TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Makauniyar soyayyah page 57-58

 _Mutuwa_


_Annabi Muhammad (s.a.w) ya hore mu da muyi hak’uri da duk wanda muka yi karo dashi, domin ba zai dauwama ba, zai wuce_

_Allah ka k’ara mana hak’uri_


 




57&58


Cikin takun k’asaita ya k’araso in da na tsaya, gaba na sai fad’uwa yake tun san da ya kira suna na.


Wani irin kallo yake min da yake nuna yana cikin fushi.


"Fatima miye had’in ki da wannan Dr da nake yawan ganin ki dashi?".


"A clinic d’in makarantar mu yake aiki, shine yake biyo wa muna gaisawa".


Wani banzan kallo ya k’ara watso min kana yace "Amma tun yaushe na ce miki ki rabu dashi, miye amfanin zuwa gurin ki da yake yi dan kawai yana duba lafiyar ki, in har ba yana da manufar shi ta yin haka ba, Fatima let me warn you for the last time, duk ran da na sake ganin ki dashi, two of you will face the consequences, kar ki ga dan ina son ki zai hana in kin shiga gona ta in hukunta ki, ya kamata ki gane ni mutum ne mai kishin abin da nake so, bare wacce nake sa ran zan aura, ki kiyaye".


Yana gama fad’ar haka ya juya ya fita ba tare da ya shiga cikin gidan ba.


Wata irin ajiyar zuciya mai k’arfi na saki don gaba d’aya a tsorace nake dashi, yau yaya Faruk na ga alamar idan da nayi wasa zai iya fasa min jiki ya bar ni da jinya.


Haka na ja jiki na koma d’aki na ina addu’ar Allah ya kawo k’arshen wannan lamarin.


Tun san da iyayen mu suka san da zancen yaya Faruk na rasa sukuni, gashi matsalar wadda nake tunanin za mu raba matsalar tawa dasu b azan iya fuskantar su ba.


Rok’o na Allah ya d’aura ni akan su, ina ganin ko wani challenges zan iya fuskanta in dai akan Dr ne, shi nake so, ba kuma dan yafi yaya Faruk ba, hasalima yaya Faruk yafi shi komai.


"Me yasa so ya zo min ta wannan sigar"


Gashi na samu wanda nake so amma ba ni da kwanciyar hankali saboda wani Katanga da ta shiga tsakanin mu.


Ga wani k’arin damuwar shine yadda Sadik yake tuhuma ta da wani zargin shi na daban, dan ma bai san halin da nake ciki ba game dashi na yadda ake so a raba mu, gashi yanzu yaya Faruk ya min gargad’i na k’arshe akan shi, na san kuwa zai iya d’aukar matakin da ya zo mai, ya kamata in kiyaye taku na don kar in fad’a trap d’in yaya Faruk ni da Sadik, ba k’aramin aikin shi ba ne yasa a kama Sadik a je a mishi horo ko shi ya d’au mataki da kanshi, ni kuwa b azan so abin da zai ta’ba min Dr ba.


Ni ma yau yadda na ke ji na ba zan iya kiran Dr in bashi hak’uri ba dan yaga ina son shi sai ya dinga min fad’a ko ya fad’a min maganar da ya ga dama, kuma ban da halin rama wa.


Don haka na share shi na tashi na ci gaba da harkoki na amma duk da haka tunani ne a raina kan matsalar da zan fuskanta nan gaba.


Yaya Faruk tun da ya bar gidan mu ya koma gida cikin zafin rai.


San da ya shiga main parlour d’in ya samu Anisa a parlour tana waya da yaya Khalil.


Saurin katse wayar tayi ta mishi sannu da zuwa.


"Ki same ni a side d’ina Anisa" yana gama fad’ar haka ya nufi side d’in shi.


Yanayin shi da Anisa ta gani yasa ta ji ba dad’i a ran ta, da alamar akwai abin da yake damun shi.


Tun da ya shiga d’akin ya rasa mai ke damun shi, ya rasa wani irin so yake ma Fatima haka da har yake jin wani irin kishin ta haka.


Anisa ce ta shigo d’akin had’e da sallama.


Ciki-ciki ya amsa mata.


A ranta kuwa addu’a take ta jerowa saboda yau yanayin yaya Faruk ya sa ta a tunani.


Cikin sanyin murya tace "yaya gani".


Wani huci ya furzar sannan yace "Anisa waye Dr Sadik?".


"A clinic d’in asibitin mu yake aiki".


"Akwai wata alak’a ce a tsakanin sa da Fatima?" ya jefa mata wata tambayar.


"Eh yaya Faruk akwai".


Wani irin fad’uwar gaba yaji a lokaci d’aya idon shi ya kad’a ya canza kala.


"Mecece alak’ar su d’in?". Anisa ta tambayi kan ta.


Anisa ta fara mamakin tambayoyin da yaya Faruk yake jero mata, to me yasa yake son sanin alak’ar su?


Wata irin tsawa ya daka mata da ta sa ta tsoro yace "ki bani amsar tambayar da na miki".


Cikin rawar murya Anisa tace "Akwai alak’ar soyayya a tsakanin su".


Wani irin kallo ya watsa mata kamar bai yarda da amsar da ta bashi ba.


"Ita ma tana son shi? Ya k’ara tambayar ta.


"Eh ta na son shi".


"Tun yaushe suka fara soyayya".


Wannan karan tambayoyin sun ma Anisa yawa, tana tunanin yaya Faruk bayan karatun sojan da yayi, ko ya had’a da aikin jarida ne a course d’in su, saboda wannan tambaya ta isa haka.


"Anisa don’t let me come near you, in ba haka ba jikin ki zai fad’a miki, don iskanci sai in miki tambaya ki tsaya wani tunani".


Anisa tana jin abin da yace da sauri ta ce "Ina ganin tun bayan gama siwes d’in mu ne".


Shiru yaya Faruk yayi yana mamakin yadda Fatima ta maida shi k’aramin yaro, ta sa shi yaci gaba da son ta alhalin ta san ba ta san shi, baa bin da ya fi mishi ciwo shine yadda tayi amfani da damarta ta yaudare shi, dole ne ya hukunta ta daidai da laifin da ta mishi, kenan duk wannan lokacin da ya furta ma ta son shi ta d’auke shi a banza, ba ta tsaya a nan ba sai da ta had’a da son wani bayan shi bayan tasan tuntuni yake son ta, hakan na nuna sai bayan da ya furta mata yana son ta sannan ta fara soyayya da wannan Dr da kullum take mishi k’aryar ce wa suna gaisawa ne.


"Me yasa wasu matan suke da yaudara ne?".


Wannan tambayar ita ce ta ke mishi yawo a k'wak'walwar shi.


Muryar shi ce a wannan lokacin tayi sanyi ya kalli Anisa yace "Anisa dake za a munafunce ni, a yaudare ni, ina tunanin ko kowa zai min haka, ban dake Anisa, saboda duk abin da na miki, ba ki da d’an uwan da ya wuce ni".


Anisa ba ta fahimci inda maganganun yaya Faruk suka nufa fa.


Kallon shi cikin rashin fahimta tace "yaya Faruk ni ban dani aka yaudare ka, hasalima ban fahimci mai kake nufi ba".


Cikin ‘bacin rai yace "kina nufin ba ki san ina son Fatima tsawon lokaci ba, ko kina so ki fad’a min cewa Fatima ba ta fad’a miki ina son ta ba? shine ke kuma ki ka ba ta shawarar tayi soyayya da Dr saboda ni ba ki d’auke ni a matsayin yayan ki ba".


Mutuwar tsaye Anisa tayi da jin wannan magangann da yaya Faruk yake fad’a.


"Yaya Faruk yana son Fatima? tun yaushe kenan yake son ta? me yasa Fatima ba ta fad’a mata ba" duk wannan jerin tambayoyin da take dashi tasan ba wanda ya dace ya amsa mata sai Fatima.


Tausayin yayan ta ne ya kama ta a lokaci guda ganin yadda a loakci d’aya yanayin shi ya canza.


"Yaya Faruk ina son ka yarda da maganar da zan fad’a maka, wallahi tun da muke da Fatima ba ta ta’ba fad’a min kana son ta ba, yaya Faruk ya za ayi in goyi bayan bare bayan nasan d’an uwa na yana son ta, yaya Faruk ba ni da kowa da zan kalla a matsayin d’an uwa fiye da kai, ina so ka yarda da magana ta" Anisa ta fad’a da murya ta dake nuna alamun ta na son yin kuka.


Ya d’an ji sanyi game da bayanin da Anisa ta mai, ya kuma yarda cewa ba ta san me ke tsakanin shi da Fatima ba.


Nuni ya mata da zo ta zauna a inda take.


Jikin ta ba k’wari ta tako ta zo ta zauna kusa dashi.


Hannun ta ya rik’e ya fara ba ta labarin tun sa da ya fara so na, da kuma san da ya furta min yana so na.


Bayan ya gama ba ta labarin ne ya d’aura da cewa "Anisa ina son Fatima wanda ni kaina ba zan ce miki ga lokacin da na fara son ta ba, na riga na mik’a mata yarda cewa Fatima za ta so ni duk kuwa da yadda a da take min kallon mak’iyin ta, sai gashi ta shammace ni a lokacin da ban yi zato ba".


Anisa ce ta kalle shi cikin tausayi tace "yaya Faruk insha Allahu in dai Fatima rabon ka ce, sai ka aure ta kuma za ta so ka, in kuma ba rabon ka bace, duk son da kake mata sai ka ga Allah bai nufa kun yi aure ba, ka ci gaba da addu’ar neman za’bin Allah, nima zan taya ka da addu’a".


Hak’ik’a ya ji dad’in maganganun Anisa da ta mishi.


Murmushin da bai kai ciki ba ya sakar mata kana yace "Anisa na gode da shawarar ki, ina son maganar nan ki bar ta daga ni sai ke, ina so in ga iya gudun ruwan Fatima d’in, kafin in san matakin da ya kamata in yanke akan ta".


"Ba zan fad’a ma kowa ba kamar yadda ka buk’ata, Allah kuma ya kawo mafita cikin sauk’i yaya".


"Amin Anisa, nagode, za ki iya tafiya".


Tashi tayi ta bar d’akin cike da mamakin wannan labarin da yaya Faruk ya ba ta.


Tun da Anisa ta koma d’aki take juya maganar da suka yi da yaya Faruk.


Sai a yanzu ta gano dalilin da yasa ban fito ta fad’a mata alak’ar su da Dr Sadik ba har lokaci da suka had’u dashi, da irin hujjojin da na kawo mata san da ta tambaye ni me yasa ban fad’a mata soyayyar mu da Dr ba, da kuma dalilin da yasa da farko na hana Dr zuwa gidan mu.


A yadda ta ke jin ta tana ganin in ba tunkara ta tayi da tarin tambayoyin dake ranta ba za taji sauk’in tunanin da yake addabar ta.


Abu d’aya ne zai hana ta tunkara ta, sai dan yadda yaya Faruk ya mata magana akan ta bar maganar daga shi sai ita.



Yau kusan 2 days kenan rabon mu da mu had’u da Sadik ko ya kira ni a waya, daurewa kawai nake yi amma ni nasan yadda nake ji na rashin ganin junan mu.


Da daddare sai ga kiran Dr ya shigo waya ta.


Murna kamar in tashi in taka rawa, dama gashi nayi missing d’in ganin shi da zazzak’ar muryar shi.


Hannu na har rawa yake wajen d’aukar wayar.


"Assalamu alaikum Prince".


"Wa alaikis salam".


Shiru ne ya ziyarce mu, cikin mu an rasa wanda zai ci gaba da magana.


Sadik ne ya katse shirun da cewa "Zarah kin min laifi ko ki kira ki ba ni hak’uri".


Cikin shagwa’ba na ce "Wani laifi na maka Dr".


"Au har kin manta kenan, yanzu dai ina son ki fad’a min kin gano dalilin da yasa shi wanna Faruk d’in yake hana ki tsayawa zance?"


"Sadik ina so ka fahimta, yaya Faruk a matsayin yaya na yake, dole ni in bi abin da yace min, yaya Faruk yana da power a familin mu ya zartar ma kowa hukunci ba tare da an tuhume shi ba, try to get my point".


Duk wannan bayanin da na mishi ba wai ya gamsu dasu ba ne, kawai dai zai bi ni a yadda ta ke so.


Nan suka ci gaba da hira irin ta masoya.



Washe gari ko da aka tashi School, Anisa suka biyo department d’in d’auka ta, na ga yanayin Anisa ya canza ba kamar yadda take ba, da na tambaye ta ko wani abu yake damun ta, sai tace min ba komai.


Ganin yadda ta share ta d’akko wayar ta tana danna wa yasa nima nayi shiru, saboda nasan akwai wataran da za ka ga mutum bai jin dad’in jikin shi.


Ni aka fara sauke wa sannan su ka tafi.


Da daddare muna cikin waya da Dr naji alamar tsayuwar mutum a gaba na.


Saurin d’ago kaina nayi don ganin wanda ke tsaye.


Ido na ne yayi tozali da yaya Faruk.


Ba yi tsammanin zuwan yaya faruk a wannan lokacin ba.


Tsananin tsoron da nake ciki yasa na fara zufa duk kuwa da AC d’in dake d’aki na.


Cikin murtukewar fuska ya kalle ni yace "Da wa kike waya".


Halin da nake ciki a yanzu ba zai ba ni damar tsayawa yi mishi bayanin da wanda nake waya ba.


"Ba ni wayar" ya fad’a cikin ba da umarni.


Hannu na yana rawa na nik’a mishi wayar.


Amsar wayar yayi ya shiga received call, last call wya duba ya ga an sa Prince Dr.


Wani irin murmushin takaici yayi sannan yace "Fatima na sha tambayar ki, miye tsakanin ki da Dr Sadik kina ce min likitan ki ne, for the last time zan k’ara tambayar ki, miye tsakanin ki dashi".


Shiru nayi na kasa cewa komai, miyau ma da k’yar nake iya had’iyar shi saboda tsoro.


Cikin tsawa yaya Faruk yace "ki fad’a min abin da ke tsakanin ku".


A karo na biyu ban ce komai sai ma k’ifta idanuwa na da nake yi.


Wani gigitaccen mari naji a fuska ta da yasa ni rik’e kunci na.


A lokaci d’aya na ji wani ‘bacin rai ya saukar min, tsoron da nake ji ya fita daga raina.


Ina ganin yanzu ba zan jure cin kashin yaya Faruk ba, ban ga dalilin da zai dinga mari na ba.


Hawayen takaici ne yake zubo min saboda yadda marin ya shige ni.


Ina ganin lokaci yayi da zan daina ‘boye ma yaya Faruk alak’ar mu da Dr, tun da shi ya buk’aci in fad’a mai, gwara in daina tsoro in fad’a mishi gaskiyar maganar, ni kaina na gaji da ‘boyewa.


Cikin rashin tsoro na ce "yaya Faruk, Dr Sadik shine wanda yake so na, ni ma nake matuk’ar son shi, ina ganin ba namijin da zan so sama dashi".


Wani irin huci yaya Faruk yake yi, fuskar shi duk tayi ja kasancewar shi fari.


Wani kallo yake mata na ba ki isa ba kana ya ce "Teemah kin yi kuskure da ki ka yaudare ni, ki kasa na ‘bata lokaci na akan ki, zan iya yin komai a kan ki in har mutum zai yi takara da ni a son ki, ya kamata ki gane hakan, kar ki bari in fito miki ta wata hanyar da kema za ki sha wuya, ba ki isa ki so wani ba, bayan ni ina son ki, ba ayi macen da za ta wulak’anta ni akan son ta ba".


Ci gaba yayi da cewa "you are the only air i breathe, you are ticking in my heart like a little clock, I value our relationship more than you’ll ever know, you are the girl of my dreams, Fatima ashe ake duk ba haka ki ka d’auka ba a gurin ki, kin nuna min soyayya na zuwa a yananyi daban-daban".


Ganin yaya Faruk da gaske yake akan furucin shi yasa zuciyata ta bani k’arfin gwiwar in k’alubalance shi ko zai bar ni nima na auri wanda nake so.


"Yaya Faruk, sai dai kayi hak’uri, zuciyata tayi nisa a son Dr, kamar yadda ka ce ba ka san lokacin da ka fara so na ba, nima ban san lokacin da na fara son Sadik ba, yaya Faruk tun san da ka ce min ka na so na, nayi k’ok’arin sa son ka a zuciya ta, amma ban san me yasa zuciya ta tak’i amincewa dakai ba, har lokacin da na had’u da Dr muka fara soyayya, ba laifi na bane, laifin so ne, yaya Faruk ka fahimce ni".


Wani irin rad’ad’i yake ji a zuciyar shi, yau wai shi Fatima take fad’a mai tana son wani bayan shi, ba tayi duba da tsawon lokacin da ya d’auka yana d’awainiya da son ta ba, yana ganin ya kamat ya d’auki mataki a kanta.


Saukar wani mari na k’ara ji a fuska ta da ya fi na farkon zafi.


Cikin k’unar rai yace "zan iya miki komai akan yaudara ta da kika yi, me yasa tun farko ba ki fad’a min in hak’ura ba, ki ka munafunce ni, sai da kika ga komai yazo gargara sannan za ki fad’a min, tun da abin na ki iskanci ne, zan ba ki mamaki".


kuka na fara yi ina cewa "yaya Faruk ko mai za ka min, ba zan gaji da fad’a maka Dr nake so ba".


Gani yake yi in dai ya ci gaba da tsayawa yana musayar yawu da ni, zai iya yin abin da zai jawo da na sani.


Yanke hukunci yayi akan ya bar d’akin kawai.


San da zai fita daga d'akin ne ya yi wurgi da wayar akan gado.


Yana fita ya had’u da Ummu a falo, gaishe da ita yayi ya mata sallama ya tafi.


Ganin yanayin shi yasa tayi tunanin akwai matsala, don haka ta tawo d’aki na.


Samu na tayi ina kuka, ga ido na da ya yi ja.


Ummu ce ta kira suna "Fatima"


Cikin kuka na amsa mata.


"Me yasa ki kuka?"


"Ba komai Ummu".


"Haka kawai ki ke kuka?"


Wannan karan ban amsa mata tambayar ta ba, sai ma kuka na ci gaba dayi.


Ran Ummu ne ya fara ‘baci, ganin ta tambaye ni nak’i ba ta amsa, gashi kuma sai kuka nake yi.


Cikin fad’a tace "Tun da ba za ki amsa min ba, me ya had’a ki da Faruk na ga ya fita cikin fushi".


"Fad’a muka yi".


"Wani irin fad’a kuma?".


"Sa’bani mu ka samu".


"Akan me?"


Shiru na k’ara yi.


Tun da ba za ki fad’a min ba, sai ki yi tayi, in kukan zai miki magani" tana gama fad’ar haka ta fita daga d’akn.


"Na ga ta kaina" Na furta hakan a bayyane.


Yanzu ban san wani mataki yaya Faruk zai d’auka ba, ina jin yau allurer sojojin ta motsa ne, gwara da Allah yasa ya tafi, in ba haka ba ban san me zai min ba.


Yaya Faruk yana fita ya shiga mota ya ja ta a guje.


Karatun da yasa a motar shi ne yasa yaji ‘bacin ran da yake ciki ya ragu.


Yana zuwa gida ya dinga danna ma mai gadi horn da k’arfi.


Da gudu mai gadi yazo ya bud’e mishi yana mishi sannu da zuwa.


Ko kallon shi bai yi ba saboda yadda yake jin zuciyar shi.


Direct d’akin Daddy ya wuce.


Abinci ya same shi ya na ci, kusa dashi yaje ya zauna.


"Sannu da gida" yaya Faruk ya furta.


Kallon shi Dadi yayi ya lura da akwai abin da ke damun Faruk d’in.


"Yawwa Faruk".


Ganin yadda Faruk d’in yayi shiru yasa Dadi yace mai "ya aka yi ne Faruk, na ga kamar kana tare da damuwa".


Ba zai iya fad’a ma Dadin shi halin da yake ciki ba, don haka yace "Ba komai Dadi".


Ba dan Dadi ya yarda ba yace "shi kenan tun da kace haka, kaci abinci ne?".


"Yanzu na shigo gidan, ban ci ba".


"Zo mu ci wannan da nake ci".



Ji yake baa bin da zai iya ci ahalin yanzu, sabida haka yace ma Dadi "na k’ashi Dadi, ba na jin yunwa".


"Me ka ci?" Dadi ya tambaye shi.


"Ba komai".


"Common, zo ka zauna mu ci, ya za ayi ka zauna da yunwa".


Bai san musu dashi, shi yasa ya matso yasa d’ayan spoon d’in dake ajiye ya fara ci.


Ji yake yi abinci bay a mishi taste a bakin shi saboda halin da yake ciki, bai fi spoon biyar yayi ba ya ajiye spoon d’in.


Dadi ne ya kalle shi cikin kulawa yace "kana nufin ka k’oshi kenan?"


"Eh Dadi".


Dadi bai ce mai komai ba yaci gaba da cin abinci.


Bayan ya gama cin abincin ne ya maida hankalin shi ga Faruk da ya fad’a cikin tunani.


"Faruk alamu sun nuna kana cikin damuwa, but I don’t know why you d’ont whant to tell me"


"Nothing is bordering me Dadi, ina tunanin nan da 2 days zan koma aiki, Dadi ina so ayi fixing d’in bikin mu da Fatima".


Murmushi Dadi yayi yace "gobe za mu tsayar da Date d’in bikin, sai ka fara shiri".


Murmushin yak’e yayi, duk da yaji dad’in maganar sa date d’in da za ayi, hakan bai say a samu peace of min ba.


Suna wannan maganar ne, Momi ta shigo da flask a hannun ta.


Ajiye flask d’in tayi kusa da Dadi da cup a hannun ta tace "wani sirri ake yi da ba za a jira ni in shigo ba" ta fad’a tana dariya.


Dariya Dadi yayi yace "tsakanin mu ne, in tayi wari za ki ji".


"Ina zaune nasan za a zo a fad’a min".


Duk wannan maganar da ake yi, yaya Faruk bai ce komai ba, hankalin shi na wani guri.

Momi ce ta zauna aka ci gaba da hira da ita, yaya Faruk ba wani dad’in zaman yake ji ba, tashi yayi ya musu sallama ya tafi sashin shi.



Washe gari Dadi ya samu Abbu da maganar tsayar da lokacin biki, sun yanke nan da wata hud’u, lokacin mun gama Diploma d’in mu.


San da Dadi ya dawo gida ya sanar da yaya Faruk, yaji dad’in labarin, sai dai shi yafi buk’atar in so shi, yana ganin soyayya ita tafi mahimmanci kafin a je ga zancen aure, sai dai ba yadda zai yi ne yasa ya buk’aci da a tsayar da lokacin bikin, fatan shi shine kafin lokacin, zan so shi.


Ko sallama yaya Faruk bai min ba ya koma Abuja.


Tun lokacin da yaya Faruk ya koma Abuja ya rage walwala, yanzu yafi so ya zauna shi kad’ai.


Ya rasa yanda zai yi ya shawo kan Fatima, a da yana ganin abu mai sauk’i ne da zai iya jawo hankalin ta gare shi, sai dai a yanzu ya gane cewa nayi nisan da ba zan saurare shi ba, yanzu duk wayar da muke yi dashi, da fad’a muke k’are wa, gashi yanzu ya dawo da fad’an shi, abu kad’an ke sa shi hassala, ni kuma ba na jurar maganganun da yake fad’a min, hakan yasa ya rage kira na.


Yau yana zaune a falon shi, yayi nisa a cikin tunanin da ya sa bar wa kanshi, Mus’ab ya shigo da sallama.


Tunanin da yake yi yasa bai ji sallamar da Mus’ab ke mai ba.


Tako wa yayi ya zauna kusa dashi.


Dafa kafad’ar shi da Mus’ab yayi yasa ya dawo daga duniyar tunanin d yake yi ya saki ajiyar zuciya.


Kallon shi kawai Mus’ab yake yi ganin tun san da ya dawo daga Kaduna yake cikin wannan halin.


"Faruk, wai me ke damun kane?" Mus’ab ya tambaye shi.


"Me ka gani?" Shima ya maida mishi tambaya.


"Faruk, nasan ba kowace matsala za kai ta fad’a min, ina so ka dubi amincin mu da yarda da muka yi da juna, ka fad’a min matsalar ka, duk wani wanda yake tare dakai, yasan ka canza, plsss Faruk, ni kaina ba na jin dad’in ganin ka a wannan halin da kake ciki na tunani, hakan xai iya jawo maka wani ciwo ya kuma yi affecting d’in ka".


Yasan ba wanda ya cancanta ya fad’a wa matsalar shi kamar Mus’ab, yasan zai iya taimakon shi da shawara, yana ganin fad’a mishi shine maslaha a gare shi, ko ba komai zai samu sauk’in tunanin da yake yi.


"Mus’ab ina cikin matsala".


Da sauri Mus’ab ya ce "Wace matsala Faruk".


Nan Faruk ya sanar dashi halin da suke ciki shi da Fatima, da kuma matsalar da yake fuskanta a guri na.


Tausayin Faruk ne ya kama Mus’ab a wannan lokacin, yasan Faruk bai san so ba sai a kaina, dole ne ya shiga wannan halin.


Cikin tausayawa yace "gaskiya Fatima abin da ta maka ba ta kyauta ba, ko waye a ka ma haka dole ne ya shiga cikin tunani, a yadda ka bani labari na fahimci son da Fatima take ma wannan Dr d’in, irin son nan ne da ake cewa *Makauniyar Soyayya*".


Faruk ne ya katse shi da cewa "Mecece Makauniyar Soyayya kuma?".


Mus’ab ne ya bashi amsa da cewa "Makauniyar soyayya wata irin soyayya ce da mutum ya ke ma wanda yake tsananin so, irin wannan soyayyar ita ce mutum bai duba wanda ya dace yaso ba, bai duba aibun shi ko laifin shi, duk abin da zai yi/za tayi daidai ne a gurin shi/ta, mutum zai iya ‘bata wa da kowa akan wanda yake so, kuma duk a ganin shi/ta duk cikin soyayya ce saboda duk a ganin su a cikin soyayya ne saboda sun makance a so, wannan soyyar ita ce Makauniyar soyayya, kuma ita wannan soyayyar yawanci tana jawo danasani a lokacin da mutum ya hankalta".


Faruk ya gamsu da bayanin da Mus’ab ya mai, ya kuma yarda da cewa irin wannan soyayyar nake yi.


Mus’ab ne yaci gaba da cewa "shawarar da zan baka Faruk shine, ka ci gaba da addu’a akan Allah ya za’ba maka abin da yafi alkhairi a gare ka, sannan ka ci gaba da hak’uri da duk abin da za ta maka, shi so da maganar aure ya k’unshi k’alubale dama, sai dai kowa da irin yadda yake zuwa masa, nan gaba z aka ga ribar hak’urin naka, ina ganin komai zai zo da sauk’i tun da har anyi fixing d’in bikin ku".


Ba k’aramin jin dad’in shawarwarin Mus’ab yayi ba, shi yasa yake jin dad’in kasancewa da Mus’ab a matsayin aboki.


Da haka suka ci gaba da zanta wa akan matsalar, a haka Faruk yaji ya samu k’arfin gwiwa.

Sallama Mus’ab ya mishi ya tafi.


Yana kwance a d’aki yaji k’arar wayar shi, sai da aka sake kira sannan ya d’auki wayar.


Sunan Binafa ya gani a jikin screen d’in wayar, kasancewar yayi saving d’in numbar ta tun da ta sake kiran shi.


Sallama ya mata ta amsa masa.


Sun d’an yi hira kafin Binafa ta d’aura da cewa "Umar, tun san da muka had’u Asaa pyramid, na ji na kamu da son ka, nayi k’ok’arin dannewa amma zuciyata ta gaza yin haka, hakan yasa na rasa walwala da sukuni, su Dad d’ina da Mom d’ina sun ta tambaya ta akan in fad’a musu matsala ta, ina ganin ko na fad’a musu bas u da maganin matsala ta sai kai, plss Umar ka tausaya ka bani masauki ko da yaya yake, zan yi farin ciki da haka".


Sauraren ta yake na yadda take bayyana mishi yanda take son shi, ina ma a ce Teeman shi ce ke furta mishi wad’annan kalmomin, da bai san dad’in da zai ji ba, sai dai kash, ita ta riga tayi nisa da son wanin shi.


Binafa ce ta katse shi da cewa "Bregadier kana ji na kuwa".


"Ina jin ki Binafa, na gode da son da kike min, sai dai ina mai ba ki hak’uri Binafa, ina da wacce ta dabaibaye zuciya ta, sai dai ina miki addu’ar Allah ya kawo miki miji nagari".


Kuka ta fara mishi tana k’ara fad’a mishi halin da take ciki a yanzu na son shi.


Tausayin ta ne ya kama shi ganin yadda take mishi kuka, shima da yana da halin kuka da yayi ko ya samu sauk’i a ranshi.


Me yasa so yake zuwa mutane mutane da launi daban-daban, ina ma bai fad’a cikin so ba, da bai tsinci kanshi a halin da yake ciki a yanzu ba.


K’arar sautin kukan ta da ya ci gaba da ji a kunnen shi ne yasa ya tuna da waya yake yi.


Lallashin ta yaci gaba dayi yana fad’a mata kalamai masu kwantar da hankali, da haka ya samu ya shawo kanta har ta hak’ura, kafin su yi sallama ta nemi alfarmarshi akan za taci gaba da kiran shi suna gaisawa sannan suka yi sallama da ita.


Yau kusan wata d’aya kenan da gama service d’in yaya Khalil, tun da ya dawo ya fuskanci ina cikin matsala, idan ya tambaye ni sai in ce masa ba komai, tun yana tambaya na har ya gaji ya zuba min ido, sannan yayi mamakin wai yaya Faruk ke so na amma ban fad’a mai ba, ya sha gani na muna da waya da Dr, ya rasa in da na fuskanta, bayan dawowar shi yaji time d’in da aka yi fixing, ya rok’i alfarmar a k’ara mishi lokacin, in yaso a fara nawa bikin da yaya Faruk, daga baya ayi nasu.



Komai yayi farko zai yi k’arshe, hakan ta kasance gare mu, mun rubuta final exam d’in mu mun yi graduation d’in mu, karatu da dad’i da wuya in aka gama shi, yanzu ba mu da wata sauran fargaba da ta rage mana game da harkar karatu.


Bikin mu bai fi saura wata biyu ba sai ga yaya Faruk ya zo Kaduna.


Hakan ya k’ara d’aga min hankali ganin yadda lokacin bikin mu yake matsowa, gashi har yau ban fad’a ma Dr Sadik halin da ake ciki ba.


Kiran shi nayi a waya akan cewa in ba ya komai ya same ni a gida, akwai maganar da nake son mu tattauna dashi.


San da ya k’araso ne ya kira ni a waya yana waje.


Hijab na san a fito na wuce gurin Ummu na mata k’aryar cewa zan je gidan su Anisa in dawo yanzu.


fatan a dawo lafiya ta min kana tace in gaishe da su Anisa da Momi.


Ina fitowa na shiga motar nace mai ya tuk’a motar mu bar layin.


Kallo na yayi da alamar tambaya, amma ganin yanayin da nake ciki yasa bai ce min komai ba ya ja motar mu ka bar layin.


Sai da naga mun bar layin mun shiga wani layin sannan na ce ya tsaya a nan.


Sai a lokacin naji zuciyata ta karye na fara kuka wanda nima ban san dalilin yin kukan nawa ba.


Bi na yake yi da kallo ganin yadda nake kuka bil hakk’i yace "Wai Zarah me yake faruwa ne kike wannan kukan, ki fito ki fad’a min me ke faruwa dake ne".


Cikin kuka nace "Sadik an kusa raba mu, za a sa almakashi a datse soyayyar da ke tsakanin mu, na kasa danne halin da nake ciki a yanzu, shi yasa na ga gwara in fito in fad’a maka halin da nake ciki a yanzu".


"Ban gane me kike nufi ba, wai waye zai raba mu?" ya tambaye ni.


"Sadik aure za a had’a ni da yaya Faruk, yanzu haka bikin bai fi saura wata biyu ba" Na k’arashe maganar cikin shashshek’ar kuka.


Wani irin takaici ne ya kama shi jin wai an kusa bikin ta da Faruk, ba ta fad’a mishi ba, sai da ta ga komai ya rinca’be sannan za ta fad’a mishi.


Shi yasa da tace mai Faruk d’in ya hana ta tsayawa zance yasa alamar question mark, yasan daman yana da dalilin yin haka, abin ta fi yi mishi ciwo a ranshi shine yadda a lokacin ya tambayeta ta nuna mishi ba wani abu dake tsakanin su.


Cikin fad’a yace "Yanzu Zarah da kike wannan kukan miye amfanin shi, bayan sai da kika bari komai ya gama ‘baci sannan za ki fad’a min, gashi har ana maganar biki, yanzu mai ki ke so in yi akai".


Cikin kuka nace "Dr dubarata ta k’are, plss ka samo mana mafita, wallahi in dai ba kai na aura ba zan shiga wani hali, lai zuciyata take so da muradi".


Ganin yadda take kuka yaji duk jikin shi yayi sanyi, shi kanshi yasan Fatima na son shi.


Cikin lallashi ya ce "Wipe your tears Zarah, ki ba ni hakalin ki muyi magana ta fahimta".


Ina jin haka nayi saurin share hawayen dake fito wa daga fuska ta, na maida hankali na gare shi.


"Zarah, kin yi kuskure da tun farko ba ki fad’a min me ke tsakanin ki da wannan yayan naki ba, duk yadda muke son junan mu, ba mu da wani power tun da har an yi fixing d’in bikin ku, ina ganin mafita a gare mu shine mu yi hak’uri da yadda k’addara tazo mana mu hak’ura da juna".


Wani irin kallo na mishi na alamar tambaya akan abin da yace.


Maganganun da Sadik ya fad’a sun k’ara sa ni a rud’ani ganin yadda yayi saurin mik’a wuya ga al’amarin, duk wani bijire wa da halin da nake ciki a yanzu duk akan shi ne, amma shi gashi a lokaci d’aya ya nuna ya hak’ura da ni.


"Ban fahimci inda maganganun ka suka nufa ba, kana nufin har ka hak’ura dani, bayan duk fad’i tashin da nake yi duk a kan ka ne, Dr kar ka sa in fara zargin ko ba so na kake yi ba" Na fad’a cikin fushi.


Cikin cool voice d’in shi da yake k’ara sace zuciya ta yace "try to understand me Zarah, maganar ba a son ki ma bai taso ba, ke kan ki kisan ina son ki, in har da ba na son ki, bazan tsaya ‘bata ma kaina time ba, kema kuma ba zan ‘bata miki lokacin ki ba, abin da yasa ki ka ga nace haka saboda na rasa wace hanya za mu bi mu shawo kan matsalar, yanzu gashi kin ce bai fi saura 2 month bikin ba".


Sai yanzu na ji sauki a raina ganin shima Sadik ya nuna damuwar shi akan maganar, nasan yanzu zan samu relief a raina.


Da haka muka ci gaba da tattaunawa akan matsalar, mun yi da Dr zai neme ni a waya mu samu mafita akan maganar.


Fitowar da zan yi naga motar yaya Faruk ta shigo layin, da alama daga wani gurin yake tun da har ya biyo wannan layin.


Shi kuwa yaya Faruk tun da ya ganni na fito a motar ya tabbatar da cewa tare muke da Dr.


Kusa da motar Dr yazo yayi parking.

Fitowa yayi daga cikin motar ya nufo inda nake, ni kuwa jiki na in banda rawa ba abin da yake yi, hakan da nayi ne yasa Dr ya lura da halin da nake ciki.




Shima fito wa yayi daga side d’in driver ya kulle motar.


Kallon kallo ake yi tsakanin yaya Faruk da Dr Sadik, da alama kowa da abin da yake sak’awa a zuciyar shi.

Post a Comment

0 Comments