TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Makauniyar soyayyah page 47-48

 *STORY & WRITTEN*



           *BY*



*MARYAM AHMAD PAKI*





*🌈KAINUWA WRITERS ASSOCIATION*🤝🏽





*Wannan shafin na sadaukar dashi ne ga masu son wannan novel d’in, masu min Magana ta pc, masu kira na daga wasu gari, ‘yan faceebook, ‘yan whatsapp, da duk group d’in da ake posting d’in wannan novel d’in da wanda na sani da wanda ban sani ba, na nesa da na kusa*


*Ba abin da zance muku sai dai fatan alkhairi, Allah ya bar zumunci*




*QUESTION OF THE DAY*


_A halayen larabawa kafin musulunci, mai suka kasance suna bauta ma wa? saboda me yasa suke kasha ‘ya’yayensu?_








47&48



Bayan gama jarabawar mu na zangon farko, aka bamu short break na hutun zangon.


Muna zaune a gurin shak’atawa ni da Ummu muna hira, motar gidan su Anisa ce ta shigo.


Bayan ta fito daga motar ne ta nufo in da muke tayi tana murmushi.


Gaisawa suka yi da Ummu kana na gaishe ta, muka nufi main parlour.


Kitchen na shiga na d’ebo drinks da snacks a d’an k’aramin tray da glass cup.


Ajiyewa na yi gaban ta, na nemi guri na zauna.


Da fara’ar ta tace "Fatima kwana biyu ba ki lek’o mu ba, tun da kun samu hutun first semester, in zan tafi sai mu tafi tare".


"Bari in je ciki Momi, in za ki tafi sai mu tafi, Ummu kya fad’a ma Abbu in ya dawo".


Mik’ewa nayi na nufi d’aki na don in basu guri.


Da na shiga d’aki, kaya set 5 na d’iba na sa a jaka.


Momi sun dad’e a falo suna hira kana ta kira ni muka tafi.


Tun da naje gidan su Anisa muke hira, mu yi ta labarin ‘yan course d’in mu da rayuwar school life.


Haka yaya Khalil ke zuwa mu zauna a parlour ko a garden muyi ta hira.


Gaskiya ina jin dad’in yin hutu a gidan su Anisa.

Kwana biyar nayi a gidan na koma gida.


Mun koma school in da muka shiga zango na biyu, karatu ya k’ara zafi fiye da zangon farko, komawar mu da 2 Weeks result ya fito, GP d’ina yayi kyau, dad’in da naji shine ban da wani matsala na carry over ba, da muka had’u da Anisa ma ta fad’a min GP d’in ta yayi kyau.


Mun yi nisa a zangon aka fara maganar siwes (Industrial training), tunani na fara yi inda zanyi siwes d’in.


Zuciya ta ce ta ba ni shawarar in sa Asibitin school d’in mu dan lecturers d’in mu sun fad’a mana ana samun experience a can.



Yau ta kasance ranar lahadi, yaya Khalil ne ya shirya cikin tsadadden yadi kalar ruwan k’asa, yadin ya matuk’ar yi masa kyau.


Ta slice window na hango shi ya fito daga side d’in shi ya nufi parking space zai shiga mota.


Da sauri na fito na k’arasa gurin shi ina cewa "yaya Khalil ina zaka ne? na ga wannan kwalliyar kamar gurin Anty na za ka, duk da ban san ko wacece ba".


Ta’be baki yayi yace "Kin ga Auta ki bari in na dawo sai muyi maganar, in ba haka ba sai ki hana ni fita da maganar ki".


Dariya nayi nace "kai yaya Khalil daga fad’ar gaskiya".


Shi ma dariya yayi yace "To yanzu dai shi kenan sister, tun da kina so in samo miki Anty, zan bincika in gani, yanzu dai bari in tafi, sai na dawo".


"Sai ka dawo yaya Khalil".


Shiga motar yayi ya kunna ya bar gidan yana d’aga min hannu, d’aga mishi hannu nayi na koma cikin gida.


Yana isa gidan, ya danna hon.


Mai gadi ne yazo ya bud’e masa ya shiga da motar.


Samun Anisa yayi a balcony d’in gidan, in da aka k’awata gurin da kujeru da tebur a can gefen gidan.


Gurin ya k’arasa yana sakar mata tsadaddan murmushi, ya nemi guri ya zauna.


Gaishe shi tayi ya amsa mata, tambayar ta yayi ko Momi na ciki?.


Amsa masa tayi "Tana ciki".


"Bari in shiga mu gaisa, yanzu zan dawo, yau akwai sabon labari da zan baki" ya fa’da da alamar wasa.


"Sai ka fito".


Tashi yayi ya nufi cikin falo d’in.


Ko da ya shiga parlour d’in ba kowa sai k’arar tv dake aiki shi kad’ai a parlour d’in.


Hango ta yayi tana sakkowa daga upstairs d’in dake parlour d’in.


"Khalil yaushe ka shigo, maimakon ka hawo sama ina can".


"shigowa na kenan".


 Momi, Ina wuni". Yaya Kalil ya gaishe ta.


"lafiya lau, ya su Hajiya da Fatima". Momi ta amsa masa.


"Suna nan lafiya".


"Haule!" Momi ta fara kiran mai aikin ta.


Cikin ladabi ta amsa ta tsuguna tana cewa "Gani Hajiya".


"Drinks da ruwa da abinci za ki kawo ma Khalil".


"Toh Hajiya" Haule ta amsa ma ta.


Khalil ne yayi saurin kar’ban zancen da cewa "Momi ta bar shi kawai, zan koma gurin Anisa ne, tana can balcony".


"Ba ayi haka ba, ke Haule je ki d’akko ki kai mishi can".


"Toh Hajiya" Haule ta amsa cikin ladabi ta bar parlour d’in, ta nufi kitchen d’in.


"Kace ba za ka zauna muyi hira ba, za ka tafi gurin mutuniyar ka" Momi ta fad'a



"Ai zan dawo ciki Momi".


"Sai dai na gan ka kawai, nasan sallama ce za ta shigo dakai, in ka had’u da Anisa ai sai Allah in kuka fara zancen ku".


Dariya yayi ya bar falon, Momi kuwa neman guri tayi ta zauna.


San da ya koma, samun ta yayi tayi playing ‘din wak’ar Rihana da tayi mai suna *if its love* bin wak’ar take yi a hankali kamar ita ta rera wak’ar.


Murmushi yayi ganin yadda take bin baitin wak’ar, ita ma murmushi tayi tace "yaya ya aka yi ne? naga kana murmushi".


Na ga ai kina son wannan wak’ar ne".


"yaya Khalil ai ta iya wak’a ne"


Haule ce ta k’araso ta ajiye tray d’in a kan table d’in, ta bar gurin.


Kwalin chivita ya d’auka yayi shaking, sannan ya tsiyaya a glass cup d’in.


Sai da ya fara sha kana ya ajiye yana kallon ta.


"Anisa! ya kira sunan ta.


Amsa masa tayi tana jiran ji mai zai ce ma ta.


"Anisa zan bayyana miki abin da ke zuciya ta ne, ina so ki ba ni shawara".


Ita dai bin shi take da kallo, saboda tasan in yaya Khalil zai yi Magana mai mahimmanci, manta wa yake da wani abu wai shi wasa, dan haka ta bashi dukkan hankalin ta.


Ci gaba yayi da cewa "Anisa akwai yarinyar da na dad’e ina son ta, mun shak’u da ita, da farko ban d’auka cewa son ta nake yi ba, na d’auka *shak’uwa ce* sai daga baya na gane son ta nake yi, shine nake neman shawarar ki akan yadda zan tunkari yarinyar in fad’a mata".


Wani abu ne taji ya tsaya ma ta a zuciyar ta, wanda ta rasa ko na menene, ba ta so yaya Khalil ya fahimci tana cikin wani hali.


Cikin dauriya ta fara da cewa "Ina ganin yaya Khalil gwara ka fad’a ma yarinyar, barin kashi a ciki ba ya maganin yunwa, kuma tun da kace kun shak’u da ya yarinyar ina ganin ba za ta k’i amsar tayin soyayyar ka ba, yaya Khalil ba wai zan yaba ka bane, amma ina ganin duk yarinyar da ka fito ka ambata mata kana son ta, za ta amince dakai, ka je ka fad’a mata".


Wani irin murmushi dad’i yayi, saboda amsar da yake son gano wa, ya gano cikin sauki duba da re-action d’in Anisa d’in.


"Anisa! Ya kira ta a karo na biyu.


Wannan karan ba ta samu damar amsawa ba, ganin yadda ya zuba mata ido.


Bai damu da amsawar ta ba yaci gaba da cewa "Anisa ba kowa bace yarinyar da nake nufi illah Anisa".


Saurin kallon shi tayi tana jiran k’arin bayani.


Lura da hakan da yayi yasa yace "Anisa ke nake nufi, ke nake so…., ina fatan za ki amshi tayin soyayya ta da na miki da hannu bibbiyu".


Saurin rufe fuskar ta tayi da tafukan hannun ta.


Cikin tsokana yace "Bari in tashi in tafi, tin da ba a amince da ni ba".


Da sauri ta bud’e fuskar ta tace ‘kai yaya Khalil ni ban ce haka ba".


"Kin amince kenan?".


Sunkuyar da kan ta tayi tana murmushi kasancewar tana jin kunya ta fito tace mai ta amince.

Duk da ya fahimci ta amince dashi, amma yana so ta fad’a da bakin ta saboda zai fi yin marhabun da hakan.


Yaya Khalil bai bar gurin ba sai da ya samu amsar shi daga bakin Anisa na cewa ta amince da soyayyar shi.


Nan ya dinga fad’a mata yadda yake son ta a zuciyar shi, hira suka ci gaba da yi kamar wanda suka dad’e a soyayya.


Da zai tafi ne ya kalle ta yace "Kin san da zan tawo nan, sai Fatima ta tsare ni wai ina zani haka, kamar wanda zai je gurin budurwa, shine n ace mata tun da Anty take so zan samo mata, kinga yanzu in na koma sai in fad’a mata Antin da na mata".


Cikin marairaicewa ta fara cewa "Plsss yaya Khalil kar ka fad’a mata, kasan Fatima tsokana ta za ta dinga yi".


Dariya yayi yace "Shi kenan tun da ba kya son k’awar ki ta sani, ni nasan Fatima da kan ta za ta gano".


"Ni ma ai zan fad’a mata, amma ba yanzu ba".


"kunyar ta kike ji kenan, ko su Ummu da Momi ki ke jin kunya su ji".


Shiru ta mishi ba tare da ta amsa mishi ba tare da ta ce mai komai ba.


Girgiza kai kawai yayi ya sakar mata murmushi ya wuce cikin falo d’in.


Cikin parlour d’in yaya Khalil ya koma yayi ma Momi sallama ya fito ya tafi.


Fitowar da yayi suka had’u za ta shiga falo d’in, kallon junan su suka yi wanda ke nuni da sak’on da suka isar ma juna sannan ya mata sallama ya tafi.



A school, Orientation na musamman aka mana akan Siwes da gurin da ya dace muyi siwes d’in mu.

An bamu form mun yi filling, inda muka cike sunan mu, account number d’in mu, Bvn number d’in mu, sai sunan inda za muyi siwes d’in da address, daga k’arshe suka amshi form d’in.


K’awancen mu na nan da Aisha amma ba mu cika had’uwa ba, kasantuwar department d’in mu ba d’aya ba, sannan akwai nisa tsakanin mu da department d’in su.


Mun fara jarabawar mu na zangon na biyu wannan karan ma cikin nasara, inda aka raba mana takardar siwes inda za mu kai ayi accepting d’in mu, period of attachment d’in 4 month ne za muyi.

Halima ce ta tambaye ni inda zanyi siwes d’ina, na fad’a mata a cikin asibitin school zan yi, jin hak ita ma tace bari tasa nan.


Naji dad’i hakan da Halima tace nan za tayi, saboda zan so ace akwai wandda na sani a gurin da zanyi a ‘yan class d’in mu.


Mun kai namu a asibitin school d’in mu, sun yi accepting d’in mu a d’aya daga cikin siwes student d’in su.


Anisa ma jin cewa a cikin school zanyi siwes d’ina yasa ita ma takai takadar ta laboratory dake cikin asibitin.


Bayan jarabawar mu da sati d’aya mu ka fara siwes d’in mu ni da Anisa da Halima a Shehu Muhammad kangiwa Medical Center dake cikin Polythecnic.



Sanye nake da lapcoat, yayin da nasa farin baby hijab, hakan sai ya k’ara min kyau da shigar.


Folder na d’auka zan kai office d’in Dr Abubakar Sadik da Dr Fatima.


Sai da na fara zuwa office d’in Dr Fatima na kira sunan patients d’in da ke waje kana na shiga ciki muka gaisa da ita na ajiye mata folder.


Gaskiya ina matuk’ar ganin girman Dr Fati kasancewar ta dattijuwa, mai son mutane, asibitin mutane na yabon halin ta ita da Dr Abubakar Sadik.


Office d’in Dr Sadik na wuce na kira sunan wanda suke waje, na yi knocking d’in k’ofar.


"Yes come in" abin da yace kenan.


Sallama nayi na shiga ciki na ajiye mai folder, amsa min sallamar yayi.


Gaisawa muka yi cikin wasa kasancewar shi ma na lura yana da wasa, amma shima na lura miskilin kanshi ne wani time d’in.


Kallo na yayi yace "Fatima Zarah ko"

Sai naji sunan ya min dad’i, ko hakan na da nasaba da dan ba a kira na da sunan ne?


"yaushe kika fara Siwes a nan" ya tambaye ni.


yau 1 week kenan da na fara, lokacin naji ance kai duty d’in safe kake dashi, ni kuma da duty na rana na fara".


"Allah ya taimaka" yace min.


Amsa masa nayi "Amin Dr"


Kallon folder dake gaban shi yayi yace "Zarah, za ki rage folder d’in nan, ba zan samu ganin duka patient d’in ba, akwai inda zani".


"Dr taimakawa za kayi tun da na riga na kawo".


Cikin wasa yace "Sai dai in za ki zo ki taya ni".


"Sai in taya ka Dr, in dai za ka nuna min yadda zanyi, amma kai zan nuna in patient suka zo kama ni na rubuta musu wrong medicine".


Murmushi yayi yace "Kin dai min dad’in baki, zan duba su, amma plss kar a sake kawo folder daga wannan zan fita ne".


"Insha Allah, za a kiyaye Dr".


Sallama na mishi na bar office d’in.


 Yau kusan wata na uku a cikin asibitin, mun sa ba da mutane da dama, daga ciki har da patients da suke kawo katin su record room.


Mun yi wani irin sabo da Dr na ban mamaki, mutane na mamakin yadda muka saba dashi kasancewar ba kowa ce mace yake kulawa ba.


Yanzu haka muke chat dashi, wani time d’in ya kira ni mu gaisa kasancewar muna da number juna.


Kusancin mu da Dr yasa na fara jin shi a raina, amma ban sa hakan a raina illah d’auka da nayi shak’uwar da muka y ice ta janyo haka

Muna cikin yi siwes ne, result d’in mu ya fito.


Naje na duba, wannan karan GP na ya k’aru fiye da firsr semester.


A haka har mu ka cinye 4 month a asibitin na gama siwes d’ina muka yi sallama du da ba wai an rabu ba kenan, tun da zan ci gaba da shigowa in mu gaisa ko zan ga likita.


Mun sami hutun 1 Week na siwes d’in mu kafin mu yi resuming mu shiga ND 2.


Wannan karan Anisa ce tazo gidan mu da niyar yin kwana biyu.


Tun da tazo na fahimci kamar akwai soyayya a tsakanin su da yaya Khalil, ganin yadda yanzu take jin kunyar Ummu, idan tana waya kalamen da suke maida wa junan su, da kiran ta da yake yi garden suna hirar su.


Sai da na matsa ma ta ne ta fad’a min cewa suna soyayya, amma ba yanzu take so a ji a family ba. 


Hakan yasa na dinga tsokanar ta ina cewa "Anty na ta kaina, ni zan fara fad’a ma su Abbu da Daddy a bani goron albishir".


Haka tayi ta rok’o na akan kar in fad’a musu kunya take ji.


Da yaya Khalil ya shigo ina tsokanar shi nace "yanzu shine kamin Anty amma ban sani ba, kuka ‘boye min, nima zan rama".


Dariya yayi yace

"Sorry Fatima, laifin Anisa ne, da nace zan fad’a miki, cewa tayi ba yanzu ba wai da kan ta za ta fad’a miki".


Hararar wasa na mata nace "Kin kyauta Anisa, yanzu ai gashi na sani, tun da ba kya so in Sani".


D’aura fuska tayi kamar da gaske tacce "ke ni fa yanzu Antin ki ce, saboda haka sai ki yi biyayya".


Duk’a wa nayi nace "Sorry Anti".


Gaba d’aya muka yi dariya saboda yadda nayi maganar.


Haka yaya Khalil ya zauna muka ci gaba da chapter kana ya mik’e ya fita.


Kwana 2 da Anisa tayi naji sun burge ni saboda yadda suke gudanar da soyayyar su cikin so da k’auna.


Tana gama kwana 2 ta koma gida.


Har yau muna zuwa islamiyya ran weekend, yanzu haka muna jarabawar shiga JSS3.


Mun koma school muka fara registration na shiga ND 2, yanzu karatu yafi zafi fiye da ND 1, yanzu ba ni da wani lokacin kaina sai na karatu.


Yau Wednesday, mun fito ni da Halima daga MSSN da muke yi duk ran Wednesday, mun fara tafiya ne zamu je masallaci saboda lokacin sallah yayi.


Waya ta ce tayi ruri alamar kira ya shigo

Sunan wanda na gani ne a jikin screen d’in yasa na saki wani sansanyar murmushi sannan na d’auka.


"Assalamu alaikum likita bokan turai".


sautin dariyar shi naji yace "Zarah manya, ya kike, ya karatu?"


"lfy lau Dr".



"ya aiki, ya patents".


"Aiki Alhamdulillah, patients kuma kullum cikin su muke".


Ci gaba yayi da cewa "yanzu kina ina ne?"


"Ina hanyar zuwa masallaci ne".


"Ok yau k’arfe nawa za ku tashi daga School?".


"Mun yi closing yau, lecturer da zai shigo mana bayan sallah ya bamu group work ne tun last week, saboda ba zai samu shigowa bay ace wanda ba su yi ba, su yi amfani da period d’in shi, gobe zai amsa, already mu mun riga munyi tun last week, yanzu in nayi sallah, zan biya SUG Hall ne, daga nan sai in wuce gida".


"In ba zan takura miki ba, bayan sallah mu had’u a fanta fun tun da ba ki da lectures, akwai maganar da nake so mu yi".


"Ok sai mun had’u".


"Bye, take care" abin da yace kenan ya katse wayar.


Bayan gama wayar mu ne na kalli Halima nace "kin san da wa muka yi waya?"


Girgiza kaai tayi alamar ba ta sani ba.


"Dr Sadik ne ya kira ni, wai yana so mu had’u a fanta fun".


"ke dai taku tazo d’aya da shi, in kun had’u ki ce ina gaishe shi’.

‘zan fad’a mai insha Allah".


Masallaci muka shiga muka yi sallah, bayan mun fito ne muka wuce cikin SUG Hall muka ci abinci, nan muka yi sallama da Halima ta wuce gida.


Direct fanta fun na je na nemi guri na zauna ina jiran k’arasowar shi.

[4/24, 21:59] Mrs Mansoor: *MAKAUNIYAR SOYAYYA*💝💖💞




Post a Comment

0 Comments