TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Makauniyar soyayyah page 51-52

 [4/29, 22:32] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞



🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀🤦🏽‍♀



*STORY & WRITTEN*


                *BY*



*MARYAM AHMAD PAKI*




*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽






_Alhamdulillahi ala kulli hal_.




*QUESTION OF THE DAY*


_Qoramun(kogi) Aljannah guda nawa ne? lissafo sunayen su_






51&52 


Tun da na koma gida na rasa sukuni akan sa’banin da muka samu da Dr Sadik.


Ni kaina nafi so yazo gida su Abbu da Ummu su san dashi, sai dai ba ni da wannan damar, tsora na shine idan wataran su ka had’u da yaya Aminu, zai iya fallasa sirrin da nake ‘boye wa tsakani na da yaya Faruk, hakan na nufin rashin amintar su da Dr Sadik kenan.


Jiki na yana bani cewa yaya Aminu yasan abin da ke tsakanin mu da yaya Faruk, idan nayi duba da amincin su, ba sa ‘boye wa junan su sirrin su.


Hakan na nufin dole in iya taku na dan ba na son kowa yasan tsakanin mu da yaya Faruk har sai ya dawo na bashi hak’uri, sannan in samu damar gabatar da Dr Sadik a matsayin wanda nake so.


Ya kamata na nemo ma kaina mafita saboda kar Dr Sadik ya d’auka da wata manufa a guri na da na hana shi zuwa gidan mu.


Kira ne ya shigo waya ta, mumban k’asar waje na gani, nasan ba kowa zai kira ni da wannan number ba sai yaya Faruk.


Nayi mamakin ganin kiran shi a wannan time d’in kasancewar mun kwana biyu bai kira ni ba kuma ba mu had’u a chat ba.


Jiki na a sanyaye na yi picking d’in call d’in.


Sallama na mishi ya amsa.


"Teemah na" abin da ya fad’a kenan.


Ban amsa kiran da ya min ba illah cewa da nayi "yaya Faruk ina wuni, ya aiki".


"lfy lau, ya su Ummu".


"Suna nan lafiya".


"Ya studies?" ya tambaye ni.


"karatu alhamdulillah".


"Nasan yanzu kun shiga ND 2 ko? ya tambaye ni.


" Eh yaya har mun yi nisa".


"To Allah ya taimaka".


"Amin yaya Faruk".


Teemah kin ji ni shiru ba na kiran ki, gashi ba ma had’uwa a chat, ba na samun zama ne, da ina sa ran a week d’in nan za mu dawo, amma ina ganin sai mun kai next month za mu dawo, nima na k’osa in dawo in ga kyakkyawar fuskar ‘yar k’anwa ta, in ga ko tayi missing d’ina".


Murmushin jin dad’i nayi don a gaskiya, nasan yaya Faruk ya damu dani, alamomi da yawa sun nuna min hakan.


"Allah ya dawo daku lafiya".


"Amin Teemah nah, na gode da addu’ar ki, bari in barki haka, sai kin sake ji na".


Sallama ya min ya katse wayar.


A zuciya ta kuwa fargabar dawowar yaya Faruk nake yi, nasan cikin biyu za ayi d’aya, ko dai ya hak’ura dani idan na fad’a mishi ina da wanda nake so, ko kuma ya bijire ma buk’ata ta saboda ni kaina nasan yaya Faruk ba k’aramin so yake min ba.


Yau ma kamar kullum, ni da Dr Sadik ne a cikin mota muna hira irin ta masoya, Tsayuwar Anisa muka gani a gaban mu tana murmushi.


Gaisawa suka yi da Dr kana ta juya kallon ta gare ni tace "Tun da naga motar Dr, nasan kuna tare, shi yasa ban wahalar da kaina gurin kiran ki ba, na k’araso".


"Kun gama lectures ne" na tambaye ta.


"Eh mun gama, ni yanzu zan tafi gida, yau b azan tsaya jiran driver ba, tun da yaya Khalil ba ya gari".


"Ok in kin je gida kya gaida su Momi da Dadi, ki ce ma Driver ba sai yazo ba, zan dawo da kaina".


"Za su ji, zan fad’a mishi".


Duk wannan zancen da suke yi, Dr bai sa musu baki ba, sai a yanzu yace "Anisa in ba damuwa, ina son yin Magana dake".


Gaba d’aya maida kallon mu gare shi muka yi don sauraren mai ze ce.


Murmushi tayi tace "Ba damuwa Dr ina jin ka".


"A gida ba a barin ku kuna kula samari ne?" tambayar da ya Dr ya fara yi ma Anisa kenan.


"Me ka gani Dr? ita ma ta jefa mishi wata tambayar ba tare da ta amsa mishi ba.


"Naso ki amsa min tambayata ta farko, amma sai ki kamin halin ‘yan nijah ki ka sake jefa min tambaya akan wadda na miki, abin da yasa na tambaye ki shine yadda Zarah tak’i bani damar gabatar da kaina a gurin parents d’in ta, beside ni ba na son abin da zai zubar min da girma na, kin ga yawancin students sun san ni, so yanzu sai ki ga an fara wa mutum wata fassara ta daban, amma ita naga hakan kamar bai dame ta ba, ina so ki mata Magana, may be za ta fi d’aukar zancen ki da mahimmanci".


Anisa kuwa tambayar da ta fara yi ma kan ta shine "Menene dalilin da yasa ba na son gabatar da Dr a gida? Duk kuwa lurar da tayi ina son shi".


"kayi hak’uri Dr, zan mata Magana inshaAllah".


Duk wannan maganar da suke yi ban ce komai ba, kamar ba na gurin.


Anisa ce ta mana sallama ta tafi.


Gaskiya yau Dr ya ‘bata min rai, ban so ya tunkari Anisa da wannan maganar ba, saboda ba na so Anisa tayi zargin ko ta kawo wani abu a ranta akan k’in gabatar da Dr da ban yi ba a gida.


Bayan tafiyar Anisa ne na kalli Dr cikin damuwa na ce "Dr!


D’agowa yayi ya kalle ni ba tare da ya amsa kiran da na mishi ba.


Ban damu da amsawar shi ba naci gaba da cewa "Sadik, ban ji dad’i ba da ka fad’a ma Anisa halin da muke ciki, ba wai dan ban yi trusting d’in ta ba, na fi so in kammala wani shiri ne Kafin in tunkare su da zancen ka".


Wayar shi yake pressing kamar ba dashi nake Magana ba, ga dukkan alamu, bai damu da yadda na nuna ‘bacin raina ba.


"shiri? Wane irin shiri ne haka da zai hana ki gabatar dani a gidan ku".


Ka k’ara hak’uri Sadik, komai ya kusa zuwa k’arshe".


Wannan karan cikin ‘bacin rai ya fara Magana "look Zarah, ina ganin haka za mu ci gaba da tafiya, to bai da wani amfani, na baki yau ki yi tunani akan wannan maganar, in ba haka ba ni zan samar mana mafita".


Wani irin sanyi jiki na yayi, yadda Dr yake fad’a min maganar da ranshi yake so, abin takaici shine na kasa nuna masa ‘bacin raina, duk kuwa da yadda maganar ta min zafi a raina.


Sai kace ba Fatima ba da ba na bari a fad’a min mai zafi ba tare da na rama ba?


Sai yanzu na yarda da Hausawa ke cewa *SO HANA GANIN LAIFI*.


"Zan tafi" Dr Sadik ya fad’a.


Jiki na kamar ba nawa ba, na fito daga motar.


"Sai an jima" na fad’a a sanyaye.


"Take care" ya fad’a a gajarce, kana ya figi motar a guje ya bar department d’in mu.


Ko da muka class, jiki na duk a sanyaye yake, wanda yasa har Halima ta tambaye ni dalilin canzawa ta.


Sanin ba ni da wani gamsashshiyar amsar da zan ba ta yasa, nace mata ba na jin dad’in jiki na ne.


Cikin kulawa ta min fatan samun sauk’i.

Ko da na koma gida, damuwa ce ta addabe ni ganin yau mun rabu da Dr Sadik cikin ‘bacin rai, babban abin da yafi d’aga min hankali shine yadda na ga Dr Sadik ya d’au zafi a yau.


Haka nayi ta tunanin halin da Dr yake ciki a yanzu, ganin ba irin sallamar da muka saba yi dashi muka yi ba.


A haka Ummu tazo ta same ni tana tambaya ta me yake damuna.


Nasan Ummu na da saurin fahimtar halin da nake ciki yasa na yi murmushin da bai kai ciki ba, na ce mata ba na jin dad’in jiki na ne.


Kallo na Ummu tayi kamar mai son gano wani abu, ganin haka ne yasa na tsargu na mik’e nace "Ummu bari in je in kwanta".


"Allah ya k’ara sauk’i" Ummu ta fad’a tana bi na da kallo.


Ni da na tafi d’aki da niyyar in samu hutu da tunanin dake addabar zuciya ta, sai gashi ina kwantawa barcin gaske ya d’auke ni.


Ba ni na farka ba sai da naji Anisa ta d’aka min duka a jiki.


A firgice na tashi ina waige-waige kamar wadda take neman wani abu.


Anisa ce ta koma gefe tana ta kwasar dariya ganin yadda nayi.


"Ba ki da abin yi ne yasa ki ke kwasar wannan dariyar". abin da nace mata kenan.


Ban k’ara bi ta kanta ba, na wuce bathroom da niyyar yin alwala, ganin yadda lokacin sallah ya wuce ina bacci.


Ko da na fito, samun ta nayi tana waya da yaya Khalil.


Sallaya na shimfid’a na ta da sallah, har na idar da sallah ba ta gama wayar da take yi ba.


Mik’ewa nayi da niyyar barin d’akin, saboda ban san lokacin da za ta gama wayar ba.


Har na kusa kaiwa bakin k’ofa naji ta kira suna na.


Juyowa nayi na kalle ta, katse wayar tayi ta ce "Fatima ki dawo ki zauna, akwai maganar da za muyi".


Ban musa mata ba na dawo na zauna a gefen gado.


"Ina jin ki" na ce da ita.


Anisa ce ta ce "Fatima, ki yi hak’uri da abin da zance miki, wata k’ila maganar ba za ta miki dad’i ba".


Anisa taci gaba da cewa "Fatima kin canza".


Da sauri na katse ta "Kamar ya na canza?".


"Fatima ki bari in gama maganar da zanyi sannan ki yi challenging d’ina, a da nasan ke ba kya ‘boye min komai naki, amma yanzu na lura ba kya son in san halin da kike ciki, ni bance ki dinga fad’a min komai naki ba, saboda ko wani mutum yana son sirri a rayuwar shi, yanzu na fara sa wa a raina cewa akwai abin da kike ‘boye min, na farko kin ga ba ki fad’a min alak’ar ki da Dr Sadik ba sai da Allah yayi naje department d’in ku, sannan ki ka fad’a min, da na miki Magana sai ki ka kawo min excuse d’in ki, na bar zancen, na biyu shine ban san hujjar ki ban a k’in ba Dr damar yazo gida su Abbu su san dashi, bayan nasan cewa in akwai dalilin ki nayin haka za ki fad’a min, shima ba ki fad’a min ba sai da Dr ya tare ni da zancen".


Tsayawa tayi da min magana tana tunanin ko zan ce wani abu, amma ban yi Magana ba.


"Fatima hakan ya tabbatar min kenan da abin da kike ‘boyewa wanda ba kya so in sani, in ba haka ba nasan ba za ki tsiri ‘boye-‘boye ba".


Ban so Anisa ta d’au zancen a haka ba, duk abin da zan fad’a ma ta zai zama k’arya, tun da b azan fito in fad’a ma ta alak’a ta da yaya Faruk ba ne yasa na dakatar da Sadik zuwa gidan mu, ba kuma na so ta ci gaba da sa zargi a ranta.


"Anisa ni fa ba ni da wani dalili da yasa ban ba Sadik damar zuwa gidan mu ba, kawai dai ina ganin kamar ba mu wani dad’e ba, shi yasa".


"Wannan ba hujjah bace, in dai kin san ba wani dalili to ki barshi ya fara zuwa zancen a gida, instead of ya dinga zuwa department d’in ku, wasu su fara muku wata fassara ta daban". Anisa ta fad’a.


Gaskiya ne da Hausawa ke cewa "Mai shawara aikin sa ba ya ‘baci" yanzu gashi d’an maganar nan da muka yi da Anisa yasa na samu relief akan tunanin da suka min dabaibayi, abin da yasa bazan nemi shawarar ta ba akan yaya Faruk da Dr Sadik, na san yayan ta za ta ba ni shawarar in za’ba, gwara dai in bar abin a raina har lokacin da komai zai zo k’arshe.


"Insha Allahu zan fad’a mishi ya fara zuwa gidan"


"hakan dai yafi".


Narai-narai da ido nayi kamar zan yi kuka nace ‘Anisa ba zan ‘boye miki ba, ina son Dr Sadik, hakan yasa ba na so in ga na ‘ba ta mishi ranshi wanda zai jawo yayi fushi da ni, yanzu haka ban san me yake min dad’i ba saboda mun samu misunderstanding dashi akan wannan maganar, Anisa ki ba ni shawara".


"Wannan wani irin so ne, Fatima take yi na Dr?" Anisa ta tambayi kanta.


"Fatima, gaskiya ya kamata ki gane ke mace ce mai class, ba wai ina zuga ki ba ne, ina so kin san mace aka sani da jan aji, kar ki bari namiji ya gano irin son da kike mishi, hakan zai sa ya raina ki, ko ya samu damar juya ki, ba wai ina nufin kar ki nuna mishi irin son da kike mai ba, a harkar soyayya yana da kyau idan d’aya ya ‘ba ta ma d’aya rai yasan cewa shine da laifi, amma ba wai ya zamana mutum d’aya shi zai dinga amsar laifin da ba shi ya aikata ba, sorry to say Fatima, son da kike ma Dr ya fara wuce limit, saboda na ga hakan a tare da ke, ya kamata ki dawo hanya, ki kuma yi karatun ta natsu, ba komai nake guje miki ba, sai dan kar ki fad’a *MAKAUNIYAR SOYAYYA*, shawarar da zan ba ki shine ki tura mai text ko kira shi a waya akan cewa kin amince ya fara zuwa gida zancen, ina ganin zai daina fushin da yake yi dake ko Zarah" ta k’arashe zancen da alamar tsokana.


Murmushi nayi saboda nasan tana tsokana ne da sunan da Sadik yake kira na.


"Na gode da shawarar ki Anisa, ba abin da zance miki sai godiya, kuma zan yi k’ok’arin gyarawa".


"Kar ki damu Fatima, matsalar ki, matsala ta ce".


Hira muka ci gaba da yi da Anisa, sai wajen yamma sannan Anisa ta tashi ta tafi gida.


Shawarar ta na d’auka na tura ma Sadik text akan cewa na amince ya fara zuwa gidan mu.


Ran da ya fara zuwa gidan mu na gabatar dashi gurin Abbu, sun gaisa da Abbu cikin mutunta juna.


Tun daga sannan jefi-jefi Dr Sadik yake zuwa gidan mu, mafi lokacin zuwan shi ran weekend.


Haka muke ta gudanar da soyayyar mu da Dr Sadik.


Yau bayan na dawo daga makaranta, Ummu ke sanar dani Hajiyan wagini (mahaifiyar su Abbu) tazo tana gidan su Anisa, murna da tsalle haka na dinga yi, saboda mun kwana biyu ba mu je wagini ba, ita kuma ta na dad’e wa, bata zo ba.


Ko abincin ban tsaya ci ba, ina watsa ruwa na canza kaya na fito, na tafi shashin Ummu.


"Sai ina?" Ummu ta tambaye ni.


Dariya nayi nace "sai wajen waccen tsohuwar za ni, ba zan iya jiran ta tazo nan gidan ba, gwara in je in ganta".


"In kin je kya gaishe su, in Abbun ku ya dawo za mu je mu mata sannu da zuwa".


"To Ummu sai na dawo".


"Sai kin dawo Auta".


Saboda yadda na k’osa in kai gidan, ban tafi a k’asa ba, na tari keke napep na hau.


Ina shiga gidan na same su a falo suna zaune.


Sallama nayi da guda na fad’a jikin Hajiya na k’ank’ame ta.


Anisa ce ta amsa sallamar ta na dariya.


Sai a lokacin na lura da Momi dake zaune a d’aya daga cikin kujerun dake girke a falon, na gaishe ta.


Amsa min tayi ta na murmushi.


Ture ni daga jikin ta tayi tana dariya tace "Ja’ira za ki k’arasa ni ne, dama yanzu mu ka gama yi da Anisa".


"Kai Hajiya mun yi missing d’in ki ne fa, shine za ki gwasale mu".


"Ke raba ni da yaren nasaran nan naku, za ki wan ice kun yi misin ko musin d’ina ne oho miki".



Dariya muka kwashe da ita ni da Anisa.


"Ja’irai ni kuke ma dariya, bari iyayen ku su zo zan fad’a musu shak’iyancin da ku ke min".


Anisa ce cikin dariya tace "Sorry Kakus, ba za mu sake ba".


Yamutsa fuska tayi tace "Abin naku gaba yake yi, har da sauro ku ke had’a ni dashi".


Sake fashe wa da dariya muka yi, ni kuwa har da rik’e ciki.


Haka muka dinga wasa da dariya da Hajiyan wagini, sai da yamma na mik’e da niyyar tafiya.


Momi ce tasa Driver ya maida ni gida.


Da daddare su Abbu da Ummu da za su gaida Hajiyan wagini na sake bin su, saboda muna shiri da ita sosai.


San da muka je gidan su Anisa, haka aka had’u a falon Dadi ana ta hira, da wasa da dariya.


Sai wajen k’arfe tara na dare muka baro gidan.


Hajiyan wagini sai da tayi kwana uku a gidan su Anisa sannan ta tawo gidan mu, tun da tazo na tare a d’akin ta, wani lokacin Anisa na zuwa a sha hira da ita.


Yau ta kasance ranar jumma’ a, ba mu da wani lectures da yawa, hakan yasa na dawo gida da wuri.


Ina dawo wa, na wuce d’akin Hajiyan wagini zaune akan carpet tana cin farfesun kaji.


Zama nayi kusa da ita ina cewa "Kai Hajiyan wagini, an samu dad’i ko Magana ba a iya yi, tun da ba za a min tayi ba bari in wa kaina".



Duk wannan maganar da nake yi Hajiyan wagini ba ta ce min komai ba, sai ma ci gaba da tayi da cin naman ta.


Hannu na saka a cikin plate d’in na d’auki yanka d’aya daga ciki na sa a baki na.


"gaskiya Hajiya dole ba za ki yi magana ba, wannan delicious haka".


Harara ta tayi tace "wannan bature bai kyauta ba, a ce mutum yana d’an bahaushe gaba da baya, in zai yi Magana sai ya had’a da harshen nasara".


"Kai Hajiyan wagini, yanzu zamani ya canza, mun riga da mun sa ba da wasu kalmomin da turanci, idan za muyi Magana sai mun had’a dashi".


"wannan bature dai ya nace mutane".


Dariya nayi nace "Hajiya kenan".


Kallo na tayi tace "Ke Fatima kina da number Soja ki nemo min shi mu gaisa".


A gaskiya bazan iya kiran yaya Faruk ba a gaban Hajiyan wagini, nasan za ta iya fahimtar wani abu, saboda nasan zai yi wuya in kira shi ba tare da ya fad’a min wata kalma da ta k’unshi so ba, ko in kira ta ya fad’a ma ta abin da ke tsakanin mu, nasan kuwa Hajiya sai tafi kowa murnar da wannan zancen, dan haka nace "Ba ni da ita, nima idan ya kira Abbu ko Ummu ne muke gaisawa".


Hajiyan wagini ce ta ci gaba da cewa "Allah sarki Mai gida na nakai na, Allah ya dawo dakai lafiya ka fito da mata mu sha biki".


Ganin Hajiya ta d’akko zancen yaya Faruk yasa na mik’e, don nasan ba ta gajiya da zancen shi.


Tafiya na fara yi ina cewa "Ni dai bari in je in huta, yanzu in kika fara min maganar shi, ba gajiya za ki yi ba".


"To ‘yar nema, da ma nasan ai ba zama za ki yi ba, tun da kin ji an ambaci wanda ba kwa shiri, dole ki tafi".


"Ni dai kin ga tafiya ta Hajiya" na fice daga d’akin.


Ran lahadi muna zaune ni da Dr a gurin shak’atar dake gidan mu, motar yaya Aminu ce na ga ta shigo gidan.


Gaba na ne yayi wani irin buga wa, nasan idan har yaya Aminu yasan me ke tsakanin mu da yaya Faruk, ba k’aramin ‘bata min zai yi ba, ko ya fad’a ma su Abbu abin da ke tsakanin mu da yaya Faruk, nasan kuwa zan fuskanci hukunci gurin Abbu.


Parking yayi a gurin parking space, Shi da Anty jidda ne da su Humaira da Nabil suka fito daga motar.


Su Humaira ne da Nabil suka rugo da gudu gurin da muke, yayin da Anty Jiddah da yaya Aminu suka shige cikin gida.


Bud’e musu hannu nayi suka fad’a jiki na suna dariya.

Murmushi Dr Sadik yayi yace "wannan yaran waye Zarah"


"yaran brother d’ina ne, yaya Aminu" na bashi amsa.


"ku zo mu gaisa, ko sai Antin ku kawai ku ka sani".


Humaira ce ta tawo gurin shi, shi kuwa Nabil k’ara mannewa yayi a jiki na, alamar ba za shi ba.


San da Dr Sadik za tafi, kud’i ya bani a siya ma su Humaira su chocolate.


Ko da na amshi kud’in, tunanin w azan ba tsakanin yaya Aminu da Anty Jidda nake yi, nasan dukkan su in suka sa tsakanina da Dr Sadik, ba za su yi wani murna da kyautar da ya yi musu ba, zuciya ta tafi kwanciya akan in ba Anti Jidda, nasan ita ba ta da wata matsala.


Godiya na mishi, kana muka yi sallama ya shiga motar shi ya tafi, ni kuma na rik’e hannun su Nabil muka nufi cikin gida.


Ina shiga cikin parlour d’in, na ga ba kowa, nasan ba za su wuce suna d’akin Hajiyan wagini ba, hakan yasa na nufi d’akin.


Sallama na musu na nemi kusa da Anti Jiddah na zauna, na gaishe ta.


Cikin Magana k’asa-k’asa tace "Fatima wanene wanda na gan ku a tare, ko da yake mu bar maganar, zan zo d’akin ki mu yi maganar, yanzu ki tashi ki je, yayan ki na neman ki, yace ki same shi a garden".


Jiki na ne ya min nauyi, nasan kiran da yaya Aminu ya min na nufin zai min magana ne akan Dr Sadik, ko kuma akan yaya Faruk.


Tashi nayi na nufi garden d’in don in ji mai yaya Aminu zai ce min.




Post a Comment

0 Comments