TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Makauniyar soyayyah page 49-50

 *STORY & WRITTEN*


                *BY*



*MARYAM AHMAD PAKI*




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽




_Wannan shafin naku ne ‘yan Kainuwa Writers fans na facebook da kuma fans 10 na whatsapp_


_Ina godiya da son da kuke ma wannan novel d’in, Allah ya bar zumunci_




_INA MUKU JINJINA TA MUSAMMAN_


*Meeynah (Princess of question of the day)*


*Ramlah*


*Fadeelah*


*Kune ku ka ba da amsar tambayar daidai, Allah ya saka muku da alkhairi, ya biya muku buk’atun ku da sauran musulmai baki d’aya*


*Amsar tambayan shine a halayen larabawa kafin musulunci shine sun kasance suna bauta ma gumaka, sannan suna kashe ‘ya’yayen su saboda tsoron/gudun talauci*




 

_TSOKACI_


_A kwanakin baya, akwai wani tambaya da nasa a question of the day, in da na ce menene sunan bishiyar dake cikin aljannah? a next post d’ina sai nasa (jannatul Kuldi), to ina nufin bishiyar sunan ta  shajaratul kuldi)_ _ganin yadda wasu suka min Magana ta pc akan cewa bishiyoyin dake cikin aljanna suna da yawa, wasu kuma suna challenging d’ina akan ba shajaratul kuldi bace_

_To ni dai har yau binciken da nayi da kuma fad’ar malamai ban samu akasin amsa ta ba_

_Amma ina rok’on duk wanda yake da cikakken amsar tambaya ta tare da hujja zai iya min Magana ta pc domin fahimtar dani, har yau ni d’aliba ce, kuma duk tambayar da nake rubutawa sai nayi bincike akai kafin nayi tambayar_




*TUNATARWA*


_Allah yana jarabtar bawansa a lokacin da yaso, a kuma San da ya so_

_Allah ka bamu ikon cin dukkan jarabawar da za kayi mana_




49&50



Kusan zaman minti biyar nayi ina jiran shi, sai ga motar Dr Sadik yayi parking d’in motar shi a gefen Fanta fun.


Sanye yake cikin tsadadden yadi kalar white, kayan sun matuk’ar yi masa kyau, kasancewar Dr Sadik akwai d’aukan wanka, k’arasowa yayi da murmushi a fuskar shi.


Kujerar dake opposite dani ya zauna yana ci gaba da sakar min sansanyar murmushin shi.


Gaisawa muka yi cikin wasa da dariya kana ya bani hak’uri akan delay d’in da yayi.


D’aya daga cikin ma’aikatan ya kira akan ya kawo mana drinks.


Juyowa yayi ya tambaye ni yace "wani kala za a kawo miki Zarah?".


Girgiza kai nayi nace "table water kad’ai ma ya isa".


Kallo na yayi bai ce min komai ba yace wa ma’aikacin ya kawo table water guda biyu, ya had’o da fanta guda 2.


Sipping yake yi kamar ba ya son shan fanta d’in.


Wucewar kusan 2 minute, gurin ya d’au shiru ba tare da yace min komai ba.


Shirun da naji yayi ne yasa na fara pressing d’in waya ta.


"Zarah" naji ya kira ni cikin cool voice d’in shi.


"Dr" nima na fad’a.


Cikin tsadaddiyar muryar shi ya ci gaba da cewa "Zarah, na dad’e ina neman wacce ta dace da rayuwa ta, amma ban samu ba sai a yanzu, ni da kike gani Zarah, da ban yarda da wani soyayya ba bare in tsaya ‘bata lokaci na akai, yanzu ne nasan mahimmancin soyayya saboda na fad’a a cikin ta, ina kuma tunanin wacce nake so d’in za ta yarda ta amshi soyayya ta".


Tsayawa yayi kamar ba zai ci gaba da Magana ba, can ya ci gaba da cewa "kar in ja ki da nisa, Zarah ke nake so…., I crown you the queen of my heart, so many reasons are there to love you, your cute smile, your sweet laugh, your innocence and your kind heart makes me love you…


Wani irin fad’uwar gaba na ji a lokacin da ya sani saurin d’agowa na kalle shi.


Wannan shine karo na biyu da aka zaunar dani aka fad’a min Kalmar soyayya.


Tunano kalaman yaya Faruk nayi a lokacin da yake ce min _INA SON KI FATIMAH, I know I am in love with you because my reality is finally better than my dreams_

Gashi yanzu Dr ya zo min da wani sabon karatun wanda ban gama gane na farkon ba.


Na so na fara warware matsalar yaya Faruk, hakan bai yiwu ba sai ga Dr ya k’ara zuwa min da wani al’amari mai wuyar fassaruwa.


Idan nace ba na jin Dr a raina nayi k’arya, sai a yanzu da ya furta min yasa na tabbatar da cewa I am in love with Dr Sadik, sai dai yanzu ba ni da k’arfin amincewa kasancewar yaya Faruk bai san a wani babi yake ba.

Dr ne ya katse min wasik’ar jakin da nake karantawa.


"Zarah, I am a free person, duk yadda nake son mutum, in ya nuna bai amince ba, bazan matsa mishi ba, nasan so gamon jini ne, u are free to tell me if i am not your choice, zan fahimce ki"..


Ajiyar zuciya na saki kana nace "Dr ka d’an bani time, zan fad’a maka ra’ayina game da kai".


Ba tare da wata damuwa ba yace "Kar ki damu Zarah, na ba ki nan da gobe, ki yi shawara, zan kira ki in ji amsar ki, ko ki turo min text".


Mik’e wa yayi yace


 "Zarah ni zan tafi, ki zo in sauke ki a gida".


Shiru nayi ina tunanin kar yaya Khalil ko direban gidan su Anisa su zo d’auka ta ba su ganni ba.


Wata dubara ce ta fad’o min na mik’e na bi shi cikin motar.


Kasancewar yasan layin, gidan kawai na nuna mishi ya ajiye ni a bakin gate.


Sallama muka yi ya ja motar shi ya tafi ya bar layin.


Ina shiga parlour d’in ban ji motsin kowa ba, hakan yasa na wuce d’aki na watsa ruwa na canza shiga zuwa English wears, kitchen na wuce na d’ebi abinci a plate na nufi d’akin Ummu.


Samun ta nayi tana gyara kayan ta a wardrope, sallama nayi na nemi guri na zauna.


Ummu ce ta amsa tana cewa "Fatima an dawo?".


"Na dawo Ummu, sannu da gida, san da na shigo ban sami kowa a parlour ba, shi yasa na wuce ciki na watsa ruwa" na ba ta amsa.


"Ai kuna shawo rana, dole sai da watsa ruwa".


Dariya nayi nace "Ummu karatu sai ka daure"..


"Allah dai ya baku sa’a a karatun ku".


Cikin jin dad’i nace "Amin Ummu".


"Ummu aiki kike yi ne?" na tambaye ta.


Amsa min tayi "mai wankin da guga ne ya kawo kayan, shine nake jera wa".


"Ummu ki bari in na gama cin abinci sai in jera miki".


"Ki barshi kawai Fatima, ke da kika dawo yanzu, ai na kusa gama wa".


A haka muka ci gaba da hira da Ummu ina cin abinci.


Bayan na gam cin abinci ne na d’auki plate d’in na tafi gurin sink na wanke.


D’aki na wuce na kwanta akan gado, kalamen Dr ne suka fad’o min a rai

*"Zarah ke nake so*., *I crown you the queen of my heart*

Wani dad’i ne ya kama ni a lokacin, ji nake yi kamar yanzu yake fad’a min wannan tsadaddun kalmomin.


D’aga kai sama nayi ina tunanin mafita.


A wannan lokacin ina cikin tsaka mai wuya, ina buk’atar mai ba ni shawara, gashi ina da masu ba ni shawara, yaya Khalil da Anisa, amma ba ni da halin tunkarar su da wannan zancen, saboda duk inda suka ji cewa yaya Faruk na so na amma nayi rejecting d’in shi na za’bi Dr, ba mai ba ni shawarar in za’bi Dr, da alamu kuma zuciya ta baza ta k’i tayin Dr ba, dan alamu sun nuna son shi ya yi dabaibayi a zuciya ta, wannan shine hausawa suke cewa "Ga biki, amma babu zanin d’aurawa".


Yaya Faruk da Dr Sadik na d’aura akan ma’auni, ko wanne na duba qualities d’in shi, sakamakon sai ya nuna min cewa yaya Faruk ya fi Dr qualities, hasalima ya fi shi kyau, son mutane, gashi kuma d’an uwana na jini, sa’banin Dr da mutane ke shakkar shi kasancewar sa miskili kuma bai damu da mutane ba

"Me yasa zuciya ta tak’i amsar gayyatar sa da ya min na so? Menene aibun shi? 

Nayi k’ok’arin dasa son yaya Faruk a cikin raina amma hakan bai samu ba,

Menene mafita?" na tambayi kaina.


Zuciya ta ce tace min "mai zai hana ki amince da yaya Faruk saboda shi yafi cancanta ki so, in hakan ta kasance iyayen mu za su yi farin ciki da haka, ga k’arin zumunci da zai k’ullu a tsakanin su, hasalima shi yaya Faruk ne ya fara fad’a mi ki yana son ki, idan kika mai haka ba ki mishi adalci ba, kin sa yana ta jiran amsar ki, amma sai ki ka za’bi wani a kansa".


Wata zuciyar kuma ce min take yi "Ba wani rashin adalci da kika masa, ko da yace yana son ki, ai baki ce kin amince ba, kuma shi so ba ruwan shi da ‘yan uwantaka, so yana zuwa ne a zuciyar mutum ba tare da yayi shawara dashi ba, ki bashi hak’uri kawai".


Shawara ta biyu na d’auka saboda ina ganin ita ce mafita a gare ni.


Zuciya tace ta bani shawarar in tura ma yaya Faruk text na ban hak’uri akan cewa yayi hak’uri dani, Allah shi ma ya bashi mai son sa.


Wani tunani ne yazo min akan cewa in bari in ya dawo daga tafiyar da yayi yazo Kaduna sai in fad’a mishi, nasan zai fahimce ni, duk da nasan akwai ciwo, ba ni da yanda zanyi ne.


Da yamma ina d’aki ina wani assignment naji yaya Khalil na kira na.


Fitowa nayi na same su a falo, dashi da yaya Aminu suna hira.


Gaishe da yaya Aminu nayi, kana nayi ma yaya Khalil sannu da gida.


Yaya Khalil ne cikin tsokana yace "Fatima yau ina kika shiga ne a school, ni da Anisa muna ta neman ki a department d’in ku, gashi wayar ki is not reachable".


"Yaya Khalil yau da kaina na dawo, ganin mun gama lectures da wuri".


Yaya Aminu ne ya fara fad’a yana cewa "Tun da kun yi closing, ba sai ki nemi numban Khalil d’in ba ko Anisa, ki fad’a musu kin tafi, amma sai ki yi tafiyar ki su yi ta shan wahala, idan kika sake, za ki had’u dani".


Cikin shagwa’ba nace "To ba kaina ne yake min ciwo ba".


A raina nace 'yanzu na rabu da fad’an yaya Faruk, saura kai".


Cikin tausayawa yaya Khalil yace "Ayya sorry sister, Allah ya k’ara sauki".


"Amin na amsa".



Yaya Aminu ne ya tashi ya nufi side d’in Ummu.


Zama nayi muka ci gaba da hira kamar ba ni bace nace kaina na ciwo.



Washe gari da daddare, kamar yadda Dr ya bani time, sai gashi ya kira waya ta.


Ko kan in d’auka, wani special smile kawai nake yi.


"Assalamu alaikum Dr" na fad’a.


"wa’alaikis salam Zarah a cikin taurari".


"dafatan kin wuni lafiya".


"lafiya lau Dr, ya aiki?".


"aiki alhamdulillahi, ya karatu".


"karatu normal".


Shiru muka yi na d’an mintuna kafin yaci gaba da Magana.


"Zarah da fatan kin gama tunanin ki, yanzu amsar ki nake jira".


Cikin jin kunya nace "Nima na amince, Dr nima ina son ka".


"Wow! Zarah, I don’t know how to show my happiness to you, na ji dad’i, Allah ya barmu tare".


"Amin Dr".


Haka ya dinga ci gaba da fad’a min irin son da yake min, ban cika bashi amsa ba, kasancewar rashin sabo da hirar soyayya.


Haka muka yi sallama muna masu shauk’in junan mu.


Yau kusan watan yaya Faruk 5 rabon shi da Kaduna, yanzu ba mu cika had’uwa ba kasancewar ba network a inda suke.


Sai dai wani lokacin Ummu tace ya kira yace a gaishe ni.


A can ‘bangaran yaya Faruk kuwa, tun zuwan su garin Adamawa, basu da wani lokaci kansu, aikin da ya kawo su suke yi na kwantar da tozarmar da ke tsakanin Fulani da Iyamurai da aka samu sa’bani a tsakanin su, wanda hakan ya jawo asara da dama, ciki har da asarar rayuka.


Bai da wani lokacin yin waya ko chat saboda rashin samun lokaci, wani lokacin in da suke zuwa akwai matsalar network a gurin, hakan yasa ba kullum yake kiran gida ba ko ya kira ni.


Duk yadda suke tunanin rikicin mai sauki ne tsakanin Fulani da Iyamurai, abin ya wuce haka.

Sun yi kusan wata uku a can Adamawa, sannan sak’o yazo musu cewa akwai wani course da za a tura su k’asar Uganda wanda za su iya d’aukan 3/4 month a can.


Ko da suka dawo Abuja, bai samu damar zuwa Kaduna ya musu sallama ba saboda dawowar su kawai ake jira su tafi.


Ko da ya kira Daddy ya fad’a mishi, fatan alkhairi ya mishi, amma yaso ganin shi ganin watannin da ya d’iba bai zo ba.


San da ya sanar da Momi, fad’a ta fara yi akan wannan wani irin aiki ne? mutum ace rabon shi da gida kusan wata uku, sannan kuma yana dawowa an k’ara tura shi wata k’asar.


Daddy ne ya dinga lallashin ta yana nuna mata aikin soja ya k’unshi haka, ta mishi addu’a da fatan nasara kawai.


Haka kuwa Momi ta dinga mishi addu’a, ji take yi kamar taje ta ga d’an ta.



Yanzu kusan wata 7 rabon shi da Kaduna, a wannan satin ne suke sa ran dawowa Abuja.


Duk wannan watannin da yaya Faruk yayi a garin Adamawa da Uganda, bai manta dani ba, kullum ina cikin ransa, yana ganin yafi kowa k’osawar su dawo Abuja ya samu a basu hutu su je gida.


Soyayyar mu da Dr ta zama wata irin soyayya da muke gudanar wa mai tafiyar da nishad’i, ba ko wani lokaci yake kira na ba, hakan bai damu na, saboda ina mishi uzurin yanayin aikin shi.


Ba laifi Dr yana bani caring d’in da nake buk’ata a gurin lover d’ina, duk da wani lokacin ina ganin gazawar shi a ‘bangaren hakan, amma ina sa wa a raina cewa in muka yi aure, komai zai daidaita.


Yau bayan mun tashi daga School ne, Ina cikin motar Dr Sadik muna hira, naji waya ta na ruri.


Ganin Anisa ce yasa na d’aga da alamar tsokana nace "Matar yaya Khalil ya aka yi ne".


Dariya tayi tace "Fatima Allah dai ya shirye ki, kina ina ne? gamu a department ni da Driver muna jiran ki".


"Ok ki k’araso gaban department d’in mu, za ki ga wata mota ash colour a gurin, ina cikin motar".


"Ke da waye a cikin motar" tayi saurin tambaya ta.


"Idan kika zo kya gani" abin da nace da ita kenan na katse wayar.


Ba a d’au wasu mintuna ba, sai gata ta k’araso motar.


Ganin ta da nayi yasa na bud’e motar ina murmushi.


"Anisa ga Dr Sadik ku gaisa" na fad’a.


Kallo na tayi kamar za tayi Magana, sai kuma ta juya kallon ta zuwa ga Dr tace


 "Ina wuni Dr".


"lfy lau Anisa, ya karatu".


"lfy lau, ya aiki".


"aiki alhamdulillah".


Ita kuwa Anisa mamaki ne ya kama ta, saboda ita a sanin ta, Dr Sadik a asibitin school yake aiki, menene alak’ar shi da Fatima da zai biyo ta Department? duk da tasan sun yi Siwes a asibitin, kuma tasan sun saba da Fatima da Dr, yanzu to zuwan me yake yi gurin ta?


Kamar nasan tunanin da take yi kenan nace "Anisa, wannan shine Dr Sadik, nasan kin gane shi, saboda yana aiki ne a cikin asibitin school, kuma shine my lover".


Na juya kallo na ga Dr nace "Dr Sadik, wannan ita ce Anisa, k’awa ta kuma ‘yar uwa ta".


Dr Sadik ne yace "Ina jin labarin ki Anisa gurin Zarah, ki ci gaba da kular min da ita, saboda ita special queen ce a guri na".


Murmushi Anisa tayi tace "kar ka damu Dr".


Sallama ta mana akan cewa tana jira na a mota.


Dr Sadik ne ya min kallon da ke sani k’ara fad’awa tarkon son shi kana yace "Zarah, bari in tafi, tun da ga Anisa can na jiran ki".


Fitowa nayi daga motar ina waving d’in hannu na.


Anisa tun da ta koma mota take tunanin yaushe na had’u da Dr, me yasa ban fad’a mata ba? 


Wannan tunanin ta ci gaba dayi har na k’araso cikin motar.


Mun fara tafiya ne Anisa ta kira suna na.


"Fatimah!


"Anty na ya aka yi ne" na fad’a da alamar tsokana.


"Fatima wai yaushe ku ka fara soyayya da Dr Sadik ne? me ye dalilin ki na k’in fad’a min, bayan kin san ba ma ‘boye wa junan mu sirrin mu, ko da ki ka ga ban fad’a miki soyayya ta da yaya Khalil saboda ba na so yanzu Abbu da Daddy su fara tunkara ta da zancen, kin ga yanzu yaya Khalil sevice yake yi, na fi so sai ya gama service d’in, kin ga lokacin mun kusa gama Diplomar mu, amma ke wace hujja kike da ita? Gaskiya bazan ‘boye miki ba, ban ji dad’in abin da kika yi ba". Anisa ta fad’a da alamar damuwa.


"Sorry Sis, ke ma kin san bazan k’i fad’a miki ba, kawai dai na ga ba mu dad’e dashi bane, shi yasa ban fad’a miki ba, kuma ina ganin nan gaba za ki iya cewa in hak’ura dashi".


Da mamaki Anisa ta kalle ni tace "akan me zan ce ki rabu dashi Fatima, bayan na ga alamun kina son shi, kuma miye aibun shi da zan ce ki rabu dashi? kawai dai kin fad’i ra’ayin ki ne".


A raina cewa nayi "da kinsan yaya Faruk ke so na kafin Dr, da ba ki ce haka ba, kuma ni nasan duk ran da kika san haka, ba za ki bani goyon baya ba akan Dr Sadik".


Saboda mu rabu lafiya da ita yasa nace "yanzu dai ki yi hak’uri Anisa, na amsa laifi na".


Murmushi tayi tace "kar ki damu Fatima, ke ai k’anwa tace tun da kina matsayin k’anwar miji, dole in hak’ura".


Hannu na ba ta muka tafa, muka ci gaba da hira, ina k’ara ba ta labarin Dr Sadik.


Bi na kawai take yi da kallo, tana jinjina irin son da nake yi ma Dr Sadik a d’an wannan lokacin da muka had’u dashi.


Yanzu soyayyar mu muke sha da Dr Sadik ba tare da wata matsala ba, yawanci lokuta yana d’auka na mu jeostrich bakery ya min siyayya.


Akwai lokacin da muka je Ostrich bakery d’in, na za’bar ma Anisa favourite snacks d’in ta da ice cream.


Da na mik’a mata ledar take cewa "Fatima, maimakon ki bari in za mu koma gida sai mu shiga gurin, kin ga yanzu ice cream d’in ruwa zai yi".


"Oh Sorry, ni da Dr Sadik ne muka je gurin ya siya mana".


Anisa kuwa mamaki na take yin a yadda na fara canza halaye na daga had’uwa ta da Dr.


"Fatimah, shawara zan baki, amma kar ki d’auka da wata manufa".


"Ina jin ki Anisa".


"Ki rage bin Dr Sadik yana fita dake, ba wai nace yana da matsala bane, hakan zai sa ya gane u a special, gwara ya siyo ya kawo miki, wani time d’in ki nuna mishi ba ki da buk’atar hakan".


Wani irin kallo na bi ta dashi, saboda ni ban gane me take nufi da hakan ba?

"yanzu ke nan nayi laifi dan mun je Ostrich bakery da Dr Sadik".


"No Fatima, ba wai na ce kin yi laifi ba ne, ina fahimtar dake halin maza ne, ki iya takun ki, kuma ai nasan Ostrich bakery da poly ba nisa, tun da tsallaka titi ne, ina nuna miki yanayin high institution ne, kin ga sometimes yana zuwa department d’in ku, yanzu in wani wanda yasan ki, ya gan ki a gurin bakery d’in ya fad’a ma wani, za a iya canza muku manufa, yanzu duniyar nan mutum ake kiwo ba dabba ba, da fatan kin fahimce ni".


Jiki na ne yayi sanyi da maganar da Anisa ta fad’a min, nima nasan gaskiya ta fad’a min.


Don haka nace "Anisa na fahimce ki, zan kuma kiyaye".


Yawwa k’anwata ta fad’a da alamar tsokana.


Hararar wasa na mata muka canza hirar.


Yanzu abin da yafi damu na shine yadda Dr Sadik ya matsa min akan yana so ya nemi izini gurin su Abbu, saboda yana so a san dashi a family d’in.

 

Hak’uri na bashi akan yayi hak’uri ba yanzu zan bashi damar ya fara zuwa gidan mu zance ba, ba kuma yanzu zan gabatar dashi gurin su Abbu ba.


Wannan kara da alama ba zai hak’ura ba, ganin yadda ya taso min cikin fad’a yace "Zarah, look, gwara ki fito ki fad’a min hujjar ki da ba kya so in fara zuwa gidan ku, na gaji da yadda kike kawo min excuse d’in ki in na miki magana, tell me what do you mean?".


Cikin salon lallashi na fara bashi hakuri "Dr ka fahimce ni, nima na fi so ka zo gida akan department d’in da kake zuwa, insha Allah zan fad’a ma Ummu zancen ka, sai ta fad’a ma Abbu, in yaso sai ka fara zuwa, sorry Dr na" na fad’a kamar zan yi kuka.


K’asaitaccen murmushi yayi yace "Na fahimce ki Zarah, sorry in na "ba ta miki rai".


Girgiza kai nayi na ce "ya wuce Dr".


A raina kuwa ban ji dad’in yadda ya min fad’a ba, ban san me yasa na kasa nuna mishi hakan a fuska ta ba, nasan ba komai yasa haka ba illa son da nake mai.


Ci gaba yayi da ja na da hira, ina bashi amsa amma ba kamar yadda muke hira a lokuta da dama ba.


Watak’ila fahimtar hakan da yayi ne yasa ya min sallama ya tafi.




Post a Comment

0 Comments