TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

MAGAJIN GARIN ZAZZAU YA RASU

 

Magajin Garin Zazzau, Alhaji Mansur Nuhu Bamalli, ya rasu.

Kafin rasuwarsa shi ne Jakadan Najeriya a Moroko, kuma ƙani ga sarkin Zazzau, Dakta Ahmed Nuhu Bamalli.

Cikin wata sanarwa da masarautar Zazzau ta fitar mai ɗauke da sannun jami'inta na hulɗa da jama'a, ta ce Ambasada Mansur Nuhu Bamalli ya rasu ne a wani asibiti mai zaman kansa da ke Legas yayin da yake kan hanyarsa ta zuwa Moroko.

Marigayin, mai shekara 42, ya bar mata ɗaya da ƴaƴa biyu.

A shekarar da ta gabata ne tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya naɗa shi jakadan Najeriya a Moroko.


Post a Comment

0 Comments