TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

DIYAM PAGE 42

 By 


Maman Maama


Episode Forty Two: A backlash


"Sadauki?" Na maimaita cikin tsananin mamaki "a ina Sadaukin ya ganku?" Sai ta bani labarin abinda ya faru dasu bayan sun bar gidan. Wannan ya kara ruda tunani na, me Sadauki yake yi a wannan hanyar a wannan lokacin har ya gansu ya taimaka musu? Duk da bansan a wanne hotel yake zaune ba amma nasan babu hotel a kusa damu, sannan unguwar mu wajen gari ne ballantana inyi tunanin ko wani abu ya fito nema kuma ma ai mutane masu kudi irinsa ba zasu fito neman abu ba sai dai suyi order a kai musu har inda suke. Tabbas ina bukatar yin magana da Sadauki. Amma dai ko menene yake yi a gurin am greatful da taimaka musu da yayi saboda I can only imagine irin horror din abinda zai faru dasu da bai zo din ba, wannan kuma sai ya kara hura wutar kiyayya da nake yiwa Saghir saboda shine ya kusa jefa su cikin wannan halin. Naso in tambayi Inna a game da Sadauki amma sai tayi min sallama tace dare yayi sai gobe zamuyi magana. Anan palo na karasa kwana saboda saman gani nake kamar na kara kusa da Saghir. 


Sa safe Subay'a ce ta tashe ni tana neman abinci, da yake ban samu nayi bacci sosai ba shi yasa na makara. Na jata muka shiga dakin kasa mukayi sallah tare sannan muka shiga kitchen na dora mata noodles na soya mata kwai, ina cikin aikin Saghir ya shigo Subay'a ta tafi gurinsa da gudu ya dauke ta suka tsaya a bakin kofa yana kallona yace "me ake dafa mana ne?" Ko kallo bai ishe ni ba, shi har yana da karfin halin pretending kamar babu abinda ya faru? Subay'a ce ta bashi amsa, sai yace "Subay'a mommy fushi take yi da Daddy saboda yace zaiyi aure" na juyo na watsa masa harara, ni har na manta ma da yace zaiyi aure. Ina jin Subay'a tana tambayarsa menene aure, na bar musu kitchen din sai ya biyo ni yana cewa "wai duk kishin ne haka? Ni na taba ganin anyi kishin wanda ba'a so?" Har zan wuce kuma sai na dawo na karbi Subay'a daga hannunsa nace taje kitchen ta dauki abincinta taci sannan nace masa "Saghir ko matan duniya zaka aura ko a tafin kafar Halima. Ni din ce dai ba zaka samu zuciya ta ba wallahi. Kuma su Inna sunje gida lafiya babu abinda ya same su, sun samu wani bawan Allah wanda yasan mutunci da darajar mutane ya taimaka musu kuma ya kaisu har gida a mota, bawan Allahn da basu hada dangantaka ta jini dashi ba" yace "ohh there is that, ashe fushin biyu ne" wato shi a nufinsa har ya manta da abinda yayi. Yace "to yanzu wanene bai san darajar mutane ba? Ni mutum ne mai ka'idoji kin sani kuma, ni bana son a shiga rayuwata sam bana son ake kawo min mutane cikin gidana" nace "gida? Amma dai kasan muma muna da gida ko? Kasan ba'a titi muke ba ko?" yace "sai su zauna a gidan naku kar su zo min nawa gidan, as simple as that" na girgiza kaina nace "ni Saghir bani da sauran karfi, na zuciya da na jiki da zanyi fada da kai, ka fadi duk abinda kake son fada ka kuma yi duk abinda kake son yi. Duniya ce, akwai ranar kin dillanci kuma ina sanar maka da cewa tana daf da zuwa" ban jira abinda zai ce ba na haye sama. Ina jinsa ya bude kofar palo ya fita, na leka naga shi da Subay'a ne suka fita a mota, na sauko kasa da sauri na tura kofa naji a rufe, wato rufe ni yayi daga waje ya tafi da key din. 


Ina zama Inna tana kira na, dama tun dazu nake ta zuba idon ganin kiranta amma sai naji muryar Asma'u tace "Adda inna fa kuka take yi tun da muka dawo jiya da dare, tun da taga Sadauki take kuka na rasa dalili" na gyada kaina, ni nasan dalilin, nace "me Sadaukin yace sanda ya dauke ku?" Tace "baice komai ba fa, kawai tsokana ta yayi tayi har muka zo gida. Inna tace masa tana son ganin sa sai yace zai zo watarana" na tambayeta "ya tambaye ki ni?" Tace "a'a" na lumshe ido ina jin hawaye yana taho min. Idan ni ce na hadu da yaya ladi misali nasan abinda zan fara tambayarta shine Sadauki. Ko dai Sadauki ya daina so nane? Duk da dai Saghir yace min baiyi aure ba amma for all I know maybe yana da budurwa yanzu, maybe ma an kusa bikin. Maybe ma yaruwarsa zai aura a Maiduguri.


Nace da Asma'u ta kira Mama ta gaya mata abinda ya faru, ni ba zan iya zuwa in lallashi Inna ba saboda Saghir ya rufe ni a gida. Na san kuma yanzu inna tana bukatar wanda zasuyi magana dashi, musamman wanda yasan abinda tayi wa Sadauki da shi kuma sakayyar da yayi mata. 


Ta barshi a titi a lokacin da yafi bukatar gida, shi kuma sai ya dauko ta daga titi ya kai ta gida a lokacin da tafi bukatar hakan.


Washegari Sunday, Saghir ya fita sai gashi ya dawo yana washe baki, ko kula shi banyi ba dan ban damu da insan me ya saka shi farin ciki ba amma sai ya zauna yana cewa "subay'a daddyn ki zai tafi kasar waje, me kike so in siyo miki?" Ta mike da murna tana tsalle tana yi masa list din kaya, shi kuma yana ta dariya, sai ya kalle ni yace "ki hada min kaya, gobe zan tafi oga ya tura ni zanyi signing contract da wani company a can" na dauke kai kamar ban ji shi ba sai yace "dama nan da two months ne tafiyar nan tazo, da da amarya ta zan tafi. Ohh ban fada miki ba ko? Nan da wata biyu ne aure na fa" nace "to ka daga tafiyar mana sai anyi bikin? Ohh na manta, ashe bada kudinka zaka yi tafiyar ba da kudin oga ne kuma dole sai abinda oga yace sannan zakayi tunda kudin sa ne. Mtsww i pity you" da naga dai neman magana yake yi sai na tashi na bashi guri saboda ni bana son rigima dashi a gaban Subay'a, amma kuma sai na samu zuciya ta da jin haushin Sadauki na budawa Saghir da yake yi.


Shi ya hada kayan tafiyar sa da kansa, da safe ya turo Subay'a ta kira ni naje na tsaya a bakin kofa yace "rashin kunyar ki, da rashin biyayyar ki shi yasa har yanzu auren mu yaki daidaita, da ace kin kwantar da kai, kin bini yadda nake so da ba karamin jin dadi zakiyi tare da ni ba. Kinga wannan tafiyar ma oga mu biyu ya biya wa, ni dake, yace in tafi da matata saboda wata daya zanyi kar in zauna gwauro a can, kinga da sai muyi tafiyar mu ni da ke da Subay'a but I guess I will have to go alone" ya ajiye kudi a kan mirror "ga kudin cefane nan, kinsan ni ina tsoron Allah dan haka ina kokarin sauke hakkin ki da yake kaina. Ban yafe ba, in kika fita ko da kofar gida ne indai ba abinda ya shafi makarantar Subay'a bane ba, sai kuma rashin lafiya, Allah yana kallonki in kika ci amana ta in bana nan" nayi murmushin takaici kawai, akwai amsoshi da yawa a raina wanda nake so in bashi amma ganin Subay'a yasa nayi shiru har ya dauki jakarsa ya fita yana cewa "gwara mutum ma ya dan bar kasar ya sarara na kwana biyu".


Tafiyar Saghir da kwana biyu Alhaji Babba ya kira ni a waya, I can't remember last sanda ya kira ni. Na dauka na gaishe shi sai naji muryarsa wani iri yace min "Diyam ki zo gida ina nemanki dan Allah" sai naji wani iri da yace min dan Allah, duk da dai Alhaji Babba yayi sanyi sosai tunda yanzu kusan hannu baka hannu kwarya suke zaune a gidan, bashi da komai sai yan abokai da suke taimaka masa da kuma kawu isa shima da yake dan bashi wani abu, duk sana'ar daya kama sai ta rushe, kullum muka je gidan yana ta cewa makiya ne suka sako shi a gaba ni kuwa deep down nasan inda matsalar dukiyar Alhaji Babba take, kudin mune da yaci, dukiyar marayu daya handame ya hada da tasa dukiyar da yasha wahala gurin nema dan haka sai yayi asarar har tasa dukiyar gabaki daya.


Na tambayeshi ko lafiya? Sai yace inzo dai kawai yana nema na. Na shirya ni da Subay'a muka tafi. Bayan mun gaisa da mutanen gida ne muka tafi palonsa na ganshi daga shi sai riga yar shara wadda duk tayi datti. Na durkusa na gaishe shi sai ya dauko wasu takardu ya miko min. Na bude a nutse ina dubawa a dan ilimi na sai na fahimci takarda ce daga kotu ta sammaci, mai kara shine 'Aliyu Usman Kollere" Wanda ake kara kuma "Alhaji Muhammadu Kollere" sai kuma sauran takardu da suka kunshi photocopy na takardar fili belonging to Aliyu Usman Kollere, da kuma takardar garage din Baffa, sannan anyi list na duk abinda yake ciki da kudinsa da kuma estimate na kudin business din gabaki daya, sai kuma akayi jimullar kudin wanda yawansu sai da yasa na kama baki na. Yanzu wannan ne dama kudin da Alhaji Babba yaci na mu? Wannan shine kudin da akace anyi min kayan daki dasu? Amma mai yasa alhajin yake nuna min a yanzu?


Kamar amsar tambaya ta sai naji yace "Diyam kinga abinda tsohon saurayin ki zaiyi min ko? Yaron da Usuman ya rike kamar shi ya haifeshi kinga sakayyar da zaiyi mana ko? Wai ya kaini kara wai naci dukiyar marayu to dukiyar ta ubansa ce? Ina ruwansa? Kudin nan ba aure nayi miki dasu ba? Ai na gaya wa Amina tun a lokacin kuma ra amince. Takamarsa shine da kason uwarsa a ciki shine yake so yayi min tonon silili" ni dai na ajiye takardun ina kallonsa har ya gama fadan sa sannan kuma sai yace "an ce min in na saka kika yi masa magana zai iya ya janye wannan maganar" na gyada kai, so that's it. Wannan shine dalilin da yasa aka shigar dani maganar. Nace "ni Alhaji bansan inda Sadauki yake ba ballantana inyi masa magana, kuma ma ba lallai ne ya saurare ni ba. Amma shi ne ya kawo takardun?" Yace "ina fa? Babu wanda yasan inda yake fa, lauyoyi ya dauka har guda uku, su suka shigar da karar alkali kuma ya aiko min da sammaci" ba gyada kaina, wato basu san waye Sadauki a yanzu ba. Nace "to ni Alhaji in zanyi masa ma maganar ai bansan inda zan same shi ba" yace "Amina ma tace bata san inda yake ba. Kuma ko number dinsa babu a jikin takardar sai ta lauyoyinsa" na dauki takardar ina kara dubawa sai naga numbobin, na dauki daya a waya ta nace "idan na same shi me zance masa?" Ya gyara zama yace "ki gaya masa ni ba matsiyaci bane ba, kaddara ce ta sauka a kaina da kuma makiya da suka sako ni a gaba wannan ne yasa a yanzu bani da kudin da zan bashi, amma kice masa yayi hakuri muyi aggrement zanke biyansa a hankali a tsakanin mu ba sai munje kotu ba" nace "shikenan Alhaji, zanyi kokarin ganin yadda za'ayi a fahimci juna" yayi ta saka min albarka sannan yace "ashe mijinki yayi tafiya? Sai da aka kawo takardar nan jiya na neme shi sannan naji ma wai baya kasar".


Na fito ina ta mamakin halin Saghir. Sai kuma na koma lissafin wannan lamari. Me Sadauki yake after? Na tabbatar ba kudin yake so ba dan yafi karfin wannan kudin a yanzu. Sai kuma na fahimci wannan shine dalilinsa na tura Saghir kasar waje saboda baya so yayi blowing cover dinsa ta matsayin ogan Saghir, duk da dai yadda ya shirya kai karar ba lallai ne ma a ganshi ba dan lauyoyinsa sun isa su wakilce shi amma me yake bukata? 


Sai dana koma gida sannan na kira number din lawyer din. Ya dauka na gaishe shi ya amsa sama sama sai nace dan Allah ina son magana da client dinsa Aliyu Usman Kollere, yace "what for? Bana bada contact din client dina gaskiya" nace "na fahimta, but please ka gaya masa in ya tuna Halima Usman Kollere to tana son magana dashi" ya amsa zai fadi sakona sannan ya katse wayar. Jira jira har dare babu amsa, haka nayi ta duba waya ina karo volume wai dan kar a kira banji ba. 


Sai safe around ten sannan kiran ya shigo, lawyer din ne dai yace "yace menene? Ki gaya min sakon sai in gaya masa" na runtse idona ina jin duniyar ma duk tayi min zafi nace "shikenan. Tell him nace dashi nake son magana ba da kai ba in bashi da guts din da zai saurare ni shi kenan na rike magana ta" na kashe watar ina jin zafin Sadauki a raina. Wato bama yason magana dani, baya son gani ba, ya manta dani yake nufi ko me? Ya manta alakar mu? Ya manta alkawarin mu? He said he will love me forever yanzu har forever din tayi? Amma sai wata zuciyar take tuna min da matsayi na na matar wani, wata zuciyar tana so in yi wa Sadauki uzuri na kin saurata ta da yayi, na gudu na da yake yi.


Around 12 wani kiran ya shigo wayata, saida zuciyata ta buga ganin sabuwar number, sai na samu kaina da rike wayar amma na kasa amsawa har ta kusa katsewa sannan na dauka a hankali na kai kunnena idona a rufe nayi sallama, shiru at first, sannan yace "kina son magana dani, ina jinki" muryar Sadauki, as clear as ever. Na hadiye abinda yaki tafiya a makogwaro na sannan nayi kokarin nima in yi irin nasa nace "maganar Alhaji Babba, yana son ayi negotiation. Can you do that?" Ya danyi shiru sannan yace "come to my office tomorrow morning, you know where it is" daga nan ya katse. Sai na zauna da waya a hannu ina mamakin wai da Sadauki nayi magana yanzu, but it sounded as if da wani stranger nayi maganar. 


Ranar bana jin nayi baccin awa daya. Da assuba na tashi nayi wanka nayi sallah sai kuma na zauna ina kallon agogo yana ta lakaki yaki yin sauri balle gari ya gama wayewa. Na tashi Subay'a na shirya ta sannan nima na shirya tana ta tambayata inda zanje, na bata breakfast nima na hada tea na kurba amma sai ya tsaya a makogwarona yakasa wucewa. A haka har lokacin kaita school yayi, na kaita sai kuma nayi tunanin is too early inje office din Sadauki dan haka na dawo gida na cigaba da kallon agogo har saida ten tayi sannan na fita. Ina gayawa mai adaidaita Abatcha Motors sai yace "okay companyn motocin nan ko?" Sai da muka isa gurin sannan na kare wa building din kallo, so all of this is owned by Sadauki, how? Na shiga trying not to act like yar kauye, shi kansa building din anyi shine da shape din mota, haka round about din da yake tsakiyar gurin shima siffar mota ce dashi. Sadauki and cars bansan wacce irin soyayya ce a tsakanin su ba. Ina shiga reception din sai na tuno da ranar da akayi party, nayi tunanin ko wasu zasu gane ni? Amma kuma ranar babu haske sosai dan haka ba lallai bane su gane fuskata. Naje desk din receptionist, kafin inyi magana tace "Halima?" Na amsa mata sai ta dauki waya tayi magana a ciki sannan ta nuna min bene tace in hau, na hau na tarar da wata tana jira na sai ta bude min wata kofa tace in shiga, na shiga na tarar da wata mata da name tunanin secretary ce, kyakykyawar gaske gata ta sha make up sai kamshi take zubawa, ta yi min murmushi sai kawai naji ina jin haushinta ba tare da ta yi min laifin komai ba, ta wuce gaba sai naga kamar tana sane take murguda min bombom ta bude min wata kofa da card din hannunta na shiga sannan ta rufe.


Yana zaune a bayan katon table din gaban sa, as majestic as ever, bai ko dago kai ya kalle ni ba yaci gaba da rubutu a takardar gabansa ni kuma ina tsaye sai daya gama sannan ya dago fuskarsa blank yace "welcome Madam, have a seat please" naji kamar in juya in fita daga office din, nayi nadamar dana sani banzo ba amma ina bukatar amsa, ina bukatar ji daga bakinsa cewa ya manta da first twenty years of his life. Na zauna a kan cussion chairs din da suke jere a office din. Ya mike tsaye, sai naga ya kara cika min ido da kwarjini da girma baki daya ya zagayo ya zauna a kujerar gaban table dinsa sannan yace "kince Alhaji Muhammadu ya turo ki akan wani negotiation, ina jinki" naji wani sabon bacin rai, ni na ma manta abinda ya kawo ni kenan, sai kawai hawate ya fara bin fuskata. Nace "abinda zaka ce ma kenan? Irin karbar da zakayi min kenan? Sadauki nice fa Diyam, how can you even......call me Madam?" Sai ya mike tsaye ya juya bayansa ya saka hannu a aljihu yace "menene sakon da Alhaji yace ki fada min?" Sai na mike na nufi kofa da sauri ina goge hawayen fuskata, bai ce min komai ba har naje na kama kokawa da kofa amma taki budewa, na juyo ina kallonsa sannan yace "ba'a fita daga office dina sai nayi wa mutum izni" sai na dawo da baya da sauri na dauki wasu magazines na motoci na jefa masa, na debo tarkacen files din kan table dinsa suma na yi ta dukansa dasu har takardun suka tarwatse a gurin amma ko motsawa baiyi ba, na durkusa a tsakiyar gurin na kama kuka sai ya dawo ya zauna akan kujera yace "menene sakon da zaki gaya min?" Sai dana gama kukana sannan na tashi na zauna na goge fuskata nace "why? Sadauki why? Me yasa kame treating dina haka?" Yace "ya kike tsammanin zanyi treating mayar employee na?" Nace "shikenan? Matsayina kenan? Matar employee dinka? Me yasa ka dauke shi aiki ma? A ina ka sami wannan kudin kuma? I need answers Sadauki, I need to talk to Sadauki not this Mr Abatcha" yace "zaki samu answers dinki in due time. Now me Alhaji Babba yace?" Na goge hawayena nace "nasan kasan bashi da kudi yanzu, bashi da kudin biyanka ko da kuwa kotun koli zaka kaishi, dan haka I think you are just wasting your time" yace "really? To tunda bashi da kudin biya na fili na da gadona sai ya shirya zuwa prison for it. Kullum takamarsa kenan, kullum maganar sa itace zai saka a rufe ni, lokacin yana da kudi ni kuma bani dashi. Ki je kiyi masa albishir da cewa the table have turned, yanzu nine zan rufe shi" na bude ido ina kallonsa nace "you don't really mean that, me zakayi da kudin? Me zakayi da filin Sadauki look at this" na fada ina nuna office din nasa "zaka iya siyan hundreds of wannan filin, kafi karfinsa yanzu" yace "Baffa ne ya siya min remember? I was suppose to build us a house a kan filin nan, gidan mu ni da ke da yayan mu remember?" Sai kuma ya mike ta sake juya bayansa yana kallon window. Mun jima a gaka sannan nace "kayi tunanin abinda Baffa zai so, Alhaji Babba yayansa ne uwa daya uba daya ba zai so ya ganku a court dakai dashi ba, ba zai so yaga ka rufe masa dan uwansa akan kudi ba" ya juyo yana kallona yace "kamar yadda ba zai so a cire ki daga makaranta exactly 40 days bayan rasuwar sa ayi miki aure ba, kamar yadda ba zai zo a siyar da abinda ya kwashe rayuwarsa yana building abar iyalinsa da hamma ba" sai yakuma juya wa sannan yace "kamar yadda ba zai so a raba mu ba" na runtse idona ina jin wound fin zuciyata yana dawowa sabo, kewar Baffa na tana lullube ni, mun jima haka sannan yace "tell Alhaji Babba nace yana da options guda biyu, na daya shine ya bar mana gidansa da yake ciki tunda shi kadai ne yanzu abinda ya rage masa, na biyu kuma shine ya tafi prison for the rest of abinda ya rage na rayuwarsa" 


Na mike tsaye, "Sadauki, ubangiji ma yana son rama sharri da alkhairi, kamar yadda kayi wa inna, dan Allah ka bar maganar nan, Allah ma daya halicce mu muna yi masa laifi kullum amma idan muka durkusa muka roke shi gafara sai ya yafe mana" ya juyo yana kallona, his eyes shining, yace "then tell him yana da third option, yazo ya durkusa ya roke ni gafara, ya saka gwuiyoyinsa a kasa ya roke ni in yafe masa kamar yadda na saka guiwowina a kasa na roke shi ya bani aurenki ya hana ni, ya durkusa kamar yadda na durkusa na roke shi kar ya aura miki that monster he calls a son amma duk da haka ya aura miki shi. Yes, I want him to cry and beg kamar yadda nayi in yaso in naki hakura duk da yayi haka sai yaji shima irin yadda naji".


Sadauki yayi t

sauri da yawa ko? Lol




Post a Comment

0 Comments