TOP HAUSA NOVELS atOptions = { 'key' : '20e08520dad54dbf6d9e963271

'YAN UWA NA NE PAGE 10

 👭❤ *'YAN UWA NA NE!*❤👭

         💎 _they're my relatives..!_💎



Written by: *BILLY S FARI💎*


Dedicated to: *FATIMA TAMBARY*


Bestowed to: *BILLYN ABDUL AND AUNTY MAIJIDDA MUSA*


_A SHORT AND TRUE LIFE STORY OF THE YEAR 2019_


_Tabbas d'aid'ai kun mutanen k'warai ne kad'ai  zasuga kayi wani kuskure acikin alamurranka suyi k'ok'arin yimaka gyara don cigabanka, hak'ik'a zuciyata na matuk'ar alfahari da samunku acikin rayuwata MOM XOXO, SANAH S MATAZU da kuma KHAIRAT UP nagode sosai bisa gyaran da kuka yimun na sunan littafina daga *'Yan uwa nane* zuwa *'Yan uwa na ne* saboda haka readers zamuci gaba da littafinmu da wancan sunan da muka gyara👆 ubangiji Allah ya tabbatar da alk'alummammu akan dai dai amin_👏🏻



💎Page_____10💎



  Amma kai Mahmud yaron banza ne, zaka k'yalemun yarinya ko saina sameka wajen, gaba d'aya idanunsa sun rufe ko sauraren abunda mom ke cewa batayi sai jibgarta yakeyi, ihun da Ummi taji yayi yawa yasa itama tafito part d'inta aguje tana kawowa mom na kawowa, cikin fushi mom ta finciko sa tare da d'aukesa wani zazzafan mari ita kuma Ummi ta duk'a ta d'auke basmah dake kwance k'asa lagyagya tana kuka.


"Wlh Mahmud ina kusa da in yafeka akan yarana, inyaso kaje ka sake wata uwar an fad'a maka cewa ita jakace da zaka rufeta da duka haka, meye tayi makane inba tsabar tsana da kake yimata ba, an riga ansa maka tsabar 'yan uwanka baka sonsu baka k'aunarsu" afusace ta jiyo ta anshe basmah dake rungume ajikin Ummi tana kuka ta hankad'e Ummi har saida takusa fad'uwa Mahmud yayi saurin tarota.


"Duk abunda yafaru kece sila don kece kika rabamun kan 'ya'ya, kuma wlh sai na tabbatar da nasakaki nadamar aikata haka, kin sawa uba tsanar 'ya'yansa yanaji yana gani za'a illatata gashi zaune amma tsabar k'iyayya ya  kasa magana" ta k'arasa maganar tana kallon dady dake zaune cikin mota yana kallon duk abunda ke faruwa,


"Haba mom wai me kike fad'a hakane, yanzu meye laifin Ummi ko kina tunanin ita zatasa in aikata haka?, to kinyi kuskure kullum bata fatar taga Allah ya had'a kanmu, Amma kidubi shigar da basmah tayi sai kace ba d'iyar musulmi ba, shin hakan da tayi mom tarbiyace, shin me kike tunani idan tafita maza suka kalleta, komaifa na iya faruwa, masha fad'a mata tadena shigar banza batada amfani zata iya haifar mata da matsalar da sai tashafi kowa agidan nan especially ku iyayenmu.."


"Innalillahi wa inna ilaihirrajiun, yanzu Mahmud lalacewar taka har takai haka, da kanka kake kamanta 'yar uwarka da arniya, kake yimata muguwar fata to da yardar Allah baza kaga haka ba, mugun bakinka ya sauka akan munafukar dake son rabaku"


Jin miyagun suruttan da mom keyi sunyi yawa yasa dady fitowa cikin motar a fusace ya buga gambun da k'arfi ya rufe sannan yabar wajen ya nufi part d'insa ransa a b'ace.


"Kin gani ko mom, duk hak'urin dady saida kika fusatasa, kidena d'aurewa basmah abunda takeyi is not good at all"


Hannun Ummi yaja suka nufi part d'inta yana bata hak'uri akan abunda mom tayi mata


"Bakomai Babanah rashin fahimta ne  ya kawo haka in sha Allah with time nasan zata fahimci komai tadena aibatani da yarana"


Saida ya tabbatar Ummi bata tare da damuwar abun ko kad'an sannan ya nufi d'akin mahaifinsu, kamar dai yanda yayita lallashin Ummi haka yayi tayi da dady har sai da yaga shima damuwarsa ta rage sannan yace


"Dady zamu iya tafiya yanzu?"


"No..kabarshi nafasa fitar kaje kafito da k'annenka dake cikin mota"


"Shikenan dady don Allah kak'ara hak'uri da halin mom"


"Tun yaushe kasan nake yin hak'uri da ita tun kafin kazo duniya, bansan meke damun mom d'in kaba, Sam bata son zama lafiya narasa me hajia Aisha tayi mata data d'ora mata karan tsana, babban bak'in cikin dake damuna bai wuce yanda taraba mani kan 'ya'ya ba ta tusawa yarana tsanar 'yan uwansu sannan kuma tana neman b'ata masu tarbiya, tabbas na tafka babbn kuskure arayuwata dana kasa daidaita gidana bazan tab'a yafewa kaina ba matuk'ar namutu da bak'in cikin mamanka"



"A'a dady kadena wannan tunani, Allah shedane akan yanda kake tsaye da sha'anin gidanka,  kana k'ok'ari sosai, kana matuk'ar kamanta adalci agidan nan wanda ba duk namiji ke iyayin hakaba sai jajir tacce, in sha Allah zan tayaka kula da 'yan uwana har sai na tabbatar kayi farinciki da alfaharin samunmu, mom kuma kaci gaba da addu'a zata canza da yaddar Allah"



"I hop so my son" da haka ya nufi part d'in mom maganganun dady nayi masa yawo a k'wak'walwarsa, yana shiga ya iske basmah kwance akan 3sitter idanunta arufe fuskarta ta kumbure saboda kukan da tayi, duk sai yaji ba dad'i cikin zuciyarsa gefenta ya zauna tare da d'ora hannunsa bisa kuncinta, 


"Basmah!" A hankali tabud'e idanuwanta suna had'a ido dashi ta kauda fuskarta, sake juyo da fuskar tata yayi sannan ya d'ago da ita daga kwancen da take


"Am sorry basmah don't mean to hurt you at all, ked'ince kin fiye kunnen k'ashi ni bana son irin wud'annan shigar da kikeyi, zata tab'a maki mutunci na har abada but Yaya is sorry kinji? Ku 'YAN UWA NA NE ina matuk'ar sonku kawai d'abi'unku da halayenku sune bana so da zaran kun dena zaku fahimci yanda yayanmu ke matuk'ar ji daku"


A hankali takoma ta kwanta ba tare data furta masa kalma ko d'aya ba saboda yanda take jin haushinsa, murmushi yayi sannan ya nufi kitchen inda ya jiyo motsin mom tana girki yana shiga yayi hugging d'inta


"Mom me kike dafawa ne?" Shiru tayi bata cemasa komai alamun fushi takeyi dashi


"Haba mom! Ur son d'inki ke maganafa kiyi hak'uri nagane ban kyautaba dana doki k'anwata, nayi maki alk'awari daga yau bazan sake dukan taba duk abunda kike tunani bahaka bane ina matuk'ar son 'yan uwana fiye da tunaninki kuma in sha Allah zan basu kulawa ta har abada, kicire komai aranki babu mai rabani da 'yan uwana" jin kalamansa yasa ta juyowa tana kallonsa fuskarta ba yabo ba fallasa tace


"Zanyi farinciki sosai idan kalamanka suka tabbata, but nasan haka abune mai wahala matuk'ar kana tare da Aisha, tariga ta shanye.." Hannunsa yayi saurin d'orawa abakinta


"Karki fad'i haka mom, ke mahaifiya tace, banida kamarki kuma banida wanda ya kaiki aduniya, zan tabbatar maki da cewa ni yaron kine, abunda nakeso dake mom shine kiyi hak'uri ki kwantar da hankalinki"


"Shikenan ammafa ka kula wlh idan ka sab'a alkawari sai na baka mamaki don wlh kowa sai yaji ba dad'i agidannan"


"A'a mom banda dady, ya kamata ace izuwa yanzu kin kula da farincikin sa, dady na matuk'ar sonki shiyasa yake jurewa matsalolin dake faruwa don Allah ki janye munannar fahimtar da kike yi akansa"


"Dallah rufemun baki kar kasa raina ya sake b'aci"


Gudun kar tasake birkice masa yasashi fitowa yana fad'in


"Mom mai duniya Allah dai yaja zamaninki, kiyi rai kiyi k'arko mamanah"


Girgiza kai tayi had'e da sakin murmushi tsabar jin dad'in kalamansa


Batool ce ta shigo falon ranta a b'ace tana faman turar baki kamar wacce akayiwa duka, mayafin hannunta tafara jifa dashi kafin can tacire takalmin k'afarta ta watsar dasu a tsakar d'aki, inda basmah take kwance ta nufa a afusace had'e da kai mata wani irin mugun duka a cinya tana fad'in


"Muguwa kawai, wlh Allah ya isana, kurum kinyi mana asarar fita don tsabar iskanci, kin jamana asarar abunda dady zai siya mana"


Cikin zafin nama da rad'ad'in dukan da tayi mata ta tashi ta kaimata naushi abaki nan fa suka kacame da fad'a, kadan cewar Basmah na cikin b'acin rai yasa Allah ya azata akan Batool tayita dukanta, dak'yar Mahmud ya fincikota akanta yana dariya



"Enough Basmah yi hak'uri kinrama dukanki shikenan har lokacin bai dena dariyar da yakeyi ba saboda yasan dama inda zata fanshe dukan da yayi mata take nema sai gashi cikin sauk'i ta samu, fizge hannunta tayi tana faman nishi tace


"Wlh kwanan nan sai kunci duka a hannuna saboda na lura gidan nan ba'a notice d'in dukan mutum sai dai yaji saukar na jaki ajikinsa don haka sai kunsha wahala a wurina keda wancan d'an iskan yaron ta nuna Bassam da ya shigo yanzu yana tuk'uburi, wata irin muguwar harara ya watsa mata shima tare da nuna ta da d'an yatsansa


"Kece 'yar iska bani ba tunda kika ja aka fasa fita don mugunta, shikenan yanzu kinja narasa ball d'in da nakeso dady ya siyamun"


Afusace tayo kukan kura akansa Mahmud ya sake saurin rik'ota


"Kai Basmah yanzu da Bassam d'in zakiyi fad'a, sorry nasan wannan rigimar duka laifina ne amma kiyi hak'uri kinji ko?"


"But yaya Mahmud..."


"Shhhh..ko meye ai nace kiyi hak'uri ko?"


Haka dai suka dinga yimasa rigima inya lallashi wannan ya koma ga waccan har mom ta k'arasa girkinta, cikin jin dad'in yanda taganesa cikin 'yan uwansa tace



"Yau kam nayarda duk tasirin asiri sai yakarye, dubeku gwanin ban sha'awa amma don tsabar hasada ake nema araba mani kanku, dole intashi tsaye nima saboda bazan juri haka ba"  Mahmud ne yace 


"Mommmm..."


"Rufamun baki samna kazo kazuba abinci kaci"


"Mom kizubo mana mana muci tare"


"Bazaka iya cin abinci da Yaran nan ba don nasan halinka"



"Zan iya mana tunda su 'YAN UWA NA NE"


 A tare mom tazubo masa abinci da k'annensa sukaci sannan yabar part d'in, d'akinsa ya nufa ya watso ruwa yayi sallah ya haye gadonsa don ba kad'an yakejin bacci na d'ibarsa ba, acan cikin bacci ya hango lil sis d'insa tana gudu cikin wani makeken daji tana kiran sunansa, mom d'insa kuma na gefe tana faman dariya, a firgice ya tashi baccin duk ransa ab'ace yana fad'in


" _Innalillahi wa inna ilaihirrajiun, a uzubillahi minashhaid'anirrajim ya fad'a har sau uku ya tofa a hannunsa na hagu sannan ya k'ara da a'uzu bikalimatillahi tammaat, min ghadabihi, wa ik'aa bihi, wa sharri ibadihi, wamin hamazatishhayad'ini, wa anyahduruun_"


Ya matuk'ar tsoratata yanayin da yaga lil sis d'insa aciki don haka ya sauko kan gadon yasa doguwar rigarsa jalabiya sannan ya nufi part d'in Ummi zuciyarsa cike da son ganin halin da 'yar uwarsa take ciki...




Post a Comment

0 Comments