TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

ZAFIN KAI

 ZAFIN KAI

Mamuhgee

#BILLONAIREsROMANCE


BismillahirRahmanirRaheem

Allah yabamu ikon gamawa lafiya


1

Gyara tsayuwarta tayi ahankali tana sauke idanuwanta daga kallon dattijuwa kuma tsohuwar matar dake a kansu tsaye tana musu fada cikin Iko da bayyanarda rashin ruwanta da abunda zai biyo bayan kuskuren da sukayi a lokacin tareda yi musu tini da ukubar dake tafe mai zafi.


Ita din dake tsaye a kan nasu tana fadan mahaifiyace ga Wanda ya haifesu ma'ana mahaifinsu babansu kaman yanda mutane ke Kiran Wanda ya haifesu da sunan baba kuma uba,

Su bazasu kirasa da kalman babansu ba sbd shi din Wanda ya haifesu ne kawai bawai babansu ba kaman yanda kowane uban yake,


Sun banbanta kalman mahaifi da baba ne sbd basu tantance me UBA Kuma baba yake nufi ba a zahirin haqiqanin gaskia dan basu taba gani ba ko samun kauna,kulawa,tausayi,jin qai ko wata fuskar dake tabbatar musu da su ‘din ‘yayane masu baba uba kaman kowane ‘yaya na halak da wainda bana halak din ba.

Amma a zahiri kusan sune suka fi tantance kalman mahaifi da ake nufi da wanda ya haifeka sbd zallar girmamamman ikonsa na haihuwarsu tareda juya rayuwarsu yanda yaga dama a mafi wulaqantacciyar hanya da karshen rashin daraja da rashin amfani shine mafi babban lamarin rayuwar dasuka tabbatar a duniya Gameda kalman mahaifi a gurinsu.


Matar data haifi mahaifinsu a zahiri itama bazasu kirata da kakarsu ba kai tsaye sbd babu wata sanyayawa ko kaunar Jini datake bayyanar musu da kalmar kaka da Ake kira a duniyar tasu,


Mahaifiyarsu,uwarsu,Annensu,Farin cikinsu kwalli daya a duniya dasike tsananin so da kauna sun kasance bayi a tare ita wadda itace asalin bautar acikinsu sbd shekarun data debo tun kafin haihuwarsu tana rayuwar bautar a tsakanin ‘da da uwar a wulaqance sbd takalmin daya saka kudi ya siya ya taka sunfita daraja a gurinsa bare mahaifiyarsa datake ganin tabbas Annen batada amfani a rayuwarsu kwata kwata saima wulaqantacciyar lalurar data zame musu da tarin ‘yayan matan data haife musu a gidan babu wata daraja ko daya dasuka qaru da ita,


Bayan shekarun data debo cikin azaba da ukubar uban nasu a yanzu gasu tareda ita cikin qangin bautar a tare,

Basuda yanci da ikon kansu sai yanda mahaifinsu yayi da raunanniyar rayuwarsu koda kuwa zaiyi gunduwa gunduwa da sassan jikinsu basa iya dago kai ko fuskarsa su kalla bare idanuwansa dan kuwa sunfi maraba da masifa kowace irice akan dago kai su kalli idanuwan mahaifin nasu domin garesu kaman aikata wani babban mummunan sabo ne dazai iya kaisu ga shiga masifar datafi ka kona kanka da tafasashen ruwan zafi.


Sumayya da datafi kowanne a cikin su hudun rauni sosai a hankali ta sake yin qasa da kanta muryarta Mai rauni na Dan rawa tace, 


"Zamu sake gyarawa kafin ya dawo Amma Dan Allah hande ki taimaka a bawa Anne abincin kafin ya dawo…"


Katseta hande tayi hankali kwance cikin Dan fada sbd batason batawa kanta karfi da rai ko lokaci akan lamarinsu sbd tasu rayuwar tagama lalacewa dan haka bazata bata karfinta a banza ba akan abinda yake tamkar matacciyar rayuwa mai numfashi tace,


"Babu ruwana da taka dokarsa,

Ita Annen taku zatace bata Saba da yunwa bane tsowon shekaru ashirin da Dori da aurenta dashi?


Kuda kuke yayanta kunzo daga baya Kuka Saba da yunwar bare ita,


Idan zata ara jarumta ta ara tayi rayuwar yanda ta Saba ni banason janye janye,

Kuje ku jira ya dawo yagama ku samu abinda zaku samu kuci din bansan sabon salon da bansaba dashiba.


Dukkaninsu babu wanda ya dago kansu na qasa suna sauraren fadan nata babu mai ikon dazai iya dagowa ya qara ko kalma daya acikinsu.

Ajiyar zuciya Annen dake tsaye jere tare dasu kaman bayi tsaye gaban sarauniyarsu ta sake tareda sake yin qasa da kanta cikin girmamawa mai tsananin gaske ta bawa Uwar uban gidan nasu hakuri sbd kwata kwata ba miji bane ko uba kaman na kowa uban gidansu ne a yanda suke rayuwar.,

Shi kansa bai daukesuba bare ya taba kallonsu a matsayin mata da ‘yaya kallonsu yake tamkar wasu dabbobi ko bayi daya saka kudi ya siyo suka zama garke.


Babu abunda Hande tasake ce musu bare ta sake kallon inda suke saima maida hankalinta datayi Kan sakon datake dubawa cikin qaramar wayar hannunta da batama gane komai da aka rubuto din.


Dagowa Anne tayi ta kalli 'yayan nata ahankali cikin sanyin murya tace su tafi.


Babu Wanda jikinsa ba amace ba suka juya a jere kaman kashin awaki suki bi bayan mahaifiyar tasu kafafuwansu a sake ba qwari kaman taliyar hausa sbd yunwa da wahalar data Dade da ginuwa ta hade da Jini da gabban jikinsu.


****BENAZIR ce kawai me qwari da dauriya tareda karfin zuciya a cikinsu,

Sumayya da mahaifiyarsu nada rauni mai karfi da yawa Dan har gwara mahaifiyar tasu akan sumayya wadda ta kasance rauninta yayi yawan da kusan koyaushe ta tsaya gaban mahaifinsu numfashinta Neman fita kirjinta yakeyi sbd tsoronsa daya dasa musu tun suna qananunsu har zuwa yanzu,


Mahaifinsu tamkar wani dodon tsawa ne a rayuwarsu,

Bai taba barin tsoronsa da shakkarsa sun girgiza daga zuciyoyinsu Koda second dayaba sbd tsananin azabarsa da mummunan horonsa garesu,

A duk lokacinda amon muryarsa ya sauka kunnuwansu Gangar jikinsu da zuciyoyinsu shiga rawa da mafi girman firgici sukeyi tareda tsananin tsoro da tashin hankali mai girgiza hankali da nutsuwa,


Shi din kaman wata tsawa da walkiyar data gurbata rayuwarsu ne ta lalata musu,

Tamkar wulaqantaccin bayi da basuda daraja suke a karkashinsa,

Tufafinsa,talarmin sawarsa da dabbobinsa sunfisu daraja a gabansa sbd dabbobinsa yana musu kallon kadarar kudi ne dazai qaru dasu sabanin su dayake kallon wahala ce kawai da rashin amfani a gabansa,


Almajirai dake cikin bola suna yawo sunfisu yanci da gata sbd su din Sunada ikon daga kansu su kalli abunda sukeson kalla tareda ikon zuwa ko karban sadaka daga duk wanda suke so Amma su daga lokacinda mahaifin nasu ya wanzu a guri numfashi mai karfi basuda iko ko yancin yi batareda shine ya bada damar ba bare motsi Mai karfi saida izininsa,


Mahaifiyarsu ta share shekaru da aurensa cikin ukuba da azabar data cinye lafiyar kwakwalwar kanta da gangar jikinta harma da ganinta,


Ta haifesu su hudu duka mata cikin azaba da wahala,

Ra rena cikinsu su duka hudun a mafi wahalallan hali da kadaici da yunwa da ciwo rashin daraja,


Haihuwarsu ta ninka azabarta,quncinta,yunwarta da rashin darajarta,

Yawansu ya ninka azabarsu suma tun zuwansu duniya,

A duk lokacinda dayansu ya qaru a duniya sai sauran sunyi kukan qaruwar azabarsu,

Azabar datayi sanadin rasuwar daya daga cikinsu,


Duka wannan tsana da azabar akan suna 'YAYA MATA ne,


Tsanar dayakewa Yaya mata ne kokuwa kaddararsa ce yasa Allah ya jarabcesa da haihuwarsu su hudu duka yaya matan?


Meye laifinsu?

Meye illarsu?

Meye illar samunsu dazai Rainesu tamkar dabbobin daya tsinto a daji.


Sun kasance tamkar mujiyoyi a cikin alumma sbd horon dasuka taso acikinsa hannun mahaifinsu da mahaifiyarsa yasa suke kallon kansu tamkar wasu halittun da kadan ne sukafi dabbobi daraja a cikin mutane.


Mahaifiyarsu ta rasa cikkakiyar lafiyar kwakwalwar kanta tun suna qananunsu,

Girmansu yasa tadawo kaman daidai sbd azabarta ta ragu anraba mata itada 'yayanta,


Abincin dasukeci agidan suna samun cinsa ne bayan Mahaifinsu da mahaifiyarsa sunci sun rage Kuma Sunada iko da daman cinsa ne a gurinda zasu wanke kayan da aka Gama cin abincin dukkaninsu a kwano daya,.


Menene ci a koshi?

Wannan kalma ce da basu taba sanintaba Dan bata taba faruwa dasuba tsawon rayuwarsu,


Hutu, Shima wani Abu ne da basusan dashiba sbd babu shi a abunda suke samu.


Bauta,

Wahala,

Yunwa,

Azaba, sune abubuwan dasukafi sabo dasu,


Ribarsu biyu dasuke gani sun samu a rayuwarsu shine ibadarsu da kaunar junansu dasuke tsananin yi..


SUMAYYAH itace babba a haihuwa,sai SAMIRAHwadda tazarar shekara biyu ne rak a tsakaninsu,

sai BENAZIR wadda itama shekara daya da watanni ce tsakaninta da Safnah sai SAFNAH wadda itace qaramarsu itama shekarun dake tsakaninta da benazir biyu ne sbd yanda ako wane lokaci mahaifin nasu yake zuwarwa mahaifiyar tasu ba tsari ba kulawa ba komai,


Bai taba shaawar qarin aure ko neman wata matar banzar ba a waje sbd tsarinsa da tsananin so da kaunar abin duniya dake ransa,


Neman mata ko caca ko sunansu baa fada a gabansa sbd tsananin son kudinsa da bazai iya hakuri ko tinanin ma rasa ficika ba aciki yasa bai taba shaawa ko kallon inda ake caca ko zina ba.


Asalin tsanar Bena a ransa tafi ta kowa acikinsu ta musamman ce sbd cikinta ne ya cinye Rabin arzikinsa dayake ganin wata mummunar kaddara ce garesa zuwanta duniyama gabaki daya bayan haihuwarta sabanin duban da likita yayi masa akan namiji ne acikin,


Bai taba son wani Abu a duniyaba kaman yanda yaso cikinta,

Allah ya jarabcesa da son cikinta

So me tsananin dayasa ya kashe dukkanin tattalinsa akan cikin Wanda akan cikin yafara Kai matar tasa asibiti sbd ko uwarsa data haifesa duk ciwo Bai taba kaita asibiti ba sai akan wannan cikin

Daga karshe dukkanin burinsa da muradinsa ya lalace a kan idonsa da aka sake iso masa da sakon 'ya mace aka haifa wadda tun a asibitin yaji tsanarta fiyeda uwar da sauran yayan da Ake haifar masa haka zalika tunda ta fado duniya bai taba daukanta a hannunsa ba haka bayajin zaiyi har abada kuma daga kanta bai sake ko kallon abinda matarsa tasa ta haifa.


Tsanar dayake wa Benazir ta bata qarfin zuciya fiyeda Yan uwanta dakejin radadi da raunin tsanar da Mahaifinsu ke musu sai dai dukkanin su basusan me kaddararsu ta tanadar musu ba a gaba dagasu har shi mahaifin nasu.



****Dakinsu suka shiga kowannensu ya nema guri ya zauna a hankali Banda safnah data tsaya daga bakin window Idanuwanta da sukai ciki sbd rashin kuzari tana kallon bayan gidansu a jikin windon jikinta na qarasa sanyi zuciyarta a ko yaushe babu abunda take tinani sai yanda rayuwa ba'a karkashin mahaifinsu ba zata kasance,


Shin sauran 'yaya ya sukejin mahaifansu acikin ransu?

Da wani ahalin aka haifesu koda a matsayin ‘yayan shegu ne zasufi farin ciki da nutsuwa,

 Meyesa basu zamto cikin yayan da ake haihuwarsu ana jefarwa ba sunfi kwanciyar hankali koda talaka ne ya tsincesu zaifi musu akan wanda suke karkashinsa a matsayin mahaifi yanzu,


A koyaushe burinta shin da gaske akwai wainda ke siyan mutane suyi bayi dasu kaman yanda mahaifin nasu keda tsananin buri da fatan Ina zai samu masu siyan bayi ya saida dukkaninsu Koda a farashi mara daraja ne a tafi dasu ya huta da ganinsu shima a rayuwarsa,


Idan da gaske akwai irinsu to tabbas itama tanason ta kasance a siyeta a tafi da ita tabar mahaifinsu da sunansa kawai aka kira dukkaninsu zuciyoyinsu tsalle sukeyi cikin tsoro Mai girma da firgici Wanda wani babban balain ne ma bayyanarda rawar jikin tsoronka a gabansa wannan ma wani nauyin horon azabar ne dasu kadai sukasan wutar tsoro da rawar dake gudana a jininsu gurin boye hakan.


Ahankali hawayenta suke gangaro 

duk tsanani hawayensu ma basuda yancin gangarowa a gidan saidai idan sun shigo dakinsu su iya sakinsu,


Ahankali cikin muryarta datake bayyanarda rauni da qulafucinta akan rabuwa da rayuwar datake ciki tace,


"Allah yakawo kaddarar dazata rabamu da gidan nan Koda ta wahala ce.


Dukkaninsu sun ji abunda ta fada cikin raunin

Sun Saba jin hakan daga bakinta sbd a cikinsu itace tafi kowa raunin son tafiya tabar gidan Koda zata tadda rayuwar wahalar datafi ta gidan,


Duk tsanani sun San bazasu taba barinta kwatanta guduwa ba kaman yanda itama bazata taba kwatanta guduwarba sbd azabar kwatanta guduwar ne yayi sanadin rasuwar SAMIRAH wadda ta rasu rasuwa Mafi Karya zuciyoyinsu.

#MAMUH#

#DEEP#

#BILLONAIREROMANCE



ZAFAFA BIYAR🔥


-ZAFIN KAI

Mamuhgee


-TABARMAR ‘KASHI

Safiyya Huguma


-FURAR DANKO

Billyn Abdul


-BAKON MUNAFIKI

Miss xoxo


Duka hudu 1k

Uku 800

Biyu 600

Daya 400


Pay at

09033181070

09032345899


Zafafa🫶🔥🔥

_*ZAFIN KAI*_

_Mamuhgee_



_ZAFAFA BIYAR_

2

Samirah ta rasu ne bayan da azabar tayi masu yawa ta girmi tinani da dauriyarsu harma da duk jarumtar da suke tinanin sunada ita,


Cikin tsakiyar dare guraren karfe uku na dare ta fita dan guduwa bayan ta tabbatarda a lokacin bacci mai karfi yake daukan Ababa sbd yawanci yana kaiwa karfe daya koma harda mintina kafin yayi bacci sbd babu daren da baya lissafin dan arzikinsa da kuma lissafin yanda zaiyi da rayuwarsu kota hanyar siyarwa kota hanyar samun masu kudin da suka amsa sunan asalin masu kudi su auresu koda a matsayin matan biyan buqata ne kawai shi dai idan zasu fita rayuwarsa amma a dayan bangaren tinaninsa shine karatun daya sakasu sbd idan har bai fanshe komai nasa a gurin masu fataucinsu ba to tabbas dole idan masu dollars ne zasu auresu kota tsiya yasan dole ana buqatan ilimin boko da 'yar wayewar ilimin a tare dasu kafin su shige.


A daren kwanon abinci daya suka samu su dukansu wanda dukkaninsu loma bibbiyu sukai suka barwa mahaifiyarsu sauran sbd karfinta na shekaru da wahala ta cinye,

A cikinsu yanzu Annen tasu ta zama tamkar itace qaramar kanwarsu gabaki daya sbd kowannensu tausayinta yake ji fiyeda junansu,

Tafi su gazawa,

Tafisu jigata hakama tafisu buqatan abinci a koda yaushe aka basu din sbd rauninta.


Samirah a cikinsu ta kasance batai jin qan sauran ba sbd a koda yaushe indai zasuyiwa 'dayansu sacrifice na wani abun itace take kasawa shiyasa koyaushe batada burin guduwa daga wannan rayuwar mai kama data fataucin bayi,

Burin guduwa da tserewa mahaifinsu yasa abin ya zauna a ranta har kusan ta shafawa Safnah kwadayin guduwa daga wannan masifar dasuke kira da rayuwar gidan ubansu.


Yunwa,azabar zafi data sauro daya zama tamkar bugun numfashinsu sbd babu yanda zaayi su kwana su tashi batareda sauro fiyeda dari a dakinsuba sakamakon rashin kofa sai labule windon dakinma kusan dan kada su gudun ne ko barayi su shigo ta nan su masa sata a gidan yasa ya saka musu sbd yana ta bayan gidan ne windon.


Tashi zaune samirah tayi ahankali daga kwancen datake gefen mahaifiyarsu akan babbar tabarmarsu dasuke kwana zube akai kaman an shanya su,


Annenta ta zubawa ido Ahankali jikinta na mutuwa tareda karayar zuciya da tsananin kaunarta da tausayinta na yanda zataji a matsayinta na uwa idan aka wayi gari babuta ta bata ta shiga duniyar da Anne da yan uwanta basu saniba ko zasu sake haduwa har abada,


Hawaye masu zafi ne suka gangaro mata sbd tinanin azabar da zasu iya sha daga mahaifin nasu akan guduwarta saidai bazata iya zama a cikin wannan rayuwar ba sbd tsoron dake zukatansu wadda mahaifinsu ya saka musu kawai zata iya kashesu kokuma su qare da juyayyar qwaqwalwa kaman mahaifiyarsu wadda ta zama ita da qaramin yaro wani lokacin banbancin kadan ne.


Hannuwanta ta daga Ahankali ta kallo tafin hannuwanta dake a cabe suna wani irin ruwa sbd azabar ruwan zafin da akai mata a jiya

Ta tabbatarda zata rube a hakan a yanke hannuwan kokuma ta warke amma bazaa taba kallonta a nuna an mata hukuncin ba bare a neman mata magani,


Zata gudu tabar gida koda yan uwanta da Annensu zasu samu ragin mutum daya abincinda ake basu ya dan qara yawa a cikinsu sbd tasani har abada idan har a gidan zasuyi rayuwa bazasu taba cin abincin da zasu qoshiba,

Qin da Ababa yayi musu zuwa gaba lokaci yakuma ja yaga baida mafita komaima zai iyayi dan ya kawai dasu daga gabansa ciki kuwa zata iya cewa harda kashewa dan karfin ransa da taurinsa babu kowane kalar tausayi ko imani acikinsa,

Abu daya ke karyar da taurin ransa da girmansa shine kudi,

Bai hada komai da dukiyarsa ba wadda idan ana maganar masu dukiya baya cikin layi ko kusa amma kaman yanda yake fada kowa da nasa yake tinkaho,

Baya roko,baya daukan reni a gurin kowa sbd a ganinsa babu mai kudin da zai iya basa irin kudin dayakeso sbd shi a gurinsa masu lissafi da dollers din America sune masu kudin gaske dasuke isa su fada ya saurara.


Bin 'yan uwanta tayi da kallo daya bayan daya hawayenta na sake gangarowa da dumi mai zafi tana sake kallon yanda kowannensu yake fidda wahalallen numfashin dake fitowa daqyar sbd yunwa amma a hakan suke bacci kaman jarirai da basusan matsalar komaiba tsaban tawakalli da rungumar rayuwar da Allah ya jarabcesu da ita.


Kan benazir da zatafi kowa daukan wahalarsa ta tsaida idanuwanta tana jin tausayinta sbd azabarta tafi ta kowannensu akoda yaushe amma Allah zai duba lamarinta da sauran yan uwan da mahaifiyarsu wadda guduwanta saiya taba Annen sosai.


Hannuwanta masu tsananin azabar ta dafa tana rintse ido sbd radadin dayake ratsata ta miqe tsaye tana sakawa zuciyarta karfi da juriya ta janyo qaton mayafin Anne dayake gefe aje ta yafa ajikinta ko takarmi bata sakaba sbd zaiyiwa yan uwanta amfani idan wani ya rasa na sakawa yayi amfani da nata din.


Kofar ficewa ta nufa batareda ta waiwayoba sbd raunin da zuciyarta keyi idan tana kallonsu,


Safnah data ji motsinta kadan ta bude idanuwanta tana kallonta batareda ta motsaba idanuwanta itama sina cikowa da hawayen tausayin Annensu da yan uwanta dazasu bari dan kuwa matuqar taji samirah din ta fice batareda matsalar komaiba to itama miqewa zatayi tabi bayanta su tsira tare.


Ahankali samirah ta ringa daga qafafunta dake rawar tsananin tsoro da bugawar zuciya mai karfi ta nufi hanyar dazata kaita kofar dakin Hande wadda mukullin qaton padlock din gidan yake hannunta bayan sakata kusan biyar dake jikin kofar shigowa gidan.


Cikin sanda tana dan rintse idon azaban hannunta dayake ruwa sosai ta isa dakin ta tura kofar a hankali tana zira kanta kadan taga handen tayi nisa a bacci sosai kan qatuwar katifarta mai taushi da tudu.


Cikon sanda ta isa inda tasan mukullan na gurin ta saka hannunta mai ciwo ta riqo mukullan ta  damqo a hannunta ta matse sbd kar suyi qara su tada Handen 

Tanaji azabar yanda ta damqesu a hannunta dayake a cabe tana ratsa zuciyarta har cikin kanta amma ta daure.


Tana numfashi da qyar ta fito daga dakin ta tsaya tsakar gidan ta saki wani wahalallan numfashi mai dumi da azaba hawayenta na kasa gangarowa daga idanuwanta dasukai ja.


Safnah dake rabe bakin kofa daga cikin dakinsu tana hango samirah din taga komai ya tafi daidai ta fito sake tsayuwa tayi daga cikin dakin tana dan sake ziro kanta kadan dan kafarta bazata sako tsakar gidanba dan hakan kawai zai iya sakata rasa qafafunta idan Ababa ya kamasu gashi tana ganin dakin Hande da samirah din ta bari a bude wanda iska da sanyi zai iya farkar da ita taganta amma bazata iya fitowa tace mata ta rufe dakinba dan ta zabi ta boye kanta ga wannan aikin dayake sunan siradin tsira kona halaka.


Kofa samirah ta nufa jikinta na rawa sosai sbd hannuwanta dasuka kasa riqe mukullan da kyau,

Hannu na wata irin rawa ta kamo katon padlock din dayafi karfin hannunta ta saka key din daqyar amma ta kasa saka karfi ta murda ya bude sbd hannuwanta dake jini gabaki daya wutar takoma mata sabuwa gashi  duka hannuwan biyu,


Ninka tashi hankalinta yayi tareda wani irin firgitaccen tsoro dataji yana shigarta mai karfi a lokacin sbd kaddararren aikin tsautsayine da babu komawa baya sbd tariga ta barko barnar tunda ta sato mukullin gwara duk tsanani ta balle ta gudu akan Ababa ya risketa tabbas hannuwanta bazasu qara moruwaba kuma.


Yanda jikinta ke rawa yana jijjigar tsoro da firgici tareda tashin hankali mara misali yasata kofar da padlock da mukullan suka fara bada sauti mai karfi,


Safnah dake labe wata irin rawa qafafunta suka dauka  zufa na tsiyayo musu a ciki zuciyarta ta hau bugawa da tsalle kaman zata fado sbd tasan komai ya lalace.


Hande da iska tareda sanyi sukai mata yawa cikin bacci sbd kusan acan suke qarshen gari anguwar da babu mutane da yawa dan sam Ababan baya kaunar zama cikin mutane sosai sbd baya kaunar ko so daya ashiga huruminsa da rayuwarsa da wainda ke karkashinsa.


Bude idanuwa Hande tayi sai kawai tayi ido biyu da hasken taurari kofarta a bude,


Bude ido tayi da kyau tana kokarin tashi zaune sbd ta tabbatarda ta rufe kofar dakint


a duk tsanani bata bacci daki a bude.


Motsin bude kofar gidan dataji ne yasata tasowa ahankali tana leqowa cikin tsoro da fargabar wane tsautsayin ne ya kawo barawo gidan dan kuwa Ababa tsaf zai harbesa da bindigarsa ta mafarauta.

Post a Comment

0 Comments