ππ»ππ»ππ»ππ»ππ»
TEAM----ZAFAFA BIYARπ₯ππ₯°π
ALLAH ka gafartama iyayenmuπππ».[7/6, 9:38 AM] : *_LITTAFIN nan na kuΙi ne. Dan girman ALLAH ki daure ki biya kafin ki karanta, idan kuma bazaki iya biya ba ki haΖura domin ALLAH karki karanta. Idan kuma kin saya dan girman ALLAH karki yaΙa manaππ»_*.
No. 72
...........Washe gari bayan sallar asuba Nu'aymah ta Ιorama Yoohan karatu kamar yanda suka saba. Daga haka ya shiga Ιakin motsa jikinsa. Ita kuma sai tayi amfani da wannan damar ta shiga Ιakinta domin Ιakko hoton nan. Duk da ta jima bata shigesaba ta fahimci an canja mata zaman wasu abubuwa da dama. Wasuma babusu. Bata bar hakan ya dametaba ta nufi Wadrobe direct inda ta ajiye hoto. Sosai gabanta ya faΙi ganin yanda kayanta suka koma a harmutse ba yanda tasan sukeba. Cikin gigita ta shiga tiΙosu Ζasa tana faman zazzagewa. Sai dai kamar da wasa babu hoto babu labarinsa. Hankalinta ya tashi, har takaita da duba indama tasan bata ajiye Ιinba amma ko mai alamarsa babu.
Jagwab ta zauna a bakin gado tanabin Ιakin da kallo daki-daki, dan sai a yanzune ma harmutsewarsa ba yanda ta barsaba yake dawo mata a zuciya daki-daki. Yoohan ta fara kawowa a zuciyarta. Sai kuma ta girgiza kanta dan bata tunanin zai mata bincike. Can Ζasan zuciyarta yace, ‘Omar ne. Bashi kika sanarma maganar hotonba’. Nanma da sauri ta girgiza kanta alamar a'a. Gebrail. ‘Kai bazai zama shiba. Dan shi manufarsa daban data masu hankali. Wannan bashi da man kai akan hakan’. Madam Chioma. Nanma a fili tace, ‘Kai ina bana sata a wannan layin dan kanta baya ja tacika kidahumanci kamar kifi’. ‘To wa zan zarga?. Ko dai papa ne?’. Mikewa tai da sauri tana kaΙa kanta hannayenta duka biyu a saman cikinta. ‘Lallai tabbas shine abin zargina, musamman daya kasance ya riga yabi diddigina akan shigar masa Ιaki da nayi, zai iya kasancewa tunaninsa ya basa zuwa nan yamin bincike. Shin minene wannan mutumin ke Ιoyewane akan mijina? Lallai ya kamata na sani kafin na sake barin Ζasar nan’. Sai kuma ta dafe goshi cike da damuwa. ‘Hoto shine kawai hope Ιina. Gashi yanzu Ιan barahazar ya sace min, bayan na gama baza bayani wajen Abbana da wannan Umar Ιin. Kenan dolene na sake satowa. (Idan bai Ζonaba ko?) zuciyarta ta ayyana mata. Karan farko da matsanancin tsoro ya risketa. Da sauri ta fita a Ιakin zuwa can cikin gidan. Gidan shiru alamar masu gidan babu wanda ya tashi kasancewar weekend ne. Kitchen ta nufa. Tako iske Blessing kawai tana haΙa breakfast kamar yanda tayi hasashe.
Ko gaisuwar Blessing Ιin bata amsaba taja hannunta suka shige cikin store. Sai da ta leΖa ta tabbatar da babu kowa sannan ta tura Ζofar store Ιin ta rufe ta juyo ga Blessing da jikinta harya fara rawa. “Please ki nutsu, ba wani abu bane tambaya zan miki, ina fatan kuma zaki bani amsa kamar yanda kike bama Omar... Oh sorry Richard”.
Cike da tsoro Blessing zata fara rantse-rantse Aymah ta tsaidata......
“Karki wahal da kanki wajen mani rantsuwa nasan komai daga wajensa. Inason nasan zuwan Richard nawa gidan nan?”.
Da tsoro sosai a fuskar Blessing tace, kusan bakwai”.
“Dama can anan yake sauka kenan tunkan aurena da Yoohan kokuwa a yanzune yake sauka anan?”.
“Eh dama yana sauka gaskiya, amma sai Oga yana Ζasar”.
Jimm Nu'aymah tayi alamar tunani, sai kuma tace, “Mikike tunanin yana zuwa yi nan gidan?”.
Cike da tsoro sosai Blessing ta buΙe Ζofar kaΙan ta leΖa, hakan yasa Yoohan daya biyo Aymah yake a laΙe saurin komawa ya lafe a bango. sai da ta sake tabbatar da babu kowa sannan ta dubi Aymah murya can Ζasa sosai. “Na yarda dake sosai Aunty na, dan tun a zuwanki gidan nan na fahimci ke mutuniyar kirkice wlhy. dan haka zan sanar miki komai duk da nima ba komai Ιin na saniba”.
“Okay ina saurarenki”.
“Tun bayan wucewarku Austria nakeji wasu maganganu masu gidan nayi a kanki. Dan akwai randama na taΙajin an bada kwangilar kasheki ta hanyar likitan da zasu miki aiki. To sai dai kwanan mutuwarki bai rigada yazoba dan ke Ζ΄ar baiwane. Sai akazo baki mutuba. Su boss sunje dubaki, bandai san miya faruba bayan dawowarsu Uncle Richard naga ya nacema zuwa gidannan. Sanan yakan sani na masa wasu abubuwa akan boss ko madam Ιin gidan nan. Sannan ko baya gida zai kirani yaji mi akayi ko mi ya faru. Badai komai nake fahimtaba gaskiya, tunda banida hurumin yin komai. Sai dai matsalar dana fuskanta shine randa su papa suka shiga sashenku ita da Solomon da Madam. Sun miki bincike a Ιaki sai dai basu sami komaiba suka fita. Bayan hakan Uncle John yazo Ζasarnan yaga yanda akai miki da Ιaki shine ya zane Gebrail a tunaninsa shine ya shigar miki. A zahiri papa baicema Uncle John komaiba akan dukan Gebrail. Amma bayan barinsa gidannan ba Ζaramin rikici akayiba tsakaninsa da maman madam dama madam Ιin. Shima kuma papan naji yana wasu maganganu tsakaninsa da Brothers Ιin nan nasa wanda ban ganema kansuba sam. Wanann rikicin ne ya saka su Maman Destiny barin gidan nan. Dan sun nuna goyon bayan Uncle Yoohan fiye da Gebrail. Shine yasa akai rikici duk suka wuce. Bayan nan kuma sai Uncle john Ιin da yazo last time madam Ιin gidan nan ta shigar masa Ι.........”
Da sauri Yoohan dake a laΙe ya rin tse idanunsa tare da shiga kiran sunan Nu'aymah tamkar ya shigo nemantane. Rikicewa sosai Blessing tayi, amma Aymah ko'a jikinta saima Ιata fuska tayi ta buΙe Ζofar bayan ta Ιebo noodles guda biyu.
“Oh Sweet boo ganinanfa a store. Nazo amsar noodles ne a wajen Blessing shine take nunamin inda take”.
Cike da mamaki yake jinjina wayonta. Amma shima sai ya waske yana mai dafe kansa da faΙin, “Kinsa duk na ruΙe na fito ban gankiba a gaba Ιaya sashen”.
“I am sorry Hubby”.
“Silly girl yana iya dake. Yanzu yaya za'ai da Noodles Ιin?”.
“Zan dafa ne anan”. Ta faΙa saboda son ya barta ta Ζarasa jin zance a wajen Blessing.
Fahimtar hakan da yayine ya sakashi hayewa saman kitchen cabinet Ιin yana cewa, “Okay dafa to mu wuce. Dan kinsan akwaima fa inda zamuji ga lokaci nata Ζurewa, Omar ma jiranmu yakeyi tuni. Koma kibama Blessing Ιin ta dafa miki muje ki shirya data gama sai kici kawai”.
Duk da Aymah bataso hakan ba sai ta amince kawai. Dan ita bama cin noodles Ιin zatayiba sam. Blessing ta Ζwalama kira. Sai gata ta fito da sauri hannunta Ιauke da abinda zata dafa da rana irin dai shi ta tsaya Ιebowa. Sai dai kallo Ιaya Yoohan ya mata ya fahimci tsoron dake tattare da ita.
Bata dahuwar noodles Ιin tayi suka fice. Gaba Ιaya hankali Nu'aymah akan Blessing yake. Amma Yoohan yay mata tsayuwar sojan badakkare aka komai tare sukayi. Koda suka fito Blessing ta kawo noodles Ιin catai ta Ζoshi. Sai Yoohan Ιinne yaci tare da Omar. Dama yasan baci zataiba ai. Dan tunda ta samu cikin nan tabar cin indomie sam.
Koda suka gama ficewa sukai a gidan batare da sunbi takan kowa ba. garama mama debora sun haΙu da ita a falo tana shan shayi. Tako hanasu fita saida akaima Aymah addu'oi ita da cikinta. Dan tace ita yanzu ta daina yarda da madam Chioma a gidan samππ€£.
Ita dai Aymah yanzu tsohuwar birgeta takeyi. Dan har suka bar gidan batabar murmushi ba akan abinda ya faru.
Tafiyarsu ta Ιanyi nisa Omar ya fahimci ana binsu a baya. Shima Yoohan ya gani amma baice komaiba. Dan babu abinda zuciyarsa ke masa sai tariyar zancen Aymah da Blessing. Tunaninsa wane abu ne Aymah ke zargin an shigar mata Ιaki akansa ana nema? Sannan kuma ashe papa ne da madam Chioma suka shigar masa Ιakin mata hardama Solomon?. wane bincike Umar keyi akan iyayen nasa? Mi Aymah ta shiga yi Ιakin papa a wancan karon daya dage kareta a wajensu amma hardayin Ζaryar taga wanda ya shiga Ιakin ashe itace? Miyasa mahaifinsa yasa a kashe masa mata? Dolene yasan waΙanan tambayoyi a lokacin ΖanΖani insha ALLAHU.
Da wnanan tunani da yakene yasa har Omar ya gudama masu binsu shi baisan yaya akaiba. Sai ganinsu kawai yayi a station Ιin su Jay.
Aymah dai har suka shiga tana maibin wajen da kallo tare da jami'an tsaro. Ko Ιar batajiba duk da ta fahimci wajene bana wasan yaraba. Yau saΙanin ranar Office Ιin Jay aka kaisu direct, acan suka sami Dawood da Little bee da bily. Sai Afrah da adalilin zuwan Aymah Jay yasa akazo da ita. Dan ita karatun lauyanci takeyi batabi ayarin su little bee ba.
Duk da a hoto sukasan juna ita da Aymah hakan bai hanasu gane junaba. Suka rungume juna kuwa cike da Ιoki dan sunyi sabo sosai ta chart da waya. Daga haka Aymah ta gaida little bee dake zaune tanata danne danne a Computer alamar miskilawan na kusa. Dan duk ihun dasu Aymah sukeyi ko kallo basu ishetaba, aikinta takeyi hankali kwance. Gaisuwarma a haka ta amsata. Sai daga baya ta Ιago ta kalli Nu'aymah sannan suka gaisa dasu Yoohan.
Nu'aymah dai bata sake bi takantaba itama ta juya ta gaida Dawood da Miemaa data amsa mata da fara'a da kulawa, dan itama ta taimaka mata ta zauna a kujera. Daga haka ta gaida Jay da a kallonsa sai da gabanta ya faΙi. Duk da ba tsananin kamanni suke da Yoohan ba dolene kaga yanayin gittawar jini tattare a tsakaninsu. Duk da ba mutum bane shi mai yawan wasa saida ya tsokaneta kaΙan. Har hakan ya bama su Yoohan mamaki. Dan su dai ba taΙa ganin dariyarsa sukaiba tunda suke mu'amula da shi.
Sai da aka lafa da gaishe-gaiahe Jay ya fara magana.
“So ba shirita ne ya taramu ananba. Inason ku bani hankulanku nan gaba Ιaya. Da farko dai kece bakisan dalilin zamanmu ananba duk da mijinki ya tabbatar mana ta hanyarki yasan wasu abubuwan. Sai ko Afrah da sanin nata baida muhimmanci daga tushe duk da itama da taimakonta ne muka samu bayanan sirri game da gidanku. So yanzu little zata miki sabon bayani, ke kuma Afrah jeki waje ki jiramu”.
Sosai Afrah ta Ιata fuska kamar zatayi kuka. Cikin magiya tace, “Abie Please ka barni dan ALLAH, wlhy nima zan taimaka muku da wani abun kaimafa ka sani. Duk da ba aikin nan nakeba so nawa ina muku aiki ta ΖarΖashin Ζasa”.
Fuska ya haΙe zai mata magana Aymah da duk kwarjininsa ya cika mata idanu tace, “Abie dan ALLAH, indai hakan ba laifi bane ka barmin Aunty zanfi samun Ζwarin gwiwa nima”.
Kasa cewa komai Jay yayi, ya kai dubansa ga little. Da wani style na Ζwarewar aiki taima mahaifin nasu alamar roΖon yabar Afrah Ιin. Dan itama tana hasashen tasirin zamanta a wajen.
Ζauke kansa kawai yayi ya maida ga Yoohan dake ta kallonsa kamar ya samu television. Sai kuma ya Ιauke ya sake maidawa ga little bee alamar ya bata damar yima Aymah bayani.
Tsaf ta gama yima Nu'aymah bayanin komai. Dan haka taketa duban Yoohan da Umar cike da mamaki. Da damuwa a harshenta tace, “Amma Yah Yoohan baka gudun Abbana kar yaga ba'a Ζyauta masaba. Sam baya son laifin jama'ar gidan nan namu, shiyyasa yake ΖoΖarin maida laifukansu kuskure dan gudun lalacewar zuminci”.
“Zeeynab inhar muka cigaba da bama Uncle goyan baya akan hakan tabbas sai an salwantar da ran Ιaya daga cikinsu ko ke ko Muhammad a wannan gidan naku. Dan ni nasan mina ganarma idona a Austria da wasu maban-banta wajaje dangane da ke”.
Bata iya tace komaiba dan tasan gaskiya Yoohan ya faΙa. Bandama ALLAH yasa tanada sauran kwana a duniya ai da tun tana jinjira an aikata barzahu Ιin. Sannan shima Muhammad Ιin ai ansha gwada rayuwarsa a mabanbanta lokuta Abba na Ιoyewane kawai........
Cikin katse mata tunani Jay yace, “Karki damu akan Sheikh, ni zan masa bayanin dazai gamsu akan hakan. Yanzu zamu tafine kai tsaye akan abinda ya taramu anan tunda kin gama jin bayanan farko. Dan dama munsa mijinki ya dawo dake Ζasarnan ne dan zamu Ιanaki a gidanku ne matsayin tarko. Dawood minene bayani akan binciken wayar matar nan da aka sakeyi?”. Ya Ζare maganar da maida hankalinsa ga Dawood.
Takardun gabansa ya Ιauka ya fara bayani. “Sir bayanan sununa tabbas ana amfani da wayarta batare data saniba. Kamar maganar yin waya da mai aiki da aka turoma matar Yoohan anan Abuja, sam ba Rabi bace ke waya da Uwaliya. Mun tabbatar da hakane ta hanyar binciken ainahin muryar da aka samu a voice recording Ιin nan. HaΙine ta hanyar makirci babba na masu ilimin sani akan na'ura mai ΖwaΖwalwa. Suna amfani da wani app... Ne da aka saka cikin wayar matar, dama kowacce waya idan ta sake sai suke sarrafa wayar tata daga wajensu batare da ita ta saniba, suna barin mata bayanan abinda sukai da tasu wayar, dan ko an tashi bincke ita za'a zarga kai tsaye. Hakan yana nufin kenan tun fil azal da aka kawota gidan dama akwai manufa a ciki, kokuma daga baya aka fara amfni da ita. WaΙanan sune tatattun bayanai akan ainahin contact dake a wayar Rabi wanda suke aiki da saninta. WaΙanan kuma sune ainahin waΙanda ake amfani da ita ta wayar batare data saniba. Kuma insha ALLAHU zasu taimaka mana mu zaΖulo kosu wanene masu aikata hakan kamar yanda Abdurrahman Sameer Saifudden ya bamu tabbaci, dan shine yay wannan bincike gaba Ιaya tun daga Ζasar india. Ya kuma tabbatar mana idan ana buΖatarsa zai iya zuwa koshi ko abokan aikinsa yan uwan tagwaicinsa kenan”.
Cikin jinjina kai Jay ya amshi takardun yana duban little bee. “Bilkisu! Minene bayanan wajenki akan zaman Afrah gidan?”.
Juyowa Little bee tayi da kujerar da take a kai tana fuskantarsu. Yoohan ta sake kallo kamar yanda dama tuni shi take kallon a sace bisa ΖyaΖyΖyawan nazari datakeyi akansa tun farkon fara ganinta da shi.
“Sir! Bayanan dake anan sun nuna wasu sunaye da Afrah ta rubuta akan zarginta, saboda wasu al'amura da suke aiwatarwa a gidan na marasa gaskiya. Akwai Rabi. Mai aikinsu, a yanzu tana a hannunmu. Sai Mai aikin sashen Addah, sai ita kanta Addah da tafi kowa kusanci da Umm a gidan. Sai Nasir wanda asali shi bama Ιan gidan bane yana zuwane lokaci-lokaci. da wasu sunaye a jerin Ιaliban Uncle Soorajidden Ιin. Ta tattara waΙan nan sunayen ne bisa dalilai mabanbanta da suka faru akan idonta da kuma yanda labarin yazo garemu. Zamu iya jin bayani daga bakinta gata nan idan da buΖatar hakan”.
A yanzu kam bily ce tai wani gutun murmushi tana kallon Jay. Cike da nuna Ζwarewar aiki tace, “Boss niko kaga a duk jerin sunayen nan mutum uku kawai naba ayar tambaya. Sauran kuma inaji a jikina basa zaune a cikin gidan. Abinda yasa nai wannan maganar shine duk lokacin da za'a cutar da ita Nu'aymah akan yine lokacin wani taro a gidan. Hakan na nufin akwai mazauna gidan dake zaune a waje cikin tafiyar. Amma Ζasurgumin azzalumin yana nan cikin gidan tare da su ko akasin haka.
Murmushi Jay yayi a karo na farko. Ya sauke numfashi da Ιan buga pen Ιinsa akan takardar gabansa. “Tabbas komai zai iya kasancewa. Dan suma sauran ai hasahe mukeyi, tunda ga Rabi a hashe muka samota kuma sai gashi babu laifinta”.
“Hakane kuma boss. suspect Ιinmu na gaba sune, Nasir, Ameer, Hamisu, Kubrah, Abdallah. Da iyayen su Abdallah n”.
Da sauri Aymah tace, “momy!” cikin zaro idanu. sai kuma ta shiga girgiza kanta da sauri-sauri tana cigaba da faΙin, “Bazai kasance hakaba Momy. Uncles Ιina suna matuΖar son Abbana. Hakama Yah Abdallah na matuΖar sona. Bazasu cutar damu ba sai dai idan Nasir ne”.
“Relax Nu'aymah. Muma bamun tabbatar bane hashene kawai. Dan dolene mu alaΖanta laifin nan da mafiya kusanci da iyayenki dake kanki, shiyyasa zamuyi amfani da wannan lokacin da mukasan duk ahalinki zasu taru a gida saboda bikin aure da saukar yaran gidan marayunku mu Ιana musu ke a matsayin tarko wajen damΖesu batare da sun fargaba.....”
Yoohan ya katse Bily da cewar, “Humm tabbas Momy bana tantama akan hakan. Musamman akan Abdallah. Dan ta dalilinsa na sakama sauran ayar tambaya. Abdallah yayi fushi yabar Nigeria saboda ba'a aura masa itaba. Amma kuma a bayan fage yana a cikin Ζasar, dan yana yawan shigowa akai-akai. Sannan kuma yana bibiyar al'amarinta dani kaina. Dalilina na biyu a kansa shine wani business da yakeyi a Ιoye batare da sanin iyayen nasaba. Dalili na uku akwai harΖalla akan aurensa da yara biyu na gidan da aka aura masa dalilin sace Zeeynab da akai ranar wancan auren nasu. Ya saki yaran batare da Ιaya ta tare ba. Wadda ta tare Ιin bincikena ya tabbatar min da tasha wahalar zama da shi. Zargi na uku. Akan hotona da aka kai gidansu ni da ita. A yanda labarin yazo kakarsu bata bari su Abdallah sunga hotunanba a waccan ranar, amma daga baya sai hotunan suka zo hannun Abdallah harya kaisu office Ιina. Hakan na nufin bayan na hannunsu akwai wasu kenan dama a wajensu komi? Zargi na biyar, Abdallah yafi kowa Ιaukar zafi akan hotunan a gidan, duk da kuwa nasan Uncle da Umm sai sunfi kowa jin raΙaΙi da zafin hakan game da tilon Ζ΄arsu. Amma sai ya nuna zaΖewa akan hakan harda kawomin abokinsa wai yay Arresting Ιina. Zargi na Ζarshe, miyasa a duk lokacin da akai tunanin Ζulla aurensu sai wani dalili ya ruguza shi?......”
“Please Yah Yoohan ya isa haka mana. Miyasa dukanin zarge-zargenka zai Ζare akan Yah Abdallah? Kana kishi da shi ba shike nufin komai ka yaya ka aza a kansaba”.
Sosai zantukan Aymah suka zafi zuciyar Yoohan, dan gani yake matar tasa tana goyen bayan tsohon saurayin natane kawai. Sai dai kuma uffan baice akan hakanba, yama Ιauke kansa daga gareta kawai.
Karan farko little bee ta saki murmushi tana kallonsu. Sai kuma ta taΙe baki da faΙin, “Wannan faΙane da ya shafeku a gidanku Mrs and Mr”.
Hararta Yoohan yayi, dan dama tunba yauba yana jin haushin yanda take zaman yimasa kallon Ζurilla a fakaice. Yana nuna bai gani bane kawai saboda kunyar iyayenta.
“A'a bar hararata malami, ni yanzu saina sassafa ka a gaban sahibar taka babu ruwana”.
“Ashe kuwa mijinki ma zai sassafu a hannuna tare da wannan miskilar fuskar taki mai Ζinyima mutane dariya”.
Harara itama little ta zuba masa tana tsuke fuska. “Oh kace dama kullum cikin takaicina kake bana maka murmushi, to Ζwalelen kare da hantar kura”.
Baki Yoohan Ιin ya taΙe da Ιauke kansa gefe yana cije lip. Dan saiya saita yarinyarnan akan layi kafin a gama case Ιin nan. shi babu ruwansa da wani Ζ΄ar-sandancin ta ehe. (Kuji Ζarfin hali irin na Yoohan. Da alama mafa little bee Ιin zata bashi shekara Ιaya a duniya, amma wai yarinyaπlol)
Babu wanda drama Ιintasu baisa dariyaba. Sai Jay da Bily basu dara Ιinba a fili sai a zuciya. Sundaita kallonsu cike da nazarin suΙutar harsunan nasu.
Kai jay ya girgiza kawai yana katse little dake son Ζara magana. “Kunga ku aje wannan shirmen naku sai kun fita can sai kuyi, idan kunso ku sassafa kawunan naku munada likita a kusa da zai duba ku. Yanzu dai Yoohan dole a yau Ιin nan Nu'aymah ta wuce kano. Dan aikin nan banason ya shige satin nan bamu kammalashi ba. Maganar Abdallah kuwa na tabbatar jin Nu'aymah na Nigeria zaizo shima koda a Ιoyen daya saba ne. Yanzu zan baza jami'ai da zasu fara bibiyar lamarin motsin kowa na gidan idan ya fito. Shima Nasir ina buΖatar a jawomin hankalinsa yazo kano. Babu sanya a aikinmu, duk wanda mukaci karo da rashin gaskiyarsa zamu kamasane mu tuhumesa kamar Rabi. Za kuma mu maida Rabi itama dan wayarta zata taimaka mana sosai wajen zaΖulo abubuwa”.
Cike da gamsuwa kowa ya amsa masa. Duk da kuwa Yoohan dai da alama baiso yin nisa da matarsaba. Amma ya fahimci hakan zai taimakesa gameda Ζudirin papa kuma a kanta. duk da kuwa a kanon ma wasu kurayen zata tarar. amma gara can akwai jami'ai masu sanya ido a lamarinta.
________★
Koda su Aymah suka dawo gida bata ga Blessing ba. Hakama Madam Chioma da papa da alama basa gidan ma. Yara kawai suka tarar da Mama debora. Joy ta wuce makaranta, Miracle kuwa mama debora ke basu labarin wai ta haΙa kayanta ta koma gida.
Ko a jikin Yoohan. Aymah kuwa yar dariyar shaΖiyanci tayi abinta ta wuce sama cike da tunanin ina Blessing ta shiga. Ζakinta ta nufa direct, ta fara zame kayanta zuciyarta taf damuwa akan maganar hoton nan. Agogonta data cire ne ya faΙi Ζasa. ta Ιan matsa baya tana dubawa ta tillesa da Ζafa yay ΖarΖashin gado. Abin ya bata haushi, dan harta barsa akan yayta zama sai kuma taji tanason Ιakko kayanta dan Yoohan ya batashi matsayin Ζyauta a ranar da suka cika shekara Ιaya da aure. Fita tai ta Ιakko mopping stick dan Yoohan bai shigoba har yanzu yanacan tare da mama debora. DurΖusawa tai gaban gadon batare da damuwa da cikin dake gabantaba saboda wauta. Ta kunna fitilar wayarta ta haska. Da Ζyar ta iya hango agogon ta saka mopping stick Ιinnan ta turosa a hankali. Sai da yazo dab da ita ta fahimci harda wani abu take jawowa. Hannu ta miΖa danta jawosu duka ta kasa. Dole ta sake zungurowa da iccen mofa Ιin sannan suka fito. Jikinta har rawa yake wajen fara Ιaukar envelope Ιin ta buΙe. Tai wani irin waro ido na al'ajabi da mamaki. Batama san sanda ta ΖwaΖume hoton a Ζirjiba saboda murna. Jin an taΙa Ζofar za'a buΙe tai saurin sakin hoton Ζasa, kafin Yoohan daya shigo ya Ζaraso ta tura hoton ciki yanda bazai ganiba.
Duk da ta masa alamun rashin gaskiya sai bai nuna yama fahimcetaba. Yay baya da fiΙin, “Oh ashe kina nan, bara na watsa ruwa saiki shirya kema zuwa biyar na yamma zamu wuce kano. Amma mi kikeyi ma a durΖushe anan? Bayan kinsan bake kaΙai bace?”.
MiΖewa tai tana nuna masa agogon data Ιakko. “Kaga abinda na yadda nan na Ιakko”.
“Ki kulafa, dan na fahimci har yanzu wautanki na nan”.
Baki ta kumbura da iska batare datace masa komaiba. Shima sai ya juya abinsa ya fice kawai ya barta batare daya sake maganaba. Sai dai bai rufe Ζofaba. Da wannan damar ya samu zarafin laΙewa kozaiga mitakeyi. Aiko tana ganin ya fita ta sake duΖawa ta Ιakko hoton tana ambaton ‘Alhmdllh ya ALLAH. Da banga hoton nanba da bazan taΙa yafema duk wanda ya Ιaukesaba. Dolene nasan wacece wannan mai kama da mijina Ιin insha ALLAHU’.
Dukkan maganganun Aymah a cikin kunnen Yoohan ne. Hakan yasa zancen tsaya masa a rai tare da son jin ganin hoton nan shima. Yayi kamar zai dawo sai kuma ya fasa. Akan idonsa ta maida hoton a Wadrobe. Tafiya yay Ιakinsa tunda yaga inda ta ajiye. Sai dai kamar tasan yana kallonta. Yana barin wajen ta Ιauke hoton ta sakashi a Ζ΄ar jikkar data haΙa kayan tafiya kano wai dan kar wani ya sake shigo ya sace mata. Tana shiga wanka Yoohan ya dawo duba hoton. Sai dai kuma komai kama da shi bai ganima. sai ma kamashi da Aymah taso yi ALLAH dai ya taimakesa ya gudu.
Haka suka kammala shirin wucewa kano mamakin atsabibancin Aymah na damun Yoohan, shi ganima yake ta gansa shiyyasa ta canjama hoton waje.
Itako Aymah ranta fal baΖin cikin rashin ganin Blessing da Yoohan yasa tabar gidan har sai sun wuce dan bayason ta sanamar Nu'aymah abinda ya faru tsakaninsa da Momynsa.
*_KANO TA DABO_*
Ζarfe bakwai dai-dai jirgin su Aymah ya sauka a kano. Batare da sanin kowa daga ahalintaba har su baba malam. Sai da Yoohan yasa suka fara biyawa sukai shopping na tsarabar da zata kaimusu sannan suka wuce gidan.
Ganin Aymah da Yoohan ya saka mai gadi buΙe musu gate mai taxi ya shiga har ciki. Nu'aymah zata fita da kwakwazo Yoohan ya riΖota yana girgiza mata kai. “Please kibi a hankali, a ganinama ba gara ki shige babu wanda ya san da zuwanki ba da safe sai kiyi musu surprise”.
Baki ta Ιan tura gaba. Sai kuma tai saurin sakin dariya da cewa, “Yes Yah Yoohan kayi gaskiya kuma”.
Murmushi yay mata da bata sumba a gefen kumatu. Daga haka suka fito a motar. Gidan shiru kowa yana a sashensa, hakan yasa Yoohan taya maigadi kaima Aymah kayanta bakin Ζofa. Sannan ya turata ciki ya sulale ya koma taxi Ιin suka fice. Dan hotel yake son guduwa kafin baba malam su fito massallaci su ritsashi.
Umm na zaune a bedroom tana karatu da jiran lokacin sallar isha'i sai ji kawai tai an rungumeta. A firgice ta juyo dan harga ALLAH ta tsorata. Ta waro idanu sabida mamakin ganin wadda batayi zatoba.
“Nu'aymah wai kece da gaske?”.
Kukan murnar ganin Umm Ιinta ta saki tana faΙin, “Nice Ummna, I miss you so much”.
Rungumeta Umm tayi da Ζyau a jikinta itama Ζwalla na cika mata idanu. Kai Ιa dabanne gaskiya. Sanin ba ita kaΙai bace yasa Umm tadata daga durΖuson da tayi a Ζasa ta zaunar da ita a bakin gado. Gaba Ιaya Aymah sai kuma taji kunyar Umm ta mamayeta, sai ta duΖar da kai Ζasa tana Ζara lulluΙe cikinta da gyale. Dariya abin ya bama Umm sosai. Sai dai bataiba. Saima tambayarta tai ina mijin nata?.
Kan Aymah a Ζasa tace waje ta barsa ita dai suna kwaso kaya shi da maigadi. Jin haka yasa Umm fita ta leΖa. Sai dai babu Yoohan babu dalilinsa sai maigadi kawai dake shigo da kayan Ιan barandar falonsu. Shine ke sanar mata Yoohan Ιin ya juya tare da mai taxi akan da safe zai dawo insha ALLAH.
Kai kawai Umm ta girgiza ta koma ciki, inda ta iske Aymah ta fito daga toilet da alama fitsari tayo. Cike da kulawa tace, “Kinji mijin naki ya tafi wai zai dawo da safe. Dama kunyi dashi hakan?”.
“A'a wlhy Umm, ni kawai yace na shigo zaije massallaci ne”. Tai maganar cikin Ιata fuska. Murmushi kawai Umm tayi ita dai, tace, “To kiyi wanka kawai sai na samo miki abinda zakici ke tunda shi ya gudu. Cike da kunyar Umm Ιin data aro ta yafama kanta ta amsa da to. Daga haka ta koma toilet Ιin danyin wanka.
Babu wanda Umm ta sanarma da zuwan Nu'aymah a gidan sai hajjo. Sai ko Muhammad daya dawo massalaci ya ganta a bazata. Baba malam ma sai da ya sallami Ιalibansa ya shigo yaci karo da ita a falo zaune ita da Hajjo da Umm da Muhammad dake liΖe da ita.
Tuni Nu'aymah ta manta da kunya, ta miΖe da sassarfa ta nufi Abbanta dake kallonta cike da kewa da so da Ζaunarta. Gabanta tai niyyar durΖusawa ya riΖota yana faΙin, “A'a mamana keda ke fama da kanki. Irin wannan zuwa haka na bazata”.
Hannunta yaja ya maida a kujera sannan shima ya zauna. Kanta a Ζasa ta shiga gaisheshi cike da kewa. Shiko yana amsawa da kulawa. Abakin Umm yaji cewar Yoohan ya gudu. Dariya kawai yayi dan ya fahimci kunya Yoohan Ιin keji da alama.
Haka sukayi murnarsu su huΙu kawai. Ganin dare ya farayi Hajjo taje sashenta danta kwanta. Aymah kuwa a Ιakin Umm zata kwana tare da Umm Ιinta data bar baba malam shi kaΙai.
Aiko maimakon barci sai suka buΙe sabon babin hira ita da Umm Ιin, sai da suka kusan kai asuba sannan barcin ya kwashi Aymah, daga nan itama Umm tayi.
__________★
Washe gari kam a bazata kowa yaga Nu'aymah a gidan. Kafin kace mi sun rikice da murna da hayaniya. Tun Aymah na Ζunshe-Ζunshen ciki harta saki jikinta ta shige cikin Ζ΄an uwanta anashan shafta. Zuwa tashin hantsi kuwa sai ga Hajarah tazo gidan, dan ita dama tasan da zuwan nata. Rungume juna sukai cike da farin ciki. Yanda suka nuna Ιin har mamaki ya bama kowa. Dan gaba Ιaya salon shaΖuwar Adawiya da Nu'aymah ne ya koma kan Hajarah a yanzu.
A ranar da yamma suma Ζ΄an Abuja suka iso. Ganin Nu'aymah kuma ya matuΖar basu mamaki dansu da suke Abujan ko a labari basusan da zuwan nataba. Har Momy ma sai da ta kasa haΖuri tai complain Ιin cewar Yoohan bai Ζyautaba. Suna matsayin iyayen Nu'aymah amma yazo da ita har Abuja bai fara kaita canba sai dai suzo su ganta anan tsulum.
Daga karshe dai Yoohan Ιinne da yazo gidan ya kare kansa akan wannan tuhuma. Dan Aymah bata iya cewa komaiba tunda itama tunanin zuwa can Ιin baizo mataba. ZumuΙinta kawai azo kano.
Ya bama su baba malam haΖuri akan rashin tsayawarsa jiya. Acewarsa aikin gaggawa ne ya samesa shiyyasa bai tsayaba. Duk sun masa uziri akan haka. Sannan suka Ιora da godiya akan hidimarsa ga gidan marayunsu daketa Ζara nunkuwa a koda yaushe. Akan bikin nanma kawai da za'ai ba Ζaramin hidima yayiba.
Washe gari baΖi suka fara cika gidan, Ζ΄an katsina, Ζ΄an lagos da sauransu, kowa kuwa yana sake yaba yanda Aymah ta Ζara girma da canjawa a cikin shekara Ιaya kacal. Gashi daga gani ansan ta samu lafiya yanzu. Sai dai fatan ALLAH ya sa ta sauka lafiya kuma.
Da yamma sukaje can orphanage akai walima, anan ta haΙu da sauran yayunta su Kubrah. Tayi mamakin ganin yanda Aunty Kubrah Ιin dukta lalace. Harta kasa haΖuri ta tambayi aunty Hajarah.
Cike da damuwa Hajarah tace, “Humm Aymah ke dai ALLAH ya Ζyauta, zaman natane babu daΙi daga ita har mijin da kishiyar. Kwanaki ai kusan watanta biyu a Lagos wajen Abbah Musbahu. Sunyi faΙa ya daketa shine taje can”.
Kasa magana aymah tayi saboda damuwa. Kodai babu komai Kubrah Ζ΄ar uwartace duk da a yauma ta nuna har yanzu ba sonta takeba.
Duk wannan hidima da akeyi kuwa su Aymah zagaye suke da yaran Jay ta ko ina. Motsin kowa akan idonsu yake faruwa. Tun daga orphanage har cikin gidansu.
Washe gari juma'a aka Ιaura auren amare ashirin da takwas maza da mata. Kowa ya kalli su baba malam yasan suna cikin farin ciki. Sai dai ai fatan ALLAH ya basu ladan hidimarsu ga marayun ALLAH babu gajiyawa.
An miΖa amare Ιakunansu, daga haka baΖi suka fara raguwa sai na jiki kawai aka bari. Kamar yanda Jay ya samu tattaunawa da baba malam a ranar Ιaurin aure a yau suka yanke hukunci bisa shirinsu. Duk da kuwa da Ζyar baba malam Ιin ya yarda da buΖatar Yoohan, Jay, Omar Ιin. Dan basu Ιoye masa komaiba game da shirin nasu gudun kar a samu matsala.
Tun a yammacin ranar baba malam ya fara takalar Umm da batun mallakama Nu'aymah wasu kaddarorinsa dan yasan lallai mai musu laΙe na tare da su saboda tuna Nu'aymah tazo garin ya fahimci mai laΙen ya Ζara Ζaimi wajen yimusu. Ta riga tasan shirinsu, itama sai ta biye masa. Sai dai zancen bai tsahoba suka barshi akan zasu Ζarasa da safe dan lokaci baba malam nada uziri..........✍
0 Comments