah ki shigo nayi magana dake, dan Allah dan girman Allah nace kinji Rashida" kasa motsi tayi dan janta yayi hakan yasa tabishi Suka shiga cikin falon still taki kallonshi to her biggest suprise saitaga ya sauke guiwowinshi kasa dasauri ta koma baya tana kallonshi yanda Babba dashi yayi kneeling tanajin wani iri hade hannayenshi yayi yana kallonta yace "Rashida | take full responsibility for my actions, nasan kin tsaneni kin tsaneni Rashida dan girman Allah ki gafarceni find a place kiyafeni ko zan sami kwanciyan hankali I'm sorry y'ata, Rashida dan darajan Allah kiyafemin kinji" yayi maganan hawaye na gangarowa daga idanunshi dasauri tadauke kanta idanunta na taruwa da hawaye she don't know but something is her ya chanza she remembers maganganun Haleema and she wanna be a better person mahaifinta yayi kuskure but harda influence na wasu mugaye she knows she's pregnant cus ta tuna maganganun Dr a asibitin da aka kaita, batason tayi feeding baby nata this hatred datake dauke dashi azuciyanta cus Ammi did not feed her hatred dudda an cuceta but ta taso da ita tana gwada mata kyawawan halayyan mahaifinta ne, she wants to change for good forgive and forget taso mijinta and just live happy ta cikama Mama burinta, saukan hawayenshi taji akan kafarta hakan yasa ta kalleshi kuka yake yabata tausayi ahankali tace "Abee" dawani irin sauri Muji yakalleta wasu sababbin hawaye na zubomai daga idanu ya kalleta ahankali ta zauna agabanshi tace

"kasan l've always wanted to call mahaifina da Abee kanason sunan"? Fashewa da kuka sosai Muji yayi saikawai ya rubgumeta tsam tsan ajikinshi tai lamo tai shiru tana tuna Mama she knows how much Mama loves mahaifinta dudda yamata laifi but Mama bata tsaneshiba ahankali Rashida ta dagoshi takai hannunta tana sharemai fuska tace "maganin me kakesha?" Yana kallonta kaman zai hadiyeta yace "na B.P ne" gyadamai kai tayi tace "meke maka ciwo?" Dasauri yace "babu komi wih yanzu

I'm the most happiest father aduniya" dan murmushi tamai sai kawai ya manna ma forehead nata kiss ahankali tace "inaso naje wajen Ammi Abee nayi wanka yunwa nakeji sosai" da sauri yatashi yana dagata yace "muje muje kici" har side na Ammi sukaje nan nan yake da ita Ammi na zaune suka shigo a kunyace Rashida ta rufe fuskanta da hijabi Ammi ta kalli Muji ganin yanda yake murmushi yasa Ammi tace "Baffan su kaine" tahowa ajen Ammi Rashida tayi har lokacin fuskanta a boye sai kawai ta rungume Ammi tace "Ammi sorry na miki kiriniya" Dasauri Ammi ta kalleta saikuma ta kalli Muji dake murmushi sosai Ammi tace "Alhamdulillah Alhamdulilah Allah mun gode maka, My Baby" kankameta Rashida tayi taki nuna fuskanta dasauri Muji yayi dinning yace "taho kici abinci" dasauri Ammi tace "maza tashi kije kici kidena zama da yunwa tunda bake kadai bane" batai musu ba ta tashi tawuce Babanta ke serving nata Ammi sai kallonsu take tanajin dadi sosai taci pepper soup aduka wanda ke kullan kasan tarage sannan ta tashi tawuce sama shikuma Muji yadawo falon yanaba Ammi labari cikeda farinciki.

Bayi tafada saida tafarayin brush sannan tai wanka kawai she's happy hakanan she's feeling very happy, agaban madubi ta tsaya ta cire bandage na kanta taduba bayin taga sunada first aid box tayi dressing kan nata da ya warke sosai sannan ta tattare kan tayi parking tafara wanka tana tuna yanda Ammi ta mammata wanka da ruwan zafi sosai tayi wankan sannan tadauro alwala taja towel tazo bude kofan tayi ta hada ido da Riyad dake gaban kofan yayi folding hannu yana jiran fitowanta dawani irin sauri tajuya zata koma yakama hannunta kulle fuskanta tayi yana jawota zuwa jikinshi tace

"wat are you doing in my room?" Ahankali yana sata ajikinshi batare daya damu da ruwan dake jikinta ba yace "I come to talk to my small baby not you" yakai hannunshi yadaura akan cikinta, kabar da hannunshi tayi a kunyace zata fita daga jikinshi da sauri yace "mehaka? Kunya kikeji small girl like you tasan namiji har yamata ciki" dukawa tayi ta manna kanta akan guiwanta tace "nika fita kona kira Ammi da Abee wih kaga salloli zan rama" dukawa yayi yana lekata yace "okay kiyi ki gama we are leaving this place gidanmu zamu yau" makemai kafada tayi kawo kanshi yayi ya manna mata kiss a cheek ahankali yace "I'm glad you're okay Wife welcome back" yana maganan yatashi yayi kofa dasauri tadago kanta tabishi da kallo wani irin sonshi takeji aranta bana wasaba.

Saukowa kasa yayi yadan kalli Ammi yace "Ammi uhmmm zamuje gidanmu anjima" wani mugun kallo Ammi tamai tace "to baka isaba sai anyi bikinku" Dasauri Riyad ya kalli Baffan shi kaman zaiyi kuka hakan yasa Muji yace "haba amai afuwa abasa matara duk randa sukaga dama sai ayi bikin, kai jeka zakuje gida abinku" Wajen Muji Riyad yaje yabashi high five sukai dariya Ammi ta kadakai yayi wajen kofa wayanshi yahau ringing tsayawa yayi yaciro wayan ganin Papa yasa yayi shiru saikuma kaman zai maida wayan aljihu sai kawai ya dauka yakai kunne yayi shiru kusan 5min har Ammi tadaga kai tana kallonshi kafin ahankali yazare wayan daga kunnenshi saikuma yadawo falon Ammi dake kallonshi tace "ya akayi?" Anatse yace "Ammi it's Mom Dad, yakira wai dan Allah dukanmu muzo Grace hospital dan girman Allah he wants to see all of us including my wife I don't know why" Shiru dukansu sukayi Muji yace "muje Ammin su?" Dan ijiyan zuciya ta sauke tacd "okay anjima kafin kuje gida saimu biya"

Gyadamusu kai yayi yafice Ammi da Muji kuma sukahau hira gwanin ban sha'awa they don't use to be close before but yara sun maidsu so close.

Wuraren 8:20 Ammi tashigo dakin ta kalli Rashida data shirya fikin wata atampa tace "muje" gyadama Ammi kai tayi ta tashi ta taho Ammi sai kallonta take cus tayi kyau fitowa sukayi tundaga saman

Riyad ke kallonta yanda ta yafa Babban gyale tai kyau sai wani glowing take kin kallon Riyad tayi Munir yace "cousin dinmu" murgudamai baki tayi dasauri yace "Ammi kin ganta ko ba mun shirya ba"

Dariya Ammi tayi tace "kacire ni daga fadan nan naku Munir kutashi muje" tashi sukayi taki kallon Riyad Munir sai hira yake mata tabiyemai sukai gaba Muji na kallonsu tareda Ammi da shi kansa Riyad din mota biyu sukayi da gangan ta shiga motan Babanta da Ammi ke ciki shi da Munir suka shiga daya sai kumbure kumbure suke har zuwa hospital din data rasa mesukazo yi dan tasan ba shine na kanta ba.

Suna shiga sukaga Papa tsaye sai zagaye yake yana ganin su yataho wajensu da sauri saikuma duk tsaya suna kallonshi, ahankali yace "thank you for coming, dan Allah come with me" yayi gaba suka bishi abaya har zuwa gaban dakin da Mom keciki dasuke Jin ihunta from there gently yabude kofan yace "ku shigo" Riyad na sako kanshi yajuyo da bala'in sauri tsigan jikinshi na tashi itama Ammi dasauri tajuyo hakama Muji itakuma Rashida tsaf ta shige ciki duk suka bita da kallo ta taka har zuwa inda Mom take tana kallonta tana ihu da muryanta <

dasauri tajuyo hakama Muji itakuma Rashida tsaf ta shige ciki duk suka bita da kallo ta taka har zuwa inda Mom take tana kallonta tana ihu da muryanta daya dishashe tana kokarin fixge hannunta tayi susa tace "wayyoo Allah na kuyafemini dama akwai azaba haka aduniya? Dama akwai cuta mai bakin azaba haka aduniya? Rashida kayakuri kiyafemin nasa an sama mahaifiyarki Hiv naso kasheki kema Allah baiyiba Rashida dan darajan Allah kiyafemin ko susan nan ne nasamu Allah ya dauke mini" kujera Rashida taja tazauna tana kallon Mom in agony da tsantsan ciwo da kawai ganinta ahaka saitaji satisfaction da bata tabaji ba, murmushi tayi Allah ya sakama Mama, murmushi take sosai feeling so happy and satisfy.


EPISODE 77

Wuraren 3 yafarka da strong erection tashi yayi yazauna idanunshi sunyi ja, yajuya ya kalli Haleema dake bacci she’s not the one he wants, wai wats wrong with him ne? Over a year kenan he’s married to Haleema all this abubuwan bayajinsu, dan ijiyan zuciya yasauke sannan ahankali yatashi bayi yashiga yayo wanka yafito Wasa wasa yau 4days kenan Ammi tahanashi ganin Rashida, kai koshi Munir dake kwana da tashi a flat din baiganta ba, the only one person dake shiga da fita adakin nan is Ammi sai Dr dake dubata dudda yaune second kwananta duk a side na Ammi yake shigowa yaci abinci but wlh baiganta ba Ammi tahana abun yasa hardan rama yafara, duk Ammi na kallon take takensa tayi banza dashi.Today is the 4th day da Maimoon take kiran wayanta nonstop, ganin she keeps calling wayan nata dake hannunshi yasa saiya daga yakai wayan kunnenshi dasauri Haleema tace “Dr Rash mesa baki zuwa clinic, I’ve been calling you baki amsawa wlh duk na damu, are you okay?” Kaman Riyad bazai amsaba anatse yace “this is her husband speaking, batada lafiya” faduwa gaban Maimoon yayi daman Rashida nada miji dasauri tace “ayyah ina yini ya aiki, in sha Allah zanzo na dubata” kaman bazaice wani abuba yace “she’s not in that house muna family house” cikeda damuwa Maimoon tace “dan Allah inane family house din? Can I come and see her”? Shiru Riyad yayi chan yace “okay” cikeda damuwa tace “wannan driver nata ya sanni, yanzu mun fito break na sallan azahar, I can come basaina koma clinic ba” dan shiru Riyad yayi tun ranan daya fara ganin yarinyar yayi running background check on her dan baison any kind of mutum tareda matarshi, yarinyar batada matsala and again an gayamai ta taba aure tanada baby but mijinta yarasu a Maiduguri a hannun boko haram he’s a military man, anatse yace “k” ya katse wayan.Ammi na zaune a falo akai sallama Ammi tace “come in” ahankali Maimoon tabude kofa tashiga Ammi tabita da kallo ganin lab coat ajikinta ga gyale ta nannada akanta looking so decent, da sauri Maimoon ta zube gaban Ammi ganin babban mace, ahankali tace “ina yini Anty, sunana Maimoon ni friend din Rashida ne, inata kiran numberta ba’a dauka, yau sai mijinta ya dauka yake sanar dani ba lafiya shine yasa aka kawoni na ganta” murmushi Ammi tayi sosai ganin Rashida nada friend mai hankali haka, cikeda tattausan murya tace “Stand up stand up” dasauri Maimoon ta tashi, Ammi tace “ya school? Hope wani test ko assignment be wuceta ba?Muje na kaiki wajenta” Maimoon dake murmushi tace “a’a babu wani mahimmin abu daya wuceta, kawai attendance mark nata ne zaiyi gibi da log book nata, but that’s not really a problem, next week zamuyi all test nan da 2weeks zamu fara exams” Ammi dake tafiya Maimoon na binta abaya har sama zuwa dakinta tace “Allah yabaku sa’a”ahankali Ammi tabude kofan ta shiga dakin Rashida na kwance kan gado dudda ba bacci takeba wayan Ammi ne a hannunta tana kalle kallen pictures na ciki, tayi wani irin kyau bana wasaba, takara haske kaman mai bleaching, dakin na lafiyayyen kamshi turaren da ake turarata dashi, tana sanye da soft gown na cotton material mai kyau tadan rame alamun ciwo but then takara kyau da ja, wajen gadon Ammi tayi ta dagota ahankali ta tashi ta zauna gently kaman irin yanda matan da suka haihu suke zama cikeda so Ammi tace “look who is here your friend” tayi pointing kofa dasauri Rashida tajuyo takalli kofa Maimoon tagani dake kallonta tana murmushi, Ammi tace “bari na barku naje kasa” tawuce tayi kofa tafita tareda maida musu da kofan tarufe takira wata yar aikinta tasa aka hadamu Maimoon’s kayan abinci da drinks da snacks aka kaimata sama.Yanda Maimoon ke kallonta yasa Rashida ta sauke kanta kasa cus gani take kaman duk wanda ya kalleta zai gane abinda yasameta, asanyaye tace “Maimoon” zuwa Maimoon tayi ta zauna gefen Rashida da sauri saikuma tarike hannunta tace “Rashida daman kinada aure shine baki taba gayamin ba”? Batare da Rashida ta kalleta ba making innocent face tace “bansan yanda ake gaya bane nima” dasauri Maimoon tace “kinsan shine yasa aka kawoni nan naganki, driver ki ya aiko” ahankali Rashida ta kalleta itama Maimoon kallonta take saikuma chan tace “Rashida wlh I really like you as a friend, I understand you, nasan bakida friends bama kisan ya ake friendship ba, but you can trust me, I know that nima bantaba gayamiki anything about me ba but nima nataba aure for almost 2yrs mukai tare, I have a son Ameer, he’s 3yrs yanzu, mijina soja ne, but….” Tadanyi shiru saikuma muryanta ta karaya ahankali tace “yarasu!” Dasauri Rashida ta kalleta ganin yanda hawaye ya taru a idanunta, cikin sanyin murya Maimoon tace “kasheshi akayi, he went to battlefield bai dawo ba saidai aka kawo mana gawansa” Rashida jitayi wani abu ya taso mata, wani ciwo a zuciyanta barinma datace kasheshi akayi she just remembered Mama sai itama hawaye ya cika idanunta, ahankali Maimoon tace “Rashida I know so many things are going on with you, nima I’ve been there, akwai lokutan da har depression saida ya kamani, my point is learn to share kidena rike abu aciki most especially to mutanen dakikaga they genuinely care about you” ahankali Rashida ta rungumeta sai kawai suka fashe da kuka tare cikin muryan kuka Rashida tace “I’m sorry about your husband Maimoon Allah jikanshi, I’m sorry for not telling you anything about me yau zan fada miki” sakin Maimoon tayi tafara bama Maimoon labari komi game da rayuwanta harda Mama da yan gidan nan da abinda yafaru ranan even though bata fadan mata sex part dinba.

Ahankali Maimoon tace “did he took virginity naki? Meya miki daya kaiki dakin?” Dasauri Rashida ta dauke kai saikuma ta sauke kanta kasa tashiga wasa da kumbanta, ganin taki amsa tambayan sabida kunya da nauyi yasa Maimoon tashare tambayan cus is even obvious jinyan datakeyi kenan. Harga Allah tazo gidan nan taga genuine love Ammi has for her, and shi mijin dudda bata sanshi ba but tasan shine mutumin data gani ranan, the act na ya tura aka daukota aka kawo ta shows yana sonta, and kome yayi mata yayi ne sabida kishi, ko ita yanda Bilal yamata ranan batasoba kowa yasan Bilal fa playboy ne akanme tanada aure zata kula wani? Banda haka is not fault nasu ai, wayanda sukayi crime ba bata rayuwan Mama an kamasu suna hannun yan sanda and again akwai wani abu she noticed wlh Rashida nason mutumin nan, inhar shine mutumin ranan nan data gani agidan nan wlh Rashida na sonshi, data furta yanada kyau saida mood din Rashida ya chanza, she was so jealous like hell. Hannunta takai ta taba kafadan Rashida tace “yanzu yazakiyi?” Ahankali Rashida takalleta murya tace “ni banson shi, awajen Ammi zanyi zamana zata rabamu banso na kara ganinshi tsoronshi nakeji” dan murmushi kadan Haleema tayi tace “to shikenan I hope zaki iya” Dasauri Rashida ta kalleta saikuma tadauke kanta dasauri kawai she’s not comfortable gani take duk wanda ya kalleta zaiga abinda ya sameta murya chan kasa tace “ni kidena kallona” dariya sosai Maimoon tayi tasa hannu tadauki abincin da aka kawo mata tafaraci, tana gamawa taciro books nata da komi dasukayi ta nunnunama Rashida wanda yawanci ta iya but still tai snapping da wayan Ammi, sunyi hira da Maimoon dudda yawanci Maimoon ke maganan but she was so happy to see her, she promised zata koyama Rashida alot bari ta warke tukunna, 6 ta tashi tana daukan jakanta tace “bari kiga natafi” ahankali Rashida tamike ta tsaya tadan dafa bango Maimoon tabita da kallo saikuma tai murmushi dasauri Rashida cikeda masifa tace “me haka?” Dan dariya Maimoon tayi tace “sannu kinsha wuya wlh” dauke kai Rashida tayi dasauri saikuma ta koma ta zauna tajuya mata baya tace “wlh nafasa rakaki tunda ni kallona kike” dariya Maimoon tayi tace “eh nima banso da wannan gwalallun kafan naki” dasauri Rashida tadauki filo tajuyo ta jefamata kaman zatai kuka Maimoon tabude kofa tafita da gudu tana dariyan Rashidan da taga ashe tanada this mugun kunyan. 

 Baiwar tazube gaban Ammi tace “Ammi ga matan mai Martaba Sarki Riyad tazo gaidaki!” Abu kawai Rashida taji ya chaki zuciyanta sai kawai kaman an tsikareta ta mike zata wuce hannunta Ammi takama tarike tace “dawo ki zauna” batare datai musu ba tadawo ta zauna ahankali gefen Ammi tadauki wayan Ammi kawai ta shiga daddannawa, Ammi tadanyi shiru yau shekara daya da watanni matar Riyad bata taba zuwa wajenta ba ta gaidata is as if batamasan itace asalin mahaifiyar Riyad ba so wat is she doing today anan? Kallon baiwan Anmi tayi tace “kumata iso”. Bayine suka fara shigowa guda shidda saikuma ga Haleema tashigo sanye da crazy alkyabba daya hadu jakadiyan ta namata fifita tasa wani exclusive super wax dake jikinta, tunda tashigo take kallon wata jan yar budurwan yarinya dake kusa da Ammi tana daddanna waya batare data dago kanta ta kalleta ba kotama nuna tasan da an shigo dakin, kujeran da bayin suka shiga sharemata da zannuwan jikinsu tazauna kujeran na facing wanda Ammi take zaune tareda Rashida dake game abinta, wani kaluluwa Haleema taji ya tsaya mata awuya cus tana kallonta tasan itane matar Riyad ce dan ancemata daman fara ce, ga kyau ga gashi, part of abinda yakawota flat din is tazo taga wacece matar da Riyad ya aura dinma, wani arnen kishi taji yarufeta takalli Ammi tareda kakalo murmushi tace “Ammi ina….” Hannu Ammi ta daga mata strictly tace “sallami mutanenki sujiraki awaje” jitayi ranta yabaci amman saitai murmushi ta danne tama Jakadiya alamun su fita sannan cikeda makirci tace “Ammi wai nayi missing period dina ne, Mai Martaba yakamata yakaini hospital tun shekaran jiya but gynea dina bata kasan gobe zata dawo, shinefa yace nadena komi adinga kula dani cus lafiya gobe ciwo, Babe ya tsani ya ganni ina rashin lafiya saisa nake yawo da bayi incase of emergency” hakanan Rashida dakejin komi kawai taji zuciyanta yakama da wuta, game din datakeyi ma bata ganewa kuma, Haleema tace “Ammi ina yini” anatse Ammi tace “lafiya lau yasu wajen Mamanki da Babanki hope you’re hearing from them”? Cikin shedanci tace “yes I think Babe yakira Mamana ma this morning cus inata amai duk hankalinshi yatashi saida tafadamai wani orange remedy yahadamin sannan ya tsaya ma” sosai Ammi ke kallon Haleema sabida taga Rashida take kafidirin nan cus ita bata isa tamata hakaba, ikon Allah Ammi kawai tasaki baki tana kallon kwainane, Haleema tasake sakin murmushi tace “Ammi Riyad is so happy about this our baby, kinsan yanason yara I can’t wait na haifa babyboy me kama dashi, Ammi kin kusan zama grandmother” daidai lokacin aka bude kofan falon, shigowa falon Munir tareda Riyad sukayi, hannun Riyad rikeda paper bag din cold stone ice cream, dakin yabi da kallo kafin idanunshi su sauka kan Rashida dake playing game da wayan Ammi, kamshin turarenshi kadai Rashida tajiyo da sauri ta dago kanta ta waigo wajen kofan da sauri, hada ido sukayi a mugun firgice takama hannun Ammi daya ta rike tashige jikin kujeran tai lamo gabanta na faduwa ba kakkautawa kaman wacce taga dodo. Anatse yashigo cikin dakin Munir biyedashi dawani irin sauri Haleema ta taso ba kunya uban kowa na dakin tawani shige jikinshi ta kankameshi tace “Baby how did you know I was craving ice cream? You understand my pregnancy cravings so well” hayaki Rashida taji yataso mata tundaga kirji yazo mata wuya yamata hake hake, ganin yanda Haleema tawani rungume Riyad.Abala’in kunyace dan Riyad na mugun kunyan Ammi yadan tureta batare dayayi magana ba dasauri ta dago kanta takalleshi ganin yanayin kallon daya mata yasa ta saken mishi murmushi takai hannunta ta karbe ice cream bag din daga hannunshi tace “thank you Baby” Rashida jitayi idanunta sun juya ganin ita da ice cream dinta wata ta karbe, Ammi bata ankara ba taji kawai tamike dudda yanda tafiya ke mata wahala amman saida takai wajen dasauri daga Riyad har Haleema suka juyo suna kallonta yanda ta taho kaman zakanya, gaban Riyad Rashida tashige batai wata wata ba tasa hannunta ta fizge paper bag na ice cream dinta tace “ai kinada Ammi kema, kije kisa taki Ammi ta aika mijin naki ya sayo miki niki ice cream din but this is mine! And I don’t share!” Daga Ammi har Munir baki suka sake suna kallon Rashida dashi kanshi Riyad din daya tsaya yana kallonta da ita kanta Haleeman dake kallon Rashida jiyake kaman ta shake Rashida itama, watsa mata lafiyayyun harara Rashida da manyan idanunta da saida tsoro ya shiga Haleema ganin yarinyar barkono ce tawuce fuuuu tayi staircase tafiya daya biyu tayi tai baya zata fadi dasauri Riyad yayi wajen yace “Jewel” daidai yana tarota tafado jikinshi afirgice takalleshi.


EPISODE 78

Around 9 yashigo falon, Ammi na zaune tabishi da kallo he’s so moody, he’s sad, murya chan kasa yace “good morning Ammi” watsamai harara tayi tace “kalau” dinning yawuce Munir yabishi da kallo duk tausayin dan uwanshi yakamashi, breakfast yagamayi yazo zai fita Ammi tace “zonan” dasauri yajuyo tace “oya kawo kudi matarka tace ice cream takeso tasha yau na aika a sayo mata” dan jim yayi saikuma chan yace “zan kawo mata” dasauri Ammi tace “mene? Ai nasan zaka iya kawo mata amman nace ka kawo kudin, ni zaka firgitama yarinya da safen nan? Bani kudi kaga kar Raina yabaci” hannunshi yasa a aljihu ya tattaba sannan yaciro wallet dinshi yan 1k sababbi yaciro duka ragowan dake ciki yabama Ammi yana kallonta idanunshi sundan chanza kala, hannu Ammi tasa ta karbe kudin batare data kalleshi ba tace “shikenan” yawuce ahankali yajuya yafita Ammi tabishi da kallo saikuma Munir yataho kusada ita yana kallonta kaman dan yaro, mugun kallo Ammi tamai tace “wat kaikuma”? Ahankali yakama hannunta ashagwabe yace “Ammi dan Allah kimai hakuri ni wlh banjin dadi ina ganin dan uwana cikin damuwa kaman nine kikemawa haka nakeji Ammi” mugun kallo tamai dayasa ahankali yace “Ammi please kinji” karbe hannunta tayi tace “kyaleni ga kudin nan jeka amso mata ice cream” karban kudin yayi yace “toh bari nayo wanka Ammi kar aga yaronki ba wanka” wucewa sama yayi tabishi da kallo tana tabe baki da girgiza kai, yayo yafice ganin fitanshi yasa Ammi tace “Rashida Rashida” daga taciki tace “na’am” Ammi tace “fito zaman cikin ya isa haka” kusan 1min tadauka sannan tabude kofa tafito ahankali take tafiya bawai bataji sauki bane taji wajen baya mata zafi kaman da kawai discomfort ne kaman ba vijay nata ba, binta Ammi tayi da kallo fatarta har kyalli yake tana sanye top and trouser na material golden, rigan mai botura sun mata mahaukacin kyau gashinta babu kitso but anyi parking ahankali ta tsaya ta kallo falon daga sama tai shiru tuna ranan data gano sune family ta, sune suka kashe mata Mama, yanda ta tsaya tai shiru yasa ahankali Ammi tasake kiran sunanta “Rashida” kallo Ammi tayi, murmushi Ammi tamata dake kwantar da hankali tace “taho kizo kinji” gyadama Ammi kai tayi takai bayan hannunta ta goge idanunta sannan tafara tahowa tana tafiya ahankali tana kama bene sosai Ammi take kallonta kai Amman Riyad yama yarinyar nan mugunta saida ta tsaya ta huta a benen ahankali Ammi tace “nazo na taimakeki?” Cikeda karfin hali ta girgizama Ammi kai takarasa saukowa tazo ta zauna kusada Ammi tana maida ijiyan zuciya daidai bayi sun shigo ana isar da zuwan gimbiya Haleema.


EPISODE 79

Bata taba tunani ko tsammani cewa Riyad zai iyacin wata haka irin wannan style din ballema har yayi sambatu hakaba kaman yau yafara samin mace, yanda zuciyanta yakama da wuta batasan sanda idanunta suka shiga kuna ba cikin mahaukacin kishi tace "na shigo din ai isa da iko tasa na shigo tunda kai mijina ne ba dadiro na ba, jiya I called you kacemin baka cikin mood look at abinda kakeyi" tanuna Rashida data turo baki tana kallon Haliman dataga tana magana da Riyad dinta, Haleema tace

"wata kakeci saikace bakatabacin wata macen ba Riyad" wandonshi yashiga sawa tass yagama sawa sannan yakalleta babu kunya ko wani dar yanuna kofa yace "get out" kallonshi tayi ganin yanda fuskanshi yasa tajuya zata fita shima Riyad yajuyo kawai ganin Haleema yayi tabiyo ta gabanshi da gudu tayi kan Rashida dake tsaye awajen har lokacin kan nipples dinta sunyi baro baro a riga, tadaga hannu zata kaimata duka karaf Rashida tarike hannunta Haleema ta kasa kwacewa dudda tanada memory loss but karfinta na nan, hadarai Rashida tayi tana turo baki cikeda fushi tawani tura Haleema baya da karfi hakan yasa Haleema ta taka egg da Riyad ya fasa akasa awajen yawani jata sai kasa timmmm Rashida tawani fashe da dariya tana tsalle tana clapping dasauri Riyad yayi wajen

Rashida dayake mugun ji da ita ya rungumeta yace

"stop jumping Jewel muje muje" yakamata yawuce da ita sama adakin shi yatasata yana rufo kofa yasauko kasa yasami Haleema kasa inda take tana kuka sosai mai tsuma zuciya ya rungume hannunshi yana kallonta yace "today should be the last day dazaki shigo side dina idan ban nemeki ba" cikin fushi ta tashi tace "tunda ka ijiyeta kana iskanci ai dole" dan tabe baki yayi yace "wat do you expect?

Kaman yanda na aureki haka na aureta, yanda nake baki hakkinki haka itama nake bata, out!" Yanuna mata kofa yace "I will see you in 2days nagama kwananta" tashi tayi tana tahowa tanaji kaman ta kasheshi tawuce tafita daidai Sarkin Gida yana zuwa da basket da Ammi ta aiko musu da breakfast da maganin Rashida da kayan sawa kuma ya karba.

Sama yakoma da maganin da abinci yana bude kofa yaganta jikin kofan tsaye tana ganinshi ta rungumeshi tana turo baki saikuma tafara hura hanci murmushi yamata yace "muje kici abinci" waina yazuba mata da miyan taushe da nama tass ta cinye waina kusan 8 yana mugun mamaki yanda takeci haka yabata fresh juice da Ammi tayi ta shanye da ruwa yabata magani da kyar tasha tai gyatsasai kawai tahau jikinshi takai hannunshi saman boobs nata murmushi yayi wih he's loving this Rashida matse mata boobs yahauyi saikuma da kanta tasa hannu cikin Riga taciro boobs din waje gurza ata boobs din yashiga yi tana lashe baki saikuma ta tashi tashiga cire wando yanda taga yana mata, matsar da kwanukan abincin Riyad yayi ya fizgo bargo daga gado ya kwantar da ita akan carpet yashiga kwakule mata kunkuru, mugunci yamata yanzu yama manta zaije fada Rashifa kawai yakeci saida tafashe da kuka sosai sabida zafi sannan ya iya yadakata tahuta yaciga.

Lalata Rashida kawai Riyad yake da abubuwa da dama yana cinta har dare abu daya suke hutawa kawai take taci abinci tai kat su fara. 


EPISODE 80

Ganin tayi bacci yasa yatashi ya fada wanka ya shirya cikin shiga na ban girma harwani glowing yake yafito fadawa na zubewa yana kallonsu yace

"ya akayi kukabar Haleema ta shigo" Sarkin Gida yace "gafarceni Sarkina harta juyafa bamuyi tsammani ba tajuyo ta keto da gudu ta shigo toh bazanu iya biyota ba saisa na kira dan sanar da kai but ba'a tababa" wucewa yayi zuwa flat na Ammi bata falo hakan yasa yawuce sama gaban dakinta yayi sallama daga ciki tace "shigo" shiga yayi tana sauna tana kokarin linke some kaya anatse ya zauna kusada ita yace "ina yini Ammi" "Ipy lau yamai jiki?" Ahankali yace "dasauki Ammi tana bacci" gyadamai kai Ammi tayi tana kallonshi saikuma anatse tace "Akwai magana a bakinka talk to me" dan shiru yayi sai chan anatse yace "Ammi inaso nafada miki wani abu idan kin yarda I will do it idan baki yardaba zan hakura" yayi shiru chan yace

"Ammi inaso na sauka daga kujeran sarautan nan!" Sosai Ammi ke kallonshi saikuma chan tace

"menene dalilan ka"? Anatse yace "my biggest reason shine Ammi I don't have passion for leadership mutane suna bina abaya yazama nine jagiransu" yayi shiru yace "woman tasani on that sit sabida personal reasons nata, tun ina yaro bantaba kwadayin ko hararo kaina nazama sarki ba, Ammi I feel I'm not competent enough, everyday ina kwana ina tashi ina tunanin wannan nauyin dake kaina, and lastly Ammi I want to protect Rashida banso na zargi kowa but nasan this house nada sa hannu in her condition Ammi duk randa akasan kuma tanada ciki zasu iya halakata da bunda ke cikinta already bana Mrs Bugaje magana ta nema mata transfer zata karba mata zamu bar kasan muje wani kagar takarasa school achan, and Ammi is not just us 1 plan on taking you da Munir dukanmu are leaving this house Ammi" kallonshi Ammi take saikuma gently takai hannunta saman kuncinshi ta shafa tana kallonshi tasan waye dandanta ita kanta tana tausaya mishi, Riyad is not a king that for a fact she knows itama ta gaji da makirce makircen gidan, Lumshe idanu tayi tabude ahankali tace "Riyad anything kakeso I will always support you with my love and prayers Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" rungume Ammi yayi dasauri yace "thank you Ammi nagode" murmushi tayi tace "tashi kaje karta tashi" ahankali yace "kafin naje zanga Baffa and Gwaggo da sauran yan uwana na sanar da su kafin nafadi afada"

Gyadamai kai tayi yawuce bangaren Gwaggo shiru sukayi duk basuji dadi ba but then they supported him Kabeer sai dadi yakeji duk Riyad na kallonsu yace "zanyi sanarwan gobe agafa".

***

Zaune take adaki around 8:00 in the morning sai soshe soshe take wayanta yahau ringing hannu tamika tadauka takai wayan kunne cikeda girmamawa Haleema tace "Mom kinji abinda nakeji kuwa wai Riyad zai sauka amatsayin sarki gobe zan sanar a fada wata baiwa dake aiki a bangaren Gwaggo ke sanar dani" tashi Mom tayi dasauri ranta yayi bala'in baci tabude baki zatai magana sai gefen fuskanta ta wajajen bakinta yay ja ga kurajen sun feso mata last night yashigan mata mugun kaikayi ta shiga sosawa kaman mahaukaciya har wayan na faduwa daga hannunta.

Tajuya takalli kanta a madubin dakin yanda fuskan nata yayi rudu rudu tace "wat is this borun jini nakeyi ne"? Ta tanbayi kanta tana cire rigan jikinta tashiga kallon jikinta yanda kujeran sun fito ko ina 

sunyi dabbare dabbare kaman makero tai tsaki tadauki wayanta tana kiran wani number tace "zoka kaini asibiti Idris"ijiye wayan tayi ta daga zaninta ta ta duka gaban madubin tana kallon gabanta kurajen sun feso mata agaba da wajajen takashi ga kaikayi da zafi duk suna mata da kyar ta shirya tasaka kaya batare data iya saka pant ba ta yafa wani arnen gyale ta sauko tana tafiya ahankali har zuwa wajen motan driver yabude mata baya tashiga yaja motan haruwa wani private clinic haka zuwa wajen wata Dr ta duk ta dubata tasa wani abu kaman na share kunne ta debi sample na ruwan kuraje tabata akai lab sannan tazauna Mom tace "wai borin jini nakeyi ne ko chicken pox? Amman ai basu fitowa area na vagina" murmushi Dr tayi tace "calm down Ma we will get the result soon" almost 20min aka kawo result na test din karban result din matan tayi tashiga warware wa tana dubawa saikuma matan tadago tace "Hajiya l've been your Doctor for a long time now, and I know mijinki almost 2yrs Kennan da rasuwan shi, can I know kinyi having sex recently ne?" Faduwa gaban Mom yayi ciki Baaba yamata? Kwata kwata ita ba yar iska bace, but ranan da aka cirota daga police station da Papa yasa cus bazai iya zuwa da kanshi ba ya aiko mata lawyer shikuma Baaba ne yazo daukanta yakaita wani gidanta anan kano dan dare yayi babu flight the next day ne zasu Kano she remembered Baaba yabata wani drink tasha dan ya kwantar mata da hankali bayan tasha she just grab d boy tacemai make me happy kota sami natsuwa rabonta da saduwa tun mijinta na raye haka yaron yacita kuma daga ranan bata karaba, ko murmushi batamai dan batason raini iya kanta dashi ta sasu aiki dan boy dinta ne su mata running errand, adan rude Mom tace "wait ciki nayi ne bakince bana growing egg bazan iya ciki ba? Ciki yaron chan yamin?"Girgiza mata kai Dr tayi tace "No Hajiya you're not pregnant" Dasauri Mom tace "to toilet infection ya samin ne dake kawomin kurajen gaba da kurajen gefen lips?" Ahankali Dr tace "please calm down Hajiya kibani attention naki although this is the first test I will advice kije wani asibiti and run the second one or lab just to be sure" Sosai Mom ke kallonta gabanta na dukan uku uku anatse ahankali DR tace

"Hajiya kinada HSV-2". Yankewa gaban Mom yayi yaadi ita bama ta taba jin wannan sunan ba balle tamasan menene shi ko wata kalan cuta ne, baki tabude zatai magana but maganan yakasa fita muryanta yarike, anatse Dr tace "HSV-2 yana nufin herpes simplex virus type 2, type 2 din yana nutin kinada ganital herpes" faduwa gaban Mom yake da kyar tace "Innalillahi wa innailaihi raji'un, La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimina" saikuma tayi shiru tace "ita cutar menene ita kaman HIV ce?" Dan shiru Dr tayi tace "kusan hakan ne dan itama virus ne banbancin shine ita Hlv garkuwan jiki takeci wato immune system itakuma wannan kurajen al'aura ce sannan itama takama ka takamaka kenan har abada sai wani iko na ubangiji ke warkan dakai". Bari ko'ina najikin Mom keyi tama kasa magana Dr tace "shi ganital herpes ana samunsa ne idan kahadu da mai ita ta hanyar saduwa idan ruwan maniyinsa ko maziyinsa ya shiga jikinka kota yawun baki, kuraje ne masu azaban zafi da kaikayi dakuma ke fashewa suyi ruwa sannan duk inda ruwan yataba kurajen zai fito awajen, ciwon zai iya kama duka jikinki kokuma gindinki thighs naki lebenki wajajen idanunki dama ko'ina, sannan yakan iya jawo abinda ake kira da viginal wart wato tsutsan gindi" rawa jikin Mom keyi tace "kinga Dr ko billion nawa kikeso zan biyaki ki warkar dani, wani kalan kurajene haka dazanyi suna ruwa wari kenan zan fara" anatse Dr tace "ban fadi rashin lafiya, da zazzabi, inflammation da burning sensation na azaba dazasuna miki ba su kurajen, Hajiya you're educated at this stage bawai I'm blaming you for seeking pleasure bane nasan bakida miji ke widow ce but educated woman like you bai kamata tai sex ba protection ba menene amfanin su condom eh?" Kai! Rawa jikin Mom yake bata taba sanin something like this will affect her ba over less than 5minuted mistake sex datayi da Baaba ba wanda ma ranta yabaci sabida gani tayi girman banza ne da karfin banza dan ko tsohon marigayinmijinta daya tsufa yafi Baba iya hakar mace, azuciye tace

"wih wih saina kulle shi wih saina kulle Baaba, dan uwar Baabarsa yasan yanada kwankwamai ajikinsa

ya kwanta dani bana hayyacina ya zubamin" saikuma tafashe da kuka tana dukan kirjinta yace

"ni zai sama cuta haka? Ai da wannan Allah natuba gwara HIV I have money to take care of myself I can live healthy for years but not da cutan da kuraje zasu cikamin gaba suna fitar da ruwa ina wari ina susa masu cutan susa kaman mahaukata suke zama fa" Saikuma ta daura hannuwanta akan bakinta gabanta har faduwa yake tayaya zata gayama Papa she slept with one of his security

Papa dayake ganin mutuncinta sabida tacemai bazata kara aure ba tunda mijinta yarasu? He gave her Baaba da Idris sudanyi protecting nata and run errands tunda tace lallai lallai saita koma kano tayaya zata fara Kodai karya Likitar nan kemata an hada baki da itane maybe is just borin jini duk ta tada hankalin kanta tashi tayi ta suncuki jakanta dasauri Dr tace "ki tsaya ki amshi magani" cikeda fada Mom tace "I don't have herpes" tawuce tafito tana tafita tana bubbude kafafu kaman wacce akama kaciya sabida yanda kurajen kemata zafi da kaikayi da kyar ta daure takai mota tana shiga takai hannunta tafara susa sosai tace "ina Baaba Idris?"

Tada motan yayi yace "bansan inda yaje ba Hajiya tun safe yafita" gurza gabanta take sosai kaman mahaukaciya da zani, wayanta na ringing ta kalla ganin Haleema ne yasa tadauka cikeda masita tana susa tace "Haleema leave me alone naji da kaina please haba! Yarinyar nan jekiyi duk yanda kikaga dama da ita, kiyi takanki" ta jefar da wayan tace

"kaini wani hospital mai kyau Idris" wani hospital sukaje data bude wajen ma is worst than before duk tagama sosashi Dr yamata confirming is herpes they need to admit her dan duk ta soshe kurajen sun suma zama ulcerated, akace tama cire kayanta gabaki daya tasa gown na hospital and tabude kafafunta tadena hadesu tana infecting ko'ina gindin da thighs din need breeze, duk tauri da bakin zuciyan Mom saita fara kuka wannan wani kalan cutane haka just last night fa taji kaikayin nan da safe ta tashi taga kuraje sun feso yanzu kuma gashi sun dawo wani iri and mahaukacin tsinannen kaikayi suke mata tana tabawa kuka su dawo ciwo su fara zafi kafin kace me mugun zazzabi yarufe Mom.


EPISODE 81

Kasa daurewa yayi yay spanking ass nata kadan dayay shaking like a water wave Riyad yadan saki kara yana sakin lips dinta. "Ahhhhh" sauketa zuwa gefe yayi yatashi yana sauka daga gadon dasauri ta taso dan wih bataso yabari, tashi tayi tai raurau da fuska kaman zatai kuka ta tsareshi idanunshi akankance with a very soulful voice yace "I want to undress" yayi maganan yanakai hannunshi wuyan jallabiyan shi yabude boturan yana kallonta kaman yanda take kallonshi tana tsaye kaman zata shige jikinshi zare jallabiyan yayi ya yar yarage just boxer ne jikinshi dark blue tundaga kirjinshi tabida kallo down to short dinshi dataga amike yake gabaki daya jikinta yawani irin haukace, ganin yanda take kallonshi yasa yakai hannunshi yakama hannunta yace "wanna touch me? Feel free I'm your big toy" yadaura hannunta daya kama kan kirjinshi yana shafawa ya lumshe idanunshi yana tafiya da hannun nata kasa yace "Mmmmm hands naki feels so gooood ajikina!" Sauke hannun nata yayi akan abdomen nashi da sauri ta fizge hannunta takai hannun da kanta saman katon abun dataga yayi kato jikin wandonshi that she's so curious about.

"Wai!! Jewel hannunki ya iya dumbuzo dick!

Auuuuch it feels soo flirtatious!" Ta sama saman boxer dataji ya jike take shafawa harwani lekawa take, ahankali Riyad yakai hannunshi yasauke boxer kasa hakan yabama dick din daman fitowa yayi wani swinging yana breathing in the quest na neman abinci, ware manya manyan idanunta Rashida tayi saikuma ta duko ta kalli dick, harwani lekashi dick din take dataga yana numfashi saikuma tadago kanta ta kalli Riyad dake kallonta cikeda so ta nunamai dick din da hannu tace "ciji" kan Riyad watsewa yayi yawani sa hannun yakamota zuwa jikinshi yayi cupping face nata da hannunshi kaman zai haukace yace "I'm so in love with you Rashida, everything you do karamin sonki yake why do i love you this much? Hmmm my baby? Yau kinga ciji but ciji me dadi ne wannan" Yayi maganan yana yana kaimata kiss yana tattaro riganta sama yadaga hannuwanta yacire mata yana kallon jikinta itama tabi jikinta da kallo ganin tafishi katon nono, saikuma ta kalli nashi jikin again ganin duk babu kaya ajikinshi saita kalleshi ta sakinmai murmushi saita kara kallon dick dinshi sai itama da sauri takai hannunta kan pant dinta tashiga daukewa kasa tana cirewa da sauri dan itama tayi tsirara like him yabita da kallo wani kalan mahaukacin sha'awa na shiganshi yanda take cire pant agabanshi, there's no single hair on her smooth wall, thighs nata duk sun jike because she's so wait, jefar da pant din tayi da gudu ta dago ta kalleshi tana murmushi daga ita sai agogonshi a hannunta, nononshi ta taba da hannu tana dariya saikuma tawani kama nata tana nunamai irin yayy nata yafi girma, wani kalan daukanta yayi ya sata ajikinshi da sauri ta daura hannunta ta waist nashi tana kankame bayan wuyanshi bakinshi yakai nata dasauri tabude bakinta ya shiga kissing nata tana ramawa cus taji yanda yamata dazu wajen switch na dakin yaje ya chanza light na dakin zuwa deem blue sannan yadawo gadon gently ya kwantar da ita kan gadon shi yayi kneeling gaban gadon ahankali yadauki kafanta yafara kissing tundaga kan toes nata, sosai numfashinta ke sauri sauri yana fita tanajin waiwayi masu shocking, yana kaiwa thighs nata yayi kissing tayi dan ihu. "Assssh yilillishhhh..." ta taso dan ganin mayeka matane takejin waiwayi haka daidai yana sauke bakinshi kan vijay nata yayi brushing tongue nata yana swiping nashi up, gigicewa

Rashida tayi ta ware kafafunta sosai tana komawa baya tarirrike zanin gado, swiping tongue din yayi down kafin ahankali yasauke bakinshi kan clits nata that was erect and it's a bit big and chunky clits kaman gindin karamin jariri dan it's so obvious, daya sashi a baki clits din feels like ya jefa karamin milkcost sweet abakinshi, idanunshi har juyawa suke yana tsotsan clits, yana shanshi kaman dick yakesha, ahaukace Rashida takai hannunta tai grabbing head nashi ta danna kanshi da kyau sosai awajen tafara surutu abirkice. "Assssshhhh!

Eeeeeehhh, uhhhhhhh! Rashida Almustapa Riyad sunana mota soda Ammi indomie, 0o00000000!" tahau kirawo duka sunayen abinda tasani tana bulbulo da ruwa totally lost, Riyad is chewing that damn Vijay! Brushing ko'ina like a professional painter da tool nashi which was tongue and lips plus nose and forehead duk yayi dama dama dasu a gindinta.......


EPISODE 82


Kawai he's passionate about Rashida he feels there's nothing about jikinta dabazai iya ci ko sha ba, soyayyan dayake mata is beyond wat kanshi knows shima din, tongue dinshi da bakinshi ya kafa kan tiny hole nata yana tura harshi shi yana f*cking wajen kafafun Rashida suka fara vibrating tafashe da kukan dadi sosai abinda mutumin nan ke mata she don't want him to ever stop, jikinta dadi yake mata sosai, ganin yanda takemai kukan dadin mahaukata yasa yataso yahayo gadon yana jawota jikinshi da sauri yace "sorry sorry nine" bakinshi tashiga kokarin kamawa da juice nata was everywhere har gemunshi da sajenshi da hancinshi har eyebrows nashi da forehead dinshi duka akwai juices nata dan da fuskanshi gaba daya ya jagwalgwala wajen, just to find ease for herself dan kaman zata shide takeji har lokacin kafafunta were shaking kafinma yabata bakin nashi ta karbe dasauri sauri take kissing nashi, taste na juice nata yabama bakinshi another different favor daya kara saukar mata da sha'awa while yataso ahankali yana ware kafafunta gently yashiga kai dick nashi wajen ganin bata hayyacinta yana karanto addu'a, ahankali yayi yunkurin tura head nashi kankameshi tayi alamun taji zafi but still bata dena kissing nashi ba, sake ware kafafunta yayi jikinshi na wani irin bari yana zabura yasake kaiwa ya danna with a slight strength dayasa tasaki bakinshi takalleshi alamun yanzu ba dadi takejiba, idanunshi har wani juyawa suke yana zabura sabida dadin daya faraji, murya chan ciki yace "continue kissing me, I will not hurt you today kinji dan Allah ki barni nayi wih zan mutu idan banyiba, Rashida I love cin gindinki" yayi maganan yana sake dannawa da kyar kan yadan shiga, bankarewa Rashida tayi sabida zafi yariketa da sauri yadakata kaman wanda ke lallaba jarababben yaro karya mai fitina yace "wait wait Jewel wai zansha nono"

Ahankali yakai bakinshi kan boobs nata yadaura bakinshi akan na dama yakai hannunshi left yafara zuka lumshe idanu tayi dadi kawai ke sauka jikinta, daddagewa Riyad yayi ya buga ciki kanshi ya shige Jiki Rashida na dan ihu. "Ahhhhhhh, Ohh'ohhh" tafadi amugun shagwabe irin ita bataso yadena mata dinnan, sararawa yayi yana shafa fuskanta yadago yana kallon fuskanta yanda hawaye suka taru a idanunta cus he is confusing her taji dadi, saitaji zafi, tarasa meyake mata haka, ita yayita mata na dadin, muryanshi rawa yake sabida yanda tiririn vijay nata yafara turara kan dick nashi daya shiga ciki yace "a.....bazan sake miki da zafi ba, don't cry I will give you Soda" cikin very weak voice tace "soda?" Gyadamata kai Riyad yayi yace "yes but you can't cry" yayi maganan yana share mata hawayen dake kokarin gangarowa daga idanunta alamun baiso tavi hakan vasa vace "| love when you kiss me, let's kiss" yasauke bakinshi kan nata dasauri ta karbi bakinshi suka fara kiss, he kissing her kaman a professional stripper that works at Las Vegas bar Rashida har ijiyan zuciyan dadi take saukewa tana kale bakinshi kaman yanda yake tando nata kaman dan iska, idan yayi getting nata to comply like this tabashi hadinkai just 3 thrusting in yake bukata zai shigar dashi cikin vijay din duka, gyara kafafunta yayi yana kissing nata kafin cikeda dabara ya daddage ya bugamata lafiyayyen gwatso dayasa tafashe da kuka sosai abakinshi harda shesheka cus wajen namata zafi, still yarike bakin nata yana kissing ya dage yamata the second one shima yakara shifting ya shiga, yana sauke ijiyan zuciya kafin ya gwale kafafunta this time around da bala in kyau ya durmamata kyakkyawan gwatso

dayasashi shigewa cikin gindinta gabaki daya shima sakin bakinta yayi yayi wani mummunan kara.

"Wayyyooo burana ahhhhhh, Jewel zaki kasheni yasin yasin!"Jijiyoyin kanshi har harbawa suke he can't believe he's having his second sex da Rashida, da kyar ya iya controlling kanshi ya kwanta jikinta ahankali batare daya sakin mata nauyi ba yanaso ya kara lallashinta batare daya fara cinta ba yace "bakison soda" kallonshi tayi tana sheshekan kuka saikuma ta dena kukan, lumlumshe idanu yakeyi yana kallonta yace "I love your p*ssy! Jewel bantaba ganin gindi irin naki ba! Gindinki is volcano!" Hannunshi yakai kan kumatunta yana shafawa murya chan kasa yace "I want to screw your p*ssy slow and steady, grinding you gently kaman ana nika egusi, ina baki some deeeeep sensational slow strokes dazasu ratsa bloodstream dinki, Jewel yau saina cinye miki duri wayyooo Allah inason vijay yarinyar nan" yayi maganan yana kawo fuskanshi dab da nata yace "look at me Jewel" ahankali take kallonshi, hannunshi ya daura kan nipples nata yafara murzawa gently yace "zanyi juyin reverse acikin hole din kafin na buga miki gwatso sassanya!" Motsi yayi a pussy kafin gently yayi hitting inside the pussy yana wani irin manna gindin nashi ciki, idanunshi na neman shutting down ita kuma tana biting lips nata, she's feeling pains and pleasure, gently yasake lashing nata another sensational stroke datajishi har maranta, ahankali yasake buga mata gwatso dan dadi taji yanda yadaki ciki, chan saiyawani karkace ya chakama left side na pussy wall nata stroke dayasa tashiga grabbing lips nata ta kankameshi sosai she's feeling dadi da zafi, yanda tamai ba karamin dadi yajiba rirriketa yayi shima kaman zai maidata ciki sannan yafara cinta da kyau amman ahankali yana playing da nipples nata sosai bala'in dadi takeji, lafiyayyen cin gindinta yayi yana mata wayau dazatai kuka saiya dakata yace soda, saida yagama kwakuleta kaman dagayau bazai iya karayiba kafin yajuye duka cum nashi cikinta bayan yamata lilis kaman maye baiciroba dan baiso tasake wahala maybe idan zaiyi later tai bacci ahaka har lokacin yana kissing nata.


EPISODE 83

Gabaki daya baiyi bacci ba he's just feeling her, he will needs to protect her and to make sure bataje wajen any man ba cus she's just like a 3yrs old yanzu dan anyone zai iya mata wayau, since memory loss baya taba sha'awa ko bukatan mutum.

Dan bacci ne ya kwasheshi shegen tashi da buranshi yayi yatadashi daga bacci ya kalleta har lokacin bacci take ahankali yashiga juya dick din acikinta har saida ta farka daga bacci wannan karan saida taita kuka hakan yasa da kyar ya kawo ya barta yatashi bayi yafada yayo wanka yafito yadauketa ruwan zafin yakaita yasata aciki wani kalan kukan banza takemai dukta gigitashi da kyar yasamu ta yarda yamata wanka yafito da ita wani t-shirt nashi white da short black daya kaimata knees yasamata kuma sun mata kyau sosai yasamata hijabi ya shimfida musu dadduma yajasu salla da yawanci wasa take saitaga yayi wani abu saita bishi suyi, yana idarwa yajuyo yakalleta yanda tarike cikinta tasake sakinmai kuka dasauri yace "yunwa kikeji"? Gyadamai kai tayi ashagwabe murmushi yamata yace "na cicciki na cinye dan abincin cikinki saisa, tashi muje lemme cook for my two Jewel the outer and inner one" tashi yayi yacire jallabiyan jikinshi ya ijiye ya rage shorts dasauri itama tafara kokarin cire rigan jikinta riketa yayi cikeda so yace

"wih kika cire rigan nan i will f*ck u again, hau babu lets go to my kitchen namiki breakfast my Raeesa" yaduka agabanta dasauri tahau bayanshi tana murmushi she loves yanda yake goyata, bayanshi dadi tun jiya daya goyata taji dadin.

Bude kofa yayi suka fito daidai sun fara hawa stairs takai bakinta daga bayanshi ta gatsama kunnenshi dataketa kallo cizo ihu Riyad yayi "wayyoo! Auch!" Kwashewa tayi da dariya sosai ta dirko daga bayanshi ta kwasa da gudu tana sauka daga bene dasauri yace "stop running Jewel stop dan Allah" ya shiga binta, guje guje tafara dashi ko zafin gudun bataji duba da yanda yacita tana dariya sosai shikuma ya damu karta je tafadi wani abu yasameta or his baby, ganin taki tsayawa ta maidashi shashasha yasa yahaderai yajuya yawuce yayi kitchen yace "nafasa baki sodan, we're not friends again" dasauri yayi kitchen yana tafiya kaman yayi fushi da gudu tazo ta rungumeshi tabaya tana dariya ita kawai tana sonshi tana bala'in sonshi, juyowa yayi ya kalleta yanda take dariya white teeths nata na showina kaman ha Rashida sarkindaure fuska ba, sai kyalkyala shi ko takeyi dariyan she looks super adorable, ahankali da dan damuwa kan fuskanshi yace "stop running" yamata alamun gudu tabishi da kallo saita gyadamai kai tace

"running" Dasauri yace "yes! Kidena is dangerous" Gyadamai kai tayi yace "let's go" bude kitchen din yayi dayake ana gyara bangaren shi so everything is neat, kujera daya cikin 3 chairs dake gaban island din yaja yadauketa yasata akai yadauki kettle na ruwa yatara ruwa ya jona a wuta for tea, yadauko egg cus that's the only thing daya iya yashiga fasawa sai kallonshi Rashida take, yanada kyau sosai, yanda he looks so serious yana cracking eggs saitaji bataso wasa takeso yamata, koyayita mata magana yana kallonta da idanunshi datakeso amman duk hankalinshi ya koma kan abinda yake, kwantar da kanta tayi kan island din tasa hannunta abaki tana tsotsa tai wani irin innocent face looking very sad kaman yarinyar da Mamanta ta mutu, sai kawai tafashe da kuka da saida Riyad yasaki one egg akasa dayake shirin cracking yajuyo yakalleta ya tsallake kwan yataho wajenta da sauri yana kallon yanda take kuka da gasken gaske yashiga tattabata yace "menene"? yahau taba kanta yace

"kanki na ciwo ne"? Yadagota yana zare hannunta daga baki yace "menene? Is something wrong with you, is my baby kicking you?" Yayi maganan yana kai hannunshi yana taba cikinta, ahankali ta nunashi da hannu zaro ido Riyad yayi yace "ni? Nine? Nike saki kuka"? Gyadamai kai tayi, tana daga hannu alamun ya dauketa kaman dai yanda yara ke rigima a daukesu. Dasauri Riyad dazaka dauka bita zaizai yaci ajikinta tsabagen yanda yakejin ta aranshi ya dauketa  kulle kafafunta tayi a waist nashi kai tsaye takai bakinta kan nashi tafara kissing nashi innocently tana sauke ijiyan zuciya na wacce tai kuka kaman tasami nono, shiru Riyad yayi yana kallon yanda take kissing nashi yana having wani banzan erection, abin ba karamin tadamai sha'awa yayi ba, ijiye fork dake hannunshi yayi a gefe ya matseta ajikinshi gamgam yana kissing nata back jikinta namata wani dadi, yanda yaji nipples nata sun fito yasa yakai hannunshi yana murza boobs nata. "Uhmmmmm Mmmm" take numfashi abakinshi making sound tana sake bankaromai kirji dayaji No he just have to shift pants nata and bangs this rigiman nata out of her body in this kitchen shorts nashi yaja kasa yadaga kafafunshi yacire ya cillar chan wajen kofan shigowa kitchen din, sannan yaja wandonta kasa shima zuwa guiwa yasauketa kan island din yana kissing nata still shi yana daga tsaye ya danna mata buran da karfin bala'i da dambe ya shige ciki tana kankameshi batare datai kuka ba cus tasoma gane shiga da zafi ciki da dadi, daidai lokacin landline na gidan yahau ringing but ina kanshi baya wajen, murje Rashida kawai yake bana wasaba yana murxa boobs nata ta saman riga ayanda tasa sha'awa yakamashi baida patient na slow sex hitting pussy dinta yafarayi a island din da karfi tanajin zafi but dadin kiss dana murza boobs ya rinjayi zafin jikake.

Fattt! Fattt! Fattt! Kaman ana fasa icon block itakuma takai hannunta ta daura saman bombom dinshi nashi tanajin yanda yake tsukewa idan yana buga mata gwatso hannunta na motsi na mugun burgeta, shafa bombom nashi datakeyi yasa yasaki bakinta. "Ahhhhh Jewel gindinki yafi na kowa dadi aduniya! Ahhhhhh wayyyo zan kawo zan kawo Jewel kaciyata namin zak....

" Bugo kofan kitchen

din da akayi yasa yajuyo da kanshi da sauri yayi ido da ido da Haleema data shigo daidai yana sakin wani malalacin involuntary sound yana kankame pussy nata yana exploding in her pussy jikinsa 

nawani jerking da sauri ya dauketa yana juyawa da ita batare daya bari Haleema taga jikinta ba, she can see his his nakedness but not Rashida, yafito da dick dinshi dake diddiga daga jikinta da kyar yaja wandonta sama yajuyo yakalli Haleema datake tsaye gaban boxer dinshi dake kasa nan wajen kofa strictly yataho ba kunya yana rikeda dick dinshi that is still erect and dripping yace "who gave you permission to shigo side dina? Get out!".

 Bata taba tunani ko tsammani cewa Riyad zai iyacin wata haka irin wannan style din ballema har yayi sambatu hakaba kaman yau yafara samin mace, yanda zuciyanta yakama da wuta batasan sanda idanunta suka shiga kuna ba cikin mahaukacin kishi tace "na shigo din ai isa da iko tasa na shigo tunda kai mijina ne ba dadiro na ba, jiya I called you kacemin baka cikin mood look at abinda kakeyi" tanuna Rashida data turo baki tana kallon Haliman dataga tana magana da Riyad dinta, Haleema tace

"wata kakeci saikace bakatabacin wata macen ba Riyad" wandonshi yashiga sawa tass yagama sawa sannan yakalleta babu kunya ko wani dar yanuna kofa yace "get out" kallonshi tayi ganin yanda fuskanshi yasa tajuya zata fita shima Riyad yajuyo kawai ganin Haleema yayi tabiyo ta gabanshi da gudu tayi kan Rashida dake tsaye awajen har lokacin kan nipples dinta sunyi baro baro a riga, tadaga hannu zata kaimata duka karaf Rashida tarike hannunta Haleema ta kasa kwacewa dudda tanada memory loss but karfinta na nan, hadarai Rashida tayi tana turo baki cikeda fushi tawani tura Haleema baya da karfi hakan yasa Haleema ta taka egg da Riyad ya fasa akasa awajen yawani jata sai kasa timmmm Rashida tawani fashe da dariya tana tsalle tana clapping dasauri Riyad yayi wajen

Rashida dayake mugun ji da ita ya rungumeta yace

"stop jumping Jewel muje muje" yakamata yawuce da ita sama adakin shi yatasata yana rufo kofa yasauko kasa yasami Haleema kasa inda take tana kuka sosai mai tsuma zuciya ya rungume hannunshi yana kallonta yace "today should be the last day dazaki shigo side dina idan ban nemeki ba" cikin fushi ta tashi tace "tunda ka ijiyeta kana iskanci ai dole" dan tabe baki yayi yace "wat do you expect?

Kaman yanda na aureki haka na aureta, yanda nake baki hakkinki haka itama nake bata, out!" Yanuna mata kofa yace "I will see you in 2days nagama kwananta" tashi tayi tana tahowa tanaji kaman ta kasheshi tawuce tafita daidai Sarkin Gida yana zuwa da basket da Ammi ta aiko musu da breakfast da maganin Rashida da kayan sawa kuma ya karba.

Sama yakoma da maganin da abinci yana bude kofa yaganta jikin kofan tsaye tana ganinshi ta rungumeshi tana turo baki saikuma tafara hura hanci murmushi yamata yace "muje kici abinci" waina yazuba mata da miyan taushe da nama tass ta cinye waina kusan 8 yana mugun mamaki yanda takeci haka yabata fresh juice da Ammi tayi ta shanye da ruwa yabata magani da kyar tasha tai gyatsasai kawai tahau jikinshi takai hannunshi saman boobs nata murmushi yayi wih he's loving this Rashida matse mata boobs yahauyi saikuma da kanta tasa hannu cikin Riga taciro boobs din waje gurza ata boobs din yashiga yi tana lashe baki saikuma ta tashi tashiga cire wando yanda taga yana mata, matsar da kwanukan abincin Riyad yayi ya fizgo bargo daga gado ya kwantar da ita akan carpet yashiga kwakule mata kunkuru, mugunci yamata yanzu yama manta zaije fada Rashifa kawai yakeci saida tafashe da kuka sosai sabida zafi sannan ya iya yadakata tahuta yaciga.

Lalata Rashida kawai Riyad yake da abubuwa da dama yana cinta har dare abu daya suke hutawa kawai take taci abinci tai kat su fara.


EPISODE 84

Ganin tayi bacci yasa yatashi ya fada wanka ya shirya cikin shiga na ban girma harwani glowing yake yafito fadawa na zubewa yana kallonsu yace

"ya akayi kukabar Haleema ta shigo" Sarkin Gida yace "gafarceni Sarkina harta juyafa bamuyi tsammani ba tajuyo ta keto da gudu ta shigo toh bazanu iya biyota ba saisa na kira dan sanar da kai but ba'a tababa" wucewa yayi zuwa flat na Ammi bata falo hakan yasa yawuce sama gaban dakinta yayi sallama daga ciki tace "shigo" shiga yayi tana sauna tana kokarin linke some kaya anatse ya zauna kusada ita yace "ina yini Ammi" "Ipy lau yamai jiki?" Ahankali yace "dasauki Ammi tana bacci" gyadamai kai Ammi tayi tana kallonshi saikuma anatse tace "Akwai magana a bakinka talk to me" dan shiru yayi sai chan anatse yace "Ammi inaso nafada miki wani abu idan kin yarda I will do it idan baki yardaba zan hakura" yayi shiru chan yace

"Ammi inaso na sauka daga kujeran sarautan nan!" Sosai Ammi ke kallonshi saikuma chan tace

"menene dalilan ka"? Anatse yace "my biggest reason shine Ammi I don't have passion for leadership mutane suna bina abaya yazama nine jagiransu" yayi shiru yace "woman tasani on that sit sabida personal reasons nata, tun ina yaro bantaba kwadayin ko hararo kaina nazama sarki ba, Ammi I feel I'm not competent enough, everyday ina kwana ina tashi ina tunanin wannan nauyin dake kaina, and lastly Ammi I want to protect Rashida banso na zargi kowa but nasan this house nada sa hannu in her condition Ammi duk randa akasan kuma tanada ciki zasu iya halakata da bunda ke cikinta already bana Mrs Bugaje magana ta nema mata transfer zata karba mata zamu bar kasan muje wani kagar takarasa school achan, and Ammi is not just us 1 plan on taking you da Munir dukanmu are leaving this house Ammi" kallonshi Ammi take saikuma gently takai hannunta saman kuncinshi ta shafa tana kallonshi tasan waye dandanta ita kanta tana tausaya mishi, Riyad is not a king that for a fact she knows itama ta gaji da makirce makircen gidan, Lumshe idanu tayi tabude ahankali tace "Riyad anything kakeso I will always support you with my love and prayers Allah yasa hakan ne mafi alkhairi" rungume Ammi yayi dasauri yace "thank you Ammi nagode" murmushi tayi tace "tashi kaje karta tashi" ahankali yace "kafin naje zanga Baffa and Gwaggo da sauran yan uwana na sanar da su kafin nafadi afada"

Gyadamai kai tayi yawuce bangaren Gwaggo shiru sukayi duk basuji dadi ba but then they supported him Kabeer sai dadi yakeji duk Riyad na kallonsu yace "zanyi sanarwan gobe agafa".

***

Zaune take adaki around 8:00 in the morning sai soshe soshe take wayanta yahau ringing hannu tamika tadauka takai wayan kunne cikeda girmamawa Haleema tace "Mom kinji abinda nakeji kuwa wai Riyad zai sauka amatsayin sarki gobe zan sanar a fada wata baiwa dake aiki a bangaren Gwaggo ke sanar dani" tashi Mom tayi dasauri ranta yayi bala'in baci tabude baki zatai magana sai gefen fuskanta ta wajajen bakinta yay ja ga kurajen sun feso mata last night yashigan mata mugun kaikayi ta shiga sosawa kaman mahaukaciya har wayan na faduwa daga hannunta.

Tajuya takalli kanta a madubin dakin yanda fuskan nata yayi rudu rudu tace "wat is this borun jini nakeyi ne"? Ta tanbayi kanta tana cire rigan jikinta tashiga kallon jikinta yanda kujeran sun fito ko ina 

sunyi dabbare dabbare kaman makero tai tsaki tadauki wayanta tana kiran wani number tace "zoka kaini asibiti Idris"ijiye wayan tayi ta daga zaninta ta ta duka gaban madubin tana kallon gabanta kurajen sun feso mata agaba da wajajen takashi ga kaikayi da zafi duk suna mata da kyar ta shirya tasaka kaya batare data iya saka pant ba ta yafa wani arnen gyale ta sauko tana tafiya ahankali har zuwa wajen motan driver yabude mata baya tashiga yaja motan haruwa wani private clinic haka zuwa wajen wata Dr ta duk ta dubata tasa wani abu kaman na share kunne ta debi sample na ruwan kuraje tabata akai lab sannan tazauna Mom tace "wai borin jini nakeyi ne ko chicken pox? Amman ai basu fitowa area na vagina" murmushi Dr tayi tace "calm down Ma we will get the result soon" almost 20min aka kawo result na test din karban result din matan tayi tashiga warware wa tana dubawa saikuma matan tadago tace "Hajiya l've been your Doctor for a long time now, and I know mijinki almost 2yrs Kennan da rasuwan shi, can I know kinyi having sex recently ne?" Faduwa gaban Mom yayi ciki Baaba yamata? Kwata kwata ita ba yar iska bace, but ranan da aka cirota daga police station da Papa yasa cus bazai iya zuwa da kanshi ba ya aiko mata lawyer shikuma Baaba ne yazo daukanta yakaita wani gidanta anan kano dan dare yayi babu flight the next day ne zasu Kano she remembered Baaba yabata wani drink tasha dan ya kwantar mata da hankali bayan tasha she just grab d boy tacemai make me happy kota sami natsuwa rabonta da saduwa tun mijinta na raye haka yaron yacita kuma daga ranan bata karaba, ko murmushi batamai dan batason raini iya kanta dashi ta sasu aiki dan boy dinta ne su mata running errand, adan rude Mom tace "wait ciki nayi ne bakince bana growing egg bazan iya ciki ba? Ciki yaron chan yamin?"Girgiza mata kai Dr tayi tace "No Hajiya you're not pregnant" Dasauri Mom tace "to toilet infection ya samin ne dake kawomin kurajen gaba da kurajen gefen lips?" Ahankali Dr tace "please calm down Hajiya kibani attention naki although this is the first test I will advice kije wani asibiti and run the second one or lab just to be sure" Sosai Mom ke kallonta gabanta na dukan uku uku anatse ahankali DR tace

"Hajiya kinada HSV-2". Yankewa gaban Mom yayi yaadi ita bama ta taba jin wannan sunan ba balle tamasan menene shi ko wata kalan cuta ne, baki tabude zatai magana but maganan yakasa fita muryanta yarike, anatse Dr tace "HSV-2 yana nufin herpes simplex virus type 2, type 2 din yana nutin kinada ganital herpes" faduwa gaban Mom yake da kyar tace "Innalillahi wa innailaihi raji'un, La'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu mina zalimina" saikuma tayi shiru tace "ita cutar menene ita kaman HIV ce?" Dan shiru Dr tayi tace "kusan hakan ne dan itama virus ne banbancin shine ita Hlv garkuwan jiki takeci wato immune system itakuma wannan kurajen al'aura ce sannan itama takama ka takamaka kenan har abada sai wani iko na ubangiji ke warkan dakai". Bari ko'ina najikin Mom keyi tama kasa magana Dr tace "shi ganital herpes ana samunsa ne idan kahadu da mai ita ta hanyar saduwa idan ruwan maniyinsa ko maziyinsa ya shiga jikinka kota yawun baki, kuraje ne masu azaban zafi da kaikayi dakuma ke fashewa suyi ruwa sannan duk inda ruwan yataba kurajen zai fito awajen, ciwon zai iya kama duka jikinki kokuma gindinki thighs naki lebenki wajajen idanunki dama ko'ina, sannan yakan iya jawo abinda ake kira da viginal wart wato tsutsan gindi" rawa jikin Mom keyi tace "kinga Dr ko billion nawa kikeso zan biyaki ki warkar dani, wani kalan kurajene haka dazanyi suna ruwa wari kenan zan fara" anatse Dr tace "ban fadi rashin lafiya, da zazzabi, inflammation da burning sensation na azaba dazasuna miki ba su kurajen, Hajiya you're educated at this stage bawai I'm blaming you for seeking pleasure bane nasan bakida miji ke widow ce but educated woman like you bai kamata tai sex ba protection ba menene amfanin su condom eh?" Kai! Rawa jikin Mom yake bata taba sanin something like this will affect her ba over less than 5minuted mistake sex datayi da Baaba ba wanda ma ranta yabaci sabida gani tayi girman banza ne da karfin banza dan ko tsohon marigayinmijinta daya tsufa yafi Baba iya hakar mace, azuciye tace

"wih wih saina kulle shi wih saina kulle Baaba, dan uwar Baabarsa yasan yanada kwankwamai ajikinsa

ya kwanta dani bana hayyacina ya zubamin" saikuma tafashe da kuka tana dukan kirjinta yace

"ni zai sama cuta haka? Ai da wannan Allah natuba gwara HIV I have money to take care of myself I can live healthy for years but not da cutan da kuraje zasu cikamin gaba suna fitar da ruwa ina wari ina susa masu cutan susa kaman mahaukata suke zama fa" Saikuma ta daura hannuwanta akan bakinta gabanta har faduwa yake tayaya zata gayama Papa she slept with one of his security

Papa dayake ganin mutuncinta sabida tacemai bazata kara aure ba tunda mijinta yarasu? He gave her Baaba da Idris sudanyi protecting nata and run errands tunda tace lallai lallai saita koma kano tayaya zata fara Kodai karya Likitar nan kemata an hada baki da itane maybe is just borin jini duk ta tada hankalin kanta tashi tayi ta suncuki jakanta dasauri Dr tace "ki tsaya ki amshi magani" cikeda fada Mom tace "I don't have herpes" tawuce tafito tana tafita tana bubbude kafafu kaman wacce akama kaciya sabida yanda kurajen kemata zafi da kaikayi da kyar ta daure takai mota tana shiga takai hannunta tafara susa sosai tace "ina Baaba Idris?"

Tada motan yayi yace "bansan inda yaje ba Hajiya tun safe yafita" gurza gabanta take sosai kaman mahaukaciya da zani, wayanta na ringing ta kalla ganin Haleema ne yasa tadauka cikeda masita tana susa tace "Haleema leave me alone naji da kaina please haba! Yarinyar nan jekiyi duk yanda kikaga dama da ita, kiyi takanki" ta jefar da wayan tace

"kaini wani hospital mai kyau Idris" wani hospital sukaje data bude wajen ma is worst than before duk tagama sosashi Dr yamata confirming is herpes they need to admit her dan duk ta soshe kurajen sun suma zama ulcerated, akace tama cire kayanta gabaki daya tasa gown na hospital and tabude kafafunta tadena hadesu tana infecting ko'ina gindin da thighs din need breeze, duk tauri da bakin zuciyan Mom saita fara kuka wannan wani kalan cutane haka just last night fa taji kaikayin nan da safe ta tashi taga kuraje sun feso yanzu kuma gashi sun dawo wani iri and mahaukacin tsinannen kaikayi suke mata tana tabawa kuka su dawo ciwo su fara zafi kafin kace me mugun zazzabi yarufe Mom.


EPISODE 85

Shigowa dakin Dr yayi da nose mask da handglove yanda yaga condition na mom yasa yace wazata kira, Who is next of king nata, rasa wanda zata kira dan batada Mama yasa takira Babanta ta gayamai gata hospital yace zaizo, wato idan Allah yatashi kama mugu within blink of an eye zai iya hakan wani irin worsening condition na Mom yake as minute goes by, anmata allurai na kashe kaikayin da kashe zafin amman kaman karawa ake gashi yanda take susa jini na fita yasa aka daure hannayenta azaban yamata yawa tafara ihu da kuka Babanta daya biyo available flight yazo dayashigo dakin datake ita kadai saiya yajuya da gudu yace

"Subhanallahi" tsigan jikinshi na mugun tashi dan yanada trypophobia cus kurajen sun hadu sunyi dot dot gasu agaban vijay nata daya gani abude ya kalli Nurse yace "menene haka? Me suka fito mata haka"? Anatse Nurse tace "Sir yarka nada ganital herpes, bamu aba samin wanda is serious haka kaman nata ba Sir" sosai Papa yace "wani irin ganital herpes mexai kawo mata" ihu Mom tayi.

"Wayyooo Papa, Papa kace su kwancemin hannu karna haukace su banni na sosa, Papa ka taimakeni" juyowa Papa yayi yana kauda fuskanshi dan baya fatan abinda zaisa ya kalli wajen nabiyu yataho wajajen kanta yana kallon na gefen lips nata zai tabata dasauri Nurse tace "kana tabata zaka dauka kasaka gloves" arude Papa yakoma baya yana kallonta Yace "Meya sameki haka Hajara"?

Kuka sosai Mom take bazata iya fadama Papa yanda ta samuba yanda takeyi yasa anatse Papa yace "Hajara kinada hannu asama kishiyar kanwar mijin ki HIV ko baki dashi"? Kallon mahaifinta Mom keyi tana kuka sosai takasa magana Papa yanunata yace "wih wih kiji soron hakkin mamaci da yarta, tell me the truth today do you have hand did you conspire da Jummai?" Gyadama Baba kai tayi tace

"ninai inntaiting plan din Baba"

"Innalillahi wa innailaihi raji'un" Baba yafadi yace "all my life ni lawyer ne nine harnazo mukamin danake ayau, l've seen so many evil people da sauransu harda wayanda intentionally sukema wasu wayau su kwanta dasu su basu Hiv but naki Hajara is different, kin kira me HIV kikasa sirinji kika jawo jininta kika bada akaje aka juyewa mai ciki a jiki HASBUNALLAHU WA N'IMAL WAKEEL KAICO!

Hajara! Hakika hadisin Annabi ya tabbata inda aka ruwaito yace "lallai Allah yanama azzalumi talala duk randa Allah ya damki axzalumin nan wih babu mai cetonshi, Hajara I can't save you today I can't!

Hakkin yarinyar cikin nan da hakkin wacce ta mutu ke binki" Mom na kallonshi tana kuka tace "Baba zan warke fa" Sosai Baba ke kallonta saikawai yatashi yace "inada meeting I will pay everything zanma barmusu kati har abinci ana baki Allah baki lafiya" yayi kofa Mom na ihu Papa, Papa amman ko wiagowa baiyiba.

**

Tun jiyan nan datai bacci take bacci har yau yanda ya tsorata har saida yakira Dictor Dr yacemai is normal dama day 2 maganin brain magani ne that put patient into sleep dan suyi aiki akanta karya damu.

After 1 yashigo bangaren yau dayay announcing a fada zai sauka saiyaji kaman kaya sun sauka akanshi side nashi ya shiga yawuce sama yabude kofa bacci take but saiyaga bakinta is moving dasauri yayi wajen yazauna abakin gado yatabata yace "Jewel" ganin bakinta yacigaba da motsi yasa yakai kunnenshi bakinta da sauri.

"Mom, Mom dan Allah kar akasheta kawai dai aje a wurgar da ita chan wata uwar duniya" dasauri ya kalli Rashida sai yakara maida kunnenshi saitin bakinta saiyaji ta chanza murya zuwa na namiji tace

"kashe wayan Haleema batada hankali!" Bala'in faduwa gaban Riyad yayi yadago da kanshi yana kallonta saiya sake maida kanshi yaji tai muryan mace tace "wat do we do with her"? Cigaba da maimaita maganan tayi in repeat dayasa yashiga dagota yana girgixata yace "Jewel Jewel Rashida" amman shiru bakinta kawai maimaita maganganun suke wayanshi yaciro yashiga kiran Dr yana gayamai Dr yace "Alhamdulillah she's regaining memory nata ne maidata ka kwantar idan tanajin sanyi cover her and let her be zata tashi lafiya lau and daidai In sha Allah".

Maidata yayi yarufe saikuma kawai yaji bazai iya daurewaba yafito yasauka kasa direct side na

Haleema yawuce ranshi abace masu announcing zuwanshi ko gamawa basuyiba yafada side din yawuce falo bayi na mata massage yanayin fuskanshi yasa kowa ya waste ta haderai tana dauke kai dan haushinsa takeji gabanta yayi bai bata lokaci ba yawani fizgota yana twisting hand mata ta baya da saida tai ihu tace "mehaka"?.

Jikinta na dan rawa ganin yanayinahi tace "karyani zaka....." ganin yanayin idanunshi yasa takasa magana yace "kinada hannu a batan Rashida?"Ayanda tambayan ya daki kanta batasan sanda baki ta ya shiga rawa ba takasa magana wani irin hankadata Riyad yayi saida tai mummunan fadi yayi

¡hu da gidan ya ansa yace "did you have hand in kidnapping Rashida?" Rawa jikin Haleema yake takasa magana kalle kalle Riyad yashiga yo ganin plate yasa ya dauka ya buga akasa ta duka yadauki wani sharp part yayi kan Haleema dashi kaman zai chakamata ta mutu ihu tayi tace "wih zan gayamaka gaskiya karka kasheni" tsayawa yayi yana kallonta hakan yasa tace "yes nina kira Mom dina but batai komiba sai kawai na gwada number Mom naka naji ya shiga I told her na tsani matanka tace karna damu she knows wat to do da ita da Abbana da Mommy na sukai komi wlh ni ina gida I was even crying ina cemusu karsu kasheta basu jiba nace ni kawai su samata HI....." tasssss Riyad ya kwashwta da mari kawai ya shiga dukanta yace "did you know my wife is pregnant da dana" da kyar yakira aka shigo yasa aka wuce da Haleema gidan yari, yashiga kiran yan sanda Waziri na zaune yan sanda sukazo suka daukeshi da matarsa da ita Haleema aka wuce dasu da solid evidence na confession na yarsu dan yayi recording fada gabaki daya yadauki labarin Gwaggo kuka take ganin gidanta gidan data taso ciki an maidashi gidan makirci.

BOOK YAFARA ENDING 


EPISODE 86

Mom na kuka kawai saita tashi Mom na "Rashida Rashida" amman tabude kofa tafito dasauri Papa yahade hannayenshi yace "Rashida dan Allah kuyafe mata, dan Allah kiyafemata" ahankali Rashida tace "abinda ni tamin na yafe but na Mamana suka hadu a lahira saisu zanta" tana maganan tawuce Papa yabita da kallo cikeda tausayin yarsa Ammi tace "Allah ya yafe mana gabaki daya Allah yabata Ipy" itama tabi bayan Rashida Muji yace "Allah yakara sauki" yayi gaba ahankali Riyad yace "Allah bata Ipy" shima yawuce Munir biyedashi suka fito, daidai Muji zai shiga mota wayanshi yahau ringing ciro wayan yagani ganin bai gane number ba yasa ya dauka daga ta dayan bangaren yaji ance "this is chef warden officer na gidan yarin mata dake nan Abuja, I called regarding wata inmate namu mai suna Jummai, "So muna nan asibiti da ita sabida condition nata ya gagarin clinic namu na prison, likitoci sun bukaci next of king nata tabada sunanka" cikeda bacinrai

Muji yace "I'm not her next of king takira family nata mana ha'a" adan hankali mutumin yace "¡ learnt ex wive naka ne sir, can you come cus condition nata is something else" dan shiru Muji yayi yana tuna Mom dasuka gani yanzun nan sai kawai yace "inane wani ward?" "A.E" zare wayan yayi daga kunnenshi yakalli Riyad da Munir dake kallonsa yace "muje general please i will explain idan muna hanya" shiga mota sukayi har General inda mutumin ke jiransu Rashida tayi tsaye tana kallon same A&E da aka kwantar da mahaifiyarta nan aka kawo Jummai itama, mutumin yace "Dr sunce tanada Hepatitis B & C, banda haka akwai HIV, sannan dawani extreme ciwon ciki that has to do with liver nata sabida hepatitis din" murmushi

Rashida tayi hawaye na faduwa daga idanunta na farin ciki kawai yau takara yarda da Allah! Takara imani! Mugayen mutane feels Allah baya kama mugu a duniya saidai lahira wih they're wrong, look at wat Allah did to this people that hurt Mamanta, hannunta taji an rike dasauri ta dago kanta Riyad ne yana kallonta ahankali yace "if you don't wanna go inside zamu iya tafiya" dasauri Muji yace "yes" kallonsu tayi sai kawai tamusu murmushi tace

"inaso naje" sosai Riyad yake kallonta sai kawai yawuce ciki da ita yana rikeda hannunta har lokacin suna bin bayan mutumin ihun Jummai kawai akeji da sumbatu da wasu officers mata agefen gadonta an samata handcuff a hannu daya, tarike cikinta kafafunta sun kumbura sabida Hepatitis din dudda bata iya bude idanu da kyau but tana ganinsu taganesu tawani yunkuro kaman tiger da sauri

Riyad ya maida yar matarsa baya, matan police din na maidata gado, Jummai tace "wih wih itace tasamin HIV sabida na sakama uwarta, kifadama mutane yanda kika samini cus bantaba kwana da wani ba banda mijina

Hannunta Rashida ke kallo da akwai wani katon ciwo a wrist nata daya Soma warkewa ta kalli officer tace "how did she get that wound" dasauri ya kalleta yace "ohh tacewai randa za'a kaita police station daga fada handcuff da aka samata yaji mata ciwon nan" murmushi Rashida tayi aranta tace

"maybe that's how she got the HIV, duk wani karfe ko allura idan jinin me HIV yataba shi virus din nazama akai for 50days kafin ya mutu saisa aka hana amfani da any sharp option ajikin wani, wani kuma yayi amfani dashi" Muji dake kallon yanda Jummai keyi tana rike cikinta dake masifar ciwo yace "I will give you family number ta ka kirasi I have nothing to do here" Yanada number yan gidansu suka juya Jummai na ihuuu wayyooo cikina

yakaru tayaya zanyi rayuwa da HIV da hepatitis da liver da ciwon ciki kumin alluran mutuwa cikina wayyo cikina azaban yamin yawa, faduwa hawaye

sukayi daga idanun Rashida tana tunawa da Mama Allah yabiwa Mama hakkinta Alhamdulilah wannan karan motanshi Riyad yayi da Rashida ya bude mata ta shiga tana boye fuska shikuma yashiga bangaren driver su Mom suka shiga mota daya Munir naja kowa yatati.

Sunyi nisa a hanya ya kalleta ganin yanda take kallon hanya yasa yace "Me ciki"? Dasauri ta kalleshi saikuma ta dauke kai dasauri tace 

kalleshi saikuma ta dauke kai dasauri tace "nine me ciki"? Murmushi yayi ya mika hannunshi yana kama nata ahankali yace "Rashidahh..." Faduwa gabanta yayi dasauri tace "uhm" ahankali yace "ina sonki Rashida sosai" dan dago da kanta tayi ta kalleshi shima ya juyo ya kalleta yana murmushi kafin yamaida kanshi a hanya yace "bazaki ce kina sona ba ko har yanzu baki sona" da gangan tace "eh" murmushi yayi yace "but memory lost Rashida loves me kaman ba gobe" akunyace ta manna kanta jikin glass tace "kadena tunamin ni" Dan murmushi yayi yay shiru sai chan yace "zan sauka daga kujeran sarauta" dasauri ta kalleshi lumshe idanu yayi yace "I want a peaceful life away from all this chaos, I want environment dake da yarana zaku taso peaceful da Munir and Ammi na, nariga nayi applying for transfer naki na school Mrs Bugaje tacemin on Monday nazo na amsa, I want us to settle down a any Muslim country of your choice, ko Dubai, Qatar, Saudi ko Oman wanne kikeso wife"? Shiru tayi saikuma ta kalleshi ahankali tace

"idan sabida nine zaka sauka a matsayin sarki karkayi! I can protect myself beside kaga makomar mugayen, nariga na yafe komi nima, I want to open a new chapter I want to work on how to be a better person for myself and my baby, work on how to be more forgiven and less stubborn so karka sauka kaji" dan murmushi yayi yana kara matsa hannunta yaji dadin maganganunta sosai ahankali yace

"you're not the only reason nima banason sarauta

Jewel, please ki banni na sauka kinji"? Gyadamai kai tayi tace "Allah yasa hakane mafi alkhairi" ahankali yace "Ameen, bakice kina sona ba" fizge hannunta tayi tana kallon window tana murmushi ahaka har sukakia gida tana tuna komi daya faru agidan parking yayi yafito yazagayo yabude mata yana kallonta fitowa tayi tana dauke kai Baice mata komiba suka wuce har kofa yabude ita tafara shiga komiba suka wuce har kofa yabude ita tafara shiga yabiyota abaya yana rufe kofan zata wuce kawai taji ya fizgota ya manna ta jikin door yakai bakinshi kan nata runtse idanunta tayi da gudu, murya chan kada yace "since you don't wanna say you love me lemme make you say it" kissing nata yafara wih she couldn't resist tanason mijinta ahankali tafara kissing nata back dauknata yayi yana cire hijabin yana yardawa yayi sama da ita ya kwantar agado yana kallonta kaman yanda take kallonshi kafin yafara making wani crazy sweet love making da ita datake feeling soyayyanshi in everybone na jikinta da saida tafara kuka tana gayamai she loves him nikuma nafito nabasu wuri

**

BAYAN 2YRS

MUHAMMAD BIN RASHEED MEDICAL UNIVERSITY.

Babban hall ne da mutane suka cika makil ga Ammi rikeda wasu kyawawan yara da bazasu wuce lyr ba mace da namiji masu kama sak da Riyad, ga Munir zaune kusada wata kyakkyawan yarinya yarike mata hannu, ga Muji sanye da fararen glasses dress as a king, ga Mrs Bugaje da glasses itama zaune tana kallon gaban halka ha Riyad shima dayayi shiga ta alfarma yana kallon gaban hall din daidai nan speaker yace "I will call on overall best student in medicine this year 2024, ladies and gentlemen can we all give a standing ovation for DR MRS RASHIDA ALMUSTAPHA RIYAD" aka tashi ana tafi yaran na tafi saiga Rashida tafito sanye da graduating gown nata tayi bala'in ta sanya wani hadadden atampa da SAPPHIREBYAISHASAMBO ta mata dinkin tundaga

Nigeria ta aiko mata sun mata kyau kaman bata haihuba ta taho tana tafiya ahankali kowa na gaisawa da ita ana tafi kaman ba gobe barinma

Riyad dake tafi dasu Ammi da mahaifinta ta karbi award nata da certificate nata aka bata podium tayi award nata da certificate nata aka bata podium tayi magana tsayawa tayi kowa ya koma ya zauna ta kallo inda Riyad yake zaune daya mata alamu da kai tai magana, ljiyan zuciya ta sauke da kowa yaji anatse tafara turenci mai bala'in dadi tace "this award and this certificate is for my late mother!" Aka fara tafi again, tasake yin shiru hawaye na kokarin zubomata a ido a hausance tace "Mama nazama likita yau! I did it Mama" hawaye yasake fadomata daya idanu, Aka bata tissue ta goge tace

"Mahaifiyar data haifeni has HIV, ta haifeni da shi, tayi protecting dina ban samu ba, I wanted to become a Doctor because of my mother itace inspiration motivation and everything nawa I wanted to become a Doctor to cure my mother but she died!" Tayi shiru kowa na hall din kallonta yake, ahankali tace "thanks to super supportive husband dina! His love support and care yasa na zama Dr da support din the best second mother da Allah yabani yanzu My Ammi" Ammi tashare fuskanta, tace "da support din Babana, my cousin" takalli Munir tace

"and my mentor" tayi shiru sannan tace "this is for all of you and for my twins ZAINAB AND ZAYYAD!"

Ahankali tace "thank you" tafi aka shiga mata tajuya zata tafi Dubai president yatashi da sauri akasa ta tsaya, anatse yace "call your family to the podium" Ihu aka fara a hall din, tasowa Ammi Riyad Munir da matarsa Muji da Mrs Bugaje duk sukayi sukazo hall din sai tafi ake yaranta suka rungumeta ta dauki Zayyad Riyad ya dauki Zainab, president yace

"inaso ku shaida cewa sabon hospital dana gina na bawa this best student Mrs Rashida Almustapa Riyad shi" ihu aka fara ana tafi Rashida tafashe da kuka President yace "with a brand new car, a plot of land and a house plus scholarship from government dina to further your study anywhere kikeso around the entire world plus all expense paid trip to 10counties of your choice you and yourtrip to 10counties of your choice you and your family" ihu ake Riyad saida yaji hawaye yazomai Ammi tafashe da kuka she wish Mama was here to see Rashida, president yace "a good daughter like you and a brilliant student like you deserves the best, go my dear excel in life Barakallahu fiki Allahumma Barik" akahau ihu Rashida ta rungume Riyad tana kuka sosai duk suka wuce.

Rashida tai kuka ranan tai kuka har saida Riyad yafara mata fada sabida yanda yaransu suka fara kuka, yau tayi kewan Mama, she wanted Mama to see all of this things, she wanted Mama tasaka English super wax da Gwaggwaro dazai taba silin Allah sarki Mama Allah ya jikanta Allah yasa mucika da imani.

Gida suka koma inda aka shirya mata graduation party tadan saki ranta but not mugu ganin haka yasa Riyad yajata ciki and makes her super happy ya goge damuwan kafin suyi wanka su fito and continue d party.

END!!!!!!

TO ALHAMDULILLAH

JAMA'A NA GAMA SANYI DA ZAFI

KUSKUREN DANAYI CIKI ALLAH YA YAFE MINIC

SAIKUN JINI IN MY NEXT BOOK IN SHA ALLAH





Post a Comment

0 Comments