TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

Da dumi duminsu

 Kotun ƙolin Najeriya ta jinkirta yanke hukunci kan ƙarar da Atiku Abubakar da jam’iyyar PDP suka ɗaukaka kan hukuncin da kotun sauraren kararrakin zaben shugaban kasa ta yanke wanda ya tabbatar da nasarar shugaba Bola Tinubu a zaben shugaban ƙasa na 2023.

Har


ila yau, ta dakatar da yanke hukunci kan ƙarar da Jam’iyyar Labour ta daukaka, yayin da ta kori korar jam'iyyar Allied Peoples Movement (APM).

Kotun ta kuma saurari buƙatu daga lauyoyi kan bukatar da Atiku ya miƙa na gabatar da sabbin shaidu kan shaidar karatun Tinubu.

Lauyan Atiku Abubakar, Mista Chris Uche, ya buƙaci kotun da ta amince da buƙatar da suka miƙa ta kuma saurari ƙarar da aka daukaka tare da soke takarar Tinubu.

Post a Comment

0 Comments