A Abuja da Lagos kawai za'a cigaba da sauraron kararrakin zabe (APPEAL)
__________
Shugaban kotun daukaka kara na Nijeriya da zata jagoranci kararrakin zaɓe
Justice Monica Bolna'an Dongban-Mensem CFR
Tace za'a mayar da shari'u na jihohin Arewa 19 zuwa birnin tarayya Abuja sai kuma jihihin kudu 17 za'a mayar da shari'unsu zuwa Lagos. A kararrakin da aka daukaka kara kan su.
Jaridar The Cable ta rawaito dalilin da ya snaya aka sauya shari'un
zuwa Abuja da Lagos shine sun bayyana yadda aka samu korafe-korafen cewa gwamnoni sunyi katsalandan ga sha'anin kotunan sauraran kararrakin zaben 2023. Da kuma wasu shugabanni.
Wanda yasa dole a dauki mataki Dan tabbatar da Adalci ga kowa da zai sanya Cigaba da kimanta Bangaren Shari'a a kasar.
0 Comments