TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 15

 👭❤ *'YAN UWANA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_



💎Page_____15💎



  Dady yaushe tafarka ne? Gaskiya am so happy  "yanzun bada jimawa ba" dady yafad'a yana d'an Sosa k'eyar kansa, sai a lokacin yake jin ba dad'i bisa abunda yafaru tsakaninsa da mom saboda gaba d'aya sai yaji kunyar yaronsa  yake ji, ganin yanayin da dady ya shiga ya sashi saurin juyar da fuskarsa yana murmushi don dama yariga da yasan ko waye mahaifinsa, Sam shi ba mutumne mai taurin rai ba yana da matuk'ar sanyin hali fiye da tunani, duk da baisan meke ransa ba yafahimci cewa izuwa yanzu har yafara jin ba dad'i akan abun da yafaru, murmushi ya sakeyi wanda har sai da kyawawan hak'oransa suka bayyana had'e da shafa gefen fuskar Billy yana fad'in "sannu ko my lil", murmushin itama ta mayar masa tare da nuna masa gorar jinin da ake k'ara mata dake batun k'arewa, d'ago kansa yai yaga kad'an yarage jinin ya ida shigewa sannan yafita domin ya kirawo likita, bayan kamar minti biyu sai gashi ya dawo tare da wata nurse a bayansa. Sai da tacire mata gorar jinin dake lak'e a hannunta ta tambaye ta shin ko akwai inda keyi mata ciwo yanzu tace a'a sannan ta juyo cikin natsuwa tana gaishe dasu Ummi dake zaune, cikin 'yar siririyar muryarta da tayi daidai da tsarin jikinta ta maido kallonta ga Mahmud tana fad'in


"Za'a iya nemo abinci a bata taci"


"OK nurse mungode" batare da tace masa komai ba tajuya tabar wajen tana murmushi, daidai k'ofar fita taci karo da dr kamal yaturo gambun k'ofar d'akin zai shigowa, sunkuyar da kanta tayi cikin girmamawa tana gaishesa,


"Lpy klw faraaha, ya aiki?"


"Alhmdulillah"


"Dama kece on duty today"


"Yes sir,"


"OK, very good naji dad'in haka don dama ina tunanin acikinku wanda zanba foler patient d'ina a kula mani da ita before indawo saboda d'azun aka kirani zamu tafi wurin seminar na tsawon two days, to tunda kece on duty nasan no trouble zaki kula fiye da yanda zan buk'ata kiyimun" ya k'arasa maganar had'e da rufe k'ofar suna tafiya yana cigaba da yimata bayani har suka iso wajen gadon, hannu ya mik'awa dady suka gaisa yana kallon fuskar Billy da tayi wani irin haske sosai, tafin hannunta ya duba sannan yasa hannu fad'an bud'a cikin k'asan idanuwanta kad'an don ya tabbatar da jinin ya isa yanda suke buk'ata


"Yawwa 'yar gidan dady! Yanzu komai  yayi daidai alhmdulillah, babu ciwon kai da jiri ko?"


"Eh dr. Amma ina jin zafi cikin kaina sosai"


"Eh dole zakiji haka saboda anyi maki d'unki a inda kikaji rauni amma insha Allah shima zai dena" nurse d'in yafara gabatar masu cikin nuna k'warewarta da sanin yakamata ga aikinta...


"Alhaji wannan d'aya daga cikin jajirtaccin ma'aikatanmu ce mai suna faraaha, duk da Bilkisu tasamu sauk'i bazaku samu sallama yauba har sai nan da kwana biyu anyi mata scanning akanta an tabbatar babu wata matsalar data shiga acan ciki, don haka duk abunda ya kamata ayi mata anyi photon shi kad'ai ake jira da kuma dawowar k'arfin jikinta, yanzu zan mik'a folder d'inta a hannun sister faraha zataci gaba da kula da ita saboda kiran gaggawa da nasamu yau d'innan akan zamuje wajen seminar, na yarda da k'warewar faraaha sosai ina fatan bazaku samu damuwa ba, faraaha ina so kibawa patient d'ina kula yanda ya kamata domin su d'in tamkar 'YAN UWANA NE"

 

"Shikenan dr. In sha Allah zanyi" sai da ya sake yiwa Billy checkup da kyau ya tabbatar babu wata matsala sannan yayi sallama da dady ita kuma faraaha ta koma bakin aikinta, hannun bilal dady ya rik'o suka fito shida dr. suna k'ara tattaunawa akan yadda abun yafaru, acan cikin d'akin kuwa wayar ummice tayi k'ara da sauri ta d'auka ganin lambar wacce takira had'e da barin d'akin shikuma Mahmud ya koma inda Billy ke kwance yana tambayarta ko me zataci,


"Bana son komai Yaya" 


"Ai kuwa kinsha k'arya dolene kifad'i abincin da za'a nemo maki kici"


"A'a Yaya ni bazanci ba"


"Zancen kike so lil sis, idan baki fad'a ba zanje inkawo maki duk abunda na samu kuma dole zakicisa in kuma kink'i inyi maki d'ure"


"A'a to zan fad'a, kasiyomun chaculate" zaro ido yayi cike da mamaki, 


"Lallai Billy kin renani da yawa, chaculate d'in ne abinci?" K'efta idanuwanta tafarayi alamar zatayi kuka, goshinsa ya dafe


"Oh! Sorry shikenan ina zuwa bari naje nakawo maki, enough ki kwanta kihuta kinji ko? kai ta d'aga masa had'e da rufe idanuwanta"


A b'angaren mom kuwa tayi abu ya shamata kai, don tsabar kishinta tunda ta isa gida takasa samun natsuwa babu abunda take ayyanawa aranta sai hango dady da Ummi suna buga sabuwar soyayya ga wata irin kula ta musamman da yake bata da 'ya'yanta ita kuma nata 'ya'yan sun wofantar mata dasu hatta bacci idan takwanta kyakkyawan murmushi take hango dady yana yiwa Ummi abu mafi munin data tsana taga yayi mata, da zaran taga haka cikin bacci a firgice take tashi kuma baccin da bazata koma ba kenan, yau kwana d'aya kenan da komawarta gidansu amma dady bai tab'a yunk'urin nemanta koda awayane haka yasa Basmah dole ta koma asibiti wajen jinyar Bilkisu sukuma Batool da Bassam yasa suka kwashe kayansu suka koma part d'in Ummi, duk abunda uwa keyiwa 'ya yiwa 'ya'yanta Ummi nayiwa su Bassam daidai gwargwado duk da ba k'aramin hak'uri takeyi da yanayin tarbiyar tasu, kullum tana kalle da Batool in lokacin sallah yayi bata tashi tayi haka safe ko rana gaba d'aya bata iya gaishesu ga rashin kunya kala-kala da take yimata agidan, dafarko Ummi na hak'uri amma ganin abun yayi worst yasa tazaunar da Batool tayi mata fad'a sosai sannan ta nuna mata matuk'ar bata gyara ba to tabbas sai ta sab'amata, hakan yasa Batool tashiga taitayinta amman kullum cikin kuka take wai Ummi na takura mata, shi kuwa Bassam bawata matsala da yakeba ta inba cutar Bilal da yake yiba, har mamakin kalolin k'etar da yakeyi take koda yake kullum cikin kallon wrestling yake shiyasa, Basmah kuwa zuwan asibitin kad'ai take amma babu wata jinya da takeyi, hatta abinci bazata iya zubawa Billy taci ba saida tagaji tazuba ma kanta ko kuma idan Yaya Mahmud yazo yazuba mata duk da ba wani ci sosai takeyi ba, kullum basmah na kwance akan caution d'in dake d'akin  rik'e da waya tana latsa tana tamnar cingum, sallah ma sama sama take yinta takomawarta kwance tana cigaba da latsar waya tana dariya, saboda yawan dariyar da takeyi yau sai da sister faraaha tayi mata magana akan tadena tana damun marasa lafiya amma tsabar rashin kirki irin na Basmah ta zauna ta zagaeta tass tare da buga mata warning akan karta sake shiga gonarta, tun alokacin taji ta tsani faraaha, duk abunda takeyi babu wanda ke iya da katar da ita inba Yaya Mahmud ba shikad'ai ne ko muryarsa taji zata shiga taitayinta, gashi yau tun safe bai samu lek'owa asibitin ba, shigowar sister faraaha d'akin yakai sau goma duk don tasamu ta gansa amma hakan ya gagara, tun ranar da idanun sister faraaha suka sauka akan fuskar Mahmud taji ya matuk'ar kwanta mata arai, duk abunda yayi na matuk'ar burgeta wannan dalilin ne yasa idan ta kammala duba lpyr patient d'inta sai tadawo d'akin suyita fira da Billy, baza tabar d'akin ba sai lokacin da taga shigowarsa, cike da jin dad'i da fara'a sun gaisa da juna tanajin wani irin shauk'in soyayyarsa na fisgarta sannan zatabar d'akin, maganar gaskiya faraaha tafad'awa son Mahmud son da bazata iya misil tashiba, turo k'ofar tayi bakinta d'auke da sallama tashigo tana kallon Bilkisu cikin fara'ah tace


"Sisto kishirya anjima zamuje wajen scanning kinji ko"


"Eh Aunty faraaha" har ta juya zata fita sai kuma tajuyo


"Yawwa sisto nace har yanzu yayanki bai zoba? Injin dai ko lpy?" Kafin billy ta bata amsa taji Basmah taja wani ubantsaki


"Mtssss..munsan komai anji haushi wlh ace ina macce in kwarewa namiji har ina zuwa neman sa tirr, wai sunan malamar asibiti kenan to kota soyayya?" Kokad'an faraaha bayani mamakin kalaman dake fitowa daga bakin Basmah ba domin tasan ko zata girmeta kad'anne, ga yanda yanayinta ke canzawa idan ta ganeta ta tabbata duk cikakkiyar budurwa irinta zatasan halin da take ciki akansa, don haka itama sai tayi murmushi cikin natsuwa tana kallonta tun daga sama har k'asa sannan ahankali itama taja nata tsukin.


"Mssss..Aikin banza harara cikin duhu, ai shi malam bahaushe yace iya ruwa fidda kai" tana rufe baki sai ga Yaya Mahmud ya iso tare dasu Bilal da bassam da kuma batool ta rik'o kulolin abinci wajen, daga ciki ta shige ta sakar masu hanyar da zasu shigo daga ciki, suna shigowa tajuya zata fita batare da tace masa komai ba Bilal ya rugo ya rik'eta yana fad'in


"Oyoyo aunty faraaha" cikin sakin fuska ba sosai ba itama tace "oyoyo aunty Bilal kana lpy?"


"Lpy klw Ummi tace agaisheki da k'ok'ari" duk'owa tayi daidai tsawonsa taja hancinsa


"Yawwa Ummi kace mata nagode" wani tsakin Basmah tasake ja acan k'ark'ashin mak'oshi yanda Mahmud bazaiji ba tace


"Munafuka" ko kallonta faraaha batayi ba taja hannun Bilal zasu fita, da sauri Mahmud dake k'ok'arin mik'ewa Billy ledar ice cream da chocolate daya siyo mata yana fad'in lil sis ya jiki ya juyo yana kallon faraaha da zata fita


"Malamar asibiti yau ba magana ne?" Batare data juyo ba cikin 'yar siririyar muryarta tace


"Naga ko 'yar k'anwata Basmah data gaisheka bakaji ba balle ka amsa mata shiyasa nima nahutar da kaina" faraaha nasane da ko sallamar da sukayi bata amsa ba balle ta gaishesa tayi hakanne don ta nunawa Basmah kuskurenta kafin ta rufe baki taji tana fad'in


"Eh.eh.Yaya inata magana bakaji ba, ina wuni?" Wani irin mugun kallo ya watsa mata had'e da cewa


"Munafuka yaushe ki kayi mani magana keda inji ko sallama kasa amsawa kikayi kina can kina latsar waya, keda aka kawo jinyar marar lpy kin koma shashanci idan bakiyi hattara ba saina karb'e wayar nabawa mai gadin asibitin nan stupid"


Murmushi faraaha tayi tana kallon Basmah dake kallonta rai ab'ace ta kashe mata ijiya d'aya tare da jan Bilal suka fita, shi kuwa Mahmud bayan faraaha dake tafiya yabi da kallo cike da jin dad'in ganinta"


Batool kuwa kallon Billy tayi tace




Post a Comment

0 Comments