TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

An Kama Masu Yunƙurin Daura Auren Jinsi A Gombe



Wasu matasa 76 da ake zargin ’yan luwadi ne da ke shirin daura auren jinshi sun fada komar hukumar tsaron farin kaya (NSCDC) a Gombe.

Kwamandan hukumar NSCDC a Jihar Gombe, Muhammad Bello Mu’azu, ya ce an kama waɗanda ake zargin ne a rukunin Du’a Plaza da ke kan hanyar Gombe zuwa Bauchi bayan samun bayanan sirri kan aniyar matasan.

Mu’azu ta bakin kakakin hukumar, SC Buhari Sa’ad, ya ce, “Mun kama wadanda ake zargin ne a loakcin da suke gudanar da bikin murnar zagayowar ranar haihuwar daya daga cikinsu da ya kasance dan luwadi, inda a lokacin ne suke kokarin kulla auren a tsakaninsu”.

A cewarsa, bisa rahoton da aka tsegunta musu kan hakan ne jami’ansa suka dira a wajen suka kuma yi nasarar cafke mutum 76 a cikin wadanda ake zargin.

Ya ce daga cikin mutane 76 da ake zargin, 59 maza ne, 17 kuma mata, daga cikinsu maza 21 sun furta da bakinsu cewa su ’yan luwaɗi ne, sauran kuma sun je wurin ne bisa gayyatar su da aka yi.

Post a Comment

0 Comments